Sashe 11
Dingishin Kwado Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Washegari tun safe muka d'au hanya, azahar muna Zaria salla kawai muka yi sai abinci da muka ci, ya kai mu tasha muka shiga mota cikin sa'a gurbin mutum biyu ya rage dan haka muka biya wajen ni da yara. Nan da nan muka kama hanyar Abuja ni da su Faruk, muka bar Amra da Babanta a Zaria sai washegari za su koma Katsina. Ni kuma dama na ce masa zamu dan yi kwanaki, daɗin da na ji, jiya mun samu hutun mid semester.
Sai da muka sauka a garin Abuja sannan na kira wayar Ya Faruku na ci sa'a ya daga k'iran ya sha mamaki da na ce masa ga ni a Abuja, addreshin gidan Baba Babba zai ba ni. Ya shanye mamakinsa, ya turo mini adreshin, mai taxi ɗin da na tare na nuna masa ya ce ya san wajen tunda fitattaciyar anguwace ta masu hali.
Danƙareren gida Ya Asad ya saka iyayensa a ciki, har sai da na saki baki ina kallon gida.
Ba kowa a gidan daga Baba Babba sai Momi sai Abida, sai ma'aikata.
Kawai suka ganmu kwatsam kamar daga sama, tunda da na isa bakin gate din gidan Yaya Farouk na k'ira ya yiwa maigadin magana ya bude mana bayan ya kinkimi kayana.
Ya ce mu shigo zai dawo ya shigo mini da sauran kayan.
Momi ce a falo tare da Baba Babba.
Dukkansu bakinsu ya kasa rufuwa na murna da mamaki.
Momi ta miƙe tana faɗin" Lale marhaban Maigado ke ce tafe?"
Ina murmushin jin daɗi na ce" Ni ce Momi."
Su Farha suka nufe ta ta tarbesu cikin farinciki. Ni kuwa gaban Baba Babba na ƙarisa na rusuna ina gaishe shi.
"Barka da zuwa, lale da Bilkisu yayar Abida!
Nan da nan idanuwana suka kawo ruwa domin na tuna shekarun da suka shud'e a lokacin da muke hade, muke rayuwa cikin jin dadi da kaunar juna.
Kaina na kasa da rawar murya na ce " Sannu Baba mun same ku lafiya?"
Ya amsa da lafiya k'alau yana tambayata sauran yaran da sauran ƴan uwana duk na amsa mishi da muna nan lafiya.
'To Alhamdulillah sannu mai gado. Allah ya yiwa rayuwarki albarka.'
Na amsa da "Amin"
K'wallah na taruwa a kwarmin idanuwana farinciki da alhini sun kewaye ni kamar na fashe da kuka haka nake ji.
'Sai kika ji yar uwar taki ta haihu ko?'
Baba Babba ya katse mini tunani.
"Ban ji ba Baba. Sai shekaranjiya ne Ya Faruku ya kira ni ya faɗa mini."
Ya jinjina kai kafin ya ce" Da ya ke sai jiya aka sallamo ta daga asibiti wataƙila ba ta samu natsuwar kiran ki ba ne maigado "
Ina kallon Baba Babba a cikin zuciyata sai ayyana har yau Abida ce raunin Baba.
"Maigado har yanzu baku samu labarin Sulaiman ba?
"E, Baba bamu samu labarinsa ba har yanzu."
Ya jinjina kai kafin ya ce" Ubangiji Allah ya bayyana shi cikin aminci"
Na amsa da Amin kasa kasa sai falon ya yi shuru, tunda Momi ta ja yaran zuwa ciki, ta gefen ido nake k'arewa Baba Babba kallo ya warware sai dai bai mayar da jikinsa ba haka nan tsufa sosai a tare da shi alamun har lokacin zuciyarsa bata nutsu sosai ba.
Mamakin Baba Babba nake yi a kullum shin wanne dalilin ne ya sanya ya zubawa Abida ido ta zauna a gida har hakan ya taimaka wajen b'acewar Yaya Sulaiman?
Duk da dai nasan itace rauninsa, amma duk da haka ina mamakin yadda ya iya zuba ido Abida take zaune a gabansa, idan a lokacin ba shi da lafiya ai daga baya ya ji sauƙi ya kamata ya mayar da Abida d'akin mijinta tunda bai sake ta ba. Bai kuma yi laifin da za'a kashe masa aure ba.
"Maigado tashi ki shiga wajen y'aruwar ta ki, ku gaisa ki yi salla ki ci abinci ki huta."
[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: Muryarsa ta katse mini tunanina, na amsa masa da to na tashi na shiga dama kayan da na zo da su tuni Momi ta shigar mini da su.
A bedroom ɗin farko na iske Momi da yara ta zuba musu abinci suna ta mata hira tana dariya.
Nan na fara shiga na duk'a har k'asa na sake gaishe ta.
"Lafiya lau Maigado, ya mutanen gidan ina me gidanki da amaryar Alhaji?"
Na amsa mata da duk suna lafiya, mun barta a Zaria tare da Babanta.
Na daɗe a wajenta muna hira itama sai da ta tambaye ni labarin Ya Sulaiman na ce mata ba wani labari cikin damuwa ta ce "Oh Allah ka bayyana wannan yaron alfarmar Annabi."
Na amsa mata da Amin.
"Za ki fara yin salla ne ko sai kin ƙarisa wajen y'aruwar ta ki?
Na ce bari na je can wajenta sai na yi, ita ta nuna mini dakin da Abida take ciki na shiga ciki na iske ta zaune a gefen gado tana shan tea ga Baby a cikin showel a gefenta yadda ta kalle ni na gane ba zan wani samu karbuwa daga gareta ba.
Ba ta yi mini mgana ba tun bayan da na yi sallama ta amsa mayafin jikina na yaye ina faɗin" Sannu "Abida."
Kai tsaye da muryata cikin dakewa ta ce" Yauwa Bilki"
Na kalle ta itama ta kalle ni, hawaye suka kawo mini amma ban bari sun zubo ba, itama ina ganin rauni a cikin idanuwanta sai dai ta yi saurin kauda kanta daga barin kallona.
Ganin haka yasa na ƙarisa wajen jariri na ɗauko shi zuwa jikina a gefen gadon na zauna, ina mai kallon yaron sai da na yi kabbara a cikin zuciyata yaron nan kamar ni ce na haife shi tsabar kammanina da ya debo, ni kuwa dama kaf ɗakinmu na fi kama da Ya Sulaiman hawayen da nake tarewa suka zubo har saman kumatun jaririn na saka hannu na share masa sai barci yake yi.
"Kai ma mu ka biyo?"
Na faɗa murya babu amo kamar shi da Farha a bayyane ba tantama, wannan jinin Ya Sulaiman ne! Da sauri na rungume jaririn ina mai fashewa da kuka har yana fidda sauti. Abida na gefe tana kallona amma ba ta yi mini magana ba sai da na sha kuka na k'oshi na share hawayena amma ina ƙankame da jaririn a hannuna zaman sama da mintina ashirin ba mu tanka ma juna ba sai ita Abidan ce da ta gaji da kanta ta kalle ni tana faɗin.
"Ina yaran ko ke kaɗai kika zo?"
Ina shirin bata amsa sai ga su Farha Momi ta kawo su Faruk ya nufi Abida yana ganinta, ta rike shi a jikinta tana faɗin" Yayanmu akwai ƙauna ashe baka manta da ni ba? Ta faɗa tana shafa kumatunsa shi kuma yana dariya.
Jaririn da yake hannuna ta nuna masa tana faɗin" Je ka kaga k'aninka? Kana son shi?
Da sauri ya ce" E Ammi ina son shi."
Don kaf yarana Ammi suke kiran Abida, wajena ya nufo yana faɗin na ba shi jaririn na ce ba zan ba shi ba Momi ta ce ya zauna sai na rike masa haka ko aka yi jikin shi har rawa yake yi.
"Mahmah da shi za mu tafi?
Ina shafa kan shi na ce" A a Faruk a wajen Ammi za mu bar shi."
Abida kuma na ta kallon Farha itama tana ta kallonta kamar ta gane ta, kamar ba ta gane ta ba, sai ta miƙa mata hannu tana faɗin"Farha zo mu gaisa."
Ta mik'a mata hannu Farha ta tafi zuwa gare ta, ta riƙe ta ta daɗe tana kallonta kafin ta shafa kumatunta tana faɗin" Farhan Bilki ta girma!
✍️
[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: *Bojuwa herbs*
*Oder your kayan mata for women of class*
*Our products are healthy and original*.
*Tested and trusted*.
*Sanyi flusher dinmu zai raba ki da dukkan nau'in infection, ya kuma sabunta Ki*.
*Ki zo ki saka order din ciccibin garari ko kazar sababi ki gode mini later domin saiwowin da nake amfani da su na yi imanin ba kowa zata iya zuba kudi ta saro masu daraja irinsu ba*.
*Duk wadda ta ciccibi sai tasan ta ci abu gangariya haka ma kazar sababi*
*Just DM for your order @08033773332*.
Na kalle ta ina mai murmusawa, duk yadda soyayyar ɗa da uwa take Abida ta yi jarumtar bar mini abin da ta haifa shi yasa nake yi mata uzziri don ta nuna mini zahirin soyayyar da ta shafe dukkan iyashegenta a zuciyata. Nan duniya na shaida Abida na cikin jerin masoyana na haƙika. Duk da tana kawaici amma yanayin yadda take kallon Farha zaka san akwai soyayya irin ta uwa a idanuwan Abida.
Ta sake tambayar Farha da 'Ina yayarku?'
Farha ta ce "Mun barsu a Zaria tare da Dady".
Ganin har biyar ta gota ya sa na mike na kwantar da jaririn a saman gado, ganin na mike yasa Farha ta saki hannun Abida ta nufo ni tana faɗin" Mahma ina za ki?"
Ina kallonta na ce" Ba inda zan je Farha salla zan yi "
Ta sake ni jin ba tafiya zan yi ba.
"Je ki zauna wajen Ammmi ku k
[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: Bilki ta fara dariya a zuciyanta ta ce yaushe rabon duniya da ayyaraye?
A fili kuma sai ta ce' Ai ni na gama, yanzu lokacin amarya ne ta yi ta zazzaga masa yara.".
Sai da muka sauka a garin Abuja sannan na kira wayar Ya Faruku na ci sa'a ya daga k'iran ya sha mamaki da na ce masa ga ni a Abuja, addreshin gidan Baba Babba zai ba ni. Ya shanye mamakinsa, ya turo mini adreshin, mai taxi ɗin da na tare na nuna masa ya ce ya san wajen tunda fitattaciyar anguwace ta masu hali.
Danƙareren gida Ya Asad ya saka iyayensa a ciki, har sai da na saki baki ina kallon gida.
Ba kowa a gidan daga Baba Babba sai Momi sai Abida, sai ma'aikata.
Kawai suka ganmu kwatsam kamar daga sama, tunda da na isa bakin gate din gidan Yaya Farouk na k'ira ya yiwa maigadin magana ya bude mana bayan ya kinkimi kayana.
Ya ce mu shigo zai dawo ya shigo mini da sauran kayan.
Momi ce a falo tare da Baba Babba.
Dukkansu bakinsu ya kasa rufuwa na murna da mamaki.
Momi ta miƙe tana faɗin" Lale marhaban Maigado ke ce tafe?"
Ina murmushin jin daɗi na ce" Ni ce Momi."
Su Farha suka nufe ta ta tarbesu cikin farinciki. Ni kuwa gaban Baba Babba na ƙarisa na rusuna ina gaishe shi.
"Barka da zuwa, lale da Bilkisu yayar Abida!
Nan da nan idanuwana suka kawo ruwa domin na tuna shekarun da suka shud'e a lokacin da muke hade, muke rayuwa cikin jin dadi da kaunar juna.
Kaina na kasa da rawar murya na ce " Sannu Baba mun same ku lafiya?"
Ya amsa da lafiya k'alau yana tambayata sauran yaran da sauran ƴan uwana duk na amsa mishi da muna nan lafiya.
'To Alhamdulillah sannu mai gado. Allah ya yiwa rayuwarki albarka.'
Na amsa da "Amin"
K'wallah na taruwa a kwarmin idanuwana farinciki da alhini sun kewaye ni kamar na fashe da kuka haka nake ji.
'Sai kika ji yar uwar taki ta haihu ko?'
Baba Babba ya katse mini tunani.
"Ban ji ba Baba. Sai shekaranjiya ne Ya Faruku ya kira ni ya faɗa mini."
Ya jinjina kai kafin ya ce" Da ya ke sai jiya aka sallamo ta daga asibiti wataƙila ba ta samu natsuwar kiran ki ba ne maigado "
Ina kallon Baba Babba a cikin zuciyata sai ayyana har yau Abida ce raunin Baba.
"Maigado har yanzu baku samu labarin Sulaiman ba?
"E, Baba bamu samu labarinsa ba har yanzu."
Ya jinjina kai kafin ya ce" Ubangiji Allah ya bayyana shi cikin aminci"
Na amsa da Amin kasa kasa sai falon ya yi shuru, tunda Momi ta ja yaran zuwa ciki, ta gefen ido nake k'arewa Baba Babba kallo ya warware sai dai bai mayar da jikinsa ba haka nan tsufa sosai a tare da shi alamun har lokacin zuciyarsa bata nutsu sosai ba.
Mamakin Baba Babba nake yi a kullum shin wanne dalilin ne ya sanya ya zubawa Abida ido ta zauna a gida har hakan ya taimaka wajen b'acewar Yaya Sulaiman?
Duk da dai nasan itace rauninsa, amma duk da haka ina mamakin yadda ya iya zuba ido Abida take zaune a gabansa, idan a lokacin ba shi da lafiya ai daga baya ya ji sauƙi ya kamata ya mayar da Abida d'akin mijinta tunda bai sake ta ba. Bai kuma yi laifin da za'a kashe masa aure ba.
"Maigado tashi ki shiga wajen y'aruwar ta ki, ku gaisa ki yi salla ki ci abinci ki huta."
[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: Muryarsa ta katse mini tunanina, na amsa masa da to na tashi na shiga dama kayan da na zo da su tuni Momi ta shigar mini da su.
A bedroom ɗin farko na iske Momi da yara ta zuba musu abinci suna ta mata hira tana dariya.
Nan na fara shiga na duk'a har k'asa na sake gaishe ta.
"Lafiya lau Maigado, ya mutanen gidan ina me gidanki da amaryar Alhaji?"
Na amsa mata da duk suna lafiya, mun barta a Zaria tare da Babanta.
Na daɗe a wajenta muna hira itama sai da ta tambaye ni labarin Ya Sulaiman na ce mata ba wani labari cikin damuwa ta ce "Oh Allah ka bayyana wannan yaron alfarmar Annabi."
Na amsa mata da Amin.
"Za ki fara yin salla ne ko sai kin ƙarisa wajen y'aruwar ta ki?
Na ce bari na je can wajenta sai na yi, ita ta nuna mini dakin da Abida take ciki na shiga ciki na iske ta zaune a gefen gado tana shan tea ga Baby a cikin showel a gefenta yadda ta kalle ni na gane ba zan wani samu karbuwa daga gareta ba.
Ba ta yi mini mgana ba tun bayan da na yi sallama ta amsa mayafin jikina na yaye ina faɗin" Sannu "Abida."
Kai tsaye da muryata cikin dakewa ta ce" Yauwa Bilki"
Na kalle ta itama ta kalle ni, hawaye suka kawo mini amma ban bari sun zubo ba, itama ina ganin rauni a cikin idanuwanta sai dai ta yi saurin kauda kanta daga barin kallona.
Ganin haka yasa na ƙarisa wajen jariri na ɗauko shi zuwa jikina a gefen gadon na zauna, ina mai kallon yaron sai da na yi kabbara a cikin zuciyata yaron nan kamar ni ce na haife shi tsabar kammanina da ya debo, ni kuwa dama kaf ɗakinmu na fi kama da Ya Sulaiman hawayen da nake tarewa suka zubo har saman kumatun jaririn na saka hannu na share masa sai barci yake yi.
"Kai ma mu ka biyo?"
Na faɗa murya babu amo kamar shi da Farha a bayyane ba tantama, wannan jinin Ya Sulaiman ne! Da sauri na rungume jaririn ina mai fashewa da kuka har yana fidda sauti. Abida na gefe tana kallona amma ba ta yi mini magana ba sai da na sha kuka na k'oshi na share hawayena amma ina ƙankame da jaririn a hannuna zaman sama da mintina ashirin ba mu tanka ma juna ba sai ita Abidan ce da ta gaji da kanta ta kalle ni tana faɗin.
"Ina yaran ko ke kaɗai kika zo?"
Ina shirin bata amsa sai ga su Farha Momi ta kawo su Faruk ya nufi Abida yana ganinta, ta rike shi a jikinta tana faɗin" Yayanmu akwai ƙauna ashe baka manta da ni ba? Ta faɗa tana shafa kumatunsa shi kuma yana dariya.
Jaririn da yake hannuna ta nuna masa tana faɗin" Je ka kaga k'aninka? Kana son shi?
Da sauri ya ce" E Ammi ina son shi."
Don kaf yarana Ammi suke kiran Abida, wajena ya nufo yana faɗin na ba shi jaririn na ce ba zan ba shi ba Momi ta ce ya zauna sai na rike masa haka ko aka yi jikin shi har rawa yake yi.
"Mahmah da shi za mu tafi?
Ina shafa kan shi na ce" A a Faruk a wajen Ammi za mu bar shi."
Abida kuma na ta kallon Farha itama tana ta kallonta kamar ta gane ta, kamar ba ta gane ta ba, sai ta miƙa mata hannu tana faɗin"Farha zo mu gaisa."
Ta mik'a mata hannu Farha ta tafi zuwa gare ta, ta riƙe ta ta daɗe tana kallonta kafin ta shafa kumatunta tana faɗin" Farhan Bilki ta girma!
✍️
[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: *Bojuwa herbs*
*Oder your kayan mata for women of class*
*Our products are healthy and original*.
*Tested and trusted*.
*Sanyi flusher dinmu zai raba ki da dukkan nau'in infection, ya kuma sabunta Ki*.
*Ki zo ki saka order din ciccibin garari ko kazar sababi ki gode mini later domin saiwowin da nake amfani da su na yi imanin ba kowa zata iya zuba kudi ta saro masu daraja irinsu ba*.
*Duk wadda ta ciccibi sai tasan ta ci abu gangariya haka ma kazar sababi*
*Just DM for your order @08033773332*.
Na kalle ta ina mai murmusawa, duk yadda soyayyar ɗa da uwa take Abida ta yi jarumtar bar mini abin da ta haifa shi yasa nake yi mata uzziri don ta nuna mini zahirin soyayyar da ta shafe dukkan iyashegenta a zuciyata. Nan duniya na shaida Abida na cikin jerin masoyana na haƙika. Duk da tana kawaici amma yanayin yadda take kallon Farha zaka san akwai soyayya irin ta uwa a idanuwan Abida.
Ta sake tambayar Farha da 'Ina yayarku?'
Farha ta ce "Mun barsu a Zaria tare da Dady".
Ganin har biyar ta gota ya sa na mike na kwantar da jaririn a saman gado, ganin na mike yasa Farha ta saki hannun Abida ta nufo ni tana faɗin" Mahma ina za ki?"
Ina kallonta na ce" Ba inda zan je Farha salla zan yi "
Ta sake ni jin ba tafiya zan yi ba.
"Je ki zauna wajen Ammmi ku k
[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: Bilki ta fara dariya a zuciyanta ta ce yaushe rabon duniya da ayyaraye?
A fili kuma sai ta ce' Ai ni na gama, yanzu lokacin amarya ne ta yi ta zazzaga masa yara.".