← Book details Dingishin Kwado Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 14

Sashe 3

Dingishin Kwado Part 2 Complete Hausa Novel · about 4 min read

Tunda na ga Abida ta hau nazarin karatu ya sanya na mike na shiga kicin dan na dora mana abin da zamu ci domin ba zata sake yi mini magana na har sai ta kammala al'amuran gabanta.
Washagari ta juya Katsina ta zarce kaitsaye.
A lokacin goyon Yaya Faruok Sahal ya samu budi sosai. Dan har Umra ya biya mana ni da shi tare da yaranmu gabadaya. Haka ya biyawa iyayensa duk da sun je. Bayan shekara da zuwanmu kuma ya biyawa su Baban Zaria da matarsa takwarar Amrah.
Gata da tattali ba wacce bai mini ba, komai zai ajiye mini tamkar ba da kudi yake siya ba. A haka na yaye Faruk tuni kuma Amrah ta shiga makaranta.
Hankalina ya koma kan rubuce rubuce akan abubuwan da suke Gina ciki. Misali zan dauka Apple na yi rubutu akansa da irin alfanunsa a jikin Dan Adam da sinadarin da yake bayarwa da nauin mutanen da suka fi bukatarsa a jikinsu. Wani lokacin Kuma sai na yi bayani akan mangwaro. Duk Kuma a kafar sadarwa ta Facebook tunda itace a lokacin kawai. Kafin na ankara sai na sake tara mabiya. Ina kuma sake fadada business dina na snacks.
.
Gabadaya na zama babbar mace da ilimi da gayu suka ratsa tunda miji ya tsaya mini sana'a kuma ta yi k'arfi. Iyayenmu kuma masu hali don ko da suka aurar da mu hidima suke yi mana kan hidima basa saka ran mu yi musu. Sai dai muna yi don neman albarka. Na zama big madam mazaunai sun fito sosai Dan haka na bude ta kasa na bada shape mai daukar hankalin masu kallona. Fata tana samun mayuka da sabulan da suka dace da ita kwarai da gaske. Haka nan kamshina na mussaman ne domin kuwa turare designer nake amfani da shi. Wadannan dalilai suka sanya na sake makalewa a zuciyar Sahal yana al'amarin kasancewata matarsa, shi da kansa yasan nafi dacewa da manyan masu kudi da suka zarta shi komai da koami dan kuwa shi din gabadaya nai bani shekaru uku cikakke ba ta bakin Abida. Sai dai har wannan lokacin da muke shekaru biyar da aure ba zan ce ina cikin rashin nutsuwa a dalilin aurensa ba. Kawai matsalar daya ce. Tabbas bashi da sha'awa mai yawa, wannan ne kawai tasgado domin ina kwaruwa sosai. Amma ba yadda na iya dan haka na saka rashin samun biyan bukata shine jarabawar aurena. Kuma abin mamaki zaman namu na nisa al'amarin na sake yawa. Dan yanzu kam sai mu kwashe kwanakin wata bai nema ba. Sai dai idan ya ga mutsumutsuna ya yi yawa zai yi romancing d'ina har sai na samu na fitar abin da ta takura ni. Na fara tunanin ko lafiyar makarfafarsa ce ta yi kadan. Na fara nazarin abubuwan cima da zasu taimaka masa wajen motsa masa sha'awarsa. Kullum cikin nazari tare da gabatar masa duk wani nauin abinci ko kayan marmari da suke taimakawa amma babu wani sauyi. Na fara magana da likitoci ana rubuta masa magani amma kuma da ya sha daya biyu to ya bar mini su kenan. A wanccan lokacin da shekararuna basu da wani yawa sai nake jin tsoron irin na gagajiya wanda ake zubawa miji a lemu ko a shayi don ina jin tsoron kada ya gane ya ce asiri nake yi masa.
Ga shi al'amarin mai matukar nauyin ka tattauna da wani ne. Kan dole na hakura nake ta kokarin na danne abin tunda haka kaddara ta zaba mini.

✏️
*Contact me 08032773332 what'sapp only*
*For all your kayan mata gangariya*
*Bridal package*
*Maijego package*
*Uwargida package*
*Bazawara package*
*Kazar sababi ta amare da uwayen gida da masu jego*
*Ciccibin garari*
*Tsumin saiwowi*
*Hakkkn daka emergency*
*Gumbar ridi*
*Gumbar saiwowi*
*Surayya ce da kanta take kawo muku su daga Chad da Sudan*.

A haka rayuwa ta cigaba da tafiya har Yaya Faruk ya isa shiga makaranta aka saka shi wacce Amrah take yi.
Har zuwa lokacin kuma Abida bata yi aure ba. Watanni uku da kammala resident dinta a jamiar kasa ta Lagos (Uni Lag).
Burinta kuma ta wuce da karatunta har sai ta zama kwararriyar likitan mata.
Ta fada mini ta riga ta gama cike ciken tafiya kasar Uk dan ta zama gynecologist, sai komai ya kankama kafin ta bari gida su sani dan kada ma a hana ta tafiya, domin matukar ta samu gurbin karatun to ba za'a hanata ba tabbas.
Bayan haka kuma ta nemi gurbin karatun a jamiar Ahamadu Bello, ma'ana raba kafa ta yi, tsakanin guda Nigeria da Kasar England.
A matukar sanyaye na yi mata murna da fatan alheri, tare da addu'ar Ubangiji ya zaba mata mafi alheri.
Tana shirin shiga shekaru ashirin da bakwai amma bata maganar aure sai dai neman ilimi tamkar alhuda alhuda.
Autar gidanmu gabadaya ta kammala sakandire a bana. Bata damuwa da yadda aka aurar da kannemu ita tana zaune.
Chapter 3 · 0% Book details