← Book details Dangina Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 14

Sashe 3

Dangina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Shiru tayi taji duniyar da take ciki ba nata ba ne domin furucin Ammi ya doketa dukar da kanta tayi tana rushe da kuka Ammi kuwa dakinta ta nufa ta dinga kuka kaman ranta zai fita Nanna ce ta shigo dakin jikinta a sanyaye domin taji duj hirar da tawanzu a tsakaninsu kusa da Ammi ta shigo ta fara rarrashinta kafun ammi ta ɗago kanta ta ce

Dama haka alhakin iyaye yake Nanna nasani ko istigifari bazanyiba Alhakin iyayen mune yake bibiyarmu tundaga kan abunda ya faru da Hafsat nafara gane haka gashi yanzu yara sunzo kuna tambayata ina yan uwanmu da wani baki zan musu bayani taya zan musu bayanin abunda muka aikata nida mahaifinsu ,shin wani hali zasu shiga idan sukaji asalinsu wayyo Allah nanna wlh da rayuwarmu tanada remote dana sarrafa na.maida komai bai faruba

Hawayen dake zuba a fuskar nanna ta share ta ce

Hakane hjy kisani kowa da kalar kaddararsa ki sani wannan itace kaddararki keda alhaji marigayi ,kuyi neman gafarar Allah zai yafe muku sannan tunda kinga yara sunason sani su suwaye ayi hakuri a waiwayi gida domin gudun gori

Haka ta dinga rarrashin Ammi kafun ta fito ta nufi dakin Hafsat ,kqman yadda tayi tinani tana zaune tana rike da hoton julabib tanata kuka karban hoton tayi ta ce

Haba Hafsat yanzu akan wannan magana shine zaki famewa kanki wani ciwon da warke a zuciyqrki

Rungume nanna tayi ta ce

Meyasa Ammi ta dage akan saian auri Abdulmallik wlh banasonsa nafiso in zauna banyi aureba ta hakane zan nunawa julabib soyayya ,wlh idan nai aure kaman naci amanarsa ce

Ba haka bane Hafsat ki sani shi kanshi julabib Allah ne ya bamushi amma ya dauke abunsa kiyi addua Allah yasa son da kikewa julabib yadawo kan Abdulmallik shikenan zaki samu saukin rayuwa

Shin Nanna bakisan abunda ya shiga tsakanina da Abdulmallik bane

Na sani nasan komai bana bukatar karin bayani kidauka kaman wannan abun bai faruba ,ki dauka kaman baayi komaiba,ki daukeshi mijin ƙawarki kawai ki aureshi kije kicigaba da ibadar aurenki ,ki manta da julabib ki manta da wani an halicceshi waishi julabib ki manta kunyi zaman mata da miji

Haba Nanna kina mahaifiyar julabib kike cewa in manta dashi

Kwarai ki manta dashi duk da cewa nina haifeshi amma nace ki mqnta dashi ,akullum idan na kalli julabib nakan tina mahaifinsa amma gashi Allah a daukesa ,nashiga kunci sosai amma da karfin addua Allah yasamun dangana don haka kema ki miƙa alamuranki gurin ubangiji

Hawayenta ta share tayi shiru tana tina rayuwarta da julabib

Flash back
Kwance take akan kirjinsa hannunsa daya akan cikinta ya kalleta ya ce

Baby yanzu zuwa dan lokaci zaki haifa mana baby ko ,wow waya hangoni da baby a hannuna

Juyowa tayi ta shafa gemunsa ta ce

Wlh my bibi koni ina burin Allah ya kaini wannan lokaci kafun Allah ya dau raina

Haba mesa kike fadar haka ai bakisan waye gawar fariba

Hakane bansan waye na farko ba amm da zaa bani zabi zan bada raina ka rayu kaida baby na nasan zaka kula da Ammina da Nannanmu ga baby na amma ni katafi ka barni bakin cikin missing ɗinka ma ya isheni nima na bika

Ah yanzu don na mutu kina nufin kema zaki bini ,gaskiya bakimun adalciba abunda nakeso dake ko bayan raina ki saki ranki kiyi aure kicigaba da walwala ,kiyiwa mijinki biyya kaman yadda kikemun koma fiye da abunda kikemun

Hawayene suka wanke mata fuska ta ce

Pls my bibi mubar magannan nan don wlh bana tinanin koda halinda zan shiga matikar na rasaka

Rungumeta yayi yana share mat hawaye ,haka kawai yakeji bazai rayuwa me tsawo tare sa Hafsat ba ...

Dafata Nanna tayi tai firfigit Ta dawo hayyacinta ta fashe da kuka hakan ya tabbatarwa da Nanna halin tinanin nata ta shiga ,haka taita rarrashinta har bacci me nauyi ya dauketa Nanna ta fita ta jawo mata kofar .

Haka ta ta shi jiki babu kwari gaba data.ta rasa ya zatayi ta rushe maganar aurenta DA abdulmalik haka Ammi taita rarrashinta akan ta amince da maganar auren ,amma gaba daya batajin zata iyq auren Abdulmallik ,yau ma kaman kullum yasha wanka yazo gidan ya tura baba me gadi ya kirata babu jimawa ya dawo akan tana zuwa ,ammice ta nufi dqkinta ta shaida mata ana sallama da ita haka ta fito da hijab ta nufi hanyar waje Ammi ce ta kira sunanta ta juyo ta ce

Waike Hafsat haka zakina zuwa babu ruwan sha

Shiru tayi kafun tai murmushi ta nufi kitchen ,glass cup me kyau ta dauko ta bule bold ta dumbuli barkwano ta zuba a cup din kafun ta nufi friedge tana zuwa ta zuba exotic a cikin glass cup din ta fita girgiza kai ammi tai ta ce

Hafsat bazakiyi hankali ba

Tana zuwa yaata baza baki yana gyara zaman hularsa baijira ta masa tayiba ya karba ya ce

Godiyq nqke da alama dai na fara samun shiga tunda har tarbata musamman nake samu

bata kulashi ba don tasan neman magana yake ,kallonta yayi ya ce

Anwuni lafiya kawarmu

Bata kulashiba yayi murmushi yana kai kofin bakinsa da sauri yq furzar jin wani zafin barkwano ya ratsa bakinsa da makokoronsa kallonta yayi yqga kaman batasan yanayi ba ya ce

Hafsat mena miki haka ,ashe tsanat da kikemun harta kai haka

Kwarqi tafi hakama kuma ta ninka shi sau dubu sabain ,wlh Abdulmallik idan ka aurenitamkar ka auri tashin hankali ne gidanka da rashin zaman lafiya ,kai bari in fada maka zan iya kasheka kuma in kashe kaina duk akan wannan lamari

Tabbas Hafsat da na dauka abun naki kaman wasane amma tunda maganar ksa ta shigo ciki ai lamari ya baci don haka kiyi hakuri idan kika aureni zakiyi farin ciki marar misaltuwa ,zan maye miki gurbin julabib kai harma na fishi

Wani tsawa ta daka masa ta ce

Karka sake fadan wannan kalma baa halicci wani namiji da zanso sama da julabib ba sannan baa halicci wanda zausoni sama dashiba ,na yarda an haifeni ne da son julabib bq koya nayiba ,kasani babu wata fuska da natsansna gani sama da taka babu wani gunjin sauti dana tsana sama da muryarka babu wata mummunan halitta da banason gani sama da kai don haka ka tattara kabar mana gidan mu tunda gidan bana hadin cinya bane ko

Murmushi yayi ko daya maganganunta basu shigesaba shdai abunda ya sani zata gama bakine daga baya ta dawo soyayyarsa don haka zai iya kokarinsa yaga ya kafa tutarsa a cikin zuciyarta ganin yanda ranta ya baci yasa ya shiga motarsa mai gadi ya bude masa ya bar gidan .

Cikin kuka ta koma cikin gida domin ta tina da abun kaunarta julabib .

Tunda ya koma gida gaba daya jikinsa a mace ita kanta zuwaira ta lura da hakan shiyasa ta ke tambayarsa

Waini dear meya faru ne meke damunka

Kallonta yayi ya ce gaskuya bazan boye miki.ba na janye raga maganar auren Hafsat

What ka janye kuma .......

Share pls
*DANGINA*
*[AKA RABANI DASU]*

STORY &WRITEN

BY

ADAMA UMAR
SECRET PEN

07081940768

LOVE AND ROMANTIC STORY

DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JINKAI

4️⃣

PAGE THREE

Eh Tabbas na janye domin na gaji da fuskantar walakancin dq takemun nibama walakanciba ki sani duk abunda tamun zan shanye amma bazan juri tana kiran sunan wancan banzan a gaba na ba kuma koda munyi aure saita kira sunansa don ta bakanta mun rai nikuma wbunda bazan jura ba kenqn

Haba honey damq na fada maka dole zaka fuskanci matsalloli kala kala karfa ka manta da babban laifin da kayiwa Hafsat kaine sanadiyar rabatada danta sannan kaine sanadiyar rabata da mijinta haba ko wannan laifin ta kalleka dashi ai bazata yafema cikin saukiba nidan abunda nakeso dakai shine dole ka zamabmai juriya a soyayya ,dole ka jure koma meye sanna kai kokari ka mallaketa ai duk wani qbu da takeyi saboda taga yanzu baa karkashib ikonka take ba amma kana aurenta kagama da wannqn babin

Shiru yayi yana nazarin maganarta tabbas a zancenta akwai kamshin gaskiya amma taya zan fara tunkarar Hafsat da maganar aure haka yayi ta sakawa da warwarewa saukar muryarta a kunnensa ne yasa ya juyo yana sauraron abunda take fada

Nasan tinanin da kake taya zata yadda a fara maganar aurenku ko ,to ba ita zamu tinkara ba Ammi itace makaminmu da ita zamuyi amfani wajen cin nasarar wannan.yakin

Haka taita nuna masa matakan nasara a aurensu har shimq yq yarda suj warware akan zataje ta samu Ammi idan ba matslaa manya su shiga lamarin .

Kaman yadda tayi alkawari hakan ta kasance zqune suke ita da ammi tana shaida mata sakon da Abdulmallik ya turota akan a bashi dama ya turo wakilansa su nema masa auren Hafsat ,Ammi tayi farincikin jin hakqn babu musu ta amince da suturo zuwa anjima zataje ta samu liman suyi magana ,sannan zuwaira ta karisa dakin Hafsat ,kwance ta sameta tanata sakawa da warwara domin taji duk abunda su ammi suka fada kenan yanzu idan tayi sanya haka zaa aura mata wanda bataso anya bazata shiga duniya ba kuwa kowama ya huta to ya ammi zatayi idan ta shiga duniya.wata zuciyar ta tambayeta saikuma wata ta bata amsa da yazatayi kuma ai itama haka tayiwa iyayenta tana cikin wqnan zancen ne zuwaira ta shigo dakin bata kalleta ba balleta mata sannu da zuwa kusa da ita ta zauna ta ce

Haba haba.Hafsat bazaki rungumi kaddara ba ,zaki zauna kiyita zama cikin kunci haba sai kace akanki akw fara meyasa kike hakane

Dallah rufemun baki munafukq ai nasani duk wannan alamari ke kike daɗa taazzarashi wato zaa kawo kudin aurena ko to sai ayi auren mugani wlh ko gawata baa ganiba balle akai cikin gidansa

Subhanallah anya kina cikin hayyacinki kuwa kike irin wannan kalamai ,anya kinsan meyake futowa daga bakinki ,aure fa akace zaa miki ba wani abu ba kiamince da Abdulmallik zakiji dadin zama dashi wlh bashida matsala ko kadan matsalarsa daya kuma ke kanki kinsan ya daina to meya rage dan Allah ina rokonki da ki amince ki yarda

Bangajrta tayi ta fita a dakin ta nufi bangaren Nanna domin ita ta gaji da jin abunda take fada mata
Chapter 3 · 0% Book details