← Book details Dacewa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 6 OF 24

Sashe 6

Dacewa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kallo 'daya neesah taiwa gurin ta 'dauke kai tareda kallon 'daya daga cikin 'yan matan shagon tayi  mata bayanin abinda za'ayi mata.

Kusan atare atare suka miqe bayan an kammalawa ko waccensu abinda yakawosu.

Tsaye suke gaban tangamemen mirror 'din gurin..

Siririn gyalen data yafo batareda 'dankwaliba neesah ke gyarawa,
Ita kuwa 'dayar powder ta qara shafawa tana gyara zaman hot red jambakin dake lips 'dinta.

Idanuwansu ne suka shiga cikin na juna ta cikin mirror gaban ko waccensu saidaya buga da qarfi.

Neesah ta fara 'dauke fararen idanuwanta cikin 'dan tamke fuska zuciyarta na tsananta nauyi.

Ita kuwa budurwar kafe neesah tayi da ido tunani kala kala na shigota.

Atare suka fito neesah ta nufi mota tashiga tana qara 'daure fuska
Ahmed kuwa harzai tada motar ya hangota ta nufo motarsa
Saurin kallon neesah yayi yaga fuskarta a tamke tana duba wayarta.

Fita motar yayi ya qarasa batareda yabari taqarasoba ya sakar mata fuska sosai.

Lafiyayyen murmushi tasaki tana kallonsa tace,

     Ahmed kaima tunda yayanka ya jonamin hawan jini yayi aure ka ajeni ko?

Dariya yayi yana cewa,
      Ayeesha me zai sakaki hawan jini tunda na tabbatarda captain bazai gujekiba kinyi masa mugun kamu da sanyin halinki alhalin kuma ba sanyin halin ne dakeba.

Dariyar data qara fitar da zallar wayonta da budewar idonta tace,

     Ahmed ina jinjina maka ako yaushe da kai kadai ke iya ganoni akoda yaushe,
Amma to ai ba laifina bane sbd captain Idan bada sanyin halina da biyayyar danake masa ba aida tuni nabi sahun sauran matan dayaqi jininsu.,
Dan haka kadakaga laifina soyayyar yayanka ce,
Kuma akansa zanmayi fiyeda hakan.

Jutawa tayi ta nufi motarta tana wani shu'umin murmushi tace,

Saimun sake haduwa brother Ahmed..

Shima murmushin yasaki mai ma'a noni ya koma mota sukabar wajen.

Ayeesha kabir 'yace 'daya tilo a gurin alh kabir zaki tsohon Senator anan Lagos,

Ayeesah tun tana yarinyarta ta iya kirsa da 6oye qiyayyarta ga maqiyinta,
Ta iya kwantar da kai da biyayya akan Abu muddin zata samesa sai dai Sam bata yafiya ko mantuwa akan Abu hakama Sam,

Ayeesha batada tarbiya ko kadan sbd gata da rashin kwa6a data taso cikinsa,
Kyakkyawace sosai hakama akwai wayewa da ilimi amma na boko kawai bana addini.

Tayi karatunta ne a qasar us inda acan ta hadu da Jamaal da farko Sam bata gabansa data lura da hakan saita ringa canza halayenta agabansa sbd ta lura shi mutum ne mai sanyi saita ringa nuna juriya,hakuri da biyayya harta samu tausayinta da soyayyarta ta shiga ransa batareda ya shedar da ainihin halintaba.

Ba wasu shekaru yabata ba saidai suzo mate amma yanda take kwantar da kai ta nuna masa girmansa sosai shiyafi burgesa da ita sbd shimafa akwai son a girmamasa.

Ahmed da ayeesha sun San juna sosai sbd aminiyarta husna da  Ahmed 'din yake tsananin so.

Jamaal kawai ayeesha ke boyewa halayenta sbd batada mutumci ko kadan uban kowa bata tsoro shiyasa Ahmed yasan halinta tsaf kuma yayi iya qoqarin fahimtar da Jamaal amma yakasa sbd Sam baimaga fuska ba.

Amma tabbas shi yasan ayeesha guba ce dazata iya tarwatsa gidansu gabaki 'daya bama kamar neesah dake basa tausayi da takaici gurin son girmanta da girman kanta tareda daukar kanta ayeesha ta lalata mata rayuwa.

*******
Kusan watanta uku kenan a Lagos ba laifi rayuwar garin ta'danyi mata saidaima miskilanci daya qaru dady ya nemar mata admission university 'din nan tafara karatunta ka sabuwar motar daya siya mata duk da haka wani lokacin tareda Ahmed suke zuwa dama can shima yake karatu kuma yanxu shine abokin yawonta kusan kullum suna gurin yawon shopping dan ita qa'idarta ne ko Biro or bathroom slippers zata siya to saidai a babban mall bare sauran kayan amfani shiyasa kusan kullum suna hanya.

Ga ummi data 'dau wani sabon so da tattali ta'daura mata
Hakama tana tsananin so da qaunar khadija itama saidai son neesah dabam yake aranta sbd 'dan uwanta yayanta wato abban neesah.

Abin duniya yataru yayiwa khadija yawa dan yanxu ko lectures bata ganewa sbd ba kullum take zuwaba ga wata uwar rama data sanyota gaba duk ta rasa sukuni kullum saitayi kuka kafin tayi bacci sbd kullum rayuwar neesah qara haskaka takeeyi,

Ummi tayi lallashinta akan tafada mata damuwarta saidai tace ba komai inna Rabi ma tayi lallashinta amma duk abanxa baqin ciki da hassadar neesah na Neman sadata da kushewarta.

Yau ansamu ta'dan saki jikinta ta fito palo suna zaune suna fira,
Ummi da inna Rabi sai neesah dake kwance kanta a cinyar ummi tana chatting da amirah akan binciken data sakata akan tahir da Habib.

Kallon neesah dake kwance jikin ummi tayi ta danne hawayenta tana gaida ummi.

Khadija Yaya ciwon kan naki?
Kodai wai asibiti zamuje ne ni naga sai rama kike koda wata matsalar ne uhumm?

Zama tayi tana maida hawayenta tadan saki fuska tace,

Bakomai ummi Kaine kuma yadaina insha Allah.

To Allah ya qara sauwaqewa.

Inna Rabi ta kalla tace,
    Inna abani abinci naci ka'dan.

Yawwa khadija kokefa bara na hadamiki yanxu kuwa.

Danne duk wata damuwarta tayi ta 'dan kalli neesah tace,

       Anty neesah ina wuni?

Qyaleta tayi taci gaba da chatting 'dinta saida takuma cewa,

     Anty neesah sannu da hutawa.

Daqyar ta bude baki tace,

     Uhummm.

Neesah Sam ta tsani mutum mai 6oye 6oye sbd ita kai tsaye take abinta bata 6oyo ko tauye kai sbd tanason rayuwar cikakken 'yanci saidai Sam bata shiga ko kallon duk wani Abu dabai dametaba.,

Tun bayanxu ba ta fahimci khadija Nada abinda take 6oyewa amma takasa fa'da Ai mata magani saidai taita duhun rai wanda ita agurinta ba dalili bane ka 6oye damuwa shiyasa Sam ita khadija batai mataba.

Wayar ummi ce tayi qara tana dubawa taga Jamaal ne tasaki murmushin farin ciki tace,

        Jamaal kan....

Ummi kadakice komai dan nasan  abinda zakice.,

To bani dalilinka na 'daga tafiyar?

Ummina pls kadaki tambayeni dalilin coz kinsan bazai wuce work,work, work ba.

Ok then yanxu fadamin when are you coming son?

Ummi ina nan tafe ranar Wednesday Insha Allah sbd wani dalilin da sainazo zan fada miki.

Cikin farin ciki tace,
   Ok son Allah yakawoka lpia.

Ameen ummi na.

Koda tagama wayar ta kalli fuskar neesah taganta a tamke ba walwala saita saki 'dan guntun murmushi kawai.

Khadija kuwa wani farin cikine ya dirar mata Wanda rabonta dashi tun zuwan neesah gidan.

Kar6ar abincinta tayi tafaraci cikin farin ciki Wanda yabawa ummi da inna Rabi mamaki matuqa.

Mamuh.

_don't forget to vote#follow#and comments viawattpad@mamuhgee._

_Don't forget to follow,vote and comments@mamuhgee#*via wattpad.._

Mamuh💋

_*DACEWA*_
_(when east meets west)_

_By_
_Mamuh geee_

*Viawattpad@mamuhgee*

*18-19*
Tunda neesah taji maganar dawowar Jamaal ta rage zama sosai a gidan
Kullum tana school sai yamma sosai take dawowa data dawo kuma zatai shigewarta 'daki.

Ummi na lure ta qyaleta gudun rigimarta,
Ahmed ne kawai yake samun ganin fara'arta harsuyi fira.

Khadija kuwa sosai take al'amuranta cikin tsananin farin ciki.
Kowa yayi mamakin sabon yanayin nata amma sukai shiru itama batareda sunce komaiba.

Ranar Wednesday tun guraren 8:00 ta tafi school sbd Sam takasa samun sukuni cikin gidan,.

Duk wata hidimar tarbonsa inna Rabi da khadija ne suka yita.

A da inna Rabi ke gyara 6angarensa idan zai dawo amma wannan karon khadija ce taje ta gyare komai ta kunna aircon tareda kunna fridge 'din dake palonsa bayan taje ta 'dauko ruwan Eva katon 'daya da drinks ta jera aciki.
Rufo qofar tayi takoma 'dakinta tayi wanka tareda zaunawa gaban mirror har zatai kwalliya saikuma ta fasa gudun kada agano manufarta,

Riga da skirt na maroon atampa tasaka tareda 'daura 'dan siririn gyale akanta tadawo Palo tazauna tana charting da wayanta cikin walwala sbd tuni Ahmed yatafi airport 'daukosa.

A nutse yake tafiya hannunsa 'daya na cikin aljihun black fanfuego trousers 'dinsa sai 'dayan hannun yana waya da ayeesha dayake dakatarwa akan kadatazo 'daukarsa Ahmed yazo daukarsa.

Kyakkyawar fatarsa dake sheqin Hutu da kyau Ahmed ya tsaya kallo harya iso gabansa daidai gama wayarsa da ayeesha ya kalli Ahmed 'din yana saka 'dayan hannunsa cikin pocket 'din wandonsa.

Murmushi Ahmed yasaki yana cewa,
Gskia Yaya zanzo na nemi Hutu kwanan nan natafi gurinka sbd nima nasamu lafiyar fata kodan nima na riqa jawa husna aji.

Murmushi kawai yasaki batareda yace masa komai akan abinda yafadaba yace,

Idan ka gama shirmenka kasaka kayan a mota ka kaini gida coz I desperately wanah see my mummy.

Shigewa yayi motan shikuma Ahmed yayi saurin
Saka kayan mota suka nufi gida.

Tun a mota ya kashe wayarsa sbd yasan Sam yanxu ba Hutu ayeesha ta dinga kiransa kenan..

Suna isa gida Ahmed ya nufi part 'dinsa kai masa kayansa shikuma ya nufi palonsu ummi kai tsaye.

Cikeda tsananin farin ciki ummi ta tarbesa zama yayi kusada ita yana riqo hannunta yace,

Ummi da fatan na sameku lpia?

Lpia klau Jamaal,
Ya hanya?

Kasalallen murmushi yasaki yana cewa,
Alhamdulillah.

A ladafce khadija ta taso har gabansa cikin sanyin murya tace,

Ya Jamaal barka da dawowa.

Batareda ya kalletaba ya qaqalo murmushi yace,

Yawwa khadija,
Ya studies naki?

Tana 'dan qaqalo fara'a itama tace,

Alhadulillah.

Da haka ta juya tabar palon jiki a mace sbd rashin ganin fuska a gunsa Wanda dama hakan suke tun farkon fari.

Inna Rabi kam kasa zama tayi sai hidimar kawo masa abubuwan sha take cikin farin ciki dan har cikin ranta Allah yadora mata qaunar Jamaal tun yarintarsa.

Murmushi yasaki har fararen haqoransa suka bayyana cikin kulawa sosai yace,

Innah,
Inna kibarshi hakanan bana buqatar ci ko shan komai yanxu Am ok,
Saidai zuwa anjima may b.

To Jamaal amma mutum yayo tafiya yace ko ruwa bazaisha ba.

Inna kadaki damu anjima zanci kuma ke zaki bani da kanki dan nasan yanxu ummi ta canzani batada time 'dina.

Cikin so da qaunarsa ummi tace,

Jamaal bani kadai na ajekaba kowama har inna 'din sbd kanada mata yanzu and all kulawanka da 'dawainiyanka yana kanta yanzu.

'Dauke wuta yayi fuskarsa na 'dan canzawa sbd gaba 'daya ya manta da zancen auren da neesah.

Anyways baida matsala da ita tunda bason auren takeba afterall bayajin zai iya zama da duk macen da bazata iya respecting 'dinsaba tabasa girman daya kamacesa amatsayinsa na mijintaba koba komai baida time 'din mata irinta.

Miqewa yayi daidai shigowar Ahmed bai kallesaba yana ficewa yace,
Chapter 6 · 0% Book details