← Book details Dacewa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 24

Sashe 3

Dacewa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Jiri taji ya fara 'dibarta kanta ya fara jujjuyawa ta sulale qasa daidai wani mai napep yakawo yayi saurin tsayawa
Itakuwa tattaro qarfi tayi ta fa'da cikin napep 'din tana fada masa inda zai kaita cikin qarfin hali.

Sosai su Abba suka razana da zancen janyewar dasu tahir sukai,
daddyn Lagos ( _dadyn Jamaal_ ) kuwa ransa ne yayi mugun 6aci ya kalli su kawun yace amma dai wannan harkar qaranta sosai kuka nuna dan banga dalilin fasa aureba kuma tsabar wulaqanci saida yarage awa biyu 'daurin aure zaku fasa ance muku baza aganta bane ko kuwa duk cikin son zubar mana da girma.....

Alh hakuri dai shine abinda zan kuma baku sbd nima nasan hakan tozarcine gareku yi muku hakan amma wlh uwar yaron ta kafe akan aure dai baza'ayiba.

Abban neesah kuwa tsabar takaici da baqin ciki ko magana ya kasa yimusu sai kallon takaici dayake aika musu dadyn Lagos ne kawai keta faman fada.

Mota ce qirar landcruiser 2018 baqa ta parker qofar gate din gidan nesa kadan sbd motacin dasuka fara cika layin na 'yan 'daurin aure.

Saurayine kyakkyawa ajin qarshe 'dan kimanin shekaru ashirin da Biyar zuwa da shida.
Ba baqi bane hakama ba fari bane saidai hutu dajin dadi tareda kwanciyar hankali yasa fatarsa haske tareda wani irin sheqi.

Sanye yake cikin wata dakakkiyar shadda sky blue light mai laushin gaske,

Hakama hular Kansa blue ce sai diamond Rolex watch dake daure a hannunsa da black half cover shoes na kamfanin _gorge phelex arman_ _Jamaal muh'd abdallah._

Babban amininsa yuseef daya 'daukosa daga airport yafito cikin motar shima cikin nasa adon na 'daurin auren.

Cikin gidan suka nufa kai tsaye,

Ahmad dake harabar gidan tareda wasu baqi yayi saurin qarasowa gurinsa yana cewa,

Yaya Jamaal sannu da hanya.

'Dan sakin fiska yayi ya amsa tareda wucewa kai tsaye Palin Abba dai dai fitowarsu gabaki 'daya daga palon.

Tsayawa yayi yagaidasu abban suka amsa kowanne rai ajagule kafin su qara wata maganar saigasu ummi da mamy sun iso gurin.
Ahmed ma matsowa yayi ya tsaya ganin kamar dukkanin iyayen nasu cikin wata damuwar bayan ta 6atan neesah.

Habib ne ya kuma bude baki yace to mu zamu tafi Allah ya hada kowa da rabonsa hakama Allah ya shirya muku 'yarku dan gskia abin da mamaki saidai kawai muce Allah yasa ta gane idanma wani ne ke hure mata kunn.......

Wani mahaukacin mari yaji yasauka a fuskarsa saida yayi baya kamar zai kife ya 'dago da sauri idanuwansa jajir ya kalli Wanda ya kwada masa Marin.

Cikin takaici yake kallon Jamaal amma sai yaga yayi masa wani irin kwarjini ya juya afusace zai fita ba zaro yaji saukar wani Marin yana 'dagowa yaganta a tsaye tana tsoyayar hawaye,

Ba Wanda ya lura da zuwanta saidatai marin ummi tayi wurinta da sauri ta cikin ga farin ciki ga baqin ciki.

A hasale ya kallesu 'daya bayan 'daya yace,
A haka kuke son a auri yar tashar 'yarku?
Yarinyar data gudu ta kwana gidan namiji a daren 'daurin aurenta
Hakama ta 'daga hannu ta mari babba agabanku amma baku iya 'daukar mataki ba,

To tabbas wannan marin wlh saikinyi dana sanin yinsa arayuwarki dan saiya zamar miki masifa.

Kaima kuma kasan baka mari banza ba,
Sannan bazansan kunji haushin fasawarmu ba saikun samar mata miji a yau kun 'daura mata aure koda yake wane me juyewar qwaqwalwar ne zai auri ragin wani...

Hannu Jamaal yakuma 'dagawa zai kai masa wani marin abban neesah ya riqe hannunsa cikin takaici da baqin cikin ga zuciyarsa datai masa nauyi ya dafe tareda girgizawa Jamaal kai.

Mudai bamayi akaiwa wani idan kuma gskia ne ga 'dankunan mai zafin kai saiku 'daura masa mudai mun fasa.
Ficewa sukai daga gidan hannunsa nakan kumatunsa har lokacin.

Kukan baqin ciki mamy da neesah suka saki lokaci 'daya kafin neesah ta sulale ta zube qasa a sume.

Ummi ce takamota jikinta a tsorace kafin tasa ahmad ya daukar mata ita suka kaita sama 'dakin mamy.

Jamaal kuwa fitowa yayi shida yuseef suka bar gidan yana mamakin yanda Sam wani lokacin mata basada tunanin komai girmansu
Yanxu ita wannan taje tahau wata soyayya da Wanda Sam familynsa basada tunani bare mutumci,,,
Unbelievable "" yafada ahankali yana yamutsa fiska.

Sosai gidan ya qara kaurewa da hayaniya ga 'yan 'daurin aure tuni suka cika layin da anguwar.

Tsit su Abban sukai a palon cikin jimami da kunyar yanda zasu sanar da jama'ar dasuka taru cewar anfasa 'daurin auren.

Jiniyar isowar gwamna da tawagarsa tacika anguwar suka kalli juna Abba cikin sanyin murya yace,

Alh kaje kasanar da jama'ar an fasa 'daurin auren kada mubarsu suita jira.

Mamy najin haka ta fashe da wani kukan Anty mamee ta dafata itama cikin tsananin damuwa.

Jiki a sanyaye dadyn Lagos yafito cikin jama'ar yana gaggaisawa da mutane
Manyan senators da members, ga gwamnoni da manyan alqalai ga maroqa tako ina waqa suke,
ji yayi sam bazai iyaba ya juyo zai dawo cikin gidan saiga Jamaal yadawo yi musu bankwana zai koma tunda aure yafasu,

Kwarjininsa da cikar zatinsa da dakakkiyar shigarsa tasa
Maroqa na ganinsa suka zageyesa sunai masa kirarin ango sbd tunanin shine ango.

Kallon da baifi sakan gomaba da tunani yasa dadyn sakin ajiyar zuciya ya nufi cikin gidan.

Kallon abban yayi yace,
Justice insha Allah nasamar mana mafita kafito yanxu afara gabatarda 'daurin aure lokaci na tafiya.

Abban baice komaiba ya miqe suka fita sbd yasan dadyn komai yaza6arwa neesah daidai ne.

_DAURIN AURE_
2:00pm

Abbah shiyayi wallicin ango yayinda babban amininsa former justice rufai yayi waliyi Amarya neesah aka fara gabatarda 'daurin aure.

Babban sarkin maroqa yafara yadawa a loudspeaker
Yau ranar asabar sha biyu ga Satan biyu an 'daura auren _jamalu muh'd abdallah_ da _aneesah justice sanda_ akan sadaki naira dubu 'dari.

Yuseef ne yaji abinda maroqin me fada ya juyo yana watsawa Jamaal kallon mmamaki yana cewa,

Amma wlh gayen nan ka rainamin hankali,
Dama aurenka ne za'a 'daura ka rude da cewar na neesah ne.

Wayar dayake tun 'dazu da ayeesha ya kashe yana kallon yuseef cikin lumshe fararen oily eyes 'dinsa yace,

Uhummm me kake fadane?

Harararsa yayi yace,

Kaga rainin wayon ya isa hakanan kuma......

Moroqane suka yanyamesu kafin yace wani Abu.

Kirari suke bakin rai yuseef ya fara yi musu 6arin kudi cikin farinn ciki batareda ya nuna damuwar komaiba.

Kallon mamaki Jamaal yatsayayi kafin shima dai yafidda kudi sosai yabasu batareda yasan meke faruwa ba.

Mamuh💋

_*DACEWA*_
_(when east meets west)_

_By_
_Mamuh geee_

*10-11*
Maroqa cikin jin dadi suka cigaba da watso kirarinsu sbd ganin yanda Jamaal da Yusuf ke musu 6arin nerori.

Wayarsa ce tai ringing
Da kamar bazai duba ba saiya 'dago yaduba.,

Siririn tsaki yaja kafin ya 'daga wayar tareda barin gurin ya nufi cikin gidan.

Part din dayake amatsayin nasa duk lokacin dayazo gidan can ya nufa.

Komai fes sai qamshin rose air freshener da sanyin ac dake tashi ga dukkan alama Ahmed qaninsa anan ya sauka.

Zama yayi a sofa tareda crossing legs yana amsa wayar cikin rashin fahimtar me ayeeshar ke fada ahankali yace,

Calm down pls ayeesha sbd I don't understand a single word acikin magananki.

Wani sabon baqin ciki da takaici suka taso mata amma gudun 6ata ransa saita danne tace,

Captain I just got a massage from a friend cewan kayi aure,I mean wai an 'daura aurenka yau.

Lumshe idanuwa yayi cikin sanyin murya yace,

Eshaah,,,,

Jiki a sanyaye ga wani bala'i dake cinta amma ta danne itama cikin sanyin muryar tace,

Uhumm captain,

Eshaah me kikeson nafada miki yanxu?

Inaso kafadamin idan gskia ne ko sa6anin hakan.

Ayeesha you know me,koda auren nayi banga wani dalilin qin fada mikiba sbd I have every right nayi abinda nakeso so pls kadaki kuma jin irin silly talks 'dinnan kifadamin,okay?

Batareda hankalinta ya kwantaba tace,

Insha Allah captain.

Yaso janta da fira amma jin duk tayi sanyi sai kawai ya kashe wayar daidai shigowar Yusuf yana sakar masa dariyar qeta yace,

Ango zakasha maifa.

Batareda ya 'dago ya kallesaba yace,

So u are the good friend da ayeesha ke fada kenan?

Zama Yusuf yayi yana shafo sumar kansa bayan ya cire hularsa cikin dariya yace,

Eh to kusan hakan ne duk da dai bansan me kake fadaba amma dai ni ina bayan ayeesha sbd bazan iya da rigimammiyar amaryarka ba dan ko kai da kake angon bansan ya zaku qareba.

Still bai 'dagoba yana daddana wayarsa yace,

Yusuf can you pls stop talking bcoz I'm reading sumtin hia and ure disturbing.

Daria Yusuf 'din yasaki ahankali sbd sosai ya hango yanayin zaman dasu Jamaal 'din zasuyi,

A yanda yasan Jamaal miskili mai sanyin hali da ko oho da abu
Ga neesah mai masifar jin aji da ganin ita babba yarinyace uwa uba ga son girma Wanda hakan yasa Sam ko gaisawa basayi da Jamaal sbd tana masa kallon 'dan rainin hnkali da girman kai yayi masa yawa tunda ko kallo bata ishesaba dukda tana matsayin wadda ta girmesa.,

Sosai ya hango rikicin zaman gashi alamu sun nuna Jamaal baimasan da aurenba.

Wayarsa ce tayi qara yaduba yaga ayeesa ce.
Kallon Jamaal yayi yaga har lokacin hnkalinsa nakan wayarsa.

Hello ayeeshan captain.

Daga can 6angarenta Murya a sanyaye tace,

Yaya Yusuf pls ka taimaki zuciyata daga halinda take shirin fadawa kafadamin gskiar zance pls Yaya Yusuf.

Tausayinta Yakama Yusuf sosai sbd shi shaidane akan irin tsananin son da ayeeshar ke yiwa Jamaal duk da shima yanayimata soyayya mai sanyi.

Ajiyar zuciya ya sauke ahankali yace,

Ayeesha ki kwantar da hankalinki dan auren Jamaal na tabbatarda bazai hanasa aurenki ba sbd yana sonki,
So ki kwantarda hankalinki sbd shima auren a bazata yazo masa.

Kuka tasaki mai cin rai tanajin wani qaton baqin cikin Jamaal 'din matar daya aura koma wacece.

Kuka take sosai Yusuf na rarrashinta a wayar qarshema kashe wayar tayi tareda wurgi da ita tana fasheewa da wani sabon kukan baqin ciki.

Kallon seconds biyar Jamaal yayiwa Yusuf cikin nazarin kalamansa sbd kallo na karantar yanayin mutum 'dabi'arsa ce.

Alamar haqiqanin gskia ya karanto a fuskar Yusuf ya aje wayarsa tareda fuskantar Yusuf idanuwansa na qoqarin 6oye 6acin ransa ya bude baki zaiyi magana Ahmed gashigo palon da sallama yakalli yayansa cikin jinjina alamarin shima yace,

Ya Jamaal su dady na kiranka.
Chapter 3 · 0% Book details