← Book details Bana Sonshi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 25

Sashe 22

Bana Sonshi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Abdul ya had'a komai domin zuwa Abuja kuma yasa uche a tafiyar Wanda besan an gane shi ya kashe Aayan ba

Suna zuwa suka bawa wurin wuta domin duk suna ciki suna meeting inda zasu ceto Samira

Daga sama aka bude musu wuta gaba d'ayansu sun mutu

Sanda suka Gama Abdul ya halbi uche caka-caka sukayi me sanan Suka d'auki gawan Suka koma dashi Suka ce Yan ta'adar ne Suka kashe shi inda Suka tarar da Samira ta mutu a inda aka ajiyeta Wanda duk plan din Abdul ne shi yasa a halbeta Amma abin sai ya nuna Kamar ita ta halbi kanta

_______

B'angaren su ummi ko

Maman nur
[2/20, 8:36 PM] Maman Noorul Hudah: 👄👄👄👄👄👄
*BANA SONSHI*
💋💋💋💋💋💋
_By maman noorul_
_Hudah__

*👄💡NUR WRITERS ASSOCIATION💡💋*

*💡N W A💡*

*Lightning and bringing smile to your world is our perority*

*NUR WRITERS* ~it's a beautiful~ ~world~

🅿9⃣7⃣-9⃣8⃣

Ummi ta gama yanke shawaran aure za ayiwa Rahma kila in ta auri amir tunda sun tab'a soyyaya ya dawo da ita inda take a da domin in ba haka akayi ba bazata tab'a samun natsuwa ba ta gaji da ganinta haka "

Zaune suke a falo Amina sai Yi Mata magana take Amma da Kai take amsawa da Amina ta isheta da surutu sai tayi tsaki ta kwanta a kujera ta jawo pillow tasa a kunni

Ummine ta sauko cikin Shirin fita anguwa ta kalleta tace"gidan umman ku zani ko Zaki je?"

Girgiza Mata Kai tayi ummi tace"toh ki tabbatar kin ci abinci

Ta amsa da Kai ummi dama ta Saba tafiyarta tayi

Bayan sun gaisa da umma ta kawo Mata ruwa da abinci Hamza ya gaisheta

Tace"Ina Yan biyu?"

Umma tace"sun tafi makaranta "

Ummi tace"magana ne ko in ce shawaran na zo muyi Alan Rahma ni a ganina me zai hana ayi Mata aure?ta auri amir tunda ta soshi a baya nasan hakan zai taimaka"

Umma tace"babu komai hajiya duk inda kika gan ya dace shekaran jiya ko mummy shi ta kirani a waya tana niman auren Rahma nace mata su bani lokaci "

Ummi tace"yauwa alhamdullilah sai kawai a aura me ita zata ji dadi nasan bazata wulakanta ba da naso Abdul ne ya aureta amma Kuma sai na duba tsakaninta da yusura za a iya samun matsala"

Umma tace"gaskiya da wanan"

Ummi ne ta amshi number mummy ta kirata tace"sun amince ranan murna a gun mummy Kamar ta zuba ruwa ta Sha "Kiran amir tayi a waya tace"ya dawo gida akwai goodnews"

Amir dake lecturing yayi saurin barin ajin ya koma gida

Ummi na komawa gida ta Kira Abdul tame bayani shima yayi na'am da shawara nan fa aka fara shiri auren

Cikin kankanin lokaci aka Saida Rana

Yau ummi take son sanar da Rahma amma tana d'an shakka

Amina tace"ummi ki fad'a mata kawai

Ummi tace"je ki kirata"

Zuwa Amina tayi sai gashi sun dawo tare a kasar tiles ta zauna tana rike kirji

Ummi tace"meke damun kirjin?"

Tace"zafi nikeji"

Ummi tace"ba dole ba mutum yasa Abu a rai Rahma tun da wuri ki dawo daga rayuwar da kika saka kanki bayi bane Ina fad'a Miki,Kuma Ina son sanar dake ranan juma'a za a d'aura Miki aure da amir"

Ji tayi zuciyarta ta buga ta rike kirji tace"ummi bana so wallahi bazan aurenshi ba ni haka zan Kare rayuwata ba aure ku barni"

Ummi tace"toh baki Isa ba ya ishe ki haka haba ke meyasa kina da kafiya ne an ce kiyi hakuri kin ki ki hakura wanan ai aikin banza ne"

Cikin kuka tace"nidai bazan aureshi na fadi zuciyata"

Ummi tace"saboda ban Isa dake bako?"

Rahma tace"ummi soja fa zai dawo na fad'a miki kuma zaiyi fushi a bar maganan kawai"

Ummi tace"Anki a bari"

Kawai sai Suka ji tayi wani ihu ta rike kirji

Ummi ta taso ta riketa da kanta ta d'auko kayan aikinta ta duba ta

Magani ta rubuta tace"Amina je ki siyo"

Amina ta fita da sauri ummi tace"Rahma kashe kanki zakiyi?toh in baki sani ba in fad'a Miki zuciyarki na gab da bugawa

Tun daga wanan ranan ba a Kara yiwa Rahma maganar auren ba sai dai an cigaba da shiri

Yau dai tana zaune wayarta yayi Kara ta d'aga Amir ne

Sallama yayi yace"ko amaryata ta tashi lafiya?"

Rahma tace"look amir nasan munyi soyyaya a baya Kuma na soka but bekai rabin soyyaya da nikewa soja ba dan girman Allah kayi hakuri ka nimi wata ni soja Nike jira"

Amir yayi dariya yace"zamu gani na Miki alkawarin sai kin dawo kina Sona kamar da"

Tsaki tayi ta Katse Kiran tun daga wanan ranan ta ajiye wayar a gefe Ashe kullum amir na Mata text Bata sani ba
__________
A yau ta kama al-hamis su yusura da Abdul sun dawo cikin yusura yayi girma Kamar zata haifeshi yau da k'yar take tafiya

Abdul na shigowa yace"honey Ina kike"

Ummi ta sauka tana dariya sai ta ji Kamar Aayan ne domin haka yake kiranta karasawa Abdul yayi Yana mata shagwab'a ta ture shi tace"ya'ta zo Nan Ashe har yanzu kina fama?"

Yusura ta rufe ido tana murmushi Abdul yace"ai na dawo da ita kenan sai ta haihu"

Gobe da yamma zan koma bayan an d'aura aure

Ummi tace"Allah ya kaimu"

Rahma dai Bata San meke faruwa ba ta dai gan ana ta zir-zirga Kuma Bata damu ta tambaya ba

Washe gari ta tashi da farin cikin da ta dade batayi ba

Ummi ta leko ta ganta zaune a d'akinta tana cin water melon

Ummi ta bata tsumin da take Bata kullum tace"shanye shi yanzu"

Amsa tayi ta shanye

Ummi tace"Amina zata kawo Miki Kaya shi Zaki sa "

Tace"toh"

Amina ne ta shigo ta Bata Rahma tayi wanka tayi kwaliya kayan ya karbeta danma ta rame

Zama tayi bakin madubi-madubi tana fesa Tulare

Bayan an sauko daga massalaci aka taru a kofar gidan ummi domin kawu cewa yayi ba ruwanshi

Mutane ne cike kofar gidan ana jiran ango domin ya makara go slow ya rike su

Basu suka iso ba sai misalin 3:29

Zama akayi har malami zai fara d'auran aure sai ga motorci sojoji sun Yi horn me gadi ya leka sai ya dawo ya bude bayan ya fadawa sauran abokan aikinsu kowa ya kimtsa

Nan fa suka Zama abin kallo domin masu gudu nayi wasu ma na zaune wurin d'auri aure Suka mike

Abdul ma mikewa yayi yayi da Wanda Suka zo d'aurin aure Suka natsu

Bayan anbude gate Wanda motar ya shigo wani ya zaga ya bude me kofa Wanda ya fito ne yasa Abdul yin wani yin tsalle taku biyu ya Isa gabanshi

Amir ko zaro ido yayi

Yace"

Kuyi hakuri da rashin samu update kamar da na fad'a muku Ina da uzuri ne but inshaallahu yau na gama aikin dake gabana

Manan Nur
Share
[2/20, 8:36 PM] Maman Noorul Hudah: 👄👄👄👄👄👄
*BANA SONSHI*
💋💋💋💋💋💋
_By maman noorul_
_Hudah__

*👄💡NUR WRITERS ASSOCIATION💡💋*

*💡N W A💡*

*Lightning and bringing smile to your world is our perority*

*NUR WRITERS* ~it's a beautiful~ ~world~
Dedicated to Na'ima Adamu maman A'A
🅿9⃣9⃣

Bismillahir Rahmanir Rahim

Amir yace"not again"

Wani wawan runguma Abdul yayiwa Aayan dake tsaye ya rame yayi baki da ka ganshi ka gan Wanda ya dade Yana jinya

Abdul yace"Ina ka shiga Muka d'au ka mutu"

Da k'yar Aayan b

yace"asibiti shekaran jiya na farfado jiya da yamma na dawo Lagos aka ce ka tafi d'aurin aure but wake aure?"

Abdul ya ji kirjin shi ya buga kawai sai yace"Amina "

Yace"Amina Kuma me..."

Katseshi Abdul yayi da cewa"je ciki Ina zuwa

Abdul ya karasa wajen malamin da zai d'aura auren yace"a d'aura da Amina

Kafin Amir yace"zaiyi wani abu an d'aura auren shi da Amina

Shidai mamaki yake

Hayaniyar jama'an waje yasa Amina saukowa tace"alhamdullila an d'aura auren Rahm..."

Wanda ta gani gaban ta ne yasa ta yin shiru tace"Yaya"rungumeshi tayi tana kuka shima ya rungumeta yace"Ina honey?"

Tace" tana ciki"

Yace"Rahma fa?"

Tace"tana Nan"

Yace"aurenwa aka d'aura?"

Amina ta fara in Ina"tsawa ya daka Mata yace"ki bani amsa yanzu na ji kin ce auren Rahma

Jiki na rawa tace"Rahma da amir Amma wallahi Rahma Bata sonsh......."katseta yayi yace"shut up"

Haurawa yayi yaje d'akin ummi,da mamaki ummi ta taso tana shafa fuskarshi tana hawaye tace"Kaine ko mafalki Nike?"

Murmushi yayi yace"ummi nine ban mutu ba"

Ummi tace"Ashe Rahma tayi gaskiya na shiga uku"

Rungumeta yayi yace"ummi farin ciki zakiyi"

Ummi dai taji dadin ganin shi Amma yanzu haukan da zaiyi in yaji da Rahma aka d'aura aure shine matsala

Yace"ummi ko baki ji dadin ganina bane?"

Zatayi magana sai ga Rahma ta shigo da gudu domin Amina ta fad'a mata

Ta baya ta rungumeshi tana kuka tace"Ina ka shiga ne ka barni?"

Dawowa gabanshi tayi ta fara shafa fuskarshi tana hawaye tace"soja is that really you? Ko mafalki nikeyi

Wani kallo yake Mata sai ya gan tayi kwalliya

Rungumeshi
Tayi tana kuka Amma sai ya tureta ta fadi a gado

Barin d'akin yayi sai binshi take a baya tana cewa"ka tsaya please na tuba mijina nasan ni Mai laifine"be kulata ba

D'akin shi taje tace"soja me nayi kaki kulani ko laifi nayi in laifin ne ka yafemin na tuba

Ko kallonta beyi ba saima zuwa gaban drawer da yayi ya fara dube-dube

Murmushi tayi ta karasa ta kara rungumeshi a fusace ya juyo yace"wai meyasa kike damuna eh?Ina kin ji dadi na mutu ko shekara banyi ba kin komawa tsohon saurayinki har an d'aura Miki aure meyasa kike damuna?"

Girgiza kai ta farayi tace" wallahi ni ban aure kowa ba na fadawa ummi Kuma ta bar zancen dan allah soja ka bari in ji d'inmin ka na wahala Sosai Allah "

Yace"really ni zaki munafurta kafin in tafi babu inda banyi ba ki fadamin kina Sona amma kika ki
ashe jira kike in je inna mutu kiyi aure toh babu komai na hakura Nima abin ya isheni kije dama yanzu aka d'aura muku aure Nima Allah ya bani Mata ta gari haka Allah yayi nawa zai kasance"

Rahma kuka take Sosai ta rike saitin zuciyarta sai girgiza kai takeyi tace"wallahi ni banyi komai ba soja ban san da auren ba ka yarda dani"
Chapter 22 · 0% Book details