← Book details Bana Sonshi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 17 OF 25

Sashe 17

Bana Sonshi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

D'aukanta yayi zuwa toilet ya sakata a ruwan zafi

A firgice ta bude ido ta saki kuka tana cewa"wayyo ka barni wallahi zan mutu"

Rungumeta yayi yace"sorry dear na Kira doctor yanzu zata zo"

Kuka sosai takeyi wai ya maidata gida mutuwa zata Yi

Knocking din da ya ji ne yasa shi fita ya bude kofar Dr ce

Bata hanya yayi ta shiga

Bayani yayi mata

Tace"toh muje in duba ta"

Suna shiga bedroom ta jira shiya ya shiga ya fito da yusura d'aure da towel

Kwantar da ita yayi jikinta sai rawa yakeyi

Bude Mata kafa Dr Aisha tayi sai ta kalleshi da mugun b'acin rai

Tace

Kiyi hakuri wallahi Dan banasan jawa fans raine da tuni na ajiye littafin Nan sai bayan sati in cigaba but no prob I will try in Gama muku ga zee Mai taimaka mun ta fiya shime da shirirta inshaallah gobe zamu Kai 79-80 din

Maman Nur
Share
[2/20, 8:33 PM] Maman Noorul Hudah: 👄👄👄👄👄👄
*BANA SONSHI*
💋💋💋💋💋💋
_By maman noorul_
_Hudah__

*👄💡NUR WRITERS ASSOCIATION💡💋*

*💡N W A💡*

*Lightning and bringing smile to your world is our perority*

*NUR WRITERS* ~it's a beautiful~ ~world~

🅿7⃣3⃣-7⃣4⃣

Bismillahir Rahmanir Rahim

Dr Aisha ta kalleshi tace"what this?wanan wani irin Rashi tausayi ne?"

Tsosa keya yayi cikin jin kunya yace"sorry I lost control"

Kallonshi tayi tace"you lost control?ko ka manta ita ba a ayi Mata training da allurar sojoji da zata iya jure wahala ba?"

Murmushi yayi Yana shafa kai

D'inki tayi Mata tare da allaurar bacci sanan ta bashi maguguna ta bar gidan

Zazzabi ne me zafi ya rufe yusura Abdul duk tausayinta ya kamashi har yake jin da bai kusance ta ba inda yasan haka zata Sha wahala

B'angaren Rahma ko tunda Aayan ya mata bayani ta tashi bata fito ba sai da yunwa ya dameta

Koda ta fito a inda ta barshi haka ta sameshi ya kwanta Amma ba bacci yake ba

Yana jin motsinta ya mike yace"Rahma dan Allah ki fahimceni please Niko so d'aya ne ki min magana your silence is driving me crazy"

Bata kulashi ba ta tafi kicin ta d'aura girki inda ta dafa shinkafa da miya ta yanka salad tayi

Ta jera a dining zuwa tayi gabanshi tace"uhmm in kana jin yunwa na gama abinci"tana Gama magana ta juya ta koma dining ta zauna

Binta yayi ita da kanta tayi me serving

Jawo na plate dinta yayi ya had'a yace"please ki bari mu ci tare"batayi magana ba ta cigaba da cin abinta

Rike Mata hanun yayi yace"Rahma kiyi magana please na kusan in Yi tafiya ki manta da komai

Kuka ta fashe dashi mikewa yayi yace"subhannallah laifi nayi Kuma?"

Batayi magana ba saima kukan da ta cigaba dayi shiko ya rungumeta Yana aikin lallashi

Lafewa tayi a jikinshi tana shakar kamshin shi sun dade a haka kafin ta janye jikinta

Murmushi yayi yace"Yi shiru finish your meal muje mu kwanta"

Tana gamawa suka haura d'akin shi ya shiga ita Kuma ta shiga d'akinta wanka ta shiga tayi ta fito ta saka rigar bacci riga da wando ta kwanta

Batayi nisa a bacci ba taji an bude kofa Kara dunkulewa tayi cikin bargo tana ji har ya kwanta bayanta ya jawota

Yi tayi kamar tana bacci sai taji yace"Rahma tafiyar mu fa jibine bazaki fad'a min komai ba?ki ce kin yafe min kimin addu'a ki nuna min so"

Bata tanka shi ba kuma yasan tana jinshi

Haka fa yayi ta rokonta akan tace"tana sonshi Amma Taki"
Gajiya yayi ya kwanta

Washe gari yusura zazzabi ya lullubeta Abdul sai fama hidima yakeyi sosai hankalin shi ya tashi

Su Rahma ko ba canji domin babu inda beyi da Rahma ba amma taki kulashi in ya masa Mata sai ta fashe da kuka haka ya gaji ya hakura

B'angaren su Amir ko

Maman Nur

Share
[2/20, 8:33 PM] Maman Noorul Hudah: 👄👄👄👄👄👄
*BANA SONSHI*
💋💋💋💋💋💋
_By maman noorul_
_Hudah__

*👄💡NUR WRITERS ASSOCIATION💡💋*

*💡N W A💡*

*Lightning and bringing smile to your world is our perority*

*NUR WRITERS* ~it's a beautiful~ ~world~

🅿7⃣5⃣&7⃣6⃣

Bismillahir Rahmanir Rahim

Aneesa ne gaban mummy sai zazzage Mata buhun rashin mutunci take wai akan me zata takurata sai ta gaisheta bayan tasan ba zamanta take ba

Baki sake mummy ke kallonta kafin tace"Aneesa ni kikewa rashin kunya?"

Aneesa ta murgud'a baki tace"kwarai kuwa ai gaskiya na fad'a miki,kin fiya takura wallahi. mace kowa da mijin shi zatayi ta biyoni tana takurani nifa bana son haka fa"

Mummy da mamaki ya lullubeta tace"ikon Allah ai Aneesa ko bakomai zaki mutuntani a matsayin yayar mahaifiya ko?"

Aneesa tayi tsaki tasa hanun a kugu tana karkad'an jiki tace"toh sai me?Dan ke yayarta ne me kika tsinana mata?Ina kin samu daular kin mantata cikin talauci shine yanzu Dan rashin kunya Zaki wani ce yar uwarki ce"

Ji tayi mummy ta wankaata Mari tace"baki Isa ba ki raina ni ko a gaban hafsat uwarki nafi karfin raini a gunki"

A fusace Aneesa ta ture mummy ta fadi a kujera dai-dai shigowar Amir

Mummy na hagoshi ta mike tana hawaye

Ga mamakinta sai ta gan ya wuceta

Tace"amir baka gan abinda ya faru bane?"

Juyowa yayi yace"eh na gani "

Mummy ta fashe da kuka tace"Amir meke faruwa ne kwana biyu baka kulani a ce a min irin wanan cin mutunci a gabanka bazaka d'au mataki ba "

Shigewa yayi ciki ya barta tsaye

Aneesa tayi kwafa tace"sai ki barmin falo mijina ya dawo"

Cikin sanyi jiki mummy ta bar part din

Tana shiga main building din sai ta gan bakine zaune a falon

Saurin b'oye damuwarta tayi da mamaki ta kallesu domin kawunin Kabir ne masu zuwa niman auren Zahra

Karasawa tayi tace"Sannu ku da zuwa bari a kawo muku ruwa"

Kawu bala yace"dakata ba wanan ya kawo mu ba Ina alhajin yake"

Mummy tace"lafiya dai ko?"

Kafin yayi magana alhaji ya shigo da jaka a hanunshi alamun daga office ya fito

Kawu Bala be Bari ya karaso ba yace"alhaji zuwa nayi in fada maka maganar auren yar'ka da Kabir babu shi"

Mummy ji tayi gabanta ya mugun fadi

Tace"alhaji meya faru?"

Kawu Bala yace"mun gano babu abinda Yarki takeyi sai iskacin"

Mummy zatayi magana ya mike yace"hajiya ba maganarki bane"

Tace"ai sharri akayi mata ni nasan ya'ta kuyi hakuri ayi auren Nan dan Allah ai ko tanayi sai a yafe Mata ya aureta ya samu ladar jihadi"

Kawo yace"oh shine ke kika Hana naki ya auri wata ko?"kina tunani bamu sani bane?"

Shidai Abba shiru yayi ya ma kasa magana wanan wani irin matsiface?"

Kawu Bala yace"mudai a dawo Mana da kayar mu"Yana Gama magana ya wuce

Cikin fushi ta Haye sama ta Sami Zahra zaune tana waya da wani

Zahrah na ganinta ta b'oye wayar

A fusace mummy tace"

Maman Nur
Share
[2/20, 8:34 PM] Maman Noorul Hudah: 👄👄👄👄👄👄
*BANA SONSHI*
💋💋💋💋💋💋
_By maman noorul_
_Hudah__

*👄💡NUR WRITERS ASSOCIATION💡💋*

*💡N W A💡*

*Lightning and bringing smile to your world is our perority*

*NUR WRITERS* ~it's a beautiful~ ~world~

🅿7⃣7⃣-7⃣8⃣

Bismillahir Rahmanir Rahim

A fusace tace"dan garin ku bani wayan"

Zahra tace"kiyi hakuri"kwacewa tayi tace"da ubanwa kike waya?"

Zahra ta turo baki

Mari ta Kai Mata tace"zahra nace da ubanwa kike waya?wai so kuke ku kasheni? yayanki besan kowa ba sai matar shi ke Kuma babu abinda kika sani sai iskanci gashi kinsa an fasa bikin ki bayan na raba Kati yanzu ya zanyi?ya kuke so inyi ne?"

Zahra tace"mummy sharesu nifa na samu wani yauwa mummy Yan da kud...."

Bige Mata baki mummy tayi tace"Dan uwarki yunwa kike jine da kwadayin kudi zai rude ki?"

Ga mamakinta sai ta gan Zahra ta hayyako Mata Kamar zata duketa tace"mummy ai gani nayi ba a kaina aka fasa auren ba shima Yaya ai har gida kika bi Rahma kika sa aka fasa duk da tarin biyyayar da take Miki toh ita ba haihuwarta akayi ba?"tana magana ta bar d'ankin mummy ta bita da kallo

Hmmm what goes around,always comes around mummy kin Manta kema kina da ya'mace gabanki yanzu ke kina tunanin a rufawa Yar ki asiri bayan ke kin tona Mata?kina ganin zai yiwu,Allah ka Kare mu daga San zuciya"

Zama tayi ta rike Kai tunanin Rahma na dawo Mata sai yanzu ta tuna tayi wauta tunawa tayi da randa Amir ya kawo Rahma ta gaisheta har suka bar gidan Rahma Bata bari sun had'a ido ba,amma a lokacin itafa ta tsaneta so take a auri Aneesa

Tsaki tayi tace'na shiga uku yanzu ba sai gobe ba zan tafi in roke su su bani auren Rahma yariyar kirki"

Amir ko cikin ikon Allah yanzu ya fara addu'a cikin dare baya bacci

__________

A yau Abdul da Aayan zasu kaisu Rahma kano daga nan su dawo Lagos kafin sutafi

Bayan Aayan ya dawo daga sallah asuba ya tarar har Rahma ta koma bacci

Kwanciya yayi ya Kai bakin shi dai-dai kunnin ta yace"baby please wake up"

Cikin magagin bacci tace"please ka bari inyi bacci jiya ka hanani bacci da iskancin ka"

Murmushi yayi ya jawota da karfi ya rungume bata San sanda murmushi ya sub'uce mata ba

Chakulkuli ya fara Mata Yana cewa"romance shi kike kira iskanci?bayan kin hanani yin main abin"

Jan jikinta tayi ta rufe fuska yace"Rahma na lura kin fara gulma zo in fad'a Miki wata magana"batayi magana ba ta shige jikinshi

Wani dadi ya ji yace"yau zamu tafi kano jibi sai mu bar kasa Rahma ki fadamin abinda zanji dadi,Rahma ki ce kina Sona please"

Ba tare da tayi magana ba ta mike ta Shiga bayi tayi wanka ta fito

Tace"Bari in had'a Mana breakfast "

Yayi murmushi yace"ok muje in tayaki"

Tare suka fita Suka dafa indomie bayan sun gama breakfast ya kalli agogo yace"Rahma muje mu shirya nasan yanzu kawarki sun gama shiri"

Tace"ok"

Bayan sun Gama shiri yace"jirani yanzu zan dawo"

Tace"toh a falo ta zauna tana jiranshi

harya dawo yace"mu tafi"

Suna fitowa suka had'u dasu yusura sun fito

Rahma na ganin yusura ta

Maman Nur
Share
[2/20, 8:34 PM] Maman Noorul Hudah: 👄👄👄👄👄👄
*BANA SONSHI*
💋💋💋💋💋💋
_By maman noorul_
_Hudah__

*👄💡NUR WRITERS ASSOCIATION💡💋*

*💡N W A💡*

*Lightning and bringing smile to your world is our perority*

*NUR WRITERS* ~it's a beautiful~ ~world~
Chapter 17 · 0% Book details