← Book details Bana Son Shi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 25 OF 25

Sashe 25

Bana Son Shi Part 1 Complete Hausa Novel · about 2 min read

Janyeta yayi daga jikinshi yace"ba mafalki bane real ne kina tare da sojan ki,muje toh mu dibo abinci

Zubawa yayi itadai tana manne dashi suka dawo falo Suka zauna

Bata yake tana karb'a aiko ya samu taci sosai tace"soja wallahi dole sai na amsa kiran nature

Yace"a ina"

Tace"toilet zani"

Murmushi yayi yace"bari in d'auke ki mu tafi"

D'aukanta yayi sai ga ummi ta fito kunya duk ya Kama Rahma

Ummi tace"toh gobe ku tattara Ina ku Ina ku, ku barmin gida bana son rashin kunya kun hana mutane bacci da surutu"

Duk da Rahma na kokarin sauka kin barinta yayi ta gaji ta bari

Suna shiga d'aki ya kaita toilet yafito ya kulle kofa ya zauna Yana jiranta

Bayan ta gama ta fito tace"na gama"

Tashi yayi yace"mu shiga muyi wanka"

Rufe fuska tayi tana murmushi yace"banson gulma fa?"

D'aukanta yayi suka shiga Nan fa suka bude wata shafin soyyaya a toilet domin shi dai Aayan haukacewa Rahma yayi ita Kuma ganin muscles dinshi da hallitar shi yasa tsoro ya kamata tace"soja please muyi wanka bacci nikeji Kuma kasan bani da lafiya

Jawota yayi jikinshi kirjinta na gogan jikinshi

Kallon cikin ido yake mata yace"I LOVE YOU Rahma "

Rungumeshi tayi gam tace"nima Ina sonka mijina"

Bayan sun gama ya d'aukota dukaninsu d'aure da towel Nan fa bacci ya kwahesu ko Kaya basu sa ba

Abdul ko sai juye-juye yakeyi a gado yana tsaki sai cewa yake"mutum da matar shi a hanasu kebawa kawai wai dan ta haihu"waya ya jawo ya Kira yusura mummy dake lallashin Aayan yusura na bacci

Ganin shine me Kira yasa ta d'auka

Tace"wallahi son in baka fita idona na rufe ba zan mugun sab'a maka"

A hankali ya sauke wayar a kunnin yace

Mama nur share
Chapter 25 · 0% Book details