← Book details Bana Son Shi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 13 OF 25

Sashe 13

Bana Son Shi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

B'angaren Rahma ko tayi kuka ta gode Allah har bacci ya saceta

B'angaren su Amir ko zazzabi yake sosai hakan yasa ba ayi wani sha'anin ba anty hafsa ko sai fada takeyi a cewarta ya lallab'a haka yaje hall

Komawa tayi wajen boka ta tace"a Bata maganin da zai sa Aneesa ta mallaki Amir Kar ya gan kowa gaban shi sai Aneesa

Da asuba Rahma ta tashi da mugun ciwon kai ga zazzabi,itama yusura haka domin har rawar sanyi take

Hakan ba karamin d'agawa ummi hankali yayi ba ta Kira Dr nan Dr tace"streess ne a bari su huta"

Komawa sukayi bacci

Sai misalin karfe 11:pm Abdul ya shigo yace"su shirya su tafi ana jiransu a Lagos

Umma tace"haba ku bari Mana su samu karfin jiki

Abdul yace"no ana jiranmu babu inda ummi ta iya haka ta tashesu badan taso ba
.yusura na bude ido ta saukeshi a fuskar Abdul kashe Mata ido yayi Yana dariya

Cikin awa d'aya duk sun Gama shiri,ummi Bata so tafiyarsu ba domin Rahman ta shiga ranta har yusura ma

Amina ce ta kaisu airport sanda ta gan shigansu jirgin ta koma

Bayan sun bar gidan duk wani Wanda ya zo bikin kowa ya fara Shirin wucewa

Wata matace makociyarsu ummi ta bi ummi bedroom inda ta ganta zaune ta d'an jigina da gado

Zama tayi a kasa tace'hajiya wallahi akwai abinda baku sani ba game da yariyar nan Rahma"

Ummi ta d'an d'ago ta kalleta tace"inaji"

Larai tace"kin San satinan na tafi Minna gida ko?"

Ummi tace"ina zan sani?"

Tace"toh wallahi gidan yayata uwa d'aya uba d'aya katanga ya raba su da Rahma a ranan naje in dubo yayana kawai sai aka biyo mahaifiyar Rahma gida"

Ummi tace"me tayi?"

Ladidi tace"Ashe wai Rahma Yar iskace wallahi har video akayi Mata tsirara tana iskanci da wani hakan ma yasa mahaifiyar Wanda zata aura tace sun fasa hajiya da idona na gani ba labari aka bani ba bansan ya akayi Kuma na ganta a Nan ba,hajiya kiyi gaggawan d'aukan mataki"

Ummi ta matso bakin gado ta zubawa ladidi ido kafin tace'

Maman Nur
Share
[2/20, 8:30 PM] Maman Noorul Hudah: 👄👄👄👄👄👄
*BANA SONSHI*
💋💋💋💋💋💋
_By maman noorul_
_Hudah__

*👄💡NUR WRITERS ASSOCIATION💡💋*

*💡N W A💡*

*Lightning and bringing smile to your world is our perority*

*NUR WRITERS* ~it's a beautiful~ ~world~

Dedicated to NANAH KHADIJA

🅿5⃣5⃣-5⃣6⃣

Bismillahir Rahmanir Rahim

Ummi ta kalleta sama da kasa tace"yaran ki nawa?"

Ladidi tace"shida ne Mata hud'u maza biyu budurwar ta isa aure kuma kyakyawa ce ko yau za iya Mata aure"

Ummi ta ja numfashi tace"toh a matsayin ki na mace Kuma uwa meyasa kike b'ata mace Yar uwarki?"

Ladidi ta fara in-ina

Ummi tayi murmushi tace"ni ban damu da abinda Rahma ta aikata a baya ba abinda na sani ita matar d'ana ne,meyasa wasu matan basu da aiki sai gulma ne?a matsayin mu na Mata muyi ta aibanta Mata Yan uwanmu?ladidi da kike fad'a min so kike insa ya saketa ya auri wata?bayan nasan in ma karuwace zai samu ladar aurenta,shin nasan abinda yakeyi ko yafi na Rahma dan da kawai anfi ganin na mata,a duniyar yau anfi son mace ta kasance kamila ta Kai budurcinta gidan miji shi Kuma namiji ko oho shiyasa suke abinda Suka gan dama suna iskanci su,sai ka gan ya namiji ya gama iskancin shi ya zo ya auri kamilan mace su Kuma Wanda ya b'ata wa zai auresu?Yan mata ma yanzu sun lalace sun biyewa rudin maza sun ki su gane komai namiji yayi ado ne.toh nidai ladidi nagode da kika sanar dani amma Ina son ki sani sai yanzu na Kara jin son Rahma har cikin zuciyata bazan tab'a wulakanta ta ba domin nima Ina da ya'mace gabana batayi aure ba bansan me takeyi a bayan idona ba haka shima Aayan din ki gan in na rufawa Rahma asiri sai Allah ya rufa min nawa asirin nagode Zaki iya tafiya Amma kema ki canja Hali gulma ba Abu ne me kyau ba"

Ai ladidi ji tayi tunda take a rayuwa Blbata tab'a jin kunya haka ba gaskiya tayi dana sanin fito da wanan maganar dama son zuciya ya kawo ta a tunanin ta hajiya zata sa a kori Rahma sanan Aayan ya auri yar'ta ashe ba haka bane"

Ai bata Kara komawa cikin gidan ba ta kofar baya tabi ta bar gidan

Ummi ko kwanciyarta ta gyra tace"aikin banza a ce kina mace ni Rahma ma batayi min Kama da Wanda Yar iska ba"

A lokacin da jirgi ya tashi fitsari ne ya rage be kubcewa Rahma Dan tsoro duk Aayan na lura da ita amma ya basar a cewarshi ai bata gaisheshi ba shima ba zai fara mata magana ba

Yusura ko bata masan jirgin ya tashi ba domin Abdul ya sata jikin shi yana Mata tafiyar tsusa

Tun tana kokuwa harta hakura ta lafe jikinshi inda wani bacci me dadi ya kwasheta

Rahma ko idonta yayi wuri-wuri kamar zatayi kuka hawaye ya cika idonta

Lumshe ido tayi sai satar kallonta yakeyi ji yake kamar ya rungumota

Wani yunwa ne ya fara damunta sai ta bude ido ta kalleshi

Tace"yunwa nikeji"

Be amsa ba saima Kiran wata flight attender da yayi ya nuna Mata Rahma

Rahma ta rasa me zata ce mata domin itadai bata tab'a Shiga jirgi ba

Tunawa tayi da ai tana gani a films

Ordering abinda zata ci tayi

Kallon su Abdul da yusura tayi inda Abdul yakeyi kamar zai mayar da yusura ciki

Murmushi takaici tayi tunawa da amir dinta

Can kuma sai ta gan rashin dacewar yin haka tana matar sure

Nima gafarar ubangiji tayi hawaye na kokarin zubo Mata a ranta tace"sabon rayuwa dole ne in yarda da kaddara in mance da abinda ya faru a baya in rungume gaba ni kaina nasan nayi bankwana da farin ciki"

Kallon Aayan tayi sai idonsu ya had'u hawaye ya zubo Mata

Shi ya fara d'auke kanshi Yana mamakin meyasata kuka

Allah dai yasa Samira bata fad'a mata wani magana ba

Suna sauka jibrin ya zo ya d'aukesu ya kaisu gida

Babban gidane me d'auke da duplex biyu sai dai suna da d'an nisa da juna

Suna fitowa a mota yusura ta fara kallon wuri sai ta kalli Abdul

Tace"

Maman Nur
Share
[2/20, 8:30 PM] Maman Noorul Hudah: 👄👄👄👄👄👄
*BANA SONSHI*
💋💋💋💋💋💋
_By maman noorul_
_Hudah__

*👄💡NUR WRITERS ASSOCIATION💡💋*

*💡N W A💡*

*Lightning and bringing smile to your world is our perority*

*NUR WRITERS* ~it's a beautiful~ ~world~

Dedicated to my fans
Nagode da comment da addu'on ku har na rasa Wanda zanyi replaying but Ina karantawa Kuma suna sani nishadi

🅿5⃣7⃣-5⃣8⃣
Bismillahir Rahmanir Rahim

Tace"a Nan zamu zauna tare da Rahma?"

Murmushi yayi yace"eh but tare Dani ba Rahma ba ,yana gama magana ya ja hanunta suka shige ciki"

Rahma ma tambayar da tayiwa Aayan kenan amma shi be amsata ba sai ma wucewa da yayi ya barta tsaye hakan yasa ta bishi a baya

Da sallama ta shiga falon dake tashin kamshi sai kallon ko Ina take domin hotunanta ne a bango Wanda ita bata San dasu ba

Shiko a zaune yake har ya d'auko ruwa yana Sha

Kallonshi tayi tace"dan Allah Ina ne toilet Ina so in yi alwala zanyi sallah

Be kulata ba ya d'auki remote ya fara latsawa

Zatayi magana sai ga Samira tana saukowa daga upstairs din cikin wani d'an iskan crazy wando da riga armless

A lokaci d'aya gaban Rahma da Aayan ya fadi

Saukowa take cikin tafiyar takama tana cewa"welcome home sweery Ashe kun iso ai kana kirana na bar abinda nikeyi nace bari in zo in tarbe amaryata

Tashi yayi Yana kallonta

Itako Rahma hawaye ya cika idonta kiris take jira ta fashe da kuka amma sai kawai ta tuna da maganganun umma data ce Rahma karki bari kowa yasan tsakanin ki da mijin ki"kawai sai tayi saurin mayar da hawayen Amma sanda ya gangaro cikin dabara ta gogeshi

Aayan yace"Samira what are you doing here?"
Murmushi tayi ta karaso ta rungumeshi tace"baby ka manta Kai ka kirani?"

Rahma tayi murmushi tace"a yau for the first time na gan karuwan da ta zo tarban amaryar abokin fasikancinta,a gaskiya na Kai mace da har kariya zata biyoni gida,toh dai tunda nice matar gidan Ina Miki barka da zuwa kin san akwai babanci karuwa da matar gida domin komai lalacewar matar gida duniya sun shaida ita yake so shiyasa ya aureta itakuma karuwa sai dai a Kare a titi "

Samira tayi murmushi tace"bani da lokacin ki"ta Kare magana da niyyar rungume Aayan sai dai kafin tayi haka Rahma ta rungumeshi tace"baby na gaji Kuma akwai salloli a kaina zanje inyi wanka inyi sallah"

Yanayin inda ta rungumeshi yasa shi shiga wani yanayi

Rahma tace"ko tare zamuyi ne baby?"

Samira ta zo zata janye Aayan Rahma tayi saurin tureta tace"karki kuskura ki ce Zaki tab'a shi domin bazan lamunta ba in kina son ki tab'ashi ki bari sai kun rage ku biyu abinda yafi rungums sai kuyi but not in my present"

Rahma ta kalli Aayan tana tura baki tace"baby please in na fito ka goyani"

Kallonta yayi sai ta d'auke ka ta janye jikinta

Har ta haura sai Kuma ta dawo tace"baby ina ne d'akina Kar inje in shiga d'akin karuwar ka"

Kallonta yayi Amma beyi magana ba,itako sai ta koma d'akin da ta fara gani na farko ta Shiga ta gan komai fes fes ga d'akin ya had'u

Zama tayi bakin gado ta fashe da wani mugun kuka ta toshe bakin ta tana kuka

Bayan taci kuka ta gaji ta mike ta shiga bayi tayi wanka ta fito d'aura da towel sai a sanan ta tuna karamin akwatin ta na falo

Hijabi ta d'auka har zata sa,sai Kuma ta cire ta fito da towel iya guiwa tana tafiya a hankali har ta sauka

Abinda ta gani ne yasa ta tsayawa tana kallo

Domin kiss sukeyi Basu man ji fitowarta

Gyran murya tayi sai Aayan yayi sauri janye jikin shi

Ratsashi tayi ta jawo akwatin tace"enjoy"sanan ta haura

Samira ta jawoshi sai ya wani tureta yakeyi

Shaketa yayi yace"ki barnan gidan kafin insa a fidda ki"

Tace"Kai ma kasan baka Isa ba "

Yace"Samira kina kaini bango na fara gajiya meyasa har yanzu bazaki gane bana sonki ba?"
Chapter 13 · 0% Book details