← Book details Anjane Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 17

Sashe 9

Anjane Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Saroro tayi tana bin Hajiya da kallo kamar wadda bata gane abinda tace ba, se da Hajiyar ta taɓa ta sannan ta sunkuyar da kai

"Amma Hajiya daga gani na yau har se ki bar min duk wannan kayan arziƙin bayan ke aka bawa?".

"Kin shiga É—akina fa kin gani mene bani dashi da zan ce zan É—auka?, wanda nace É—in ma sha'awa ce kawai irin ta É—an Adam amma gwargwado ai Allah yayi min suttura, kinga ki kwantar da hankalin ki ni ba haka nake ba dan haka ki shiga É—aki in har yayi miki gobe zaki bani kuÉ—i na".

Tana faɗa tayi gaba abinta Salame ta bi bayan ta da kallo tana murmushi, da alama matar zata yi daɗin zama ɗan alamu sun nuna bata da ƙyashi da hassada haka kuma bata da san kai.

Jakar su ta shigar sannan ta shiga ta tsaya tana sake bin ɗakin da kallo, labulaye masu kyau kuma sababbi, fenti me kyau ga katifa ma me taushi da tudu, flower vase ƙarama a gefe, dustbin, tiles, carpet ƙarami tabarma nannaɗe a tsaye ga kuma wardrobe madaidaiciya itama a gefe.

Hamadala ta shiga yi tana hawaye kafin ta kwance yaranta ta shimfiɗe kowacce kan zanin ta ta shiga gyara ɗakin..........................✍🏻.

©️ Ouummey 📚✍🏻.

☑️Ote, Comment and share please.

Ouummey 06 [ 11/27/2022 9:29 PM ]

★★★ *ANJANE* ★★★
(Rashin sani)
★★★★★★★★★

_*PAID BOOK*_

Story/written by Ouummey.

Wattpad @ouummey.

From The author of:

*HAƘORIN DARIYA*
*ƘASAR MU A YAU*
*BA NI DA LAIFI*
*SARAKI (the accused prince)*
*ABOTA CE KO SOYAYYA*
*And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK*

₦300 to the below account details
Rabiatu Abdullahi
2391368231
ZENITH BANK, screenshot and send the evidence of payment to 09013101854 or MTN recharge card o 09013101854, note VTU is not acceptable.

                      FREE PAGE 06

_______________________📖 Seda ta Gama gyara ko ina dan dama ƙura ce kawai a ɗakin sannan ta lura da ƙaramin toilet tsayuwar mutum ɗaya, wanke shi shima tayi da ruwan da Hajiya ta bata jarka biyu ta roƙe ta gawayi ta ɗora musu ruwan wanka.

Ƴan biyu ta fara yi wa wanka sannan itama ta samu tayi, bata iya ta nemi abinci ba ta kwanta bacci saboda gajiya.

★★★★

"Haba bawan Allah, ya kamata a ce ka saurara wa kanka wannan ɗimbin damuwar, fisabilillah shikenan kai in aka ga fara'a a fuskar ka sedai fake, ka sake kayi rayuwar kamar kowa ka ƙi, in ance dalilin da yasa rayuwa take zamar maka baibai kuma kaƙi yarda".

A hankali mutumin da aka kira da bawan Allah ya shiga É—ago kan sa daga sunkuye da yake har ya É—ago baki É—aya.

Tsurawa wanda ya gama magana ido yayi na wasu sakanni kafin ya miƙe tsaye yana duban agogon hannun sa, bece masa komai ba ya shiga tarkata takardun sa ya zuba cikin briefcase sannan ya fita.

Baki buÉ—e É—ayan mutumin ya bishi da kallo kafin kuma ya gyaÉ—a kan sa ganin yau iskancin bawan Allah har a kan sa, halin sa ne dama Amma ze iya rantsewa ya manta rabon da ya karta masa in ba yau ba.

Fita yayi yana sanar da masinjan sa ya kulle office É—in shima ya fita, kamar yadda yayi tsammani be ga ko shatin tayar motar sa a parking space ba, tasa ya shiga ya bar building É—in shima.

★★★★★

'Ban san wane irin aiki na tafka ba, ban san wace irin ƙwaƙwalwa gare ni ba da kullum bata bani mafita miƙaƙƙiya, duk da Riyya ta faɗa min nayi gaggawa in jira tukunna amma ni gani nake in na zauna to zan ta jira ne har na gaban abada, in bana son haka ya faru me zanyi kenan, me zan yi?!'

Wannan shine tunanin da matashiyar ke tayi tana kai kawo a madaidaicin falon da yaji kayan alatu da alama dai tana cikin state of confusion ne dan se cije yatsun hannunta take cikin son samun mafita.

Shigowar wata dattijuwa É—akin yasa ta nemi kujera ta faÉ—a kamar wadda bata da laka, kallon ta dattijuwar tayi tana kaiwa zaune itama kan wata kujerar kafin ta shiga mata kallon tambaya

"Yanzu shikenan Anna mu haka zamu zuba ido muna kallon komai na faruwa a gidan nan, ki duba fa watan yaya nawa yanzu da rasuwa amma ba wanda ke bin takan mu ke kuma naga ma abin ko ɗaɗa ki da ƙasa be yi ba".

"Ni kin sa ba wani gane magana cikin magana nake ba gwara ki fito fili ki sanar dani me ke faruwa a gidan bamu sani ba".

"Amma Anna kin san in mukai sake mun kusa barin daular nan mu koma kwana ƙarƙashin gada ko?".

"Tuf tuf, Allah ya tsare ni.....". Anna ta faÉ—a tana tofar da miyau a gefe

".....banda neman masifa da bala'i irin naki me yakawo batun komawa ƙarƙashin gada kuma da ko a mafarki na gani in na tashi se na yi sadaka".

"Nima ba so nake yi ba sedai in dai bamu motsa ba abinda ke daf da faruwa kenan".

"Dan Allah yi min dalla dalla dan kin san bana san jan rai a magana".

"Kamata yayi ace nice Abdu ze aura amma muna nan mun zuba ido yanzu haka naji jita jitar ze aure Æ´ar uwar Hajiya Babba".

"Kam babban bu**uba, ni za'a kawo wa iskanci har gida, lallai Hajiya Babba ta É—ebo ruwan dafa kanta, ki kwantar da hankalin ki Audu bashi da wata mataa gidan duniya suke, da alama zan gwada musu barikanci na da basu sani ba".

Cikin jin daÉ—i matashiyar ta gyara zama tana kai fuska gefe

"Atoh abinda ya kamata dai muyi kenan dan yana auro wata kin san dole zamu bar gidan nan tun da yaya da ta haÉ—a mu ta raba Ni kuma shine bana fata".

"Ki sa a ranki hakan ma baze taɓa faruwa ba, mu da gidan nan kuma mutu ka raba, mun shigo shi kenan fita kuma ba rana".

★★★★★

"Amma dai kin san ni ke san auran yarinyar nan shine kike wani batun wancan lusarin, yanzu da nayi magana kuma kice komai dan mu kike yi, ko ina basira a wannan tunanin naki oho, na daɗe ina faɗa miki tsufa yasa duk wata basira taki gujewa amma kin ƙi yarda, to wannan karon kam sedai kiyi haƙuri dan wallahi ba zan iya bin tsarin ki ba".

"Kai kam ai dama baka da fahimta, komai se an zauna an maka gwari gwari kafin kake ganewa, yanzu kamata yayi mu kama yaron nan a hannun mu kuma dole se ta hanyar matar sa dan ai shi ba sakarai bane da ze dawo ya yarda damu bayan duk abinda suka dinga faruwa, amma ina matar sa ta zama tamu ai ruwa tasha kaga ta nan zamu dinga samun duk bayanan da muke so a kan sa kuma mu dinga aiwatar da shirin mu a kan shi hankali kwance har mu kai shi ƙasa".

"A soke shi, ban yarda da wannan tsarin ba in har se ita zaki aura masa to a fasa".

"Zo tsaya mana jarumina, tsaya ka saurare ni kaji?".

Ta faɗa tana bin bayan shi da sauri sedai ko juyowa be yi ba balle ya tsaya saurarar ta kamar yadda take so, seda ya kai bakin ƙofar falon ya juya gare ta

"In har aka gabatar da tsarin nan tabbas za'a samu matsala dan haka kar kuce ban faÉ—a muku ba, a soke shi shine kawai kwanciyar hankali".

Yana faɗa ya fice yayin da dattijuwar ta dafe kanta tana koma wa bedroom ɗin da sauri ta ɗauki phone ɗin ta ta shiga dialing wasu numbers, tsawon lokaci tana ringing amma ba'a ɗauka ba har ta katse, tsaki taja ta kuma dialing, wannan karon ma kamar ba za'a ɗauka ba dan se a kusan ringing ɗin ƙarshe aka ɗauka, bata jira wani gaisuwa ba ta shiga kora dalilin kiran da tayi

"Plan cancelled, a daƙile komai a kuma tsayar da komai zuwa lokacin da zan sanar dake yanzu akwai matsala a ƙasa".

Tana gama faÉ—a tayi hanging call É—in tare da wurga wayar kan bed itama ta biya cikin tunaninnikan dake yawo a kwanyar ta.

                         ★★★★★★
                         5 years later
                         ★★★★★★

Cikin sauri sauri take Rolling veil ɗin a zagayayyar fuskar ta, pin ta manna a jiki bayan ta daidaita zaman mayafin sannan ta matsa daga wajen mirrorn, rashin ganin su a ɗakin yasa ta ja ƙwafa ta kwashi bags da food flask ɗin su ta fita dashi tare da jawo ƙofar ɗakin ta sa mata key.

ÆŠakin dake kusa da nata ta idasa tana É—aya labulen

"Barka da asuba Hajiya".

"Barka kadai uwar biyu, ina dai kun tashi Lafiya".

"Lafiya lau na tashi, su kam na san tuni kin san ya suke tin da sun ƙaura nan".

"Aikuwa dai muna tare da ƙawaye tun ɗazu muna gaisawa".

"Ai yayi kyau, bari mu wuce mun kusa makara, Ibty, Ifty maza ku taho mu tafi".

"To se kun dawo, Allah ya tsare ya bada Sa'a".

"Ameen Hajiya, mungode".

Daga bayan labulen Hajiya suka fito se zarar ido suke yi dan sun san sun yi ba daidai ba, ita kam bata tsaya wata wata ba ta kama hannun su a each hand É—in ta suka fita daga gidan.

Napep ta tare musu suka hau inda ta e ya kai ta Star light Academy wato makarantar yaran.

Juyowa tayi ta kalli Ibty dake gefen daman ta, da sauri yarinyar ta sunkuyar da kanta haka ma da ta kalli Ifty kafin kuma su haÉ—a baki wajen faÉ—in

"We are sorry Mamma".

Girgiza kai tayi ta maida hankalin ta batare da tayi responding masu ba

"Please kiyi haƙuri Mamma, Allah Ifty ce tace muje mu gaida Hajiya tun da baki gama da wuri ba".

"So Ifty ce yayar ki ko kece yayarta?".

"Ba zamu kuma ba, insha Allah Mamman musu".

"Allah yayi muku Albarka". Ta faÉ—a tana rungume kawun su, suma sosai suka kwanta a jikin ta suna faÉ—in ameen.
Chapter 9 · 0% Book details