Sashe 7
Anjane Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ƙura mata ido Inna tayi tana kallon yadda yarinyar ke sharar hawaye gwanin ban tausayi.
"Baki kyauta ba da kika yi aure ba tare da sanin dangin ki ba ko ya suke kuwa kuma ko me suke yi yanzu dai dubi yara kyawawa wanke hannu ka taɓa amma ana yaɓa musu baƙin fenti kamar wasu mara sa galihu.
Amma me yasa ba kuje gida da ita shugabar makarantar ta ku ta musu bayani ba?".
"Tare da ita muka je Inna sedai duk sun ƙi yadda wai se mijin yazo shi ba waya ba balle mu kira shi, shiyasa bana son yin nisa kar ya dawo be same ni ba".
"Wannan gaskiya ne, tun da haka ne me ze Hana ki zauna tare da mu zuwa ya dawo É—in se ki tafi, ina ganin ba matsala ai ko".
"Babu Inna, nagode ssae Allah ya saka muku da alkhairi ya raya muku zuri'a, amma ragowar Æ´an uwan ki zasu yadda tun da ba sani na kuka yi ba kuma naga al'adun ku da Yaren ku daban da nawa?".
"Sam kar ki damu, ba su da matsala akan haka, mu ɗin wani yanki ne na Larabawan ƙauyen Sudan, anyi yaƙe yaƙe a kusa damu har aka cimmana yasa muka haɗa kan mu da muka rage muka gudo ƙasar nan, Allah da ikon sa be nufe mu da zama a ko ina ba se nan da muka kafa wannan ɗan ƙaramin garin da kike gani, wasu daga cikin mu sun yi ilimi daga na addinin har na boko, wasu ko iya na addini ne kamar dai ni dan babana liman ne a can garin mu na ainahi".
Inna ta faÉ—a cikin alhini na tunawa da dangin su da aka kashe musu, dukiyoyin su da aka lalata wasu kuma aka kwashe.
"Allah ya jiƙan wanda suka rasu ya tsare ku ku da ke da rai ya amfanar daku".
"Ameen Æ´ata, kinga ni sunana Husaila".
"Kuma sunan ki me daÉ—i irin na Æ´an gayu, ni kam daga yau baba Husaila zan ke ce miki".
Dariya suka yi duka yayinda baba Husaila ta miƙe tare da faɗin tana zuwa ta fice.
Bata daɗe sosai ba ta dawo hannun ta riƙe da wasu garin magani a jiƙe a kofi ta miƙa mata tace ta shanye, bata yi gardama ba ta kafa kai ta shanye duk da baurin maganin, wani abu me kauri kamar koko ta bata shima a kofi da kuma garin magani shima ta sa ta shanye.
Tun daga ranar haka take bata jiƙe jiƙe dan hatta ruwan wankan ta kullum se an sa masa wasu saiwoyi da garin magani har kwana huɗu.
Shigowar baba Husaila yasa ta ɗagowa tare da cire hannun ta daga shafa ƙirjin ta da suka cicciko da ruwa da take yi ta maida hankali kan ta, yamutsa fuska tayi ganin yanzun ma dai wani haɗin ne dai sedai bata ƙi ba ta karɓa ta shiga sha tana runtse ido dan ta san komai take yi dan taimakon ta take yi da kuma ƴaƴan ta dan ita ma zata so ace tana shayar dasu tun da ba kuɗin siyan musu abu ne inganci da ze gyara jikin su ya ƙara musu lafiya gare ta ba.
Da hannu ta ringa share zufar da take yi dan damun kunun gyaɗa ne mai zafi aka sa masa magani aka baya tasha, seda ta gama tas kafin baba ta karɓi kofin ta fita dashi ta dawo hannun ta riƙe da Hassana da wata matashiya ta amsa ta fita da ita zagaye dan kowa so da ƙaunar yaran yake dan sha'awa suke bawa Kowa hatta matasan cikin su shiyasa yanzu kaya kam suna dasu gwargwado da suke siyo musu.
Ɗora mata ita tayi kan cinyar ta ita kuma ta shiga yi mata wasa yarinyar kuwa ta shiga murmushi dan har sun gane fuskar ta dan ko kuka suke tana karɓar su suke shiru musamman uwar rigima Ussaina.
"Maza bata tasha dan nasan zuwa yanzu ruwan yazo gashi nan yana ta lema ta cikin zanin ki, gyara ki bata dan tafi yar uwar ta haƙuri, in waccan acicin ta riƙe nasan ba saki zata yi ba".
Murmushi tayi dan dama baba Husaila da Ussaina basa shiri saboda rigimar ta, a hankali ta janye zanin daga ƙirjin ta tare da matsar da fuskar yarinyar gaban ta na dukan tara tara na rashin sabon abin da baka taɓa yi ba ita kuwa baba se ta fice a tunanin ta ai ta iya.
Da sauri Hassana ta cafke tana sauke ajiyar zuciya dan rabon su da nono tun rabuwar su da mahaifiyar su sati da kwanaki kenan.......................âœðŸ».
Â©ï¸ Ouummey 📚âœðŸ».
☑ï¸Ote, Comment and share please.
Ouummey 05 [ 11/27/2022 9:24 PM ]
★★★ *ANJANE* ★★★
(Rashin sani)
★★★★★★★★★
_*PAID BOOK*_
Story/written by Ouummey.
Wattpad @ouummey.
From The author of:
*HAƘORIN DARIYA*
*ƘASAR MU A YAU*
*BA NI DA LAIFI*
*SARAKI (the accused prince)*
*ABOTA CE KO SOYAYYA*
*And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK*
₦300 to the below account details
Rabiatu Abdullahi
2391368231
ZENITH BANK, screenshot and send the evidence of payment to 09013101854 or MTN recharge card o 09013101854, note VTU is not acceptable.
          FREE PAGE 005
_________________________📖 A sittin ta runtse ido tana taune leɓen ta sabida zafin da ya ziyarce ta ita kuwa Hassana da zaƙuwa take zuƙa tana sauke ajiyar zuciya har ta ƙoshi kafin ta saki.
Se lokacin ta buɗe idon ta da ya ɗan canja kala ta kalli yadda yarinyar ke numfashi a hankali a hankali tana ciccilla ƴan ƙafafuwan ta tare da wasa da hannayen ta se ta ji wani sabon farin ciki ya kamata har ma taji zafin ya tafi.
Zanin ta ta gyara a ƙirji ta miƙe ta saɓa ta a kafaɗa ta shiga jijjiga ta dan tayi gyatsa, a haka baba Husaila ta tadda ta se ta kwantar da Ussaina ta karɓi Hassana ta fita da ita a kafaɗa ita kuma ta koma ta zauna tare da ɗaukar Ussaina.
Haka ta shayar da ita itama sedai ba kamar Hassana ba Ussaina akwai ci dan se da ta daɗe kafin ta ƙoshi hakan ma se da ta canja mata ɗayan shiyasa gaba ɗaya ƙirjin nata ya ɗume da zafi.
Tun daga lokacin take shayar dasu amma duk da haka baba Husaila na haɗa musu da ƴan dabaru musamman Ussaina da ta fahimci yarinyar akwai tsotso in aka barta bata ƙi ta wuni da nono a baki ba.
Iya ƙauna da mutuntaka baba Husaila da ƴan uwan ta sun gwada mata, Abinci da abin sha bata taɓa rashin su ba, ga kula da ita da ƴaƴan ta da suke yi tun bare baba dan ko rigimar Ussaina ce ta tashi da dare bata bari ta tashi cewa take ta koma tayi kwanciyar ta ita kuma tayi ta fama har se tayi bacci tukunna hankalin ta ze kwanta.
Ruwan wankan su kuwa kullum se ta sa musu magani shiyasa alhamdulillah jikin su yayi ƙwari se fatar su da ta ɗan dafe saboda zafin ruwa da kuma kalar magani duk da yanzu sun fara sabawa da zafin ruwan.
Sannu a hankali har ta cinye wata ɗaya tare dasu basu ankara ba saboda zama da yayi daɗi, jakar ta kuwa baba ta adana mata dan ce mata tayi da su ne za'a bar ta ta shiga makarantar in taje, yadda ƴan uwan baba ke son ta ita abin har mamaki yake bata, wai yau ita Salame da kowa ke gudu itace yau ake so ko da yake ai ba ita ake so ba ƙaunar ƴaƴan ta ce ta shafe ta dan haka be kamata tayi wani kauɗi ba.
Mace ɗaya ce ta taɓa son ta a Karan kanta yadda take wato Hajiya Hadiza principal ɗin su, Allah ya sani tana son matar a ranta irin son da bata san yadda zata kwatanta shi ba.
Ta so ta a lokacin da kowa ya ƙi ta, ta bata gatan da bata taɓa zaton samu ba, a bayyane yake badan ita ba da ba zata taɓa samun damar karatun da take so ba, ita ta ɗau ɗawainiyar komai na makarantar ta, kuɗin PTA, uniform, littattafai, takalmi, Safa, abinci da komai da zata buƙata a makaranta tun da ta fara kuwa bata gaza ba har wata ɗaya da kwanaki baya da ta gama, ita kuwa ai sedai tace da ita Allah ya saka da kuma ya zame mata wajibi ta so ta.
Kallon baba Husaila dake zaune gaban ta tana mata lissafi kawai take yi yayin da idanun ta suka tara ƙwalla, kuɗi ne daga kan ƙwandala zuwa na takarda wai wanda aka haɗa mata dan tafiya makarantar su da zata yi duba mijin ta in yazo (kamar yadda tace musu).
Hannu ta sa ta share hawayen
"Dan Allah baba ki maida musu kuɗin nan kin ji, zan fa iya zuwa da ƙafa".ta faɗa murya na rawa
"Amma dai salamatu baki da kirki, ya za'a yi mutum yayi alkhairi a maida masa, to kul kar in Kuma ji ko ke kin yi hakan kin ji ko?".
Da kai ta amsa wa baba kafin ta shiga yi musu godiya da addu'a kamar Allah ne ya aiko ta har se da baban ta gaji ta fice ta bar mata É—akin.
Tuhumar kanta take kan me yasa tayi masu ƙarya gashi su kuma sun yarda da ita sun zauna da ita da zuciya ɗaya, jaddada wa kanta take Allah ma ya sani ba'a san ran ta tayi ƙaryar ba, bata so a raba ta da yaranta ne kawai.
Da wannan ta tattara kuɗin da suka tasamma dubu ɗaya ta zuba cikin jakar makarantar ta, ta kuma haɗe kayan ƴan biyu ta ninke ta zuba cikin jakar su ta rakuɓa nata kala huɗu da take dashi.
"Baki kyauta ba da kika yi aure ba tare da sanin dangin ki ba ko ya suke kuwa kuma ko me suke yi yanzu dai dubi yara kyawawa wanke hannu ka taɓa amma ana yaɓa musu baƙin fenti kamar wasu mara sa galihu.
Amma me yasa ba kuje gida da ita shugabar makarantar ta ku ta musu bayani ba?".
"Tare da ita muka je Inna sedai duk sun ƙi yadda wai se mijin yazo shi ba waya ba balle mu kira shi, shiyasa bana son yin nisa kar ya dawo be same ni ba".
"Wannan gaskiya ne, tun da haka ne me ze Hana ki zauna tare da mu zuwa ya dawo É—in se ki tafi, ina ganin ba matsala ai ko".
"Babu Inna, nagode ssae Allah ya saka muku da alkhairi ya raya muku zuri'a, amma ragowar Æ´an uwan ki zasu yadda tun da ba sani na kuka yi ba kuma naga al'adun ku da Yaren ku daban da nawa?".
"Sam kar ki damu, ba su da matsala akan haka, mu ɗin wani yanki ne na Larabawan ƙauyen Sudan, anyi yaƙe yaƙe a kusa damu har aka cimmana yasa muka haɗa kan mu da muka rage muka gudo ƙasar nan, Allah da ikon sa be nufe mu da zama a ko ina ba se nan da muka kafa wannan ɗan ƙaramin garin da kike gani, wasu daga cikin mu sun yi ilimi daga na addinin har na boko, wasu ko iya na addini ne kamar dai ni dan babana liman ne a can garin mu na ainahi".
Inna ta faÉ—a cikin alhini na tunawa da dangin su da aka kashe musu, dukiyoyin su da aka lalata wasu kuma aka kwashe.
"Allah ya jiƙan wanda suka rasu ya tsare ku ku da ke da rai ya amfanar daku".
"Ameen Æ´ata, kinga ni sunana Husaila".
"Kuma sunan ki me daÉ—i irin na Æ´an gayu, ni kam daga yau baba Husaila zan ke ce miki".
Dariya suka yi duka yayinda baba Husaila ta miƙe tare da faɗin tana zuwa ta fice.
Bata daɗe sosai ba ta dawo hannun ta riƙe da wasu garin magani a jiƙe a kofi ta miƙa mata tace ta shanye, bata yi gardama ba ta kafa kai ta shanye duk da baurin maganin, wani abu me kauri kamar koko ta bata shima a kofi da kuma garin magani shima ta sa ta shanye.
Tun daga ranar haka take bata jiƙe jiƙe dan hatta ruwan wankan ta kullum se an sa masa wasu saiwoyi da garin magani har kwana huɗu.
Shigowar baba Husaila yasa ta ɗagowa tare da cire hannun ta daga shafa ƙirjin ta da suka cicciko da ruwa da take yi ta maida hankali kan ta, yamutsa fuska tayi ganin yanzun ma dai wani haɗin ne dai sedai bata ƙi ba ta karɓa ta shiga sha tana runtse ido dan ta san komai take yi dan taimakon ta take yi da kuma ƴaƴan ta dan ita ma zata so ace tana shayar dasu tun da ba kuɗin siyan musu abu ne inganci da ze gyara jikin su ya ƙara musu lafiya gare ta ba.
Da hannu ta ringa share zufar da take yi dan damun kunun gyaɗa ne mai zafi aka sa masa magani aka baya tasha, seda ta gama tas kafin baba ta karɓi kofin ta fita dashi ta dawo hannun ta riƙe da Hassana da wata matashiya ta amsa ta fita da ita zagaye dan kowa so da ƙaunar yaran yake dan sha'awa suke bawa Kowa hatta matasan cikin su shiyasa yanzu kaya kam suna dasu gwargwado da suke siyo musu.
Ɗora mata ita tayi kan cinyar ta ita kuma ta shiga yi mata wasa yarinyar kuwa ta shiga murmushi dan har sun gane fuskar ta dan ko kuka suke tana karɓar su suke shiru musamman uwar rigima Ussaina.
"Maza bata tasha dan nasan zuwa yanzu ruwan yazo gashi nan yana ta lema ta cikin zanin ki, gyara ki bata dan tafi yar uwar ta haƙuri, in waccan acicin ta riƙe nasan ba saki zata yi ba".
Murmushi tayi dan dama baba Husaila da Ussaina basa shiri saboda rigimar ta, a hankali ta janye zanin daga ƙirjin ta tare da matsar da fuskar yarinyar gaban ta na dukan tara tara na rashin sabon abin da baka taɓa yi ba ita kuwa baba se ta fice a tunanin ta ai ta iya.
Da sauri Hassana ta cafke tana sauke ajiyar zuciya dan rabon su da nono tun rabuwar su da mahaifiyar su sati da kwanaki kenan.......................âœðŸ».
Â©ï¸ Ouummey 📚âœðŸ».
☑ï¸Ote, Comment and share please.
Ouummey 05 [ 11/27/2022 9:24 PM ]
★★★ *ANJANE* ★★★
(Rashin sani)
★★★★★★★★★
_*PAID BOOK*_
Story/written by Ouummey.
Wattpad @ouummey.
From The author of:
*HAƘORIN DARIYA*
*ƘASAR MU A YAU*
*BA NI DA LAIFI*
*SARAKI (the accused prince)*
*ABOTA CE KO SOYAYYA*
*And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK*
₦300 to the below account details
Rabiatu Abdullahi
2391368231
ZENITH BANK, screenshot and send the evidence of payment to 09013101854 or MTN recharge card o 09013101854, note VTU is not acceptable.
          FREE PAGE 005
_________________________📖 A sittin ta runtse ido tana taune leɓen ta sabida zafin da ya ziyarce ta ita kuwa Hassana da zaƙuwa take zuƙa tana sauke ajiyar zuciya har ta ƙoshi kafin ta saki.
Se lokacin ta buɗe idon ta da ya ɗan canja kala ta kalli yadda yarinyar ke numfashi a hankali a hankali tana ciccilla ƴan ƙafafuwan ta tare da wasa da hannayen ta se ta ji wani sabon farin ciki ya kamata har ma taji zafin ya tafi.
Zanin ta ta gyara a ƙirji ta miƙe ta saɓa ta a kafaɗa ta shiga jijjiga ta dan tayi gyatsa, a haka baba Husaila ta tadda ta se ta kwantar da Ussaina ta karɓi Hassana ta fita da ita a kafaɗa ita kuma ta koma ta zauna tare da ɗaukar Ussaina.
Haka ta shayar da ita itama sedai ba kamar Hassana ba Ussaina akwai ci dan se da ta daɗe kafin ta ƙoshi hakan ma se da ta canja mata ɗayan shiyasa gaba ɗaya ƙirjin nata ya ɗume da zafi.
Tun daga lokacin take shayar dasu amma duk da haka baba Husaila na haɗa musu da ƴan dabaru musamman Ussaina da ta fahimci yarinyar akwai tsotso in aka barta bata ƙi ta wuni da nono a baki ba.
Iya ƙauna da mutuntaka baba Husaila da ƴan uwan ta sun gwada mata, Abinci da abin sha bata taɓa rashin su ba, ga kula da ita da ƴaƴan ta da suke yi tun bare baba dan ko rigimar Ussaina ce ta tashi da dare bata bari ta tashi cewa take ta koma tayi kwanciyar ta ita kuma tayi ta fama har se tayi bacci tukunna hankalin ta ze kwanta.
Ruwan wankan su kuwa kullum se ta sa musu magani shiyasa alhamdulillah jikin su yayi ƙwari se fatar su da ta ɗan dafe saboda zafin ruwa da kuma kalar magani duk da yanzu sun fara sabawa da zafin ruwan.
Sannu a hankali har ta cinye wata ɗaya tare dasu basu ankara ba saboda zama da yayi daɗi, jakar ta kuwa baba ta adana mata dan ce mata tayi da su ne za'a bar ta ta shiga makarantar in taje, yadda ƴan uwan baba ke son ta ita abin har mamaki yake bata, wai yau ita Salame da kowa ke gudu itace yau ake so ko da yake ai ba ita ake so ba ƙaunar ƴaƴan ta ce ta shafe ta dan haka be kamata tayi wani kauɗi ba.
Mace ɗaya ce ta taɓa son ta a Karan kanta yadda take wato Hajiya Hadiza principal ɗin su, Allah ya sani tana son matar a ranta irin son da bata san yadda zata kwatanta shi ba.
Ta so ta a lokacin da kowa ya ƙi ta, ta bata gatan da bata taɓa zaton samu ba, a bayyane yake badan ita ba da ba zata taɓa samun damar karatun da take so ba, ita ta ɗau ɗawainiyar komai na makarantar ta, kuɗin PTA, uniform, littattafai, takalmi, Safa, abinci da komai da zata buƙata a makaranta tun da ta fara kuwa bata gaza ba har wata ɗaya da kwanaki baya da ta gama, ita kuwa ai sedai tace da ita Allah ya saka da kuma ya zame mata wajibi ta so ta.
Kallon baba Husaila dake zaune gaban ta tana mata lissafi kawai take yi yayin da idanun ta suka tara ƙwalla, kuɗi ne daga kan ƙwandala zuwa na takarda wai wanda aka haɗa mata dan tafiya makarantar su da zata yi duba mijin ta in yazo (kamar yadda tace musu).
Hannu ta sa ta share hawayen
"Dan Allah baba ki maida musu kuɗin nan kin ji, zan fa iya zuwa da ƙafa".ta faɗa murya na rawa
"Amma dai salamatu baki da kirki, ya za'a yi mutum yayi alkhairi a maida masa, to kul kar in Kuma ji ko ke kin yi hakan kin ji ko?".
Da kai ta amsa wa baba kafin ta shiga yi musu godiya da addu'a kamar Allah ne ya aiko ta har se da baban ta gaji ta fice ta bar mata É—akin.
Tuhumar kanta take kan me yasa tayi masu ƙarya gashi su kuma sun yarda da ita sun zauna da ita da zuciya ɗaya, jaddada wa kanta take Allah ma ya sani ba'a san ran ta tayi ƙaryar ba, bata so a raba ta da yaranta ne kawai.
Da wannan ta tattara kuɗin da suka tasamma dubu ɗaya ta zuba cikin jakar makarantar ta, ta kuma haɗe kayan ƴan biyu ta ninke ta zuba cikin jakar su ta rakuɓa nata kala huɗu da take dashi.