Sashe 20
Aisha Siddiqa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shiyasa fa AbdulRasheed ke matukar son Kakan nasa, yake kuma amsa kiransa a duk lokacin da ya bukaci ganinsa a ko’ina yake kuma kome yake komai muhimmancin abun zai bari yazo. Sabida a duniya ba mai son farin cikinsa irin Sarki. A daren ranar sunyi hirarraki iri-iri wadda ta shafi lafiyar Kakan nasa, da cigaban rayuwar AbdulRasheed kacokam. Wani abu da yasa Abdulrasheed yake sakewa da Kakansa yake kuma yin doguwar hira dashi saboda shi baya matsa masa akan maganar aure, kullum addu’a yake masa don ya yarda rashin auren AbdulRasheed har zuwa yanzu ba haka kawai bane, akwai dai abinda Allah ya boye a ciki, ko dai aljana ta aureshi, ko kuma akwai wani boyayyen dalili da kowa bai sani ba. Bayan sunyi sallama da Kakan kan zai je ya kwanta, kafin AbdulRasheed ya kai ga isa turakarsa dake gidan sarautar Ilorin, Kawunsa Turaki, wato mai bin mahaifinsa a haihuwa ya aiko ace dashi lallai suna son ganin shi su duka gobe (kannen mahaifinsa Akanni’s gabadayansu) kafin ya koma Qatar. Tun daga nan AbdulRasheed ya sha jinin jikinsa, cewa ganawa ce ta musamman iyayen nasa maza zasu hada a kansa, ayi masa taron dangi a titsiyeshi kuma ba’a kan komai ba sai akan maganar aure da baya ko son jin an alaqanta shi da ita. Ya so ya gudu cikin daren kafin wayewar garin, to ‘booking’ dinsa sai akayi rashin sa’a na jibi talata ne. Haka yayi ta kokarin canza ‘booking’ don dai ya samu ya kubucewa wannan haduwar wadda yasan bazata yi masa dadi ba, Akannis sun gama zura masa ido da bata yawun bakinsu akan maganar aurensa, duk yadda yayi kokarin barin Ilorin a daren don gujewa fushin iyayensa maza bai samu damar hakan ba. A washegari mahaifin Prince wato Engnr. Idrees Akanni da shima suka gayyato don ayi zaman tare dashi ya iso Ilorin, a ranar taron ya iso don ta jirgin sama ya taho daga Lagos. **** **** **** THE TEN AKANNIS’ S u goma dinnan, wato kannen mahaifinsa da mahaifin nasa haka suka saka shi a tsakiya yau suka zagayeshi a fadar Maimartaba Sarkin Ilorin, akan yau ba inda zaije sai ya gaya musu ‘exactly’ me ya hana shi aure a rayuwarsa? Duk kannensa na cikin family dinsu sunyi aure, ga albarkar ‘ya’ya, daga mai yara hudu sai mai biyar. Wannan masifa a cewar Akanni’s, sun kasa gane mata. Yo masifa mana?! Rashin aure babu dalili wanda addini ya yarda dashi ga mai shekaru sama da 40 ya zama masifa a cikin zuri’arsu. Suka hada baki wajen cewa “bazasu amince ya bata musu ‘image’ na gidansu da maluntarsu ba, don kawai ya ga Sarki yana daure masa gindi yana abinda yaga dama, ba don komai ba sai don yana gudun bacin ransa. Suka ce Sarki yafi kowa damuwa da son yayi aure ya dauki ’ya’yansa yana raye, kawai baya nuna masa ne don ya ga baya so, amma su sun sani, Sarki baida damuwa a halin yanzu sai ta rashin aurensa, suka taru akan cewa bazai kashe musu tsoho da damuwa ba dole ya bashi tattaba kunne ya dauka yana raye. Mutawalle Abdulfatahi ya ce “idan macece bai samu ba, su iyayensa maza zasu bashi ko guda nawa yakeso a cikin ‘ya’yansu mata matasa da basu kai ga yin aure ba. Idan kuma baya son auren gida, ya fadi duk diyar Sarkin da yake so a masarautun Najeriya, na kudu dana arewa, su kuma za suje su auro masa. In kuma lafiyar yin aure ce bashi da ita, itama yau dai sunaso su sani, zasu shiga ko’ina su fita daga nan har birnin Sin, su nema masa magani, su iyayensa ne da suka haifeshi, ya yarda cewa babu boye-boye yau a tsakaninsu. Tunda ya nuna Ubansa wato Waziri bai isa dashi ba, saboda Polo da abunda yake samu cikinta dake rudarsa, suka ce to Waziri Idreesu ya basu dama su yanke masa duk hukuncin da suka ga ya dace da shi yanzu. Su kuma a adalci irin nasu da Allah yace musu su yiwa ‘ya’yan su, bazasu yanke masa kowanne hukunci ba, sai sun bashi dama sun ji ta bakinsa tukunna, wato sai sun ji hujjarsa ta kin yin aure daga bakinsa. Alhalin mahaifinsa nada shekaru 25 mahaifiyarsa Sappa nada 15 aka yi musu aure, wanda albarkar hakan ne har suka sameshi cikin kuruciyarsu suka girma tare dashi. Shi yau Abdulrasheed shekaru 43 yake nema, me kuma ya rasa a rayuwarsa? The Akannis’ suka kara da cewa; wannan rashin auren nasa masifa ce babba a garesu da zuri’arsu. Suka kuma rufe zancen da cewa, “idan har bashi da hujjar kin yin aure, bashi kuma da wadda ta kwanta masa da yake ganin zai iya aure, gobe-goben nan zasu aura masa mata hudu, akai masa su gidan sa, kuma sun yi rantsuwa da Allah dole ya zauna dasu gabadaya in yana son albarkarsu, bijirewa wannan umarnin na nufin zasu cireshi cikin ‘ya’yansu tunda dai Allah yasa ba shikadai suka haifa ba. Shine babba cikin family duka, amma yafi duk kannensa basu wahala akan maganar aure da janyo musu magana daban-daban daga al’ummarsu duk akan rashin aurensa”. Prince AbdulRasheed Idris Akanni, tunda iyayensa suka fara wannan cece ku ce din yake sauraronsu, ya rasa irin amsar da zai bayar da zata gamsar da iyayensa maza hujjarsa ta gudun aure a yau. Cewa mata sun dade da sire masa, bashi da wani buri a kan diya mace yanzu, ba macen da zai kara so a rayuwarsa. Shin shi mai maganar cewa yazo ga kannensa nan a gida ya bashi wato, Abdulfatahi Akanni, yanada masaniyar cewa dansa ne ya raba shi da mata bakidayansu??? Ko yanada masaniyar cewa dansa Adetokumbo ne yayi masa cin amanar data sa ya tsani mata koda gold aka kerasu tun daga kan Hasinah Ambursa??? He is speechless a lokacin, sai zufa, jibi, da gumi da yake ta yankawa daga zaune cikin kurkukun idanun iyayensa da suke zazzare masa su daya bayan daya irin nasu na jiga-jigan yarbawa. Da suka takura da jin ta bakinsa sai yace musu yana jin nauyin dukkanninsu, su yi masa alfarma ya gayawa Nenne amsarsa in yaso ta gaya musu. Ganin irin halin da ya shiga ne na rudu mai yawa da gigita yasa suka kyaleshi, domin sun tado masa kwantaccen bacin ransa, aka yi addu’a aka rufe taron a haka. Suka ce lallai a gobe suna jiran jin amsa daga bakin Nennensa, in ba haka ba, zasu dauki matakin da ya dace ne kawai wanda shine aura masa kannensa mata hudu kuma a rana daya daga cikin ‘ya’yansu mata. Ita kanta Nenne din zille mata yayi ta yi basu hadu ba har ya koma Qatar. Ya san kuma bazata jira zuwansa ba don a ranar da asubah zata tashi zuwa pilgrimage (aikin hajji) daga hukumar alhazai ta jihar Lagos, kuma in ta tafi Hajj sai tayi kwanaki arba’in wato jirgin karshe sannan take dawowa gida. Kafinnan ya samu ya yanke mai fishsheshi, su kuwa kannen Ubansa yasa a ransa bazasu kara ganinshi nan kusa ba. Bayan tashin Nenne zuwa Hajj, ya koma Qatar, ya cigaba da fuskantar aikin sa na (Oil Refinery), wata irin rayuwa Prince Abdulrasheed keyi ta cikawa kai aiki a gida da ofis da daukewa kai kewa a ‘stable’ din dawakansa a kowanne yammaci ta hanyar bankawa cikinsa Nescafe (coffee) alhalin likita yayi limiting shan (coffee) dinsa, a cewarsa in ya sha yana jinsa fresh babu damuwa ko kankani a cikin ransa, shan coffee yana kara masa kuzari, kwana biyu dai bai hau Doki ba don har zuwa lokacin hadewar karayar jikin sa bata bar dan motsa masa lokaci zuwa lokaci ba. **** **** **** ZAMAN HEMAR ALHAZAI A MINNA N enne Sappa, ta sauka a kasar Saudiyyah domin sauke farali na wannan shekarar tare da diyarta autarta Princess Firdausi. A zaman Hema ne na kwana uku da ake yi a Minna, ana zuwa jifan shaidan ana dawowa Hema a huta ko ayi kwanan ibada, Nenne ta hadu da Haj. Zainab. Wadda tazo daga jihar Gombe, maigidanta Malam Yunus ma’aikacin hukumar alhazai na jihar Gombe. Ba Hemar su daya ba, don kamar yadda kowa ya sani ne Hema din (is state by state), Haj. Zainab na Hemar Alhazan Gombe, Nenne tana Hemar Alhazai Yarbawa na jihar Lagos. Wajen tafiya jifan Shaidan ne suka tafi tare, tafiya ce da alhazai ke yi mikakka wadda bata karewa kamar bata da karshe, zuwa inda za’a jefi la’anannen Allah. Suna tafiya suna Hailala, Princess Firdausi bata biyo su ba yau, tana kwance a Hema domin rashin tsarki da ya sameta a ranar. Jiki na girma, tafiya tayi tafiya sai Haj. Zainab taga Nenne na neman faduwa, domin ba karamin jigata tayi ba. Sai ta kama hannun Nenne, ta karfafeta, tace “baiwar Allah don Allah mu dan tsaya mu sha zam-zam ko ma samu karfin cigaba da tafiya.” Nenne tace “kin kyauta diyata, ni fitsari ma nake ji”. Suka sha zam-zam suka koshi, suka zagaya bayan wata Hema don shiga bayan gida. Nenne Sappa ita ta fara shiga ta fito ta gama zata wuce ba tareda ta jira Haj. Zainab ta shiga ba, don dama ba wai tare suke tafiyar ba a’ah, hanya ce kawai mai hadin zumuntar dole. Da ta fito, bayan sun yi sallama ta kuma gode mata bisa kulawar data nuna mata. Har ta gaya mata ita daga Lagos tazo, ita kuma tace mata daga Gombe tazo. “Ashe ‘yar kasata ce, madallah dake. Nima asalina ‘yar Gombe ne, aure ne ya kaini jihar Lagos”. Sukayi sallama, Nenne ta wuce ta cigaba da tafiyar ibadah, Haj. Zainab kuma ta shiga toilet din. Har ta gama abinda zatayi ta fito, ta lura da bakar jakar nan ta guzurin mahajjata ta matar can ‘yar Lagos rataye a jikin kofar bandakin. Wato ta manta guzurinta gabadaya. Ta dauka ta bude, yawan dalolin data gani ‘yan dari-dari a ciki ya firgitata, domin ya zarce normal dalolin guzurin mahajjata da ake basu, daloli ne tsura abin tsoro da firgitarwa, domin ita dai da idonta bata taba ganin irin wadannan takardun kudin a zahiri ba. Da sauri Haj. Zainab ta fito ta duba hagu da dama, gabas da yamma, kudu da arewa babu Hajiyar lagos babu alamarta, ta bace a cikin dubunnan mahajjata masu