Sashe 8
A Dalilin Da Namiji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Maganata ta qarshe akan wannan qungiya taku shi ne, wallahi ko da zan yi yawo tsirara saboda tsammanin talauci ba zan tava yin qazantacciyar rayuwa irin ta qungiyarku ba, kuma a cikin ‘yan matan da nake tare dasu ma babu wacce za ku samu hadin kanta. Don haka ki tattara tsufanki ki qara gaba, kuma kar ki qara cewa kina so na idan ba haka ba sai na zubar miki da haqora.”
Ina gama fadin haka na katse wayata ina numfarfashin fusata, Rintse ido na yi na kwanta a kan kujeran da nake zaune, minti biyu tsakani duk suka fara sulalewa zuwa dakunansu.
“Zo mu tafi dakina Fatima, duk abin da ba ki gane ba sai in qarasa amsa miki.”
Rahama ce ta furta hakan, sannan ta janye hannun Fatima suka nufi dakinta, tsawon minti goma sha biyar ina kwance idanuna a runtse daga bisani na miqe na nufi dakina.
“Tsawon wani lokaci kenan da kafuwar wannan qungiya taku?” Fatima ta tambayi Rahama bayan ta zauna a kan kujeran dressing mirror.
“Wata shida kenan.”
Rahama ta amsa mata batan ta zauna a gefen gado.
“Bani tarihin Aysha mana”
Sai da ta yi murmushi sannan ta amsa mata da cewa
“Duk gidan nan ba wacce ta san tarihin Aysha, ko wani lokaci idan ta yi niyyar fada mana sai wani abin ya taso kamar dai yanda ya faru yau, amma duk mun qosa qwarai mu ji tarihinta, bayan sunanta da shekarunta babu wani abu da muka sani a kanta.”
“Shekarunta nawa?”
Fatima ta sake tambayarta.
“Sati biyu ya rage ta shiga shekaru goma sha bakwai.”
Shiru ya ratsa tsakaninsu harna tsawon minti biyu, kowacce a cikinsu da irin saqe-saqen da take yi a zuciyarta.
“Amma kun san tana shan kayan maye?”
Fatima ta sake tambayarta fuskarta na bayyana damuwa da jimami.
“Qwarai kuwa, duk gidan nan mun san haka, a taqaice ma ba ta iya barci in dai ba ta sha kayan mayen ba. wannan yana daya daga cikin dalilin da yasa duk gidan nan muka qosa mu ji tarihinta, akwai abubuwa masu matuqar ban mamaki da daure kai a tattare da ita. Karamin misalin da zan baki shi ne dukkanmu babu wacce ta bata tarihinta da kanta, daga haduwarta dani ta karanto min tarihina daga farko har qarshe, kuma duk sauran ‘yan matan hakan ta kasance dasu, kema ranar da aka yanke miki hukunci ita ta karanta mana tarihinki.”
Ajiyar zuciya ta sauke tana qara jinijna abin a cikin ranta, can kuma ta yi qarfin halin fadin “Wannan gidan qasan da kuke rayuwa a ina kuka samu kudin ginawa?”
Sai da Rahama ta qyalqyale da dariya sannan ta fara tunanin tsarin gidan nasu da Fatima ta radawa gidan qasa.
Daga can kofar gidan dai shi kadai ne kwal a tsakiya dajin, sai ka yi tafiya mai nisa kafin ka tadda wani gida a can gaba. Get ne mai matuqar kyau da girma a jikin qofar gidan, katanga ne mai tsananin tsawo wanda duk wayon barawo bai isa ya tsallakaba, idan ka shiga harabar gidan, rumfuna ne aka yi gurin adana motoci a ko wani kusurwa na harabar gidan. Daga can tsakiya aka yi ginin wani daki wanda shi kadai ne qwallin qwal a duk girman harabar gidan, ko wani rumfa motoci ne guda hudu, sai daga gefe aka jera mashinai ‘wayyo kudina' guda goma. Motoci masu matukar kyau da tsada guda goma sha biyu ne a gidan.
Idan ka bude wannan dakin da yake tsakiyar gidan babu komai a ciki sai wani hanya a tsakiyar dakin daya gangara yayi kasa an jera matakala tamkar dai gidan sama amma wannan ne qasa ne, idan ka miqe zuwa kasan matakalan ba inda za ka tsinci kanka sai a wani qaton falo mai matuqar girma da qyatuwa, an zuba duk wani kayan more rayuwa da ake bukata, a cikin falon akwai dakuna guda guda goma sha biyu, ako wani daki akwai bayi aciki, daga can gefe aka yi kichin hade da sitor dauke da katan-katan na lemuka da buhu-buhu na abinci, a takaice tsaruwar gidan ya wuce in bayyanashi a wannan dan qanqanin littafin.
Ajiyar zuciya ta saki bayan ta gama tunanin tace,
“Duk girman gidan nan da duk wani kayan alatu da siturun da muke sakawa mallakin Aysa ne, yanda kika ga gidan nan mu ma haka muka tarar da shi.”
“Tabxijan!”
abin da Fatima ta iya furtawa kenan sannan ta zabga uban tagumi da hannu biyu.
***
Qarfe biyar da minti ashirin da bakwai muka yi parking din motocinmu a qofar ‘MANGAL PLAZA’ Siyama, Rahama, Safiyya mota daya suka hau, Sadiya, Suhaila, Nafisa suka hau mota daya.
Farar mota kirar marsandi na hau, kamar yanda duk kayan jikina farare ne, wandon jeans ne wanda ya dan kamani daga sama ta kasan kuma sayya bude, T. shirt din dana saka ita ma fara ce an rubuta ‘Baby’ da golden colour a gaban rigar, ban sanya hula ba illa wani farin qyalle dan siriri dana daura a saman kaina zuwa qeyata na fitar da gashin kaina mai matuqar kyau da tsawo ya bazu har saman kafadata, a saman qyallen dana daura an rubuta ‘Azzahara’u’ da qananan rubutu ruwan golden ta gaban goshi.
"kin yi kyau matuqa….. amma a hakan za ki fia?” abin da Fatima ta ce min kenan lokacin da muke gab da fitowa daga gida.
Murmushi kawai na yi mata kamar yanda yanzu ma nake murmusawa bayan na tuno abin da ta ce min, ni ce a gaba sauran ‘yan matan suka rufa min baya, muka nufi cikin qaton kantin.
Tun kafin ya daidaita fakin din motarshi a harabar gurin yaga fitowarta daga cikin motar, “Tabbas ita ce” ya fadi hakan a zuciyarshi, kwanaki biyar kenan ya taba haduwa da ita da sauran ‘yan uwanta a ‘check point’, a lokacin ba a mota ya gansu ba, a kan mashina ‘wayyo kudi na’ ne sun goya junansu, abin da ya baiwa duk mutanen gurin mamaki shine, a dokar da yayi tsanani a garin Kaduna shi ne matuqar kana kan mashin idan ka je check point sai dai ka sauka ka tura mashin din har ka wuce sojoji, sannan ka hau ka cigaba da tafiya, Sukam kansu tsaye suke ratsa tsakanin motocin, a lokacin yana can tsallaken titi a tashi motar yana jiran layi ya zo kanshi, Har sun sa kai zasu wuce sojojin biyu suka dakatar dasu a fusace.
A lokacin bai yi tsammanin mata bane don sun sanya hular kwano duk sun rufe fuskokinsu, dakatar dasu din da aka yi ya sanya wacce take gaba ta sanya hannu ta sabule hular kwanon da yake kanta, sai su ma sauran mahaya mashin din wanda suke biye da ita suka fara sabule hulunan kwanon da suke sanye a kawunansu.
Kanannadadden gashin kai mai matuqar kyau da sheqi da tsawo shi ya fara bayyana daga bisani kyakkyawar fuskarta ta biyo baya, idanunta a lumshe tsawon daqiqa goma sannan ta bude su tana kallon sojojin bayan ta qawata fuskarta da murmushi, da hannunta daya ya ga ta yi musu alamar ya aka yi? bakinta yana motsi a hankali, ya ga alamar ta qara furta wata kalmar amma bai fahimci abinda tace ba.
Nan take ya ga sojojin sun yi musu umarnin wucewa ba tare da wani daukar mataki ba, harda karin Sara mata, sannan suka bi ta kallo ido da hanci bude.
Wannan abinda ya faru yaba duk wani wanda ya ke tsaye a gurin matuqar mamaki, A lokacin ya yi tunanin ita din ‘yar gidan wani babban kusa ne a garin Kaduna, tun ranar fuskarta ya qi bacewa daga idanunsa…
“Abdul-Ahad tunanin me kake yi?”
Yasmin da take zaune a gefenshi ta tambayeshi fuskarta ba walwala ko kadan, bayan ta lura da kallon da ya bi ‘yan matan da suka shige cikin kantin da shi.
Murmushi ya jefeta da shi don kwantar da hankalinta daga bisani ya yi qarfin halin fadin “Babu komai, kaina ne yake dan sara min.”
Kallon rashin yarda ta bi shi da shi na tsawon daqiqu sannan ta ce, “Kar dai ka manta watanni shida nan gaba za a daura mana aure, kuma zan iya yin komai ciki kuwa har da kisa ga duk yarinyar da ta nemi rabani da kai, ko da kuwa kai ne ka ce kana sonta.”
Tana gama fadin haka ta bude qofar mota ta fita ta jingina da motar tana jiran fitowarshi.
Share gumin goshinshi yayi sannan ya gyara zaman tabaran da yake sanye a idanunsa ya fito daga motar jikinsa ya yi matuqar sanyi, kai tsaye kantin da ‘yan matan suka shiga ta ja hannunsa suka nufi ciki.
***
Tun daga nesa rigar take daukar hankalina, don haka na qarasa da nufin in dauko ta duk da dai kalar yellow bai cika burgeni ba, dora hannuna akan rigar ke da wuya na ga wani hannu ya riqe rigar, daga faratan kantin masu matuqar tsawo da suke sanye a kunbunan hannun na gane mace ce, sakin rigar nayi na kara gaba ba tare ko fuskarta na kalla ba.
Sai da ta yi qwafa saboda takaici, ta so a ce na tanka mata ta yi min wulaqanci a gaban Abdul don ya tabbar ba cika baki take a kanshi ba, za ta iya aikata duk abinda ta ce za ta aikata a kan soyayyarshi. Don haka ba ta haqura ba ta ci gaba da bin duk inda na nufa.
Hantar cikinshi sai da ta kada saboda tsabar tsorata, lokacin da ya yi arba da hannun Yasmin damqe da rigar da na fara dauka, a zatonshi zan tanka mata, amma wani abin armashi da birgewa a tattare da ni shine kallon ta ban yi ba na sakar mata rigar na yi wucewa ta.
Ganin ta nufi hanyar da na bi ya sa ya fara addu’ar Allah ya sa ba abinda zai faru har sai sun gama abinda ya kawo su su fice, don ya san Yasmin tamkar yunwar cikinshi, fitinanniya ce ta gaban kwatance.
Ina gama fadin haka na katse wayata ina numfarfashin fusata, Rintse ido na yi na kwanta a kan kujeran da nake zaune, minti biyu tsakani duk suka fara sulalewa zuwa dakunansu.
“Zo mu tafi dakina Fatima, duk abin da ba ki gane ba sai in qarasa amsa miki.”
Rahama ce ta furta hakan, sannan ta janye hannun Fatima suka nufi dakinta, tsawon minti goma sha biyar ina kwance idanuna a runtse daga bisani na miqe na nufi dakina.
“Tsawon wani lokaci kenan da kafuwar wannan qungiya taku?” Fatima ta tambayi Rahama bayan ta zauna a kan kujeran dressing mirror.
“Wata shida kenan.”
Rahama ta amsa mata batan ta zauna a gefen gado.
“Bani tarihin Aysha mana”
Sai da ta yi murmushi sannan ta amsa mata da cewa
“Duk gidan nan ba wacce ta san tarihin Aysha, ko wani lokaci idan ta yi niyyar fada mana sai wani abin ya taso kamar dai yanda ya faru yau, amma duk mun qosa qwarai mu ji tarihinta, bayan sunanta da shekarunta babu wani abu da muka sani a kanta.”
“Shekarunta nawa?”
Fatima ta sake tambayarta.
“Sati biyu ya rage ta shiga shekaru goma sha bakwai.”
Shiru ya ratsa tsakaninsu harna tsawon minti biyu, kowacce a cikinsu da irin saqe-saqen da take yi a zuciyarta.
“Amma kun san tana shan kayan maye?”
Fatima ta sake tambayarta fuskarta na bayyana damuwa da jimami.
“Qwarai kuwa, duk gidan nan mun san haka, a taqaice ma ba ta iya barci in dai ba ta sha kayan mayen ba. wannan yana daya daga cikin dalilin da yasa duk gidan nan muka qosa mu ji tarihinta, akwai abubuwa masu matuqar ban mamaki da daure kai a tattare da ita. Karamin misalin da zan baki shi ne dukkanmu babu wacce ta bata tarihinta da kanta, daga haduwarta dani ta karanto min tarihina daga farko har qarshe, kuma duk sauran ‘yan matan hakan ta kasance dasu, kema ranar da aka yanke miki hukunci ita ta karanta mana tarihinki.”
Ajiyar zuciya ta sauke tana qara jinijna abin a cikin ranta, can kuma ta yi qarfin halin fadin “Wannan gidan qasan da kuke rayuwa a ina kuka samu kudin ginawa?”
Sai da Rahama ta qyalqyale da dariya sannan ta fara tunanin tsarin gidan nasu da Fatima ta radawa gidan qasa.
Daga can kofar gidan dai shi kadai ne kwal a tsakiya dajin, sai ka yi tafiya mai nisa kafin ka tadda wani gida a can gaba. Get ne mai matuqar kyau da girma a jikin qofar gidan, katanga ne mai tsananin tsawo wanda duk wayon barawo bai isa ya tsallakaba, idan ka shiga harabar gidan, rumfuna ne aka yi gurin adana motoci a ko wani kusurwa na harabar gidan. Daga can tsakiya aka yi ginin wani daki wanda shi kadai ne qwallin qwal a duk girman harabar gidan, ko wani rumfa motoci ne guda hudu, sai daga gefe aka jera mashinai ‘wayyo kudina' guda goma. Motoci masu matukar kyau da tsada guda goma sha biyu ne a gidan.
Idan ka bude wannan dakin da yake tsakiyar gidan babu komai a ciki sai wani hanya a tsakiyar dakin daya gangara yayi kasa an jera matakala tamkar dai gidan sama amma wannan ne qasa ne, idan ka miqe zuwa kasan matakalan ba inda za ka tsinci kanka sai a wani qaton falo mai matuqar girma da qyatuwa, an zuba duk wani kayan more rayuwa da ake bukata, a cikin falon akwai dakuna guda guda goma sha biyu, ako wani daki akwai bayi aciki, daga can gefe aka yi kichin hade da sitor dauke da katan-katan na lemuka da buhu-buhu na abinci, a takaice tsaruwar gidan ya wuce in bayyanashi a wannan dan qanqanin littafin.
Ajiyar zuciya ta saki bayan ta gama tunanin tace,
“Duk girman gidan nan da duk wani kayan alatu da siturun da muke sakawa mallakin Aysa ne, yanda kika ga gidan nan mu ma haka muka tarar da shi.”
“Tabxijan!”
abin da Fatima ta iya furtawa kenan sannan ta zabga uban tagumi da hannu biyu.
***
Qarfe biyar da minti ashirin da bakwai muka yi parking din motocinmu a qofar ‘MANGAL PLAZA’ Siyama, Rahama, Safiyya mota daya suka hau, Sadiya, Suhaila, Nafisa suka hau mota daya.
Farar mota kirar marsandi na hau, kamar yanda duk kayan jikina farare ne, wandon jeans ne wanda ya dan kamani daga sama ta kasan kuma sayya bude, T. shirt din dana saka ita ma fara ce an rubuta ‘Baby’ da golden colour a gaban rigar, ban sanya hula ba illa wani farin qyalle dan siriri dana daura a saman kaina zuwa qeyata na fitar da gashin kaina mai matuqar kyau da tsawo ya bazu har saman kafadata, a saman qyallen dana daura an rubuta ‘Azzahara’u’ da qananan rubutu ruwan golden ta gaban goshi.
"kin yi kyau matuqa….. amma a hakan za ki fia?” abin da Fatima ta ce min kenan lokacin da muke gab da fitowa daga gida.
Murmushi kawai na yi mata kamar yanda yanzu ma nake murmusawa bayan na tuno abin da ta ce min, ni ce a gaba sauran ‘yan matan suka rufa min baya, muka nufi cikin qaton kantin.
Tun kafin ya daidaita fakin din motarshi a harabar gurin yaga fitowarta daga cikin motar, “Tabbas ita ce” ya fadi hakan a zuciyarshi, kwanaki biyar kenan ya taba haduwa da ita da sauran ‘yan uwanta a ‘check point’, a lokacin ba a mota ya gansu ba, a kan mashina ‘wayyo kudi na’ ne sun goya junansu, abin da ya baiwa duk mutanen gurin mamaki shine, a dokar da yayi tsanani a garin Kaduna shi ne matuqar kana kan mashin idan ka je check point sai dai ka sauka ka tura mashin din har ka wuce sojoji, sannan ka hau ka cigaba da tafiya, Sukam kansu tsaye suke ratsa tsakanin motocin, a lokacin yana can tsallaken titi a tashi motar yana jiran layi ya zo kanshi, Har sun sa kai zasu wuce sojojin biyu suka dakatar dasu a fusace.
A lokacin bai yi tsammanin mata bane don sun sanya hular kwano duk sun rufe fuskokinsu, dakatar dasu din da aka yi ya sanya wacce take gaba ta sanya hannu ta sabule hular kwanon da yake kanta, sai su ma sauran mahaya mashin din wanda suke biye da ita suka fara sabule hulunan kwanon da suke sanye a kawunansu.
Kanannadadden gashin kai mai matuqar kyau da sheqi da tsawo shi ya fara bayyana daga bisani kyakkyawar fuskarta ta biyo baya, idanunta a lumshe tsawon daqiqa goma sannan ta bude su tana kallon sojojin bayan ta qawata fuskarta da murmushi, da hannunta daya ya ga ta yi musu alamar ya aka yi? bakinta yana motsi a hankali, ya ga alamar ta qara furta wata kalmar amma bai fahimci abinda tace ba.
Nan take ya ga sojojin sun yi musu umarnin wucewa ba tare da wani daukar mataki ba, harda karin Sara mata, sannan suka bi ta kallo ido da hanci bude.
Wannan abinda ya faru yaba duk wani wanda ya ke tsaye a gurin matuqar mamaki, A lokacin ya yi tunanin ita din ‘yar gidan wani babban kusa ne a garin Kaduna, tun ranar fuskarta ya qi bacewa daga idanunsa…
“Abdul-Ahad tunanin me kake yi?”
Yasmin da take zaune a gefenshi ta tambayeshi fuskarta ba walwala ko kadan, bayan ta lura da kallon da ya bi ‘yan matan da suka shige cikin kantin da shi.
Murmushi ya jefeta da shi don kwantar da hankalinta daga bisani ya yi qarfin halin fadin “Babu komai, kaina ne yake dan sara min.”
Kallon rashin yarda ta bi shi da shi na tsawon daqiqu sannan ta ce, “Kar dai ka manta watanni shida nan gaba za a daura mana aure, kuma zan iya yin komai ciki kuwa har da kisa ga duk yarinyar da ta nemi rabani da kai, ko da kuwa kai ne ka ce kana sonta.”
Tana gama fadin haka ta bude qofar mota ta fita ta jingina da motar tana jiran fitowarshi.
Share gumin goshinshi yayi sannan ya gyara zaman tabaran da yake sanye a idanunsa ya fito daga motar jikinsa ya yi matuqar sanyi, kai tsaye kantin da ‘yan matan suka shiga ta ja hannunsa suka nufi ciki.
***
Tun daga nesa rigar take daukar hankalina, don haka na qarasa da nufin in dauko ta duk da dai kalar yellow bai cika burgeni ba, dora hannuna akan rigar ke da wuya na ga wani hannu ya riqe rigar, daga faratan kantin masu matuqar tsawo da suke sanye a kunbunan hannun na gane mace ce, sakin rigar nayi na kara gaba ba tare ko fuskarta na kalla ba.
Sai da ta yi qwafa saboda takaici, ta so a ce na tanka mata ta yi min wulaqanci a gaban Abdul don ya tabbar ba cika baki take a kanshi ba, za ta iya aikata duk abinda ta ce za ta aikata a kan soyayyarshi. Don haka ba ta haqura ba ta ci gaba da bin duk inda na nufa.
Hantar cikinshi sai da ta kada saboda tsabar tsorata, lokacin da ya yi arba da hannun Yasmin damqe da rigar da na fara dauka, a zatonshi zan tanka mata, amma wani abin armashi da birgewa a tattare da ni shine kallon ta ban yi ba na sakar mata rigar na yi wucewa ta.
Ganin ta nufi hanyar da na bi ya sa ya fara addu’ar Allah ya sa ba abinda zai faru har sai sun gama abinda ya kawo su su fice, don ya san Yasmin tamkar yunwar cikinshi, fitinanniya ce ta gaban kwatance.