Sashe 5
A Dalilin Da Namiji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta jikin katangar nake leqan abinda yake faruwa, ganin suna bata mana lokaci yasa na yi bismillah na saita qafafun mutum biyu daga cikinsu na harbe su a qafa da bindigogin da sike riqe a hannuna dama da hagu.
Nayi nasarar samun su, hakan ne ya ankarar da sauran mutum hudun daga inda harbin ya fito, wani ragon azanci da suka yi sai dukkansu suka biyo bangaren katangar da nake cikin sanda suna haska tocila, su Rahma ne suka miqe da hanzari suka dauki bindigogin ‘yansandan da suke kwance suna kici-kicin kwance qafafunsu suka harbi ‘yan sandan a qafafunsu ba tare da sun ankara ba.
Da sauri duk muka bi su muka shaqa musu hodar da take hannun Sadiya minti biyu tsakani nannauyan barci ya yi awon gaba da su. Mu kuma muka shiga cikin gidan hankali kwance. Don muna da tabbacin ba za su farka ba sai sun xauki tsawon awa goma sha biyu suna barci.
Mabudi ne da yake bude kowane irin kwado mukayi amfani dashi gurin bude dakin da take ciki, don haka ba mu sha wahalar bude dakin ba, suna tsaye cirko-cirko tamkar kajin da suke fada Sun tsaya maida numfashi.
Ganin shigowarmu ya sa suka nufo mu suna zazzaro ido. Kallon sakan biyar ya ratsa tsakaninmu, da alamun mamakin yadda muka shigo cikin gidan har muka bude dakin da suke ciki, ba tare da mun fuskanci matsala daga masu gadin gidan ba suke yi,mu kuma kallonsu muke don tanrance wace ce Fatima a cikinsu? Can kusurwar dakin na hangi wata ta takura kanta a tsakanin cinyoyinta.
Da hanzari na nufi gurinta don jikina na ba ni tabbacin ita ce Fatima. Hannu na sa na dafa kafadarta bayan na durqusa kusa da ita.
Da sauri ta dago kanta a dan firgice take kallo na sannan ta maida dubanta zuwa ga su Safiyya.
“Wace ce ke? Ku su waye?" Ta tambayi hakan bakinta na rasa, idanunta a warwaje, wadanda suka kumbura kuma suka rine zuwa jajaye, saboda tsabar kuka.
“Mu ‘yan’uwanki ne, kuma mun zo mu tafi da ke ne.” Na fada mata hakan da tattausar murya don in kwantar mata da hankali.
Kallo ta bi ni da shi na rashin yarda da abinda na fada. Dagabisani kuma ta ce “Ban san ku ba, don haka ba zan taba bin ku ba. ku bar ni kawai. Haka Allah ya qaddara zan qarasa rayuwata a gidan yari…”
tana gama fadinn haka ta fashe da kuka, sannan ta qara maida kanta tsakanin cinyoyinta, kamar yadda muka tarar da ita da farko.
Muna da tabbacin za mu fuskanci tirjiya daga gare ta, don haka ranmu bai vaci ba ko kadan. Da yatsu biyu na kira su Rahma zuwa gare mu, sannan na qara dafa kafadarta a karo na biyu. Hawaye ne wasu na korar wasu tamkar ruwa suke bin kyakkyawar fuskarta. Ban ba ta damar fadin komai ba nace, “Ga wannan tocilan ki haska bayan rigarmu ki ga me aka rubuta.” Na miqa mata tocilan hannuna, sannan duk muka jujjuya bayan rigarmu zuwa gare ta.
Tsawon minti uku kafin na jiyo muryarta na faxin, “na amince zan bi ku.”
Da matuqar murna na rungume ta, sannan na kama hannunta duk muka nufi hanyar ficewa daga dakin.
“Ku taimaka don Allah ku fitar da mu gaba daya.”
Muka jiyo muryar wasu daga cikin fursunonin suna fadin haka.
“Kofa a bude take ga duk wanda ya yi niyyar fita, amma mu dai ga wacce muka zo dauka nan.” Ina gama fadin haka muka fice da sauri don ganin lokaci yana dad'a qurewa.
Karfe uku da minti biyu muka isa gida, Sadiya ce ta dauki dan muqullin qofar get din a cikin mota ta bude mana aka shiga da motar. Baba tana zaune a falo kamar yadda ta saba idan muka fita komai tsawon dare bata kwanciya barci sai ta ga dawowarmu, Yau ma hakan ce ta kasance. Tana zaune da casbaha a hannunta tana lazumi muka shiga cikin falon.
Fatima ta nufa kai tsaye bayan ta amsa sallamarmu, da fara’arta ta tarbe ta sannan ta yi mana barka da zuwa.
“Abinci kike buqata, ko wanka za ki fara yi ko sallah?” Duk na jera mata wadannan tambayoyin ina kallon ta cikin kulawa.
“Wanka da sallah.” Ta amsa muryarta a sanyaye.
“Rahma a kai ta dakina a ba ta duk abin da za ta buqata.” Na fadi haka bayan na zube a kujera ina lumshe idanu.
Suna wucewa na kalli Baba, “Baba a jera mata abinci a dinning in ya so kowa sai ya je ya kwanta.”
“An gama Ranki ya dade.” Ta fad'a da tsokana don ta san na tsani wannan sunan.
Murmushi na yi ina kara gyara kwanciya a kan kujera mazaunin mutum uku.
“Sannu da aiki ranki ya dad'e, mu kwana lafiya.” Na fad'a wa Baba hakan bayan na lura ta gama jera ma Fati duk abinda za ta buqata.
“Kin rama kenan?” ta fad'a tana dariya.
Shiru na yi mata ina motsa baki. Ganin haka yasa sum-sum-sum ta wuce zuwa dakinta. Sauran ‘yanmatan ma duk sallama suka yi min. ina amsa musu da kai suka wuce dakinansu.
Tsawon minti talatin da biyar ta dauka kafin ta fito zuwa falon tana sanye da jallabiya baqa wacce ta yi matuqar dacewa da farar fatarta.
“Kin fito? Barka da fitowa…” na fadi hakan idanuna a rufe. Ban bari tace komai ba na ci gaba da cewa, “Ga abinci can a kan dinning, idan akwai abinda kike buqata ki yi magana.” Na fadi ina mata ishara da inda dinning table din yake.
Tun fitowarta ta lura da idanuna a rufe suke, a zatonta barci na ke yi, jin na yi magana ya bata tabbacin idanuna biyu. Isharar da na yi mata ina daga kwance ya daure mata kai, sai ta ja ta tsaya ba tare da ta yi gaba ko baya ba.
Tsawon minti biyu tana kallo na, ba tare da ta furta komai ba.
“Ki je ki ci abinci mana, dare yana qara yi fa. Idan kuma kin qoshi mu je mu kwanta.” Na fadi duk da haka idanuna suna rufe.
Qafafunta har hardewa suke gurin zuwa dining din, don al’amarin ya fara ba ta tsoro. Tsattsakar abincin ta yi ta sha lemo kadan, daga inda take zaune ta furta a ciki. “Na qoshi.” Wanda tana da tabbacin ban ji abinda ta ce ba.
“Toh, mu je dakin da kika yi wanka mu kwanta.” Na fada ba tare da na tashi ko na bude idanuna ba.
“Na shiga uku ni Fatima!” ta fada a zuciyarta, kuma a tsorace, Allah yasa dai ba gidan Aljanu na Kawo kaina ba"
Murmushi nayi, don ganin tana neman sa wa zuciyarta kokwanto a kanmu, yasa nace, "Ba gidan aljanu bane, mutane ne 'yan uwanki"
Tsananin tsoro ne ya sake cika mata ciki, hannu biyu tasa ta dafe kirjinta,
“Taya aka yi kika san abinda na fada a zuciyata?”
Wannan karon sai da na qyalqyale da dariya mai isa ta, sannan na ce “Sanin abinda yake zciyar wani sai Ubangijin da ya halicce mu Fatima, kar ki gurbata imaninki mana.” Na fada mata hakan, amma har lokacin ban bude idona ba.
Kallo na take ta rasa abinda za ta furta saboda rudanin da na jefa ta a ciki. Ta buxe baki kenan za ta sake magana na dora dan yatsa manuniya a baki na ce “Shiiii….!!! Kar ki tsananta magana Fatima, ina miki rantsuwa da Alllah mu ba masu cutarwa ba ne gareki, saboda haka ki kwantar da hankalinki karki tsananta magana kan duk wani abinda zaki gani a tare dani. Ki tashi ki shiga ciki ki kwanta nima yanzu zan shigo.”
Ina gama fadin haka na juya mata baya idanuna a rufe. Tana son ta qara magana amma bakinta ya kasa furta komai, tamkar an daure mata bakin don haka ta lallaba ta miqe zuwa dakin da ta yi wanka wanda tun farko ta ji na fadi mallakina ne.
Minti goma tsakani na bi bayanta, jikina ya bani idonta biyu don haka ban kalli inda ta ke kwance ba, bandaki na shiga na dauro alwala, ina fitowa na dauki doguwar riga ta akan daddumar sallah na koma ban dakin na sanya.
duk abinda nake idanunta na kaina har na ta da sallar nafila lokacin agogo ya buga qarfe hudu da rabi na dare, Ina zaune ina lazimi da casbaha a hannuna har aka kira sallar asubah, tashin Fatima na yi a lokacin har barci mai nauyi ya dauke ta.
Ban tashi daga kan daddumar ba sai qarfe bakwai na safe, “Kin ta shi lafiya?” Na fadi hakan ina kallon ta bayan na fara gajiya da kallon da take bi na da shi tunda ta idar da sallar asubahi. A zatona barci za ta koma amma sia na ga ta ci gaba da zama a gefen gado.
Gyada kai kawai nayi, sannan na janyo wata ‘yar qaramar akwati a qarqashin gadon, budewa na yi cikin nutsuwa na fara ciro wasu qananan kwalabe a ciki.
“Idan kwai abinda kike buqata kina iya tambayar duk wanda kika gani cikin gidan nan. Zan yi barci… idan za ki yi kallo ki fita falo.” Na fadi haka ina kallon Fatima ido cikin ido.
Kai kawai ta daga a maimakon buda baki, ta ba ni amsa. Ban damu ba na bude kwalba daya daga cikin kwalaban na shanye ruwan ciki, Sai da nasha kwalabe uku, sannan na dauko wata qwaya na sanya a bakina na taune na hadiye ba tare da na kora ruwa ba.
Nayi nasarar samun su, hakan ne ya ankarar da sauran mutum hudun daga inda harbin ya fito, wani ragon azanci da suka yi sai dukkansu suka biyo bangaren katangar da nake cikin sanda suna haska tocila, su Rahma ne suka miqe da hanzari suka dauki bindigogin ‘yansandan da suke kwance suna kici-kicin kwance qafafunsu suka harbi ‘yan sandan a qafafunsu ba tare da sun ankara ba.
Da sauri duk muka bi su muka shaqa musu hodar da take hannun Sadiya minti biyu tsakani nannauyan barci ya yi awon gaba da su. Mu kuma muka shiga cikin gidan hankali kwance. Don muna da tabbacin ba za su farka ba sai sun xauki tsawon awa goma sha biyu suna barci.
Mabudi ne da yake bude kowane irin kwado mukayi amfani dashi gurin bude dakin da take ciki, don haka ba mu sha wahalar bude dakin ba, suna tsaye cirko-cirko tamkar kajin da suke fada Sun tsaya maida numfashi.
Ganin shigowarmu ya sa suka nufo mu suna zazzaro ido. Kallon sakan biyar ya ratsa tsakaninmu, da alamun mamakin yadda muka shigo cikin gidan har muka bude dakin da suke ciki, ba tare da mun fuskanci matsala daga masu gadin gidan ba suke yi,mu kuma kallonsu muke don tanrance wace ce Fatima a cikinsu? Can kusurwar dakin na hangi wata ta takura kanta a tsakanin cinyoyinta.
Da hanzari na nufi gurinta don jikina na ba ni tabbacin ita ce Fatima. Hannu na sa na dafa kafadarta bayan na durqusa kusa da ita.
Da sauri ta dago kanta a dan firgice take kallo na sannan ta maida dubanta zuwa ga su Safiyya.
“Wace ce ke? Ku su waye?" Ta tambayi hakan bakinta na rasa, idanunta a warwaje, wadanda suka kumbura kuma suka rine zuwa jajaye, saboda tsabar kuka.
“Mu ‘yan’uwanki ne, kuma mun zo mu tafi da ke ne.” Na fada mata hakan da tattausar murya don in kwantar mata da hankali.
Kallo ta bi ni da shi na rashin yarda da abinda na fada. Dagabisani kuma ta ce “Ban san ku ba, don haka ba zan taba bin ku ba. ku bar ni kawai. Haka Allah ya qaddara zan qarasa rayuwata a gidan yari…”
tana gama fadinn haka ta fashe da kuka, sannan ta qara maida kanta tsakanin cinyoyinta, kamar yadda muka tarar da ita da farko.
Muna da tabbacin za mu fuskanci tirjiya daga gare ta, don haka ranmu bai vaci ba ko kadan. Da yatsu biyu na kira su Rahma zuwa gare mu, sannan na qara dafa kafadarta a karo na biyu. Hawaye ne wasu na korar wasu tamkar ruwa suke bin kyakkyawar fuskarta. Ban ba ta damar fadin komai ba nace, “Ga wannan tocilan ki haska bayan rigarmu ki ga me aka rubuta.” Na miqa mata tocilan hannuna, sannan duk muka jujjuya bayan rigarmu zuwa gare ta.
Tsawon minti uku kafin na jiyo muryarta na faxin, “na amince zan bi ku.”
Da matuqar murna na rungume ta, sannan na kama hannunta duk muka nufi hanyar ficewa daga dakin.
“Ku taimaka don Allah ku fitar da mu gaba daya.”
Muka jiyo muryar wasu daga cikin fursunonin suna fadin haka.
“Kofa a bude take ga duk wanda ya yi niyyar fita, amma mu dai ga wacce muka zo dauka nan.” Ina gama fadin haka muka fice da sauri don ganin lokaci yana dad'a qurewa.
Karfe uku da minti biyu muka isa gida, Sadiya ce ta dauki dan muqullin qofar get din a cikin mota ta bude mana aka shiga da motar. Baba tana zaune a falo kamar yadda ta saba idan muka fita komai tsawon dare bata kwanciya barci sai ta ga dawowarmu, Yau ma hakan ce ta kasance. Tana zaune da casbaha a hannunta tana lazumi muka shiga cikin falon.
Fatima ta nufa kai tsaye bayan ta amsa sallamarmu, da fara’arta ta tarbe ta sannan ta yi mana barka da zuwa.
“Abinci kike buqata, ko wanka za ki fara yi ko sallah?” Duk na jera mata wadannan tambayoyin ina kallon ta cikin kulawa.
“Wanka da sallah.” Ta amsa muryarta a sanyaye.
“Rahma a kai ta dakina a ba ta duk abin da za ta buqata.” Na fadi haka bayan na zube a kujera ina lumshe idanu.
Suna wucewa na kalli Baba, “Baba a jera mata abinci a dinning in ya so kowa sai ya je ya kwanta.”
“An gama Ranki ya dade.” Ta fad'a da tsokana don ta san na tsani wannan sunan.
Murmushi na yi ina kara gyara kwanciya a kan kujera mazaunin mutum uku.
“Sannu da aiki ranki ya dad'e, mu kwana lafiya.” Na fad'a wa Baba hakan bayan na lura ta gama jera ma Fati duk abinda za ta buqata.
“Kin rama kenan?” ta fad'a tana dariya.
Shiru na yi mata ina motsa baki. Ganin haka yasa sum-sum-sum ta wuce zuwa dakinta. Sauran ‘yanmatan ma duk sallama suka yi min. ina amsa musu da kai suka wuce dakinansu.
Tsawon minti talatin da biyar ta dauka kafin ta fito zuwa falon tana sanye da jallabiya baqa wacce ta yi matuqar dacewa da farar fatarta.
“Kin fito? Barka da fitowa…” na fadi hakan idanuna a rufe. Ban bari tace komai ba na ci gaba da cewa, “Ga abinci can a kan dinning, idan akwai abinda kike buqata ki yi magana.” Na fadi ina mata ishara da inda dinning table din yake.
Tun fitowarta ta lura da idanuna a rufe suke, a zatonta barci na ke yi, jin na yi magana ya bata tabbacin idanuna biyu. Isharar da na yi mata ina daga kwance ya daure mata kai, sai ta ja ta tsaya ba tare da ta yi gaba ko baya ba.
Tsawon minti biyu tana kallo na, ba tare da ta furta komai ba.
“Ki je ki ci abinci mana, dare yana qara yi fa. Idan kuma kin qoshi mu je mu kwanta.” Na fadi duk da haka idanuna suna rufe.
Qafafunta har hardewa suke gurin zuwa dining din, don al’amarin ya fara ba ta tsoro. Tsattsakar abincin ta yi ta sha lemo kadan, daga inda take zaune ta furta a ciki. “Na qoshi.” Wanda tana da tabbacin ban ji abinda ta ce ba.
“Toh, mu je dakin da kika yi wanka mu kwanta.” Na fada ba tare da na tashi ko na bude idanuna ba.
“Na shiga uku ni Fatima!” ta fada a zuciyarta, kuma a tsorace, Allah yasa dai ba gidan Aljanu na Kawo kaina ba"
Murmushi nayi, don ganin tana neman sa wa zuciyarta kokwanto a kanmu, yasa nace, "Ba gidan aljanu bane, mutane ne 'yan uwanki"
Tsananin tsoro ne ya sake cika mata ciki, hannu biyu tasa ta dafe kirjinta,
“Taya aka yi kika san abinda na fada a zuciyata?”
Wannan karon sai da na qyalqyale da dariya mai isa ta, sannan na ce “Sanin abinda yake zciyar wani sai Ubangijin da ya halicce mu Fatima, kar ki gurbata imaninki mana.” Na fada mata hakan, amma har lokacin ban bude idona ba.
Kallo na take ta rasa abinda za ta furta saboda rudanin da na jefa ta a ciki. Ta buxe baki kenan za ta sake magana na dora dan yatsa manuniya a baki na ce “Shiiii….!!! Kar ki tsananta magana Fatima, ina miki rantsuwa da Alllah mu ba masu cutarwa ba ne gareki, saboda haka ki kwantar da hankalinki karki tsananta magana kan duk wani abinda zaki gani a tare dani. Ki tashi ki shiga ciki ki kwanta nima yanzu zan shigo.”
Ina gama fadin haka na juya mata baya idanuna a rufe. Tana son ta qara magana amma bakinta ya kasa furta komai, tamkar an daure mata bakin don haka ta lallaba ta miqe zuwa dakin da ta yi wanka wanda tun farko ta ji na fadi mallakina ne.
Minti goma tsakani na bi bayanta, jikina ya bani idonta biyu don haka ban kalli inda ta ke kwance ba, bandaki na shiga na dauro alwala, ina fitowa na dauki doguwar riga ta akan daddumar sallah na koma ban dakin na sanya.
duk abinda nake idanunta na kaina har na ta da sallar nafila lokacin agogo ya buga qarfe hudu da rabi na dare, Ina zaune ina lazimi da casbaha a hannuna har aka kira sallar asubah, tashin Fatima na yi a lokacin har barci mai nauyi ya dauke ta.
Ban tashi daga kan daddumar ba sai qarfe bakwai na safe, “Kin ta shi lafiya?” Na fadi hakan ina kallon ta bayan na fara gajiya da kallon da take bi na da shi tunda ta idar da sallar asubahi. A zatona barci za ta koma amma sia na ga ta ci gaba da zama a gefen gado.
Gyada kai kawai nayi, sannan na janyo wata ‘yar qaramar akwati a qarqashin gadon, budewa na yi cikin nutsuwa na fara ciro wasu qananan kwalabe a ciki.
“Idan kwai abinda kike buqata kina iya tambayar duk wanda kika gani cikin gidan nan. Zan yi barci… idan za ki yi kallo ki fita falo.” Na fadi haka ina kallon Fatima ido cikin ido.
Kai kawai ta daga a maimakon buda baki, ta ba ni amsa. Ban damu ba na bude kwalba daya daga cikin kwalaban na shanye ruwan ciki, Sai da nasha kwalabe uku, sannan na dauko wata qwaya na sanya a bakina na taune na hadiye ba tare da na kora ruwa ba.