← Book details A Dalilin Da Namiji Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 2 OF 20

Sashe 2

A Dalilin Da Namiji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ba su fara samun matsala ba sai da Xan Alhajin mai suna Nasir ya dawo gida daga inda ya ke karatu acan qasar Malesia, tunda suka je air port da niyyar xauko shi ita da Alhaji da Hajiya ta lura da irin kallon da yake binta da shi, Nasir bunsuru ne gurin bin mata tun kafin ya tafi karatu qasar Malesia da ya je can kuma sai idonshi ya qara buxewa duk yarinyar da ya qyalla ido a kanta sai ya bi duk hanyar da yasan zai samu biyan buqatar shi.
Tun yana can ya ji labarin Dadyn shi ya yi aure amma bai tava tunanin daqwalwa irin wannan ya aura ba, ganin farko da ya yi mata gabanshi ya yanke ya faxi daqyar yayi qarfin halin daidaita nutsuwarshi don karya bada kanshi a gaban iyayan shi.
Suna tafe a mota zuciyar shi tana saqa mishi hanyar da zai bi dan cimma mummunan manufarshi a kanta, a zuciyar ta take ta addu’a Allah ya daidaita zaman su dashi dan sam bata fahimci wane irin kallo yake yi mata ba, a zaton ta kallon tsana ne da tunani yana taya mahaifiyar shi kishi ne, a minti biyar ya mantar da ita wannan tunani ta hanyar fara janta da hira yana kiran ta “Aunty Fati” duk iyayan ransu cike yake da farin cikin dawowar xan nasu dan haka sam hankalin su ba shi a kan Fatima, idan ya tsomata a hirar shi a xarare ta ke amsawa muryarta a sanyaye.
Hakan ba qaramin burgeshi yake ba, shauqin sha’awarta yayi ta xibar shi, har su ka isa gida, ba ta bar babban gidanshi ba zuwa gidanta sai bayan magariba gab da isha’I da yake Alhajin a gidan yake da kwana sai ya haxa ta da Driver ya kai ta gida da sauri Nasir ya miqe ya na kallon iyayan shi fuska a sake ya ce, “Ba ri in raka aunty Fati gida sai mu dawo ta re da Drivern”
jikinta sanyi qalau ta ke kallon shi don rashin ga ne manufar wannan cusa kai da ya ke mata. Izinin tafiyar daya samu daga gurinsu ya hanata tankwavar da shisshigin shi , sai ta qara yi musu sallama ta nufi harabar gidan.

Dukkansu suna zaune a bayan motar ba mai cewa wani uffan, amma idon shi ya na kanta tamkar zai cinyeta xanye, ba qaramin takurata yayi da idanun shi ba don haka ta takure acan jikin motar, a zuciyarta ta ke addu’ar Allah yasa su isa gidanta lafiya ko zata samu sa’ida da ga mayataccen kallon da yake bin ta da shi.
Suna isa ta dakatar da Driven a qofar gida, ta valle murfin motar ta fita sannan ta leqa kanta ta saqon glashi ta ce, “Nasir Allah ya huta gajiyan tafiya mu kwana lafiya” ta qarasa da sauri ta ciro key a jaka ta na buxe get xin gidan ba taga fitowar shi daga mota ba balle lokacin da ya nufota kawai muryarshi ta ji a kusa da ita ya na faxin “Haba aunty na rowar ruwan gidan ki za ki yimin?”
a firgice ta sa ki key xin ya faxi qasa muryar ta na rawa ta ce, “Ba… ba… ba haka ba ne, na… naga su Alhaji suna can suna jiranka ne.” bai ce komai ba ya ya tsuguna ya xauki makullin ya buxe get xin ya shige ciki ya bar ta nan a tsaye. Ganin da ta yi ba sarki sai Allah ga idanun Driver tun xazu ya na kanta ya sa ta yi shahadar bin bayan shi, har ya samu nasarar buxe qofar falonta ya shige ciki don haka ta haxa da sassarfa zuwa cikin falon.
Yana kwance akan kujera mazaunin mutum uku idanun shi alumshe, jakarta ta aje akan kushin ta nufi kiching ta jero mishi lemuka da ruwa ma su matuqar sanyi a cikin faranti ta xora Cofi guda biyu ta kawo mishi.
A zaune ta tarar da shi hannun shi riqe da remot xin T.V ya na canza tashoshi, a gefe xaya ta aje ta xauko xan qaramin table ta xora sannan ta kalle shi ta saki fuskarta ta ce “Bisimillah.” Maqe ka faxar shi ya yi tamkar wani qaramin yaro sannan ya fara kashe ma ta ido irinna gogaggun ‘yan duniya. Muryar ta da mamaki ta ce
“Me ya sa? Bayan ruwa ka buqaci sha”

“Ni ba irin wannan ruwan nake so ba”
Ya faxa yana tura baki, ya fara kwarkwance mata tunanin ta don kuwa ya girme mata nesa ba ku sa ba, a qalla zai girmeta da shekaru goma sha huxu, wanda ya riga ka kwana dole ya riga ka tashi. Sam bata fahimci inda ya dosa ba don haka ta ce,
“dare yana qara yi fa kar su Hajiya su ji shirun ya yi yawa"
“Bikin Magaji ya na hana na Magajiya ne?" ya jefa mata tambayar yana qara qura mata ido. Kallo kawai ta bishi dashi ba tareda ta amsa mishi ba. Tashi ya yi ya matso dab da ita sannan ya ce,
“Gaskiya Fatima bazan voye miki ba sam baki dace da irin su Dady ba, da irin mu ki ka dace, kina da kyau matuqa, kina da dirin da duk wata qasaitacciyar mace za ta so ta mallaki irinshi, ganin farko da nai miki sha’awarki ta mamaye zuciya ta “Ina sonki” zanso ace kin rabu da mahaifina ki dawo gareni, idan kuma hakan bazai samu ba to gaskiya sai dai mu raba shi daidai da Daddy, don wallahi tunda na xora qwayar idanuna a kanki to tabbas sai na biya buqatata.
Gobe Daddy zai dawo gidan nan donhaka kwana biyu na baki ki yanke hukunci a ranar da Daddy ya koma gidan Momy zanzo danjin shawarar da kika yanke”
ba tare da ya qara kallota ya fice da ga falon.

Tofa! In ka ji qi gudu sa gudu ne bai zo ba, tsawon minti arba’in batasan a wace duniyar ta ke ciki ba dawowa hayyacinta ta yi ta ganta zaune dirshan a kan kafet xin da ya malale tsakiyar falon. A ranar idan ta ce tayi barci to tabbas ta yi qarya, duk qwarewar sarkin varayin gurin satar mutane a ranar bai yi nasarar satarta ba, daga qarshe ta xauro Alwala ta fara jera nafilfili tana kai kukanta da Ubangijin talikai.

Har Alhaji Muhammad ya bar gidan ta rasa mafitar da tafi dacewa a tsakanin zavin da Nasir ya bata, Alhajin da kanshi ya fahimci bata cikin walwala kuma ya tambaye ta amma ta kasa sanar dashi gaskiyar abinda yake damunta.

Tun qarfe shida da yamma ta kulle get xin gidan da qofar falonta, a tsammaninta ta kuvuta daga zuwan Nasir, don ko yazo zai koma tunda gidan yana rufe ne. fitowarta kenan daga wanka misalin qarfe takwas da rabi na dare, taji kamar hayaniyar T.V take jiyowa daga falonta, don haka ta xora hijabi akan towel xin da take xaure dashi ta fito zuwa falon. Yana hakimce akan kujeara yana karkaxa makullin motar mahaifinshi wanda ya ke haxe dana qofar get xin gidanta dana qofar falonta, hakan shi ya ba ta tabbacin inda ya samu makullin cak ta tsaya tana kallonshi ta kasa furta ko kalma xaya. “Babyna…” shiya katse mata tunanin da take yana mata kallon qurilla tamkar zai cinyeta.
“Me ya kawo ka gidannan?”
Ba tambayeshi fuskarta ba walwala ko kaxan, saida ya xan ja fasali kamar bazai yi magana ba sannnan ya ce,
"Amsar buqatata nazo ji”

“Ni ba irin ‘yan iskan matan daka saba hulxa da su bane, ka je can ka samu dai dai dakai ni matar mahaifinkace ko mun rabu dashi aure ya haramta a tsakaninmu kuma ba zan tava yin zina da aure na ba, don haka karka qara zuwa min da zancen banza.”
Ta fadi hakan muryanta cike da masifa, idanunta a kankance.

“Kin manta abinda na faxa miki rannan koh? To wallahi bazan tava haqura dake ba, ko da tsiya ko da arziqi sai na cimma burina a kanki kinsan irin azabtarwar da nayi a kwana biyun nan kuwa? To wallahi sai kin haxa jikinki da nawa a gobe goben nan.”
Ya fadi haka cikin nuna rashin damuwa da masifa da take mishi.

“Qarya kake Nasir Allah bazai tava barinka ka cimma qazantacciyar manufarka a kaina ba, kuma idan baka janye wannan maganar ba zan kira mahaifinka in sanar da shi duk abinda kace.”

“Wannan shine babban kuskuren da zaki tabka a rayuwar ki kin manta irin son da iyayena suke min ne? ko kin faxa musu wallahi bazasu tava yarda ba, a qarshe sai dai ma ki janyowa kanki wani bala’in don zan tabbatar musu da cewar tunda na dawo qasar nan kike bibiyata, don naqi amincewa buqatarki ne kikai niyyar shiga tsakanina dasu.”
Ya qara matsawa dab da ita, ita kuwa ta fara ja da baya har sai da ta qure da jikin bango yana kusantar ta. Hannu biyu yasa ya dafa bango ya tare ta a tsakiya, fuskarshi ya matsar dab da ta ta sannan yace, “Kinsan kuma tsab zasu yarda da abinda nace, don ana canza mata amma ba’a canza da, kiyi tunani ki samu nutsuwar yau gobe zan dawo in kashe qishirwata.”

Daga haka bai qara furta komai ba ya fice ya barta tsaye a gurin kamar mutum-mutumi.
yau kam kasa yin sallar ta yi kawai sai ta rushe da kuka mai tsananin qarfi tsawon awa biyu tana kuka wa wannan mummunan al'amari da ke tunkarar ta, daga qarshe sarkin varayi ya yi awon gaba da ita a tsakar falon.
Washe gari ba abinda ta iya hassalawa a gidan jikinta sanyi qalau tana kwance akan kujera tana jan carbi, lokaci zuwa lokaci gabanta yana faxuwa tanajan “Inna lillahi wa’inna ilaihir raji’un” har Alhaji ya shigo ya dubata kamar yadda ya saba idan ba’a gidan ya kwana ba.
“Bana jin daxi ne” amsar da ta bashi kenan lokacin daya matsa da tambayar abinda ke damunta.
Chapter 2 · 0% Book details