← Book details A Bakin Aurenki Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 24 OF 29

Sashe 24

A Bakin Aurenki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Jahilcina bai kai nan ba Ja'afar, a bazan ta6a
abinda ka ke so ba, a gareni yanzu k'allon Yaya
nake ma,da kuma uban yarinyar dana haifa,
bayan haka..

Kai ta girgiza, kan tace "you mean
nothing to me a yanzu kam..

Jin baice komai ba yasa taci gaba.

"Banzaci haka daga gare ka ba Garba,a ganina in
shi ya 6ata kai mey dawo dashi kan hanya ne,
wallahi auren t'sakani da Allah zanyi, ku sani
kuma auren so zanyi,wanda nake fatan mutu ka
raba ne,dan Allah,dan kaunar ka da Allah ka bar
bibiyata,dan Allah..

Shiru tai dan ganin shima idonshi ya taru da
hawaye,da sauri ta shige gida tana goge
hawaye..

Har ta shige yana binta da ido ba magana, sai
hawayen da ya zubo mishi shar, da sauri yasa
hannu ya share.

Kafad'arshi Garba ya dafa, "kaji zancenta, tai
mana fassara baibai,ya kamata kai hakuri ka bar
kulata in har kana wa Allahn data had'a ka dashi.

Kai ya daga, "InshaAllah..
~~~~
Taro ne iya taro,taron shedar auren Salma da
Alhaji Usman, daga inda yake t'saye a chan nesa
da kofar gidan yana k'allon komai har aka shafa.

Juyawa yai da jaka biyu hannunshi tare da sanya
bakin glass dan 6oye sirrin dake idonshi.

Yasan yanzu kam Salma ta mishi nisa.

"Mama taki ta bud'e dakin fa,daga ina jiyo sautin
kukanta Allah.

Ta window Ummi ta leka,gata k'wance ta tasa
tsohuwar wayarta a akan fuska tana razgar kuka,
So ba karya bane Salma.

Feenat Ja'afar.
[8/7, 11:08 AM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN
AURANKI*
Feenat Ja'afar*.
37_Har aka kai amarya gidanta bata bar kuka
ba,dayawa sun zata kukan na Mama ta cire
Miemie ne, dan basa ji koh auren farkonta tayi
haka.

Kowa ya wat'se sai ita kad'ai, ko'ina take kallo a
dirare, gida ne iya gida,tun bata fita ba ta
zaga,yau gata a gidan da ba Ja'afar, ba kuma
Miemie,tuni ido ya cika da kwallar tuna baya.

Anya tai ma Ja'afar adalci kuwa?..

Anya bata ci
amanar so ba kuwa?..

Ta sani da takai Ja'afar
bango,hakan yasa bai kara waiwayarta ba,ta
yuwu yai zuciya...

Ido ta goge da sauri jin motsin
za'a bud'e d'akin.

Ango ne yasha babbar bunjima da rike da leda,
bakin nan har kusan kunne,jan mayafinta ta kara
yi ta rufe fuska.

"Amarya!

Amarya!!..

Ba k'ya laifi wai koh kin
kashe dan maigida koh?..

Murmushi ta k'akalo mishi, zama yayi a gefenta
tare da ajiye ledar a gefen bedside, bata aune ba
taji ya yaye mata g'yale yana kallon fuskarta.

Alwala yace ta d'auro suyi nafila,dan wai
agareshi babbar kyauta ce ita daga Rabba.

Sun gabatar da duk wani al'ada,sai dai har ango
ya d'ane gado amarya tana t'saye a gaban
madubi
sai sininiki take,gabanta sai mugun fad'uwa yake
tamkar wacce tai auren fari.

Murmushi yayi da kanshi ya taso ya karaso har
gaban madubin tare da kamo hannunta.

"Muje ki kwanta haka dare nayi sosai..

Kamar yarinya ya kwantar ta gefen shi yana kallo
da murmushi.

Salon ya sauya,tuni ta fara digar da hawaye,shi
kadai yake kid'anshi yana rawarshi,sai dan sautin
kukanta dake fita kad'an-kadan,wanda a gareshi
tamkar zigi take mishi.

Kai ta juya ta kallo Alhajin dake bacci
hankalinshi k'wance,abu uku sun hanata bacci,na
farko kukan zamanta ta wani ba Ja'afar ba,na
biyu tunawa da Miemie, na uku minsharin Alhaji..

Har gari ya waye bacci sai jefi-jefi-jefi ke
dibanta,sam taki jinin minshari kusa da ita,tsaf
yake hanata bacci.

Shikam da farin ciki ya tashi irin na sabbin
ango,ita kam da ido kawai take binshi.

Tara sai ga yaron uwargida ya kawo abinci,da
fara'a ya gaida ta,kanshi ta shafo kan tace ya
sunan shi?

"Sunana Ja'afar"....

Kallonshi take da mamakin
jin sunanshi, koh dai bataji dakyau bane?...

Kat'seta yai da fad'in
"K'anwata kuma Nabila,Umman mu tace sai
anjima zamu shigo kar mu tashe ki a bacci.

Murmushi tai mishi yace ya tafi..

"Ja'afar...

Ido ta rint'se jin maigidan ya kira sunan,ba shiri
ta d'au abincin tai kitchen.

Bayan sun gama komai yace suje bangaren uwar
gida zai magana dasu.

Batai zatan da kishiyoyi masu kaunar kishiyar su
ta ra6e su sama da matar Alhaji ba,sosai tai
mata bazata,tun tana d'ari-d'ari har ta saki jiki da
ita da yaranta, musamman Ja'afar..

Yau Miemie ce tazo mata,sai murna take taga
Auntyn ta.

Duk babyn ta rame,yaye bai amsheta ba.

''Miemie, ga nan Abdul yazo ku tafi gun Mama
koh?...

Kafad'a ta make halamar taki tana neman kuka,
"Yi hakuri gobe zanje gida mu taho koh?..

Kuka ta saka mata baji ba gani, sai mak'e
kafad'a take tana ita "um-um.

Sai ta sallami Abdullahi kan gobe yazo ya d'auke
ta, har ya jima da tafiya Miemie bata bar kuka
Sai um-um kawai take fad'i, suna haka Alhaji ya
shigo,duk yai kicin-kicin da fuska, cikin fad'a-
fad'a yace ta lallasheta man,shi baison hayaniya
bare ta yaro...

Baki sake take kallonshi,kaya ya ajiye ya juya ya
fice harda dan tsakinshi,toh mey yake nufi?...

Y'arta ta d'auka ta sa6a a baya sukai kitchen
tana fad'in tai shiru ba inda zata toh,kan aje
ko'ina sai ga nan Miemie harda dariya tana bata
labarin Mama cikin gwaranci.

Har dare ba Alhaji ba duriyarshi,abinci ma sai
Ja'afar ya turo ya d'auka.

Suna k'wance Miemie sai k'allonta take,gani take
kamar guduwa zata yi ta barta.

Kanta ta shafo tana mata murmushi,
"Yi baccinki my Miemie, ina nan fa tare da ke
kinji?.

Kai ta daga mata tana k'allonta.

"Antee...

Kai ta dago kan tace
"Na'am Miemie nah...

"Abba...

Tsam tai tana k'allon Miemien,Abba?

Ta nanata a
ranta.

Murmushin dole ta k'akalo tana fad'in Abba yana
nan Miemie,bata aune ba taji ta kara fad'in
Abba...

Hawayen da take makalewa ne suka zubo
mata,da halama yanzu Miemie ce matsalar
ta,dan zata dawo mata da hannun agogo baya.

Da dabara ta d'auke hankalinta daga tunanin
Abban ta hau lalla6ata har tai bacci.

Photocopyn Ja'afar ce Miemie,barin yanzu data
kara girma, tunani take koh dai Ja'afar har yanzu
baya zuwa gida, laifinta ya shafi Miemie?

Dan tasan sai Miemie ta kwana biyu bata ganshi
ba take nemanshi haka.

Tana nan har maigidan ya shigo,sai wani k'allo
yake aikama Miemie wanda ta kasa fassara shi.

Tun daga ranar ya zamana in dai Miemie zata
zo,toh fa zata rasa gane kan maigidan, ta rasa
dalili, musamman in tai la'akari da hadithn
hausawa na Duk mai son uwa toh yaso d'iyanta.

Ranar har ta kasa d'aurewa tai mishi magana,
amsar da ya bata ta jima tana sata hawaye.

Ga Miemie da kulafuci bare tace kar a sake kawo
ta,asalima duk randa tazo fara'arta karuwa take.

Sa6anin in tazo mata,data gane sai take d'akko
ta duk randa bata da girki su k'wana, ranar da
maigidan yake da ita su wuni ai rabuwar kuka
har uwar.

Allah yaga Miemie kadai take gani taji sanyi a
ranta.

Ranar suna fira a bangaren uwar gida take mata
korafi kan halin maigidan akan Miemie.

Murmushi tayi kamin tace
"Sai kinyi hakuri da halin Alhaji Salma,ba tone-
tone ba,a'a kawai dai ya kamata ki sani, Alhaji
sam baya son yara,musamman hayaniyar
su,hakan yasa ya d'aurawa kansa kin haihuwar
k'arfi da yaji, nayi ta zaman takaicin halin nan na
Alhaji har t'sawan shekara bakwai,a lokacin aka
tada kayar baya kan sai ya kara aure tunda ni
sun zuba ido shiru.

"Hanna ta shigo itama ta shekara biyu shiru, ni
dai nasan kusan kullum yakan tasa ni da Hanna
dan shan maganin daukan ciki.

Ana nan ranar wata kawar Hanna tazo suna
jajanta ko dai matsalar gun mijin ce,toh a ranar
dai asirin Alhaji ya tonu,dan kawar Hanna taga
magani tace na hana d'aukar ciki ne.

"Ranar muka mishi tawaye har Hanna,in takaice
miki yace shi bai shirya haihuwa ba yanzun,anan
sukai baram-baram da Hanna ya bata takardar
"Haka sauran mata biyun kowa tazo zai fad'a
mata ra'ayinshi, da taga bazata iya ba zata fice,
duk kuwa da tarin arzikin shi,a lokacin muna da
shekara kusan sha uku da aure,koh mai zaiyi na
daina shan magani, hakurina ya kare,nan na kai
kara gun Hajiyarshi.

"Ya saduda muka haifi Ja'afar, yace daga nan ta
isa haka,wai incigaba shan magani,a gabanshi
zanyi kamar nasha, daya kauce zan zubar.

Koh shekara Ja'afar bai ba na samu cikin
Nabila,cikin da a kullum sai naga tasku gun
Alhaji,gar da gar zai nuna bai kaunar su,barin in
Ja'afar na kuka,haka nai ta hakuri har na haifi
Nabila.

"Yanzu kam magani sai dai shi yai tasha,amma
banda ni,kinga Nabila har ta shiga shekara ta
biyar.

Tsam tai tana tunani bayan kammala bata labarin
waye Alhaji, ita ba kullen ne yafi damunta ba
sama da rashin son haihuwa..

A kalla yanzu ta doshi wata na biyar a gidan nan
amma ba bayani,sam bata kawo wani abin
ba,ashe wannan ne dalili?..

Bazata iya tuna ranar fitarta ta karshe a gidan
nan ba,tun kwa bayan aure sau daya taje gida sai
dai aukin waya koh azo mata, lalle duniya labari.

"Zaman hakuri kawai zamuyi Salma,sai adu'ar
shirya in da rabon zai gane, amma shawarata
gareki ki rike y'arki, dan kar kiyi sakiyar da babu
ruwa tun kina yarinyar ki dake,shi ba ruwanshi.

Kai ta kad'a mata,Allah sarki Ja'afar, ta tuno
lokacin data fara period tana kukan samun ciki
yana murna.

Ta tuno da abinda yace mata
"Allah sa Miemie ta samu k'ani a kusan nan...

Ta tuna data hau bori ya hau lallashinta,
harda alkawarin shi zai mata reno in bata shirya
ba...

"Ba kuka zakiyi ba Salma,muyi ta adu'a.

Hannu takai fuskarta, ashe kuka take bata sani
Feenat Ja'afar.
[8/7, 11:08 AM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN
AURANKI*
Feenat Ja'afar*.
38_Ranar sakwa-sakwa ta yini tana tuna halin
Alhaji, bai da mugun hali koh daya sai na bakin
kulle da kin yara,bayan nan baza tace ga mugun
halinshi ba.

Zataso sanin wane hali Ja'afar yake ciki a
yanzu,dan tabbas tasan ya zuciya da ita,tunda
gashi ance koh wajen Miemie baya zuwa sai
aike?..

"Mey nai kenan?..

Mey nayi ni Salma?..

Mey yasa
ban iya jure zama ba aure ba a rayuwa kamar
yadda yaso muyi..mey yasa?..

Juyi tayi tana hawaye,
Kila rabon Miemie kadai take dashi a
duniya,tasan kuma aure dai ana yinshi ne dan
abu biyu,samun zuri'a na daga ciki, gashi ita
anan ana son a haramta mata.
Chapter 24 · 0% Book details