Sashe 23
A Bakin Aurenki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tun daga ranar Mama ta zama y'ar rakiyar
Salma hanya,sai ta tabbatar ta hau abin hawa
zuwa makaranta zata juyo tana aika mishi
harara,da tai na sati sai ya bar tare hanya kuma
ya dawo waya.
Ana haka shima admission nashi ya fito
shima,tuni ya shiga kunci,dan yasan ya kusa yin
nisa da Salma,hakan yana nufin komai zai iya
faruwa.
Ranar da yamma ana washegarin zai tafi yazo
mata sallama duk da sunyi fad'a.
Taimakonshi daya Mama bata nan ranar ma,dan
yana ga ita kad'ai zata iya tsaida shi a yima
Salma kashedi.
Shigarshi zauren kenan sukai kicibis zata
fito,harara ya sakar mata kan yaja ya t'saya.
Fita take shirin yi ya ruko gyalenta da sauri har
yana zamewa,don haka a fusace ta juyo da niyar
balbaleshi ya marairaice mata fuska.
"Saken g'yale toh..
Murmushi yake yaki saka, ''ka
saken gyale koh na fuce...
Da sauri ya cika yana
tare kofar fitar.
"Maganar fahimta nake so muyi dake,dan Allah ki
t'saya..
Hannu ta hard'e a kirji ta k'alleshi,itama zata so
su fahimci juna.
"Ina wuni toh,tunda har gaisuwa kin soke dani.
Da kalar tausayi ya kara yana sukui da kai har
taso yin dariya kamin ta gaishe shi.
"Ina Miemie?.
"Da Mama suka fita,kayi kai maganarka kan su
dawo fa.
Tsayuwa ya gyara tukun ya kira sunanta, rai sake
ta amsa,fatan ta yasa zancen azziki zai mata ba
wai shirme ba.
"Salma"..
A karo na biyu ya kara kiranta, bai jira
amsarta ba ya cigaba,
"Gobe zanje Zaria kan batun makaranta da zan
fara, kima Allah Salma ki yi kamar ina nan dan
Allah,banda kula tsagerun samarin nan wanda
har yau basu mallaki hankalin kansu ba dan
Allah.
"In ma aure naso kiyi ina ga ni ya dace na baki
mijin aura,bare a agendar mu bamuyi haka dake
ba...
T'sam tai tana kallonshi da halamun ya zare tana
murmushi, amma zata bishi a haka a wanye
lafiya.
"Toh naji,zan kuma kiyaye,happy?..
Kai ya kad'a da murmushi, "yauwa koh ke fa,dan
Allah Salma ki riken alkawari nan..
Kai ta kad'a tana taji ai..
Da haka suka rabu ya
bata kayan zakin Miemie, murna fal ranshi suka
rabu ranar.
K'warai ta samu sakewa sosai bayan tafiyar
shi,tuni ta kara bud'e shafin zawarci sabo,duk da
kasan ranta tausayinshi take ji sosai.
A wata daya tai samari biyu irin son Mama, barin
Alhaji Usman Dan chanji.
Kud'i sosai yake kar mata kamar ba gobe,
albarka kwa kullum samunta take gun
Mama,yace shi ba yaro bane,dan haka yana so ai
auren cikin k'ank'anin lokaci.
Ya sanar mata yana da mata daya da yara biyu
kachal,aurenshi uku,sun rabu da biyu sai Hajiya
ta k'arfen.
Tunda suka rabu tazo gida tana tuna abu uku,
tabbas a yanzu bata da ra'ayin auren mey
mata,dan taga aya akan Bintu.
Sannan bata son mutum mai irin kud'in Alhaji
Usman sam a rayuwarta.
Gwara ma Kamal dan shi matashi ne kamar su
Ja'afar, kuma yafi kwanta mata a rai,gashi da
saukin hali da saukin kud'i.
"Oh ni y'an nan,ashe arziki ke binki Salma a
rayuwa?..
K'allon Maman take yadda take daga abubuwan
da Alhaji ya bata,ita dey nata ido.
"Bana jin koh lokacin y'an matancinku kun ta6a
had'uwa da irin wannan, babbar harka ai tayi y'an
nan...
"Mama ni fa mutumin nan bai kwanta min ba
sam Allah,gashi har ya fara maganar aure tun
yanzu,ga yana da mata fa,ga ni sam irin kud'in
nan baya...
Baki sake Mama ke k'allonta,tuni ta tsayarta
cikin fad'a.
"Rufe baki ni sauraniyar y'an iya t'sari, ashe har
yau kina nan da halin nan Salma?
Arziki na binki
kina zura da gudu?..
"Ina ruwanki da matarshi?..
Koh a kanta zaki
zauna?..
Kai ta girgiza zatai magana ta dakatar ta.
"Koh dai Salma hudubar yaron chan tai tasiri
akanki?..
Kai ta kad'a,
"Allah Mama ba haka bane,ni ina tsoron kishiya
ne,kinaji fa wai aurenshi uku suna rabuwa sai ita
ke zama...
"Sai mey toh?..
Kar ki bada mata mana Salma?..
Baki sake take k'allon Maman,kamar ba ita ke
fad'in ba mai zama da kishiya ba a yaranta tunda
itama bata zauna ba,wace daga ce ba'aci ba
lokacin auren Bintu da Ja'afar amma yanzu kud'i
ya warware Mama?...
Kat'seta tai,
"Saboda haka komai yace ki ce toh, in ma ita ke
fidda su toh ke zama daram,dan wannan ba
gidan fita bane in an shiga...
Hawaye ke zubar mata yayin da tazo k'wanciya
tana tariyo zancen Mama, dole in dai tana son
faranta mata wai ta ba wa Alhaji dama.
Waya ta d'auka jin shigowar text message,tasan
na Ja'afar ne.
_"Salmatee,remember, a heart dat truly loves
never loses hope..but always believes in d
promise of love,no matter how long d time and
how far d distance,at d right time,love will fine a
way".._ ki rike alkawarin ki,love you..
*Ja'afar*
Kukanta ne ya karu sosai bayan ta gama
karantawa, tabbas in ta cigaba da sauraran
kalaman Ja'afar zasu sa ta karaya har ya ci
galaba akanta..
"Bani da kamar ka har kullum Ya Ja'afar, sonka
gareni ba mai misaltuwa bane,amma kai kaja
mana koma meye...
Fuska ta goge sakamakon jin tahowar Mama da
Miemie na kuka.
Washegari kanta t'saye ta bawa Alhaji damar ya
turo magabatanshi kawai koh ta huta da
dawainiya da son Ja'afar.
Sabon sim ta siya tasa a sabon wayar Alhaji da
ya bata,a haka suka raka wata kusan biyu, duk
da tai kewar text da kiran Ja'afar din.
Shikam yana chan hankali tashe na rashin samun
wayar Salma, ga Abba ya sanarshi kar ya sake
ya dawo sai an nemeshi a makaranta,
Duk da an sanarshi ana kawo Miemie gidansu ta
yini.
A jikinshi yaji abu na faruwa,duk sai yaji bai da
nut'suwa sai ya je gida dan tabbatar da
zarginshi.
Tunda daga d'anno kanshi layin su Salman ya ja
ya t'saya.
T'saye take da dan murmushi a
fuskarta, sanye cikin favorite dinshi riga da skirt
na atamfa purple, tai kyau matuka gyalen nan a
kafada,daga inda yake zai iya gano bakin
gashinta a tufke ta chan kasan dankwalinta,
tasha ado tamkar zata party.
Wani abu ne yazo dai dai makogwaronshi ya
tsaya,kishi...
Bai san ya isa gun ba sai da yaji ana "lafiya?..
Kallo shi yayi, duk sai yaji yau baida ma k'warin
g'wiwar fad'a,Salman ya kalla,da sauri ta kawar
da fuskarta gefe ta had'e rai.
Sai ya dawo kan Alhajin,tsaf sai ya haifi
Salma,sai t'sabar kud'i da jindadi da suka 6oye
shekarunshi.
Kallonshi yake tun daga sama har zuwa kafa, so
yake ya gano ta inda ya fishi har Salma ke mishi
murmushi haka.
A zuciya yace
"Babu...
Sai dai kud'i kawai da sa kaya masu
t'sada.
"Kai fa,daga ina ba koh sallama?..
Cike da haushi ya kallota, "baki sanarshi ko ni
waye ba ne?..
Kan Alhaji ya dawo,ba shakku
yace "matata ce ita,zaifi mana k'yau in ka daina
zuwa gunta Alhaji.
Murmushi yayi Alhajin,kan ya kallo Salman, "sai
kinji ni kawai..
A takaice ya k'alli Ja'afar din,ba
sai an fada mishi waye ba,halamu ya nuna
tsohon mijinta ne,har zaga wa tai ta rufe mishi
tana daga mishi hannu d'auke da murmushi, har
ya kule tana daga mishi hannu kan ta d'au
kayanta koh ta kanshi bata tai hanyar gida,da
zafin nama.
"Wato abinda ki ke kenan tun bayan tafiya ta
shine yasa ki ka kashe waya?
Salma mey yasa
kike son ki 6ata min rai wai?..
Jibi fa shigar ki,ji
gashi a waje,wace iriyar rayuwa ki ka za6a
mana?
Cike da fada tace
"Wace iriyar ka za6arwa kanka dai Ja'afar..
Ya
zaka zo kana fad'an wata iriyar magana mijin da
zan aura?..
Karan nan bazan dau abinnan naka
ba wallahi, aure zamuyi dashi nan da wata biyu...
Sai kayi abinda zaka yi.
Feenat Ja'afar.
[8/7, 11:07 AM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN
AURANKI*
Feenat Ja'afar*.
36_Kan yai k'wak'waran mot'si ta shiga gida tare
taru kofa harda sa sakata.
Jiginna tai hawaye na neman zubo mata,daga
yar bular dake jikin kofar ta leka waje,kofar gidan
yake kallo jiki a sanyaye kamar yasa kuka,juyawa
tayi hawayen dake makale mata ya zubo,dak'yar
ta seta kanta ta shiga ciki rai cike da tausayin
Ja'afar.
Kusan kullum zai zo ba zuciya dan bata baki
akan Alhaji tana mishi wulakanci,shi kam Alhajin
har dariya yake bashi wani sa'in, dan baijin da
abinda zai iya rabashi da Salma a dai dai lokacin
nan,sai dai jin saki uku ne kawai sai ya bar jin
komai,iyaka ma yai ta tusa ma Ja'afar din bakin
ciki in ya gansu da kalamai ma Salman.
Biki ya karato ga makaranta,amma haka duk
week end daga Zaria zai zo kan batun Salma ta
janye zancen bikin nan.
Duk ya fita a hayyacinshi duk akan auren Salma.
Da halamu ya fara hankalin daina zuwa gun
Alhajin,sai dai in yazo ya tsaya chan gefe sai
tazo shiga ya tare ta da magiya.
Yau saura k'wana biyu biki, sai gashi shi da
Garba,dawowarsu daga gidan g'yaran jiki kenan
ita da Ummi.
Turus ta ja ta t'saya ganin Ummi ta wuce ita ya
tare mata hanya.
"Ka ga yau bani da lokacin jin wannan
mahaukatan zantukan naka,jibi iyanzu na d'aura
aure, ya kamata kasan inda dare ya maka,
sabuwar rayuwa zan fara,saboda haka kai yanzu
ya rage ma,danni yanzu baka gabana...
Kai ya kad'a mata,
"Karan nan bazan hanaki aure ba Salma,sai dai
ba da Alhaji ba.
Baki sake take kallonshi, Garba ya nuna,
"Garba zaki aura Salma,kimin wannan alfarmar.
Kai ta dauke daga kallonshi ta k'alli Garban
wanda shima ya cika da al'ajabin kan maganar
Ja'afar.
Sai ta girgiza kai da murmushin takaici.
"Tanan kuma ka bullo min?..
Auren kisan wuta
Ja'afar?
Lalle kayi nisa ba zakaji kira ba.
Bayab hannunta tasa tana goge hawayen idonta.
"Wai ka zata ni din auren kisan wuta zanyi da
wanda zan aura?..
Kai ta kara kadawa,
"Kai kuskure toh,dan ni aure zanyi na tsakani da
Allah,ba wai nayi na fito ba Ja'afar..
"A'a Salma,ba haka ne nufi na ba..
Da muryar
kuka ta tareshi,
"Hakane man,haka kake nufi,wato ka kawo min
abokin ka na aura bayan wani lokaci ya sake ni
sai ka halartawa kanka ni koh?..
Baki sake duk suke k'allonta,ganin yadda hawaye
ke zubar mata.
Salma hanya,sai ta tabbatar ta hau abin hawa
zuwa makaranta zata juyo tana aika mishi
harara,da tai na sati sai ya bar tare hanya kuma
ya dawo waya.
Ana haka shima admission nashi ya fito
shima,tuni ya shiga kunci,dan yasan ya kusa yin
nisa da Salma,hakan yana nufin komai zai iya
faruwa.
Ranar da yamma ana washegarin zai tafi yazo
mata sallama duk da sunyi fad'a.
Taimakonshi daya Mama bata nan ranar ma,dan
yana ga ita kad'ai zata iya tsaida shi a yima
Salma kashedi.
Shigarshi zauren kenan sukai kicibis zata
fito,harara ya sakar mata kan yaja ya t'saya.
Fita take shirin yi ya ruko gyalenta da sauri har
yana zamewa,don haka a fusace ta juyo da niyar
balbaleshi ya marairaice mata fuska.
"Saken g'yale toh..
Murmushi yake yaki saka, ''ka
saken gyale koh na fuce...
Da sauri ya cika yana
tare kofar fitar.
"Maganar fahimta nake so muyi dake,dan Allah ki
t'saya..
Hannu ta hard'e a kirji ta k'alleshi,itama zata so
su fahimci juna.
"Ina wuni toh,tunda har gaisuwa kin soke dani.
Da kalar tausayi ya kara yana sukui da kai har
taso yin dariya kamin ta gaishe shi.
"Ina Miemie?.
"Da Mama suka fita,kayi kai maganarka kan su
dawo fa.
Tsayuwa ya gyara tukun ya kira sunanta, rai sake
ta amsa,fatan ta yasa zancen azziki zai mata ba
wai shirme ba.
"Salma"..
A karo na biyu ya kara kiranta, bai jira
amsarta ba ya cigaba,
"Gobe zanje Zaria kan batun makaranta da zan
fara, kima Allah Salma ki yi kamar ina nan dan
Allah,banda kula tsagerun samarin nan wanda
har yau basu mallaki hankalin kansu ba dan
Allah.
"In ma aure naso kiyi ina ga ni ya dace na baki
mijin aura,bare a agendar mu bamuyi haka dake
ba...
T'sam tai tana kallonshi da halamun ya zare tana
murmushi, amma zata bishi a haka a wanye
lafiya.
"Toh naji,zan kuma kiyaye,happy?..
Kai ya kad'a da murmushi, "yauwa koh ke fa,dan
Allah Salma ki riken alkawari nan..
Kai ta kad'a tana taji ai..
Da haka suka rabu ya
bata kayan zakin Miemie, murna fal ranshi suka
rabu ranar.
K'warai ta samu sakewa sosai bayan tafiyar
shi,tuni ta kara bud'e shafin zawarci sabo,duk da
kasan ranta tausayinshi take ji sosai.
A wata daya tai samari biyu irin son Mama, barin
Alhaji Usman Dan chanji.
Kud'i sosai yake kar mata kamar ba gobe,
albarka kwa kullum samunta take gun
Mama,yace shi ba yaro bane,dan haka yana so ai
auren cikin k'ank'anin lokaci.
Ya sanar mata yana da mata daya da yara biyu
kachal,aurenshi uku,sun rabu da biyu sai Hajiya
ta k'arfen.
Tunda suka rabu tazo gida tana tuna abu uku,
tabbas a yanzu bata da ra'ayin auren mey
mata,dan taga aya akan Bintu.
Sannan bata son mutum mai irin kud'in Alhaji
Usman sam a rayuwarta.
Gwara ma Kamal dan shi matashi ne kamar su
Ja'afar, kuma yafi kwanta mata a rai,gashi da
saukin hali da saukin kud'i.
"Oh ni y'an nan,ashe arziki ke binki Salma a
rayuwa?..
K'allon Maman take yadda take daga abubuwan
da Alhaji ya bata,ita dey nata ido.
"Bana jin koh lokacin y'an matancinku kun ta6a
had'uwa da irin wannan, babbar harka ai tayi y'an
nan...
"Mama ni fa mutumin nan bai kwanta min ba
sam Allah,gashi har ya fara maganar aure tun
yanzu,ga yana da mata fa,ga ni sam irin kud'in
nan baya...
Baki sake Mama ke k'allonta,tuni ta tsayarta
cikin fad'a.
"Rufe baki ni sauraniyar y'an iya t'sari, ashe har
yau kina nan da halin nan Salma?
Arziki na binki
kina zura da gudu?..
"Ina ruwanki da matarshi?..
Koh a kanta zaki
zauna?..
Kai ta girgiza zatai magana ta dakatar ta.
"Koh dai Salma hudubar yaron chan tai tasiri
akanki?..
Kai ta kad'a,
"Allah Mama ba haka bane,ni ina tsoron kishiya
ne,kinaji fa wai aurenshi uku suna rabuwa sai ita
ke zama...
"Sai mey toh?..
Kar ki bada mata mana Salma?..
Baki sake take k'allon Maman,kamar ba ita ke
fad'in ba mai zama da kishiya ba a yaranta tunda
itama bata zauna ba,wace daga ce ba'aci ba
lokacin auren Bintu da Ja'afar amma yanzu kud'i
ya warware Mama?...
Kat'seta tai,
"Saboda haka komai yace ki ce toh, in ma ita ke
fidda su toh ke zama daram,dan wannan ba
gidan fita bane in an shiga...
Hawaye ke zubar mata yayin da tazo k'wanciya
tana tariyo zancen Mama, dole in dai tana son
faranta mata wai ta ba wa Alhaji dama.
Waya ta d'auka jin shigowar text message,tasan
na Ja'afar ne.
_"Salmatee,remember, a heart dat truly loves
never loses hope..but always believes in d
promise of love,no matter how long d time and
how far d distance,at d right time,love will fine a
way".._ ki rike alkawarin ki,love you..
*Ja'afar*
Kukanta ne ya karu sosai bayan ta gama
karantawa, tabbas in ta cigaba da sauraran
kalaman Ja'afar zasu sa ta karaya har ya ci
galaba akanta..
"Bani da kamar ka har kullum Ya Ja'afar, sonka
gareni ba mai misaltuwa bane,amma kai kaja
mana koma meye...
Fuska ta goge sakamakon jin tahowar Mama da
Miemie na kuka.
Washegari kanta t'saye ta bawa Alhaji damar ya
turo magabatanshi kawai koh ta huta da
dawainiya da son Ja'afar.
Sabon sim ta siya tasa a sabon wayar Alhaji da
ya bata,a haka suka raka wata kusan biyu, duk
da tai kewar text da kiran Ja'afar din.
Shikam yana chan hankali tashe na rashin samun
wayar Salma, ga Abba ya sanarshi kar ya sake
ya dawo sai an nemeshi a makaranta,
Duk da an sanarshi ana kawo Miemie gidansu ta
yini.
A jikinshi yaji abu na faruwa,duk sai yaji bai da
nut'suwa sai ya je gida dan tabbatar da
zarginshi.
Tunda daga d'anno kanshi layin su Salman ya ja
ya t'saya.
T'saye take da dan murmushi a
fuskarta, sanye cikin favorite dinshi riga da skirt
na atamfa purple, tai kyau matuka gyalen nan a
kafada,daga inda yake zai iya gano bakin
gashinta a tufke ta chan kasan dankwalinta,
tasha ado tamkar zata party.
Wani abu ne yazo dai dai makogwaronshi ya
tsaya,kishi...
Bai san ya isa gun ba sai da yaji ana "lafiya?..
Kallo shi yayi, duk sai yaji yau baida ma k'warin
g'wiwar fad'a,Salman ya kalla,da sauri ta kawar
da fuskarta gefe ta had'e rai.
Sai ya dawo kan Alhajin,tsaf sai ya haifi
Salma,sai t'sabar kud'i da jindadi da suka 6oye
shekarunshi.
Kallonshi yake tun daga sama har zuwa kafa, so
yake ya gano ta inda ya fishi har Salma ke mishi
murmushi haka.
A zuciya yace
"Babu...
Sai dai kud'i kawai da sa kaya masu
t'sada.
"Kai fa,daga ina ba koh sallama?..
Cike da haushi ya kallota, "baki sanarshi ko ni
waye ba ne?..
Kan Alhaji ya dawo,ba shakku
yace "matata ce ita,zaifi mana k'yau in ka daina
zuwa gunta Alhaji.
Murmushi yayi Alhajin,kan ya kallo Salman, "sai
kinji ni kawai..
A takaice ya k'alli Ja'afar din,ba
sai an fada mishi waye ba,halamu ya nuna
tsohon mijinta ne,har zaga wa tai ta rufe mishi
tana daga mishi hannu d'auke da murmushi, har
ya kule tana daga mishi hannu kan ta d'au
kayanta koh ta kanshi bata tai hanyar gida,da
zafin nama.
"Wato abinda ki ke kenan tun bayan tafiya ta
shine yasa ki ka kashe waya?
Salma mey yasa
kike son ki 6ata min rai wai?..
Jibi fa shigar ki,ji
gashi a waje,wace iriyar rayuwa ki ka za6a
mana?
Cike da fada tace
"Wace iriyar ka za6arwa kanka dai Ja'afar..
Ya
zaka zo kana fad'an wata iriyar magana mijin da
zan aura?..
Karan nan bazan dau abinnan naka
ba wallahi, aure zamuyi dashi nan da wata biyu...
Sai kayi abinda zaka yi.
Feenat Ja'afar.
[8/7, 11:07 AM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN
AURANKI*
Feenat Ja'afar*.
36_Kan yai k'wak'waran mot'si ta shiga gida tare
taru kofa harda sa sakata.
Jiginna tai hawaye na neman zubo mata,daga
yar bular dake jikin kofar ta leka waje,kofar gidan
yake kallo jiki a sanyaye kamar yasa kuka,juyawa
tayi hawayen dake makale mata ya zubo,dak'yar
ta seta kanta ta shiga ciki rai cike da tausayin
Ja'afar.
Kusan kullum zai zo ba zuciya dan bata baki
akan Alhaji tana mishi wulakanci,shi kam Alhajin
har dariya yake bashi wani sa'in, dan baijin da
abinda zai iya rabashi da Salma a dai dai lokacin
nan,sai dai jin saki uku ne kawai sai ya bar jin
komai,iyaka ma yai ta tusa ma Ja'afar din bakin
ciki in ya gansu da kalamai ma Salman.
Biki ya karato ga makaranta,amma haka duk
week end daga Zaria zai zo kan batun Salma ta
janye zancen bikin nan.
Duk ya fita a hayyacinshi duk akan auren Salma.
Da halamu ya fara hankalin daina zuwa gun
Alhajin,sai dai in yazo ya tsaya chan gefe sai
tazo shiga ya tare ta da magiya.
Yau saura k'wana biyu biki, sai gashi shi da
Garba,dawowarsu daga gidan g'yaran jiki kenan
ita da Ummi.
Turus ta ja ta t'saya ganin Ummi ta wuce ita ya
tare mata hanya.
"Ka ga yau bani da lokacin jin wannan
mahaukatan zantukan naka,jibi iyanzu na d'aura
aure, ya kamata kasan inda dare ya maka,
sabuwar rayuwa zan fara,saboda haka kai yanzu
ya rage ma,danni yanzu baka gabana...
Kai ya kad'a mata,
"Karan nan bazan hanaki aure ba Salma,sai dai
ba da Alhaji ba.
Baki sake take kallonshi, Garba ya nuna,
"Garba zaki aura Salma,kimin wannan alfarmar.
Kai ta dauke daga kallonshi ta k'alli Garban
wanda shima ya cika da al'ajabin kan maganar
Ja'afar.
Sai ta girgiza kai da murmushin takaici.
"Tanan kuma ka bullo min?..
Auren kisan wuta
Ja'afar?
Lalle kayi nisa ba zakaji kira ba.
Bayab hannunta tasa tana goge hawayen idonta.
"Wai ka zata ni din auren kisan wuta zanyi da
wanda zan aura?..
Kai ta kara kadawa,
"Kai kuskure toh,dan ni aure zanyi na tsakani da
Allah,ba wai nayi na fito ba Ja'afar..
"A'a Salma,ba haka ne nufi na ba..
Da muryar
kuka ta tareshi,
"Hakane man,haka kake nufi,wato ka kawo min
abokin ka na aura bayan wani lokaci ya sake ni
sai ka halartawa kanka ni koh?..
Baki sake duk suke k'allonta,ganin yadda hawaye
ke zubar mata.