Sashe 7
Yayan Miji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shiru ne ya ratsa na wasu 'yan mintuna zuwa can Baba yace "kina jina ko Aishatu, ni da kike ganina bazan yi miki dole ba hakanan kuma bazan zuba miki idanu kiyi ta zama babu aure ba don haka idan har kinsan akwai wanda kika tsayar kiyi gaggawar turoshi idan kuma babu to ki tabbatar da kin samu zaki gabatar dashi dimin kuwa har ga Allah zamannan naki a haka ba sonshi nakeyi ba".
Tace "In Sha Allahu Baba bazan baka kunya ba". Daga haka suka shiga hirar duniya. Bata bar dakin Baba ba sai kusan karfe sha daya. Dakin Goggo ta shiga tayi shirin kwanciya sannan ta kwanta.
Tunda ta fita da safe yawon gaishe-gaishe bata dawo gida ba sai gaf da sallar magriba. Sosai take cikin gajiya. Ko don ta dade ba tayi yawo irin haka ba gaba daya sai taji jikinta yana mata ciwo.
A ranar da ta kwana biyu da zuwa gida wurin karfe sha biyu na rana suna zaune da Goggi, gyaran zogalen da Goggo zatayi dambu takeyi. Yarone ya shigo yace wai ana sallama da ita. Mamaki ne ya kamata, waye kuwa zaiyi sallama da ita da safennan. Ita wa ma ta sani da har za'azo wurinta.
Ganin bata da niyyar amsawa ne yasa Goggo tacewa yaron kace tana zuwa sanna ta cewa Aisha "tashi kije ki ga waye, ai ba'a san inda za'a dace ba". Kasancewar tayi wanka tun tashinta, sanye take cikin atamfar Holland dinkin riga da zani. Hijabi kawai ta saka ta fita don ganin mai sallama da ita.
Mallam Adamu ta gani zaune cikin mota. Cikin sassarfa ta karasa wajenshi, tana zuwa ki gaishe shi batayi ba ta tambayeshi lafiya. Murmushi yayi sannan yace "lafiya lau Mami ce tace nazo na daukeki" "Mami fa kace kuma lafiya Mallam Adamu ka tabbata" ta tambayeshi fuskarta dauke da mamakin jin cewar Mami tace a zo a dauketa ganin sun rabu ne akan zatayi sati daya kafin ta koma. Yace "lafiya lau kawai dai tace ne nazo na daukeki". To ina zuwa tace mishi sannan ta juya zuwa cikin gidan.
Sanarwa da Goggo tayi batun tafiyarta. Itama Goggo tarrarrabi takeyi cewa anya kuwa lafiya. Daki Aisha ta shiga ta hada kayanta sannan ta fito tayi sallam da Goggo tana cewa ta fadawa Babanta batun tafiyarta idan ya dawo. A sosron gidan sukayi kacibis da Baba, kafin tayi Mayans ya rigata da cewa "naga Mallam Adamu yazo daukarki ko, Allah ya kiyaye hanya ki gaida mutanen gidan. Tace "amin Baba fatana dai Allah yasa lafiya" yace "lafiya lau kawai dai bata ji dadi bane Mamun taku amma yace jikin da sauki".
Sallam Ragusa Baba sannan ta wuce mota suka dauki hanyar kano. Hakanan taji gabanta na faduwa don haka ta fiddo da AlQur'ani daga jakarta tana karantawa. Sai da suka isa kano sannan ta rufe AlQur'anin ta mayar cikin jaka.
Suna shiga layin gidansu taga cincirondon motoci a kofar gidansu. Mummunar faduwar gaba ce ta sameta, cikin rawar murya tace "Mallam Adamu me je faruwa ne, don Allah ka gaya mini". Cikin dakewa Mallam Adamu yace mata "sai dai muyi hakuri Aisha Hajiya Mami Allah yayi mata rasuwa jiya da darea sanadiyar ciwon ciki".
Sandarewa kawai Aisha tayi a zaunen da take ta rasa gane ne kunnuwanta suka jiye mata. Wani irin kuka ne yazo mata, kifa kanta kawai tayi akan cinyoyinta tana kuka. Mami wai Maminta ce ta rasu. Mamin data tafi ta bari cikin koshin lafiya ashe bazata dawo ta tarar da ita ba. Wannan rayuwar abar tsoro ce, wato tsakanin rayuwa da mutuwa dan takin kalilan ne ( Allah yasa muyi kyakkyawan karshe, Amin).
Ta dade a zaune cikin motar kafin tayi karfin halin fitowa, gidan a cike yake da mutane 'yan karbar gaisuwa. Ta kofar kitchen tabi ta shiga cikin gidan. A parlour ta tarar dasu Hajiya da Hajiyarsu Mami da wasu daga cikin 'yanuwanta. Durkushewa tayi kawai a wurin tana wani irin kuka, mutanen wurin gaba daya suka hau bata hakuri.
Da kyar ta iya tsaida kukan tayiwa su Hajiya gaisuwa sannan ta tashi ta haya sama zuwa dakinsu. Su Ummie ne a dakin tare da kawayensu. Tana shiga Ummie ta taso ta rungumeta tare da fashewa da kuka, itama Aisha kukan takeyi.
UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): 👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
'YA'YAN MIJI
👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
Na Umm Asghar
13
Mutuwar Mami ba karamin girgiza al'ummar gidan tayi ba tun daga kan maigidan zuwa yaran gidan da ma'aikatan gidan gaba daya. Ga Aisha kam ko mutuwar mahaifiyarta bata shigeta haka ba ko don lokacin da mahaifiyarta ta rasu bata mallaki hankalinta kanta ba.
A cikin kwanaki bakwai da akayi ana karbar gaisuwa sunga tururuwar jama'a 'yan zuwa ta'aziyya. Kodayake Mami ta mutane ce, fata dai a koyaushe shine halinta na gari ya bita.
A bangaren Aisha ma Babanta da Goggo da Yaya Huwaila ne suka zo musu ta'aziyya don Goggo ma da Yaya Huwaila zama sukayi har saida akayi sadakar uku sannan suka koma.
Bayan anyi sadakar bakwai ne kowa ya watse sai suka ji gidan yayi musu fadi. A wannan lokacin ji sukayi mutiwar ta dawo musu sabuwa tamkar a lokacin akayi ta.
Sauki daya da suka samu shine da Hajiya bata koma gidanta ba taci gaba da zama dasu to sai dai suma sun sani zamanta dasu ba mai daurewa bane.
A ranar da Mami tayi kwana ashirin da hudu da rasuwa ne Aisha na tare da Hajiya a dakin da Hajiyan ta sauka. Man zafi take shafa mata a kafafunta kasancewar tana fama da larurar ciwon kafa.
Daddy ne yayi sallama ya shigi ckin dakin. Amsa mishi Aisha tayi sannan ta gaisheshi ta tashi ta fita. Zama yayi a kasa ya jingina da jikin gadon sannan yace "Hajiya barka da dare an yini lafiya" "lafiya lau Alhamdulillahi" Hajiya ta amsa mishi "ya hidimomi, yanzu ka dawo hala?"
Yace "eh Hajiya komai lafiya lau mun gode Allah. Ya kafartaki, tana matsa miki ne har yanzu ko sai kun koma asibiti". Lankwashe kafafuwan tayi tace "a'a basa mini wani ciwo ai naji dadin maganin da aka canja mini a asibitin, sai dai dama akwai maganar da nakeso muyi".
Gaba daya ya tattara nutsuwarshi zuwa ga Hajiya don daga yanayin yadda ta mishi magana yasan maganar da zata fada mai muhimmanci ce sosai.
"Kana jiko dama akan maganar yarinyar nan ne Aisha, da iyayenta suka zo gaisuwa mahaifinta ya bukaci da ta koma gabanshi tunda ta gama karatu gashi uwar rikonta Allah yayi mata rasuwa. Ta na dai ce mishi ya dakaceni kadan In Sha Allahu zan nemeshi akan maganar".
Ta dan numfasa sannan ta cigaba da cewa " ni ina ganin mai zai hana ka aureta ta maye maka gurbin Zainab ko babu komai kasanta kasan halinta tunda tarbiyyarkuce kuma zata zamewa 'ya'yanka uwa tunda akwai shakuwa sosai a tsakaninsu, bama dai Ruqaiya da Zainab don sunfi sauran bukatar uwa amma kasancewar su da Aisha maraicin da zasuyi kalilan ne".
Tunda Hajiya ta ambata mishi aure yaji wata iriyar zufa ta keto mishi hankalinshi ya tashi yawun bakinshi gaba daya ya kafe ya rasa mai zaicewa Hajiya. Da kyar ya samu ya tattaro dauriya yace " Hajiya wani irin aure a yanzu kuma da yarinyar nan Aisha, ai 'yata ce kamata yayi ace ni zan aurar da ita ba wai ni na aureta ba".
Tsuke fuska Hajiya tayi ta bata rai sannan cikin kausashiyar murya tace "wace irin magana ce kakeyi haka, haram ne auren Aishar ko menene, kuma da kake maganar aure yanzu wuri yayi maka ko me. Idan bakayi aure yanzu ba sai yaushe zakayi. Kasan dai ni bazan cigaba da zama maka a gida don na kula maka da yaraba dole suna bukatar uwa bama dai kananun kuma a ganinka akwai wacce tafi dacewa da zame musu uwa fiye da Aisha ne. Yarinyar da tun haihuwarsu take faman hidima dasu. Kuma ni nayi maka sha'awar aurenta ne saboda yarinyar mutuniyar kirki ce sosai zakaji dadin zama da ita don bata da raini kwatakwata bata da rawar kai irin ta 'yanmatan yanzu. Amma bazan tursasaka akan abin da bakayi niyya ba tunda bakaso shikenan fatana Allah ya hadaka da abokiyar rayuwa ta gari, Allah ya jikan Zainab"
Tunda ya sunkuyar da kanshi ya kasa dagowa don gaba daya sai yaji mutuwar Zainab ta dawo mishi sabuwa, rashin Zainab da yayi ne yasa har Hajiya keyi mishi maganar aure a cikin kasa da kwana da talatin da mutuwarta kuma auren ma da karamar yarinya 'yar cikinshi da bata wuce sa'ar Mu'azzam ba danshi na biyu bama Khalifa ba.
Tunda ya mallaki hankalin kanshi bazai iya tuna wata rana da yayiwa Hajiya musu akan wata bukatarta ba don haka bazai fara daga yanzu ba.
Aure tace tana so yayi to In Sha Allahu zaiyi da kuma yarinyar da takeso. Kamar yadda tace ne yaranshi sunyi sabo da yarinyar sosai, sai dai har cikin ranshi yasan zaiyi auren nan ne kawai don farin cikin Hajiya bawai don yana ra'ayi ba, shikam matarshi daya ce Zainab babu wata diya mace da zata iya maye mishi gurbinta.
Dauke kai Hajiya tayi tayi tamkar bata san da dashi a zaune ba. Ta san har ga Allah bada wani abu tace yayi aure ba sai don sanin cewa auren ne zai sama mishi nutsuwa ya dauke mishi damuwar da yake ciki ta rashin Zainab.
Kuma da tace ya auri Aisha tasan itace kawai zata iya hakurin zama da yaranshi tunda ba yau suka fara zama tare ba amma mawuyacin abu ne yayi dace da matar kwarai da zata kula mishi da yara tsakaninta da Allah bare da ya kasance mai ido ne shi akan harkar yaranshi ba kiwacce mace bace zata iyayin hakuri da halinsu ba amma Aisha fa tasan halinsu ta kuma iya zama dasu tunda duk tsawon zamanta dasu ba'a taba jin kansu ba ta kuma dade da sanin cewa ba dadin zama dasu take jiba tun ma ba Farida ba da Mu'azzam dama kuma sune fitinannun.
Tace "In Sha Allahu Baba bazan baka kunya ba". Daga haka suka shiga hirar duniya. Bata bar dakin Baba ba sai kusan karfe sha daya. Dakin Goggo ta shiga tayi shirin kwanciya sannan ta kwanta.
Tunda ta fita da safe yawon gaishe-gaishe bata dawo gida ba sai gaf da sallar magriba. Sosai take cikin gajiya. Ko don ta dade ba tayi yawo irin haka ba gaba daya sai taji jikinta yana mata ciwo.
A ranar da ta kwana biyu da zuwa gida wurin karfe sha biyu na rana suna zaune da Goggi, gyaran zogalen da Goggo zatayi dambu takeyi. Yarone ya shigo yace wai ana sallama da ita. Mamaki ne ya kamata, waye kuwa zaiyi sallama da ita da safennan. Ita wa ma ta sani da har za'azo wurinta.
Ganin bata da niyyar amsawa ne yasa Goggo tacewa yaron kace tana zuwa sanna ta cewa Aisha "tashi kije ki ga waye, ai ba'a san inda za'a dace ba". Kasancewar tayi wanka tun tashinta, sanye take cikin atamfar Holland dinkin riga da zani. Hijabi kawai ta saka ta fita don ganin mai sallama da ita.
Mallam Adamu ta gani zaune cikin mota. Cikin sassarfa ta karasa wajenshi, tana zuwa ki gaishe shi batayi ba ta tambayeshi lafiya. Murmushi yayi sannan yace "lafiya lau Mami ce tace nazo na daukeki" "Mami fa kace kuma lafiya Mallam Adamu ka tabbata" ta tambayeshi fuskarta dauke da mamakin jin cewar Mami tace a zo a dauketa ganin sun rabu ne akan zatayi sati daya kafin ta koma. Yace "lafiya lau kawai dai tace ne nazo na daukeki". To ina zuwa tace mishi sannan ta juya zuwa cikin gidan.
Sanarwa da Goggo tayi batun tafiyarta. Itama Goggo tarrarrabi takeyi cewa anya kuwa lafiya. Daki Aisha ta shiga ta hada kayanta sannan ta fito tayi sallam da Goggo tana cewa ta fadawa Babanta batun tafiyarta idan ya dawo. A sosron gidan sukayi kacibis da Baba, kafin tayi Mayans ya rigata da cewa "naga Mallam Adamu yazo daukarki ko, Allah ya kiyaye hanya ki gaida mutanen gidan. Tace "amin Baba fatana dai Allah yasa lafiya" yace "lafiya lau kawai dai bata ji dadi bane Mamun taku amma yace jikin da sauki".
Sallam Ragusa Baba sannan ta wuce mota suka dauki hanyar kano. Hakanan taji gabanta na faduwa don haka ta fiddo da AlQur'ani daga jakarta tana karantawa. Sai da suka isa kano sannan ta rufe AlQur'anin ta mayar cikin jaka.
Suna shiga layin gidansu taga cincirondon motoci a kofar gidansu. Mummunar faduwar gaba ce ta sameta, cikin rawar murya tace "Mallam Adamu me je faruwa ne, don Allah ka gaya mini". Cikin dakewa Mallam Adamu yace mata "sai dai muyi hakuri Aisha Hajiya Mami Allah yayi mata rasuwa jiya da darea sanadiyar ciwon ciki".
Sandarewa kawai Aisha tayi a zaunen da take ta rasa gane ne kunnuwanta suka jiye mata. Wani irin kuka ne yazo mata, kifa kanta kawai tayi akan cinyoyinta tana kuka. Mami wai Maminta ce ta rasu. Mamin data tafi ta bari cikin koshin lafiya ashe bazata dawo ta tarar da ita ba. Wannan rayuwar abar tsoro ce, wato tsakanin rayuwa da mutuwa dan takin kalilan ne ( Allah yasa muyi kyakkyawan karshe, Amin).
Ta dade a zaune cikin motar kafin tayi karfin halin fitowa, gidan a cike yake da mutane 'yan karbar gaisuwa. Ta kofar kitchen tabi ta shiga cikin gidan. A parlour ta tarar dasu Hajiya da Hajiyarsu Mami da wasu daga cikin 'yanuwanta. Durkushewa tayi kawai a wurin tana wani irin kuka, mutanen wurin gaba daya suka hau bata hakuri.
Da kyar ta iya tsaida kukan tayiwa su Hajiya gaisuwa sannan ta tashi ta haya sama zuwa dakinsu. Su Ummie ne a dakin tare da kawayensu. Tana shiga Ummie ta taso ta rungumeta tare da fashewa da kuka, itama Aisha kukan takeyi.
UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): 👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
'YA'YAN MIJI
👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
Na Umm Asghar
13
Mutuwar Mami ba karamin girgiza al'ummar gidan tayi ba tun daga kan maigidan zuwa yaran gidan da ma'aikatan gidan gaba daya. Ga Aisha kam ko mutuwar mahaifiyarta bata shigeta haka ba ko don lokacin da mahaifiyarta ta rasu bata mallaki hankalinta kanta ba.
A cikin kwanaki bakwai da akayi ana karbar gaisuwa sunga tururuwar jama'a 'yan zuwa ta'aziyya. Kodayake Mami ta mutane ce, fata dai a koyaushe shine halinta na gari ya bita.
A bangaren Aisha ma Babanta da Goggo da Yaya Huwaila ne suka zo musu ta'aziyya don Goggo ma da Yaya Huwaila zama sukayi har saida akayi sadakar uku sannan suka koma.
Bayan anyi sadakar bakwai ne kowa ya watse sai suka ji gidan yayi musu fadi. A wannan lokacin ji sukayi mutiwar ta dawo musu sabuwa tamkar a lokacin akayi ta.
Sauki daya da suka samu shine da Hajiya bata koma gidanta ba taci gaba da zama dasu to sai dai suma sun sani zamanta dasu ba mai daurewa bane.
A ranar da Mami tayi kwana ashirin da hudu da rasuwa ne Aisha na tare da Hajiya a dakin da Hajiyan ta sauka. Man zafi take shafa mata a kafafunta kasancewar tana fama da larurar ciwon kafa.
Daddy ne yayi sallama ya shigi ckin dakin. Amsa mishi Aisha tayi sannan ta gaisheshi ta tashi ta fita. Zama yayi a kasa ya jingina da jikin gadon sannan yace "Hajiya barka da dare an yini lafiya" "lafiya lau Alhamdulillahi" Hajiya ta amsa mishi "ya hidimomi, yanzu ka dawo hala?"
Yace "eh Hajiya komai lafiya lau mun gode Allah. Ya kafartaki, tana matsa miki ne har yanzu ko sai kun koma asibiti". Lankwashe kafafuwan tayi tace "a'a basa mini wani ciwo ai naji dadin maganin da aka canja mini a asibitin, sai dai dama akwai maganar da nakeso muyi".
Gaba daya ya tattara nutsuwarshi zuwa ga Hajiya don daga yanayin yadda ta mishi magana yasan maganar da zata fada mai muhimmanci ce sosai.
"Kana jiko dama akan maganar yarinyar nan ne Aisha, da iyayenta suka zo gaisuwa mahaifinta ya bukaci da ta koma gabanshi tunda ta gama karatu gashi uwar rikonta Allah yayi mata rasuwa. Ta na dai ce mishi ya dakaceni kadan In Sha Allahu zan nemeshi akan maganar".
Ta dan numfasa sannan ta cigaba da cewa " ni ina ganin mai zai hana ka aureta ta maye maka gurbin Zainab ko babu komai kasanta kasan halinta tunda tarbiyyarkuce kuma zata zamewa 'ya'yanka uwa tunda akwai shakuwa sosai a tsakaninsu, bama dai Ruqaiya da Zainab don sunfi sauran bukatar uwa amma kasancewar su da Aisha maraicin da zasuyi kalilan ne".
Tunda Hajiya ta ambata mishi aure yaji wata iriyar zufa ta keto mishi hankalinshi ya tashi yawun bakinshi gaba daya ya kafe ya rasa mai zaicewa Hajiya. Da kyar ya samu ya tattaro dauriya yace " Hajiya wani irin aure a yanzu kuma da yarinyar nan Aisha, ai 'yata ce kamata yayi ace ni zan aurar da ita ba wai ni na aureta ba".
Tsuke fuska Hajiya tayi ta bata rai sannan cikin kausashiyar murya tace "wace irin magana ce kakeyi haka, haram ne auren Aishar ko menene, kuma da kake maganar aure yanzu wuri yayi maka ko me. Idan bakayi aure yanzu ba sai yaushe zakayi. Kasan dai ni bazan cigaba da zama maka a gida don na kula maka da yaraba dole suna bukatar uwa bama dai kananun kuma a ganinka akwai wacce tafi dacewa da zame musu uwa fiye da Aisha ne. Yarinyar da tun haihuwarsu take faman hidima dasu. Kuma ni nayi maka sha'awar aurenta ne saboda yarinyar mutuniyar kirki ce sosai zakaji dadin zama da ita don bata da raini kwatakwata bata da rawar kai irin ta 'yanmatan yanzu. Amma bazan tursasaka akan abin da bakayi niyya ba tunda bakaso shikenan fatana Allah ya hadaka da abokiyar rayuwa ta gari, Allah ya jikan Zainab"
Tunda ya sunkuyar da kanshi ya kasa dagowa don gaba daya sai yaji mutuwar Zainab ta dawo mishi sabuwa, rashin Zainab da yayi ne yasa har Hajiya keyi mishi maganar aure a cikin kasa da kwana da talatin da mutuwarta kuma auren ma da karamar yarinya 'yar cikinshi da bata wuce sa'ar Mu'azzam ba danshi na biyu bama Khalifa ba.
Tunda ya mallaki hankalin kanshi bazai iya tuna wata rana da yayiwa Hajiya musu akan wata bukatarta ba don haka bazai fara daga yanzu ba.
Aure tace tana so yayi to In Sha Allahu zaiyi da kuma yarinyar da takeso. Kamar yadda tace ne yaranshi sunyi sabo da yarinyar sosai, sai dai har cikin ranshi yasan zaiyi auren nan ne kawai don farin cikin Hajiya bawai don yana ra'ayi ba, shikam matarshi daya ce Zainab babu wata diya mace da zata iya maye mishi gurbinta.
Dauke kai Hajiya tayi tayi tamkar bata san da dashi a zaune ba. Ta san har ga Allah bada wani abu tace yayi aure ba sai don sanin cewa auren ne zai sama mishi nutsuwa ya dauke mishi damuwar da yake ciki ta rashin Zainab.
Kuma da tace ya auri Aisha tasan itace kawai zata iya hakurin zama da yaranshi tunda ba yau suka fara zama tare ba amma mawuyacin abu ne yayi dace da matar kwarai da zata kula mishi da yara tsakaninta da Allah bare da ya kasance mai ido ne shi akan harkar yaranshi ba kiwacce mace bace zata iyayin hakuri da halinsu ba amma Aisha fa tasan halinsu ta kuma iya zama dasu tunda duk tsawon zamanta dasu ba'a taba jin kansu ba ta kuma dade da sanin cewa ba dadin zama dasu take jiba tun ma ba Farida ba da Mu'azzam dama kuma sune fitinannun.