Sashe 13
Yayan Miji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ita kuma Farida me mata ne ta samu, ya dade yana sonta tana share shi duk da son data ke mishi sai dai kuma rashin son auren mai mata yasa bata wani kula shi. Ganin Daddy ya dibar musu takaitaccen lokaci don su fitar da miji yasa ta amince da aurenshi.
Duka manemannasu sun turo magabatansu an tsaida magana don haka aka yanke lokaci watanni uku masu zuwa daidai da lokacin da aka yanke na auren Khalifa.
Tunda lokacin bikinnan ya matso Aisha bata samu zama ba don kuwa hidima tayi mata yawa. Komai na harkar bikin a hannunta Daddy ya damka shi duk da dai amaren basu so hakan ba to amma babu yadda zasuyi.
Kullum cikin fita sayyaya suke tun daga kan furniture zuwa kayan kitchen dasu rugs da labulaye har kan kayan decoration na gida da kuma kayan da zasu saka na biki.
Ita ma kuma Aisha bata bashi kunya ba don kuwa ta tsaya taga anyi musu kaya na fita kunya duk da dai kowacce ra'ayinta aka bi wajen sayen kayan.
A wajen karbar kudin events din biki ne Daddy yayi musu jan ido don kuwa kudaden da suka nema a wurinshi sunyi yawa don events suka shirya zasuyi na rashin hankali a kalla sun tsara yin events sunkai shida. Dole suka rage events din zuwa guda uku.
Kowanne event sun fitar mishi da anko tun daga kan kamu da yini jar luncheon da dinner da zasuyi kuma duka masu tsada nan ma da kyar Daddy ya yarda yayi wa su Ruqaiya don yace abin yayi yawa su kuma yaran ba tausayinshi suke yi ba sun manta cewar hidimar auren 'ya'ya uku ne a gabanshi.
An fara bikin ne da kamu inda suka shirya yinshi anan cikin gidan inda amare sukayi shigar atamfa super exclusive akayi musu dinkin zannuwa falle biyu sai polo shirt da suka hada da zanin suka rufa da dayan zanin. Suma 'yammata ankon Zanin atamfar Julius holland sukayi da polo shirt din.
Anci abinci na alfarma an zubarwa da makada naira inda amare suka zage sukayi ta tikar rawa tamkar dai ba amaren ba.
Kasancewar kamun da yamma akayi yasa Maman Farida ta shirya musu mothers night a meena event center.
An kawo wa Aisha cards guda biyar nata dana wadanda zata gaiyata, Farida ce ta tura Zainab ta kai mata cards din a lokacin tana kitchen tana aiki tana jin Faridan na fadawa Ummie cewa wai wallahi da Mummynta tayi shawara da ita bazata bawa Aisha kati ba don har yanzu da takaicinta a ranta duk lokacin data tuna cewa Daddy bai taba daga musu murya ba sai akanta.
Dariya kawai Aiaha tayi don tasan dama Farida ta sama mata lafiya daga rashin mutuncinta ne don tasan yanzu Daddy bazai yadda da iskancinsu ba.
Ko lokacin data basu gudunmawarta ta sarka gold kirar dubai data saya musu Farida karba kawai tayi babu godiya sai cewa da tayi ai dole ne ma ta saka tunda dai tasan da kudin ubanta aka saya, ko a lokacin Aisha bata kalleta ba don tasan duk abinda zata yi mata na dan lokaci ne.
Anyi mothers night din inda amare sukayi shiga cikin bridal lace da sukayi dinkin doguwar riga. Komai da suka saka iri daya ne sai colour data bambanta. Ita Farida tayi amfani da colour fari da blue yayinda Ummie tayi olive green da orange.
Tunda aka fara bikinnan Aisha bata zauna ba ga hidimar yara gata Daddy da kullum cikin yi mata korafi yake yana cewa tunda ta fara hidimar auren 'ya'yanta ta manta dashi.
Gaba daya hidimar bikinnan ta gajiyar da ita. A ranar asabar ne bayan an daura aure ta shirya musu walimah inda aka gaiyato malamai sukayi wa'azi sosai akan hakkin miji akan matarshi da kuma hakkin matar akan mijinta da zama da abokiyar zama.
Da yamma ne aka kai amare gidajensu. Ita dai Ummie an kaita redbricks ne yayinda Farida aka kaita lamido crescent. Ita kuma amayar Khalifa nan unguwarsu aka kawota gidanshi babu nisa da gidan iyayenshi.
*****
Asghar da Sajjad nayi muku barka da sallah da fatan Allah ya maimaita mana ya amshi ibadunmu. Sorry for the long silence wallahi tunda na Sligo kano sallah ban samu zama ba.
UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): 👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
'YA'YAN MIJI
👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
Na Umm Asghar
21
A yanzu da akayi wa su Farida aure Aisha bata da wata matsala a cikin gidanta don sosai Ruqaiya da Zainab ke yi mata biyayya kuma dama dai a yadda yaran suka taso tare da ita bata da matsala dasu.
An gama biki da sati biyu Daddy ya kwashi Aisha da yaranta masu watanni biyar suka tafi umrah sai Zainab da Ruqaiya kasancewar Yaran na hutu.
Mu'azzam kawai aka bari a gida don har lokacin Daddy ba wai ya huce daga fuahin da yakeyi dashi bane. A lokacin da Daddy yayiwa Aisha maganar tafiyarsu Umrah sosai tayi murna sai ta tuna lokacin da Farida tayi ta mata kafafa akan zasuyi tafiya su barta to itama yanzu gashi nata lokacin yayi don dama komai yana da lokacin.
Sosai Ruqaiya da Zainab ke taimaka mata wajen rainon twins, duk da Daddy na fadan yawan bawa yaran twins da take yi wai kar su kada su. Idan yana fadanshi kawai sai dai tayi dariya tana mamakin son 'ya'ya irin na Daddy shi komai a harkar yaranshi idonshi yana kai.
Sai dai ta sakawa ranta cewa ita kam bazata yadda ya bata mata yara ba irin yadda yayiwa su Ummie shine kuma dalilin da yasaka suke taka kowa ba tare da fargaba ba don sun san komai sukayi a wurin ubansu ba laifi bane.
Sai da sukayi sati uku sannan suka dawo gida nigeria, gaba daya a wannan lokacin Aisha ta canja ta kara yin kyau saboda kwanciyar hankali data samu ga uwa uba soyayya da kulawar mijinta data samu.
Bayan sati daya da dawowarsu ne Daddy yace ta shirya ta rakashi gidajensu Ummie yaje yaga dakunansu don tun da akayi auren bawai yaje bane.
Tayi shirinta cikin atamfar super exclusive kalar navy blue da ratsin fari da light yellow a jiki sai tayi amfani da farin mayafi da takalmi. Bata dauki jaka ba sai wayarta data rike a hannunta.
A gida ta bar twins qurin masu rainonsu kuma ganin su Ruqaiya na gidan yasa bata damu sai ta fita dasu ba.
Gidan Farida suka fara zuwa, Daddy yace ta shiga ta sanar musu da zuwan shi. Ta shiga cikin gidan da sallama, a main parlour su ta tarar da uwargidan Faridan tare da yaranta da maigidan.
Cikin girmamawa sosai matar ta karbeta duk da cewa zata iya girmewa Aisha. Bayan sun gaisa ne Aishan ke tambayar Farida tace mata tana dakinta ta saka yarinyarta ta raka Aisha.
Kafin su wuce ne Aisha ke sanar musu cewa tare da Daddy suke ai kuwa maigidan naji yayi hamzarin tashi yana cewa bari yaje ya shigo dashi.
Ta shiga dakin Farida tana ta kwala sallama amma ba'a amsa ba don haka ta zauna a parlour tacewa yarinyar ta shiga dakin ta yi mata magana. Ta shiga babu dadewa ta fito ta ce mata wai gata nan zuwa.
Tayi zaman fiye da mintuna goma kafin Farida ta fito tana yatsina fuska ta zauna. A dakile tace mata ina yini, lafiya kawai Aisha tace mata tace "tare muke da Daddynku yace na rakoshi yaga gidanku so yana kasa idan kinga dama kina iya zuwa ki gaisheshi".
Jin cewa yare suke da Daddy ya sa tayi saurin tashi ta fita. Ta dan jima kafin ta dawo, kamar bazata yiwa Aisha magana ba sai kuma tace mata "Daddy yace kije ku tafi" mikewa tayi ta ajiye mata ledar tsarabarta tace mata "to Allah ya bamu alkhairi" bata jira amsawarta ba ta fice.
Daga gidan Farida gidan Ummie suka nufa. Anan ma Daddy bai shiga ba. Ita kam Ummie ta karbeta da mutunci da murnarta har tana tambayarta twins tana cewa me yasa ba'a zo dasu ba.
Bayan sun gaisa ne take sanar mata cewa tare suke da Daddy. Sosai tayi murnar jin Daddy yazo gidanta. Tashi tayi ta shiga part din maigidan ta sanar mishi, babu wani dadewa kuwa ya fito.
Har kasa ya tsugunna ya gaida Aisha sannan ya fita don ya shigo da Daddy. A parlourshi ya saukeshi don haka can Ummie ta bishi ta gaidashi. Sun danfi dadewa a gidan Ummie sannan Daddy yace ta fito su tafi.
Itama ajiye mata tsarabarta tayi sannan sukayi sallama ta fita. Har wurin mota suka raka su sunata godiya. Ummie na rokon Daddy don Allah ya bari su Ruqaiya suzo mata don tunda akayi auren ya hanasu zuwa.
A hanyarsu ta komawa gida ne ya biya da ita grand square sai dai be yadda ta shiga ba, bayan ya fito ne ya miko mata leda mai dauke da turaruka designers guda uku. Sai kuma chocolates da biscuits na yara.
UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): 👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
'YA'YAN MIJI
👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
Na Umm Asghar
22
Tunda ta tashi yau bata zauna ba. Aiki takeyi kamar bazata gama ba. Ita kam wannan abu ya isheta ace aikin kenan kullum ta tashi bata da hutu, tace tana bukatar cook ance a'a ta bukaci house help nan ma yace mata a'a. Gashi yanzu ya kawo mata aikin girki wai zaiyi baki bayan duk wannan wahalar data keyi ta kuma san ba appreciating zaiyi ba don kullum tayi girki sai ya kushe. Ita kam har ga Allah bazata iya ba don ko a gidansu bata saba da aikin wahala ba kitchen kuwa kwata-kwata basa shigar shi da sunan girki.
Duka manemannasu sun turo magabatansu an tsaida magana don haka aka yanke lokaci watanni uku masu zuwa daidai da lokacin da aka yanke na auren Khalifa.
Tunda lokacin bikinnan ya matso Aisha bata samu zama ba don kuwa hidima tayi mata yawa. Komai na harkar bikin a hannunta Daddy ya damka shi duk da dai amaren basu so hakan ba to amma babu yadda zasuyi.
Kullum cikin fita sayyaya suke tun daga kan furniture zuwa kayan kitchen dasu rugs da labulaye har kan kayan decoration na gida da kuma kayan da zasu saka na biki.
Ita ma kuma Aisha bata bashi kunya ba don kuwa ta tsaya taga anyi musu kaya na fita kunya duk da dai kowacce ra'ayinta aka bi wajen sayen kayan.
A wajen karbar kudin events din biki ne Daddy yayi musu jan ido don kuwa kudaden da suka nema a wurinshi sunyi yawa don events suka shirya zasuyi na rashin hankali a kalla sun tsara yin events sunkai shida. Dole suka rage events din zuwa guda uku.
Kowanne event sun fitar mishi da anko tun daga kan kamu da yini jar luncheon da dinner da zasuyi kuma duka masu tsada nan ma da kyar Daddy ya yarda yayi wa su Ruqaiya don yace abin yayi yawa su kuma yaran ba tausayinshi suke yi ba sun manta cewar hidimar auren 'ya'ya uku ne a gabanshi.
An fara bikin ne da kamu inda suka shirya yinshi anan cikin gidan inda amare sukayi shigar atamfa super exclusive akayi musu dinkin zannuwa falle biyu sai polo shirt da suka hada da zanin suka rufa da dayan zanin. Suma 'yammata ankon Zanin atamfar Julius holland sukayi da polo shirt din.
Anci abinci na alfarma an zubarwa da makada naira inda amare suka zage sukayi ta tikar rawa tamkar dai ba amaren ba.
Kasancewar kamun da yamma akayi yasa Maman Farida ta shirya musu mothers night a meena event center.
An kawo wa Aisha cards guda biyar nata dana wadanda zata gaiyata, Farida ce ta tura Zainab ta kai mata cards din a lokacin tana kitchen tana aiki tana jin Faridan na fadawa Ummie cewa wai wallahi da Mummynta tayi shawara da ita bazata bawa Aisha kati ba don har yanzu da takaicinta a ranta duk lokacin data tuna cewa Daddy bai taba daga musu murya ba sai akanta.
Dariya kawai Aiaha tayi don tasan dama Farida ta sama mata lafiya daga rashin mutuncinta ne don tasan yanzu Daddy bazai yadda da iskancinsu ba.
Ko lokacin data basu gudunmawarta ta sarka gold kirar dubai data saya musu Farida karba kawai tayi babu godiya sai cewa da tayi ai dole ne ma ta saka tunda dai tasan da kudin ubanta aka saya, ko a lokacin Aisha bata kalleta ba don tasan duk abinda zata yi mata na dan lokaci ne.
Anyi mothers night din inda amare sukayi shiga cikin bridal lace da sukayi dinkin doguwar riga. Komai da suka saka iri daya ne sai colour data bambanta. Ita Farida tayi amfani da colour fari da blue yayinda Ummie tayi olive green da orange.
Tunda aka fara bikinnan Aisha bata zauna ba ga hidimar yara gata Daddy da kullum cikin yi mata korafi yake yana cewa tunda ta fara hidimar auren 'ya'yanta ta manta dashi.
Gaba daya hidimar bikinnan ta gajiyar da ita. A ranar asabar ne bayan an daura aure ta shirya musu walimah inda aka gaiyato malamai sukayi wa'azi sosai akan hakkin miji akan matarshi da kuma hakkin matar akan mijinta da zama da abokiyar zama.
Da yamma ne aka kai amare gidajensu. Ita dai Ummie an kaita redbricks ne yayinda Farida aka kaita lamido crescent. Ita kuma amayar Khalifa nan unguwarsu aka kawota gidanshi babu nisa da gidan iyayenshi.
*****
Asghar da Sajjad nayi muku barka da sallah da fatan Allah ya maimaita mana ya amshi ibadunmu. Sorry for the long silence wallahi tunda na Sligo kano sallah ban samu zama ba.
UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): 👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
'YA'YAN MIJI
👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
Na Umm Asghar
21
A yanzu da akayi wa su Farida aure Aisha bata da wata matsala a cikin gidanta don sosai Ruqaiya da Zainab ke yi mata biyayya kuma dama dai a yadda yaran suka taso tare da ita bata da matsala dasu.
An gama biki da sati biyu Daddy ya kwashi Aisha da yaranta masu watanni biyar suka tafi umrah sai Zainab da Ruqaiya kasancewar Yaran na hutu.
Mu'azzam kawai aka bari a gida don har lokacin Daddy ba wai ya huce daga fuahin da yakeyi dashi bane. A lokacin da Daddy yayiwa Aisha maganar tafiyarsu Umrah sosai tayi murna sai ta tuna lokacin da Farida tayi ta mata kafafa akan zasuyi tafiya su barta to itama yanzu gashi nata lokacin yayi don dama komai yana da lokacin.
Sosai Ruqaiya da Zainab ke taimaka mata wajen rainon twins, duk da Daddy na fadan yawan bawa yaran twins da take yi wai kar su kada su. Idan yana fadanshi kawai sai dai tayi dariya tana mamakin son 'ya'ya irin na Daddy shi komai a harkar yaranshi idonshi yana kai.
Sai dai ta sakawa ranta cewa ita kam bazata yadda ya bata mata yara ba irin yadda yayiwa su Ummie shine kuma dalilin da yasaka suke taka kowa ba tare da fargaba ba don sun san komai sukayi a wurin ubansu ba laifi bane.
Sai da sukayi sati uku sannan suka dawo gida nigeria, gaba daya a wannan lokacin Aisha ta canja ta kara yin kyau saboda kwanciyar hankali data samu ga uwa uba soyayya da kulawar mijinta data samu.
Bayan sati daya da dawowarsu ne Daddy yace ta shirya ta rakashi gidajensu Ummie yaje yaga dakunansu don tun da akayi auren bawai yaje bane.
Tayi shirinta cikin atamfar super exclusive kalar navy blue da ratsin fari da light yellow a jiki sai tayi amfani da farin mayafi da takalmi. Bata dauki jaka ba sai wayarta data rike a hannunta.
A gida ta bar twins qurin masu rainonsu kuma ganin su Ruqaiya na gidan yasa bata damu sai ta fita dasu ba.
Gidan Farida suka fara zuwa, Daddy yace ta shiga ta sanar musu da zuwan shi. Ta shiga cikin gidan da sallama, a main parlour su ta tarar da uwargidan Faridan tare da yaranta da maigidan.
Cikin girmamawa sosai matar ta karbeta duk da cewa zata iya girmewa Aisha. Bayan sun gaisa ne Aishan ke tambayar Farida tace mata tana dakinta ta saka yarinyarta ta raka Aisha.
Kafin su wuce ne Aisha ke sanar musu cewa tare da Daddy suke ai kuwa maigidan naji yayi hamzarin tashi yana cewa bari yaje ya shigo dashi.
Ta shiga dakin Farida tana ta kwala sallama amma ba'a amsa ba don haka ta zauna a parlour tacewa yarinyar ta shiga dakin ta yi mata magana. Ta shiga babu dadewa ta fito ta ce mata wai gata nan zuwa.
Tayi zaman fiye da mintuna goma kafin Farida ta fito tana yatsina fuska ta zauna. A dakile tace mata ina yini, lafiya kawai Aisha tace mata tace "tare muke da Daddynku yace na rakoshi yaga gidanku so yana kasa idan kinga dama kina iya zuwa ki gaisheshi".
Jin cewa yare suke da Daddy ya sa tayi saurin tashi ta fita. Ta dan jima kafin ta dawo, kamar bazata yiwa Aisha magana ba sai kuma tace mata "Daddy yace kije ku tafi" mikewa tayi ta ajiye mata ledar tsarabarta tace mata "to Allah ya bamu alkhairi" bata jira amsawarta ba ta fice.
Daga gidan Farida gidan Ummie suka nufa. Anan ma Daddy bai shiga ba. Ita kam Ummie ta karbeta da mutunci da murnarta har tana tambayarta twins tana cewa me yasa ba'a zo dasu ba.
Bayan sun gaisa ne take sanar mata cewa tare suke da Daddy. Sosai tayi murnar jin Daddy yazo gidanta. Tashi tayi ta shiga part din maigidan ta sanar mishi, babu wani dadewa kuwa ya fito.
Har kasa ya tsugunna ya gaida Aisha sannan ya fita don ya shigo da Daddy. A parlourshi ya saukeshi don haka can Ummie ta bishi ta gaidashi. Sun danfi dadewa a gidan Ummie sannan Daddy yace ta fito su tafi.
Itama ajiye mata tsarabarta tayi sannan sukayi sallama ta fita. Har wurin mota suka raka su sunata godiya. Ummie na rokon Daddy don Allah ya bari su Ruqaiya suzo mata don tunda akayi auren ya hanasu zuwa.
A hanyarsu ta komawa gida ne ya biya da ita grand square sai dai be yadda ta shiga ba, bayan ya fito ne ya miko mata leda mai dauke da turaruka designers guda uku. Sai kuma chocolates da biscuits na yara.
UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): 👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
'YA'YAN MIJI
👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
Na Umm Asghar
22
Tunda ta tashi yau bata zauna ba. Aiki takeyi kamar bazata gama ba. Ita kam wannan abu ya isheta ace aikin kenan kullum ta tashi bata da hutu, tace tana bukatar cook ance a'a ta bukaci house help nan ma yace mata a'a. Gashi yanzu ya kawo mata aikin girki wai zaiyi baki bayan duk wannan wahalar data keyi ta kuma san ba appreciating zaiyi ba don kullum tayi girki sai ya kushe. Ita kam har ga Allah bazata iya ba don ko a gidansu bata saba da aikin wahala ba kitchen kuwa kwata-kwata basa shigar shi da sunan girki.