Sashe 2
Yayan Miji Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
3
A yammacin wata asabar ne tana zaune a sitting room tana kallon movie a tashar mbc2. Farida da Ummie ne suka shigo suka zauna. Remote Farida ta dauka tare da canja channel zuwa musicplus. Dagowa tayi ta kalletaganin yadda sukazo suka iske ta tana kallo suka canja mata salon tayi magana suyi mata rashin kunya. "Fadi karta kasheki" shine abinda Farida tace mata. Dauke kai tayi tamkar bata san cewa da ita takeyi ba.
A guje Ruqaiya da Zainab suka shigo suna rige-rigen hawa kanta suka ce "Aunty Aisha mun dawo" da fara'arta ta dagosu tare da cewa "to sannunku da dawowa, sai aje a cire uniform ayi haramar yin sallah magriba ko". A tare suka ce to suna masu wucewa don su canja kayan islamiyyarsu zuwa na gida. "Kai kuzo nan" Farida tace musu "ban hanaku kula wannan matar ba amma shine dayake kunnuwanku na kashi ne ku bakwa ji kullum sai kunje inda take ko, kuna kallonmu amma ko sannu baku ce mana ba kun tafi wurin kanwar uwarku, to wallahi bari kuji na gaya muku daga yauidan na kara gani ko kallonta kunyi sai nayi muku shegen duka, ku wuce ku bani wuri".
Sum-sum suka wuce zuwa dakinsu. Su kam har kullum suna mamakin yadda yayyensu ke yiwa Aunty Aisha tamkar dai ba 'yaruwarsu bace. Ita kam Aisha suna fara yiwa yaran fada ta haya sama ta bar musu parlour. Dakinta ta nufa don yin sallar magriba don kuwa har an fara kiran sallah.
Koda ta idar da sallah bata tashi a wurin ba sai taci gaba da wuridi har aka kira sallar isha ta tashi tayi sannan ta sauka kasa don tayi serving dinner. Akan table ta iskesu sun fara cin abincin kasancewar Daddy baya nan yasa suka fara cin abincin ba tare da sun jirata ba. Tana bude warmers din taga wayam babu komai a ciki, takaici ne ya kamata ganin yadda suka cinye abincin ba tare da sun rage mata ba. Juyawa kawai tayi ta koma daki don bakin ciki bazai barta ta shiga kitchen don neman abinda zata ci ba.
Khalifa ne ya kalli kannenshi dake haramar barin table din yace "ina kuke tunanin tashi kuje ba tare da kun cinye abincinku ba, wannan din wa kuka barwa shi". Turo baki Farida tayi tace "to Yaya Khalifa mun fa koshi ne". Harara ya doka mata sannan yace "come on dawo ku zauna ku cinye, kunsan bazaku ciba kuka kwashe abincin gaba daya ita mai daguwar baku rage mata ba. Idan ma kunyi ne don kuyi mata mugunta to kanku kuka yiwa don kuwa sai kun cinye abincinnan tas ina kallonku".
Haka suka zauna suka tuttura abincin da kyar yana kallonsu har sai da suka cinye tukunna ya tashi ya bar wurin. Tuntsirewa Mu'azzam yayi da dariya har yana rike ciki ganin yadda suke ymutsa fuska kamar masu shirin yin amai. Tsaki Ummie tayi tace "to miye abin dariyar kuma". Wata dariyar ya karayi sannan yace "ai kune kuka sakani dariyar, ai idan kuna son yiwa matarnan tsiya bari zakuyisai Daddy na nan yanda duk abinda zakuyi ba maice muku uffan, amma Yaya Khalifa kam ai kinsan he always has a soft spot for her. Aurenta da Daddy ne ma yasa yaja baya da ita". "Wannan kuma shi ya jiyo, amma mudai ba'a isa a hanamu takurawa yarinya ba tunda dai ta yarda ta auri ubanmu" cewar Farida. Mu'azzam yace "lallai ma Farida bakida kunya, Aishan kike cewa yarinya agemate dina cefa don nasha jin Mami na cewa watanni 2 na bata".
Taking tayi tare da cewa "to shine me don sa'arka ce ko sa'ar Yaya Khalifa ce ai na kirata yarinya tunda kuwa dai a haife Daddy ya haifeta sannan kuma girman da tayi mana bai wuce na shekaru uku zuwa hudu ba. Ni ai tunda ta yarda ta auri Daddy naji na tsaneta ni inaga dama can tana sonshi ta rasa yadda zatayi ne sai kuma ta samu Hajiya ta bullo da maganar aure a tsakaninsu, bakuga ko musu batayi ba ta amince ita a dole ga mai biyayya".
TUSHEN LABARIN.
UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): 👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
'YA'YAN MIJI
Na Umm Asghar
4
TUSHEN LABARIN
Ja'afar Bello Danmaliki haifaffen garin kano ne a cikin unguwar gadon kaya sai dai iyayensu asalinsu mutanen karamar hukumar gaya ne. Su biyu iyayensu suka haifa shi da kaninshi Ismail. Daga Ismail mahaifiyarsu da suke kira da Hajiya bata kara haihuwa ba hakanan kuma mahaifinsu bai yi sha'awar kara aure ba ko don ganin ya samu wasu 'ya'yan.
Ja'afar yayi karatu tun daga primary anan kano har ya gama secondary, daga nan ya wuce Nigerian defence academy wato nda a kaduna inda ya karanci engineering a bangaren army ya fito da mukamin 2nd lieutenant. A shekarar daya fito daga nda ne ya auri dadaddiyar budurwarshi tun ta yarinta wato Zainab wacce ta kasance 'yar makotansu.
Watannin aurensu goma Zainab ta haifi danta na farko Muhammad Bello mai sunan mahaifin Ja'afar suna ce mishi Khalifa. Khalifa nada shekaru uku ta haifi Ibrahim Mu'azzam. Bayan Mu'azzam ne ta haifi Khadija (Ummie) mai sunan mahaifiyarta. Tsakanin Mu'azzam da Ummie ma shekaru uku ne. A shekarar da Zainab ta haifi Ummie ne Ismail kanin Ja'afar yayi aure a cikin kuma shekarar ne dai Allah yayi mishi rasuwa a dalilin hatsarin mota, ya rasu ya bar matar shi da cikin wata shida.
Mutuwar Ismail ta kada Ja'afar sosai don kuwa akwai shakuwa sosai a tsakaninsu. Bayan watanni uku da rasuwar Ismail matarshi ta haifi diya mace akasa mata suna Farida. A lokacin da Farida ta isa shiga makaranta nevya karbota ya kawowa Zainab sannan ya sakata a makaranta tare da Ummie. Farida da Ummie sun taso tamkar 'yan biyu kasancewar duk sunyi kama da iyayensu maza ne don sau tari mutanebna dauka 'yan biyu ne.
Tun bayan Ummie Zainab bata kara haihuwa ba sai da aka shekara goma don har ta fara cire rai da haihuwa sai kuma Allah ya kawo. A ranar wata litinin ne da safe tana zaune tana shayar da jaririyar data haifa Ruqaiya Hajiya wato surukarta tayi sallama a tare da wata yarinya da bazata wuce shekaru goma sha biyu zuwa sha uku ba.
Mikewa tayi tsaye tana cewa "Hajiya sannu da zuwa" "yauwa sannu Zainabu sai ke kadai ko yaran duk sun tafi makaranta" tace bayan ta zauna akan kujera. Zaman itama Zainab din tayi tana cewa "wallahi kuwa Hajiya kinji yanda gidan yayi shiru sai sun dawo kuma, barka da asuba Hajiya an tashi lafiya" tace tana mai rusunawa. "Lafiya lau ya kwanan yaran" "lafiyarsu lau Alhamdulillah". "To Masha Allah dama yarinyace na kawo miki, ina take ne ma kame Aisha" tace tana waigawa. Tasowa yarinyar tayi daga inda take a bayan kujera tazo ta tsugunna tacr "Hajiya gani". Gyara zamanta tayi sannan tace "kinaji ba Zainabu yarinya ce 'yar kanwata a kauye uwar ta rasu shine na dauko ta ganin ita kadai uwar ta bari to shine naga gara na kawota nan wurinku tunda dai akwai yara sai ki hadasu ki rike ko 'yan aikace-aikace ta taya ki, amma don Allah Zainab ki rike mini ita amana tamkar 'yarki tunda dai da na kowa ne ladanki na wurin Allah bare ma rikon maraya Allah ne kadai zai biyaki".
Dagowa tayi ta kalli yarinyar. Ba laifi kam yarinyar tsaf take babu wani alamu na kazanta ko kauyanci a tare da ita. Tace "to Hajiya nagode Allah ya kara girma, Allah kuma ya tayani riko yaya sunanta". "Aisha sunanta, abokan wasa muke da uwar ta jima bata haihu ba saida girma ya fara kamata sannan Allah ya bata Aisha daga ita kuma bata kara haihuwa ba". Ta juya ta kalli Aisha tace "kina jina Aisha ga Zainabu nan a wurinta zaki zauna ki dauketa tamkar mahaifiyarki kiyi mata biyayya, da nan gidan da can wurina duk daya ne don haka kar ki sanu wata damuwa kinji, Allah yayi miki albarka"
"Bari na tafi Zainabu idan yaran sun dawo ace ina gaishesu" tace tana mikewa. Har wurin mita suka rakata sannan suka dawo ciki. "Zo nan kusa dani ki zauna" Zainab tace mata. Tasowa tayi ta zauna a darare akan kujera inda ta nuna mata. Dafata tayi tare da cewa "ki saki jikinki dani kinji Aisha, ki daukeni tamkar mahaifiyarki duka abinda kikeso ki gaya mini In Sha Allahu zanyi miki shi idan har baifi karfina ba, kuma daga yau Mami zaki na ce mini kamar yadda 'yanuwanki suke kirana, basanan suna makaranta yanzu amma idan sun dawo zaki gansu".
A hankali ta gyada kai tace "nagida Mami In Sha Allahu zaki sameni mai bin abin da kika ce". Mami tace "to haka ake so yanzu tashi muje na nuna miki dakinku". Tashi tayi ta dauki ledar kayanta tabi bayan Mami suka hau sama zuwa dakinsu Ummie. Daki ne babba yana dauke da gado 6by6 sai wardrobe din jikin bango da madubi. A wardrobe din Mami tace ta ajiye kayanta sannan ta nuna mata bandaki ko tana da bukatar shiga ta juya ta fita.
UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): 👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
'YA'YAN MIJI
Na Umm Asghar
A yammacin wata asabar ne tana zaune a sitting room tana kallon movie a tashar mbc2. Farida da Ummie ne suka shigo suka zauna. Remote Farida ta dauka tare da canja channel zuwa musicplus. Dagowa tayi ta kalletaganin yadda sukazo suka iske ta tana kallo suka canja mata salon tayi magana suyi mata rashin kunya. "Fadi karta kasheki" shine abinda Farida tace mata. Dauke kai tayi tamkar bata san cewa da ita takeyi ba.
A guje Ruqaiya da Zainab suka shigo suna rige-rigen hawa kanta suka ce "Aunty Aisha mun dawo" da fara'arta ta dagosu tare da cewa "to sannunku da dawowa, sai aje a cire uniform ayi haramar yin sallah magriba ko". A tare suka ce to suna masu wucewa don su canja kayan islamiyyarsu zuwa na gida. "Kai kuzo nan" Farida tace musu "ban hanaku kula wannan matar ba amma shine dayake kunnuwanku na kashi ne ku bakwa ji kullum sai kunje inda take ko, kuna kallonmu amma ko sannu baku ce mana ba kun tafi wurin kanwar uwarku, to wallahi bari kuji na gaya muku daga yauidan na kara gani ko kallonta kunyi sai nayi muku shegen duka, ku wuce ku bani wuri".
Sum-sum suka wuce zuwa dakinsu. Su kam har kullum suna mamakin yadda yayyensu ke yiwa Aunty Aisha tamkar dai ba 'yaruwarsu bace. Ita kam Aisha suna fara yiwa yaran fada ta haya sama ta bar musu parlour. Dakinta ta nufa don yin sallar magriba don kuwa har an fara kiran sallah.
Koda ta idar da sallah bata tashi a wurin ba sai taci gaba da wuridi har aka kira sallar isha ta tashi tayi sannan ta sauka kasa don tayi serving dinner. Akan table ta iskesu sun fara cin abincin kasancewar Daddy baya nan yasa suka fara cin abincin ba tare da sun jirata ba. Tana bude warmers din taga wayam babu komai a ciki, takaici ne ya kamata ganin yadda suka cinye abincin ba tare da sun rage mata ba. Juyawa kawai tayi ta koma daki don bakin ciki bazai barta ta shiga kitchen don neman abinda zata ci ba.
Khalifa ne ya kalli kannenshi dake haramar barin table din yace "ina kuke tunanin tashi kuje ba tare da kun cinye abincinku ba, wannan din wa kuka barwa shi". Turo baki Farida tayi tace "to Yaya Khalifa mun fa koshi ne". Harara ya doka mata sannan yace "come on dawo ku zauna ku cinye, kunsan bazaku ciba kuka kwashe abincin gaba daya ita mai daguwar baku rage mata ba. Idan ma kunyi ne don kuyi mata mugunta to kanku kuka yiwa don kuwa sai kun cinye abincinnan tas ina kallonku".
Haka suka zauna suka tuttura abincin da kyar yana kallonsu har sai da suka cinye tukunna ya tashi ya bar wurin. Tuntsirewa Mu'azzam yayi da dariya har yana rike ciki ganin yadda suke ymutsa fuska kamar masu shirin yin amai. Tsaki Ummie tayi tace "to miye abin dariyar kuma". Wata dariyar ya karayi sannan yace "ai kune kuka sakani dariyar, ai idan kuna son yiwa matarnan tsiya bari zakuyisai Daddy na nan yanda duk abinda zakuyi ba maice muku uffan, amma Yaya Khalifa kam ai kinsan he always has a soft spot for her. Aurenta da Daddy ne ma yasa yaja baya da ita". "Wannan kuma shi ya jiyo, amma mudai ba'a isa a hanamu takurawa yarinya ba tunda dai ta yarda ta auri ubanmu" cewar Farida. Mu'azzam yace "lallai ma Farida bakida kunya, Aishan kike cewa yarinya agemate dina cefa don nasha jin Mami na cewa watanni 2 na bata".
Taking tayi tare da cewa "to shine me don sa'arka ce ko sa'ar Yaya Khalifa ce ai na kirata yarinya tunda kuwa dai a haife Daddy ya haifeta sannan kuma girman da tayi mana bai wuce na shekaru uku zuwa hudu ba. Ni ai tunda ta yarda ta auri Daddy naji na tsaneta ni inaga dama can tana sonshi ta rasa yadda zatayi ne sai kuma ta samu Hajiya ta bullo da maganar aure a tsakaninsu, bakuga ko musu batayi ba ta amince ita a dole ga mai biyayya".
TUSHEN LABARIN.
UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): 👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
'YA'YAN MIJI
Na Umm Asghar
4
TUSHEN LABARIN
Ja'afar Bello Danmaliki haifaffen garin kano ne a cikin unguwar gadon kaya sai dai iyayensu asalinsu mutanen karamar hukumar gaya ne. Su biyu iyayensu suka haifa shi da kaninshi Ismail. Daga Ismail mahaifiyarsu da suke kira da Hajiya bata kara haihuwa ba hakanan kuma mahaifinsu bai yi sha'awar kara aure ba ko don ganin ya samu wasu 'ya'yan.
Ja'afar yayi karatu tun daga primary anan kano har ya gama secondary, daga nan ya wuce Nigerian defence academy wato nda a kaduna inda ya karanci engineering a bangaren army ya fito da mukamin 2nd lieutenant. A shekarar daya fito daga nda ne ya auri dadaddiyar budurwarshi tun ta yarinta wato Zainab wacce ta kasance 'yar makotansu.
Watannin aurensu goma Zainab ta haifi danta na farko Muhammad Bello mai sunan mahaifin Ja'afar suna ce mishi Khalifa. Khalifa nada shekaru uku ta haifi Ibrahim Mu'azzam. Bayan Mu'azzam ne ta haifi Khadija (Ummie) mai sunan mahaifiyarta. Tsakanin Mu'azzam da Ummie ma shekaru uku ne. A shekarar da Zainab ta haifi Ummie ne Ismail kanin Ja'afar yayi aure a cikin kuma shekarar ne dai Allah yayi mishi rasuwa a dalilin hatsarin mota, ya rasu ya bar matar shi da cikin wata shida.
Mutuwar Ismail ta kada Ja'afar sosai don kuwa akwai shakuwa sosai a tsakaninsu. Bayan watanni uku da rasuwar Ismail matarshi ta haifi diya mace akasa mata suna Farida. A lokacin da Farida ta isa shiga makaranta nevya karbota ya kawowa Zainab sannan ya sakata a makaranta tare da Ummie. Farida da Ummie sun taso tamkar 'yan biyu kasancewar duk sunyi kama da iyayensu maza ne don sau tari mutanebna dauka 'yan biyu ne.
Tun bayan Ummie Zainab bata kara haihuwa ba sai da aka shekara goma don har ta fara cire rai da haihuwa sai kuma Allah ya kawo. A ranar wata litinin ne da safe tana zaune tana shayar da jaririyar data haifa Ruqaiya Hajiya wato surukarta tayi sallama a tare da wata yarinya da bazata wuce shekaru goma sha biyu zuwa sha uku ba.
Mikewa tayi tsaye tana cewa "Hajiya sannu da zuwa" "yauwa sannu Zainabu sai ke kadai ko yaran duk sun tafi makaranta" tace bayan ta zauna akan kujera. Zaman itama Zainab din tayi tana cewa "wallahi kuwa Hajiya kinji yanda gidan yayi shiru sai sun dawo kuma, barka da asuba Hajiya an tashi lafiya" tace tana mai rusunawa. "Lafiya lau ya kwanan yaran" "lafiyarsu lau Alhamdulillah". "To Masha Allah dama yarinyace na kawo miki, ina take ne ma kame Aisha" tace tana waigawa. Tasowa yarinyar tayi daga inda take a bayan kujera tazo ta tsugunna tacr "Hajiya gani". Gyara zamanta tayi sannan tace "kinaji ba Zainabu yarinya ce 'yar kanwata a kauye uwar ta rasu shine na dauko ta ganin ita kadai uwar ta bari to shine naga gara na kawota nan wurinku tunda dai akwai yara sai ki hadasu ki rike ko 'yan aikace-aikace ta taya ki, amma don Allah Zainab ki rike mini ita amana tamkar 'yarki tunda dai da na kowa ne ladanki na wurin Allah bare ma rikon maraya Allah ne kadai zai biyaki".
Dagowa tayi ta kalli yarinyar. Ba laifi kam yarinyar tsaf take babu wani alamu na kazanta ko kauyanci a tare da ita. Tace "to Hajiya nagode Allah ya kara girma, Allah kuma ya tayani riko yaya sunanta". "Aisha sunanta, abokan wasa muke da uwar ta jima bata haihu ba saida girma ya fara kamata sannan Allah ya bata Aisha daga ita kuma bata kara haihuwa ba". Ta juya ta kalli Aisha tace "kina jina Aisha ga Zainabu nan a wurinta zaki zauna ki dauketa tamkar mahaifiyarki kiyi mata biyayya, da nan gidan da can wurina duk daya ne don haka kar ki sanu wata damuwa kinji, Allah yayi miki albarka"
"Bari na tafi Zainabu idan yaran sun dawo ace ina gaishesu" tace tana mikewa. Har wurin mita suka rakata sannan suka dawo ciki. "Zo nan kusa dani ki zauna" Zainab tace mata. Tasowa tayi ta zauna a darare akan kujera inda ta nuna mata. Dafata tayi tare da cewa "ki saki jikinki dani kinji Aisha, ki daukeni tamkar mahaifiyarki duka abinda kikeso ki gaya mini In Sha Allahu zanyi miki shi idan har baifi karfina ba, kuma daga yau Mami zaki na ce mini kamar yadda 'yanuwanki suke kirana, basanan suna makaranta yanzu amma idan sun dawo zaki gansu".
A hankali ta gyada kai tace "nagida Mami In Sha Allahu zaki sameni mai bin abin da kika ce". Mami tace "to haka ake so yanzu tashi muje na nuna miki dakinku". Tashi tayi ta dauki ledar kayanta tabi bayan Mami suka hau sama zuwa dakinsu Ummie. Daki ne babba yana dauke da gado 6by6 sai wardrobe din jikin bango da madubi. A wardrobe din Mami tace ta ajiye kayanta sannan ta nuna mata bandaki ko tana da bukatar shiga ta juya ta fita.
UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): 👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
'YA'YAN MIJI
Na Umm Asghar