Sashe 14
Yayan Miji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yanzu wannan aikin abincin ya zatayi dashi fisabilillahi tunda dai yasan ba iyawa tayi ba. Tana tsaye a kitchen din ta tasa kayan aikin a gaba tana kallo ya shigo ya kare mata kallo ganin yadda ta doka tagumi tana kallon kayan ya kara bata mishi rai. Tsaki yayi abinda ya maido da hankalinta gareshi. Cikin dakewa yace mata "su Maryam zasu zo su tayaki aikin amma na yau kawai, gara tun wuri kisan me kike ciki don bazan dauki wannan sakarcin ba. Ace kina 'ya mace amma baki iya komai ba, I've had enough of ur nonsense. Duk yadda zaki yi ki koyi tsaftar muhallinki da girka abincin gidanki kije kiyi don na gaji da barnar Kudina kina mini asara" wani tsakin ya karayi kafin ya fita ya bar mata kitchen din.
Har cikin ranta taji dadi da yace su Maryam suzo su tayata aikin sai dai kuma bata san ya yake so tayi ba wajen koyon girki. Ita yanzu wa zata samu da zata na koya mata girki har ta iya, mts ita fa harka da kitchen ma kwata-kwata batayi mata ba. Ita kam Farida taji dadinta wallahi komai tana kwance za'ayi mata shi amma ita nan gata an saka ta a gaba kullum cikin fadan wani kuskure nata yake.
Da taimakon kannenshi Maryam da Amina suka hada lafiyayyen lunch inda suka yi musu arabian zirbiyan da farfesun kayan cikin rago da potato salad sai zobo drink din daya wadatu da cucumber da kayan kamshi.
Sun shirya table tsaf sannan suka kara kimtsa gidan sukayi wa Ummie sallama cewa zasu koma gida don suna zuwa islamiyya. Sosai taji dadin aikin da suka mata, da zasu tafi ta musu kyautar kayan kwalliya da turare.
Tun bayan tafiyarsu take tunanin abinyi akan matsalarta, kamar tace musu su rinka zuwa suna koya mata abubuwan da suka danganci girki sai kuma taji kunyar yin hakan kannen mijinta nefa, to ko Farida zata kira ta bata shawarar yadda zatayi. Kai a'a tasan halin Farida sarai bawai zata bata wata shawarar arziki bane.
Idanunta ne taji sun cika da hawaye, sai yau ta kara tabbatar da tayi rashin uwa don kuwa da Mami na nan tasan da bata shiga cikin matsalar da take ciki ba yanzu tasan babu yadda za'ayi ayi aurenta ba tare da Mami ta koyar da ita kula da hidimar gidanta ba.
Ta jima tana kuka kafin ta rarrashi kanta tayi shiru, gashi Abdulhalim tunda suka ci abinci da abokanshi suka fita bai dawo ba. Wayarta ta janyo ta kira Yaya Khalifa.
Yana amsa wayar ta saka mishi kuka, sosai ta tayar mishi da hankali jin kukanta. Da kyar ya lallasheta tayi shiru sannan ya bukaci yaji damuwarta. Cikin rishin kukan ta sanar dashi duk abinda Abdulhalim yace ta karasa da fadin "ni bansan ya zanyi ba Yaya Khalifa wallahi na gaji komai nayi a gidannan baya appreciating sai yayi ta fada bayan kuma yasan cewa ban iya ba".
Shiru Khalifa yayi ya ma rasa me zaicewa Ummie, ganin shirun shi bazai taimaketa da komai ba yada yace mata "why not da bazaki nemi Aunty Aisha ba ina ganin idan har kika gaya mata zata san yadda zata bullo wa al'amarin kuma kinga catering ta karanta so ko ita ma ai zata iya koya miki girkin, amma
ke me kike gani".
Tasan Aunty Aisha bazata ki koyar da ita ba to amma tana jin kunyarta ganin irin rashin mutuncin da suka dinga mata. Jin tayi shiru bata amsa ba yasa Khalifa yace "bafa nace lallai ne sai kin nemeta ba na ga ne kamar ita yafi dacewa ki nema don ina ganin bazata ki taimaka miki ba".
"Banki ta taka ba Yaya Khalifa kawai dai ina jin kunyarta ne akan abubuwan da suka faru amma zan kirata a waya In Sha Allahu, nagode Yaya Khalifa". Sosai yayi mata nasiha kan hakuri da juriya a dukkan al'amuranta.
Ta jima tana juya wayarta tana contemplating kiran Aisha a waya ko kar ta kirata. Daurewa kawai tayi tayi dialling number, bata jima tana ringing ba taji amsawarta da sallama.
Cikin dauriya sosai ta iya amsa mata sallamar sannan ta gaisheta tare da tambayar lafiyar twins dasu Zainab. Da kyar ta iya yi mata bayanin dalilin kiran datayi mata. Shiru Aisha tayi tana saurarenta ba tare da ta katse ta ba har saida ta lura cewar ta gama maganar sannan tace mata "ina ganin abinda za'ayi shine ki nemi izininshi sai ki rinka zuwa gida muna yin girkin tare har ki kware batun gyaran gida kuma Ummie dole ne ki cire lalaci da kyuiya ki zage damtse kike gyaran muhallinki, kuma ma idan banda abinki ke da ba yara gareki ba ya za'ayi ki dinga barin gidanki yanayin datti ai bazai yiwu kice wai sai gidanki yayi datti sannan zaki gyara shi ba. Idan kina kula da gyaranshi akai-akai ko ace wata rana zaki tashi baki gyara ba ba za'a gane ba don yana samun kula. Kiyi kokari ya barki kina zuwa gidan sai ku tsara ranakun da zaki na zuwa idan d weekends ne to idan kuma ranakun aiki ne ma dai duk ina gida amma ina ganin kamar weekdays din zaifi tunda lokcin yana wajen aiki sauran bayani kuma sai kinzo gidan".
"Nagode sosai Aunty Aisha Allah ya saka da alkhairi In Sha Allahu zanyi mishi maganar nasan ma bazai ki ba duk yadda mukayi kuma zan kiraki a waya sai na shaida miki".
Sosai taji dadin maganar da sukayi da Aunty Aisha, In Sha Allahu kuma zata gyara al'amuran gidanta don kuwa tana son mijinta sosai bata so tana yawan bata mishi rai kuma ita ma tana so taga tayi abinda zata burgeshi har ya yaba mata.
UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): 👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
'YA'YAN MIJI
👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
Na Umm Asghar
23
Kusan sati biyu kenan kullum da safe Ummie ke zuwa gida wurin Aisha don koyon girki. Zuwa yanzu kam Alhamdulillahi tana iya shiga kitchen tayi girkin abincin kuma a cinye ana santi. Ita kanta tana jin dadin yadda kullum tayi girki Abdulhalim ke yabawa don tun baya yadda cewa ita keyi har ya yadda don Aunty Aisha tana directing dinta ne kawai amma komai ita keyi aikin Aisha kawai ta saka ido.
A yammacin wata talata ne Aisha na zaune tare da Daddy a parlournshi na sama, yana karatun jaridar daily trust ne ta ranar ita kuma tana kallon tashar Africa magic hausa sai dai ba duka hankalinta ne akan kallon ba tana kula da twins da suke wasa.
Zainab ce ta shigo parlour da sallama sannan ta durkusa tacewa Aisha "Mummy Yaya Farida ce tazo tana parlour a kasa", jim Aisha tayi cikin tunanin lafiya Farida tazo yanzu da yamma don magriba ma ta kusa kuma ita din tun bayan aurensu zuwanta gidan baifi a kirga ba shima kuma bata fin mintuna goma take tafiya.
Tashi tayi ta sauka zuwa parlournsu na kasa. Farida na zaune akan kujera double seater ta hada kai da gwiwa. Koda Aisha ta shiga parlour bata dago ba ga alama bata ma san ta shigo parlourn ba har saida Aishan ta mata magana sannan ta dago kanta. Fuskarta tayi jajawur alamun taci kuka ta koshi.
Ganinta a haka gaba daya sai Aisha ta rude cewa takeyi "Farida lafiya wani abu ya faru ne ko baki da lafiya, ina maigidan? Me ke faruwa ne, kiyi mini magana mana". Gaba daya Aisha ta manta wacece Farida da irin zaman da sukayi tare yanayin data ganta a ciki ya sanyayar mat da jiki sosai.
Ita dai Farida banda kuka babu abinda takeyi tun Aisha na bin kanta don taji damuwarta harta gaji ta kyaleta. Suna zaune a wurin akayi kiran sallar magriba don haka Aisha tace mata "ko meye yake damunki hakuri zakiyi ki fawwalawa Allah al'amuranki ita wannan rayuwar da kike gani hakuri shine jigonta dolene ki koyi hakurin zama da mutanen da Allah ya hada ki dasu. Yanzu ki tashi kiyi sallah in yaso sai ki samu Daddy kuyi magana".
Bata jira jin amsawar Farida ba ta haya sama don yin sallar magriba. Sai da ta fara shiga parlour Daddy ta dauki 'yanbiyu ta mika su wurin nannysu sannan ta wuce dakinta tayi sallah. Koda ta idar bata tashi ba sai bayan da tayi salkar isha sannan ta fito.
Ta samu su Zainab da Ruqaiya akan table suna jiransu don yin dinner amma har lokacin Daddy bai fito ba. "Zainab je ki kira Farida tazo taci abinci" Aisha tace mata. Tashi tayi ta nufi aiken da akayi mata, dawowa tayi tace mata wai tace ta koshi.
Cewa tayi da yaran suci abincinsu kawai ba tare da sun jira Daddy ba. Bayan sun gama cin abincin ne ta koma sama don ta tambayi Daddy ko akwai abinda yake son ci ta mishi don tunda taga bai sauko dinner ba tasan ba cin abincin zaiyi ba.
Koda ta shiga parlour ta iske shine tare da Farida tana zaune a kasa akan rug din tsakiyar kanta a sunkuye a kasa sai dai hakan bai hana kukanta fitowa ba. Juyawa tayi zata bar parlour Daddy ya tsaida tare da cewa "ya zaki fita ko ba wurina kika zo ba" yace yare da kashe mata ido daya😉.
Murmushi kawai tayi amma sosai Daddy ya bata kunya. Cewa tayi "na gani ne dama baka sauko kayi dinnwr ba shine zan tambayeka ko akwai wani abu da kake so na shirya maka kafin dare yayi". "Thanks for the gesture amma bana bukatar komai sai tea sai ki hada mini da cake, ai akwai ko?" tace "um akwai" ta juya ta bar parlour.
A lokacin da suka zo kwanciya ne Daddy ke fada mata dalilin zuwan Farida wai mijin ne ya korota saboda tana da matsala da matarshi da yaranshi yace bazai iya zama da matar da bata son 'ya'yanshi ba. Ita kuma Farida tace wai yaran ne keyi mata rashin kunya kuma wai uwarsu ke saka su ba kuma tayi magana ba sai yace ita fitinanniya ce bata son zaman lafiya shi yaranshi nada tarbiyya baza suyi mata rashin kunya ba.
Har cikin ranta taji dadi da yace su Maryam suzo su tayata aikin sai dai kuma bata san ya yake so tayi ba wajen koyon girki. Ita yanzu wa zata samu da zata na koya mata girki har ta iya, mts ita fa harka da kitchen ma kwata-kwata batayi mata ba. Ita kam Farida taji dadinta wallahi komai tana kwance za'ayi mata shi amma ita nan gata an saka ta a gaba kullum cikin fadan wani kuskure nata yake.
Da taimakon kannenshi Maryam da Amina suka hada lafiyayyen lunch inda suka yi musu arabian zirbiyan da farfesun kayan cikin rago da potato salad sai zobo drink din daya wadatu da cucumber da kayan kamshi.
Sun shirya table tsaf sannan suka kara kimtsa gidan sukayi wa Ummie sallama cewa zasu koma gida don suna zuwa islamiyya. Sosai taji dadin aikin da suka mata, da zasu tafi ta musu kyautar kayan kwalliya da turare.
Tun bayan tafiyarsu take tunanin abinyi akan matsalarta, kamar tace musu su rinka zuwa suna koya mata abubuwan da suka danganci girki sai kuma taji kunyar yin hakan kannen mijinta nefa, to ko Farida zata kira ta bata shawarar yadda zatayi. Kai a'a tasan halin Farida sarai bawai zata bata wata shawarar arziki bane.
Idanunta ne taji sun cika da hawaye, sai yau ta kara tabbatar da tayi rashin uwa don kuwa da Mami na nan tasan da bata shiga cikin matsalar da take ciki ba yanzu tasan babu yadda za'ayi ayi aurenta ba tare da Mami ta koyar da ita kula da hidimar gidanta ba.
Ta jima tana kuka kafin ta rarrashi kanta tayi shiru, gashi Abdulhalim tunda suka ci abinci da abokanshi suka fita bai dawo ba. Wayarta ta janyo ta kira Yaya Khalifa.
Yana amsa wayar ta saka mishi kuka, sosai ta tayar mishi da hankali jin kukanta. Da kyar ya lallasheta tayi shiru sannan ya bukaci yaji damuwarta. Cikin rishin kukan ta sanar dashi duk abinda Abdulhalim yace ta karasa da fadin "ni bansan ya zanyi ba Yaya Khalifa wallahi na gaji komai nayi a gidannan baya appreciating sai yayi ta fada bayan kuma yasan cewa ban iya ba".
Shiru Khalifa yayi ya ma rasa me zaicewa Ummie, ganin shirun shi bazai taimaketa da komai ba yada yace mata "why not da bazaki nemi Aunty Aisha ba ina ganin idan har kika gaya mata zata san yadda zata bullo wa al'amarin kuma kinga catering ta karanta so ko ita ma ai zata iya koya miki girkin, amma
ke me kike gani".
Tasan Aunty Aisha bazata ki koyar da ita ba to amma tana jin kunyarta ganin irin rashin mutuncin da suka dinga mata. Jin tayi shiru bata amsa ba yasa Khalifa yace "bafa nace lallai ne sai kin nemeta ba na ga ne kamar ita yafi dacewa ki nema don ina ganin bazata ki taimaka miki ba".
"Banki ta taka ba Yaya Khalifa kawai dai ina jin kunyarta ne akan abubuwan da suka faru amma zan kirata a waya In Sha Allahu, nagode Yaya Khalifa". Sosai yayi mata nasiha kan hakuri da juriya a dukkan al'amuranta.
Ta jima tana juya wayarta tana contemplating kiran Aisha a waya ko kar ta kirata. Daurewa kawai tayi tayi dialling number, bata jima tana ringing ba taji amsawarta da sallama.
Cikin dauriya sosai ta iya amsa mata sallamar sannan ta gaisheta tare da tambayar lafiyar twins dasu Zainab. Da kyar ta iya yi mata bayanin dalilin kiran datayi mata. Shiru Aisha tayi tana saurarenta ba tare da ta katse ta ba har saida ta lura cewar ta gama maganar sannan tace mata "ina ganin abinda za'ayi shine ki nemi izininshi sai ki rinka zuwa gida muna yin girkin tare har ki kware batun gyaran gida kuma Ummie dole ne ki cire lalaci da kyuiya ki zage damtse kike gyaran muhallinki, kuma ma idan banda abinki ke da ba yara gareki ba ya za'ayi ki dinga barin gidanki yanayin datti ai bazai yiwu kice wai sai gidanki yayi datti sannan zaki gyara shi ba. Idan kina kula da gyaranshi akai-akai ko ace wata rana zaki tashi baki gyara ba ba za'a gane ba don yana samun kula. Kiyi kokari ya barki kina zuwa gidan sai ku tsara ranakun da zaki na zuwa idan d weekends ne to idan kuma ranakun aiki ne ma dai duk ina gida amma ina ganin kamar weekdays din zaifi tunda lokcin yana wajen aiki sauran bayani kuma sai kinzo gidan".
"Nagode sosai Aunty Aisha Allah ya saka da alkhairi In Sha Allahu zanyi mishi maganar nasan ma bazai ki ba duk yadda mukayi kuma zan kiraki a waya sai na shaida miki".
Sosai taji dadin maganar da sukayi da Aunty Aisha, In Sha Allahu kuma zata gyara al'amuran gidanta don kuwa tana son mijinta sosai bata so tana yawan bata mishi rai kuma ita ma tana so taga tayi abinda zata burgeshi har ya yaba mata.
UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): 👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
'YA'YAN MIJI
👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
Na Umm Asghar
23
Kusan sati biyu kenan kullum da safe Ummie ke zuwa gida wurin Aisha don koyon girki. Zuwa yanzu kam Alhamdulillahi tana iya shiga kitchen tayi girkin abincin kuma a cinye ana santi. Ita kanta tana jin dadin yadda kullum tayi girki Abdulhalim ke yabawa don tun baya yadda cewa ita keyi har ya yadda don Aunty Aisha tana directing dinta ne kawai amma komai ita keyi aikin Aisha kawai ta saka ido.
A yammacin wata talata ne Aisha na zaune tare da Daddy a parlournshi na sama, yana karatun jaridar daily trust ne ta ranar ita kuma tana kallon tashar Africa magic hausa sai dai ba duka hankalinta ne akan kallon ba tana kula da twins da suke wasa.
Zainab ce ta shigo parlour da sallama sannan ta durkusa tacewa Aisha "Mummy Yaya Farida ce tazo tana parlour a kasa", jim Aisha tayi cikin tunanin lafiya Farida tazo yanzu da yamma don magriba ma ta kusa kuma ita din tun bayan aurensu zuwanta gidan baifi a kirga ba shima kuma bata fin mintuna goma take tafiya.
Tashi tayi ta sauka zuwa parlournsu na kasa. Farida na zaune akan kujera double seater ta hada kai da gwiwa. Koda Aisha ta shiga parlour bata dago ba ga alama bata ma san ta shigo parlourn ba har saida Aishan ta mata magana sannan ta dago kanta. Fuskarta tayi jajawur alamun taci kuka ta koshi.
Ganinta a haka gaba daya sai Aisha ta rude cewa takeyi "Farida lafiya wani abu ya faru ne ko baki da lafiya, ina maigidan? Me ke faruwa ne, kiyi mini magana mana". Gaba daya Aisha ta manta wacece Farida da irin zaman da sukayi tare yanayin data ganta a ciki ya sanyayar mat da jiki sosai.
Ita dai Farida banda kuka babu abinda takeyi tun Aisha na bin kanta don taji damuwarta harta gaji ta kyaleta. Suna zaune a wurin akayi kiran sallar magriba don haka Aisha tace mata "ko meye yake damunki hakuri zakiyi ki fawwalawa Allah al'amuranki ita wannan rayuwar da kike gani hakuri shine jigonta dolene ki koyi hakurin zama da mutanen da Allah ya hada ki dasu. Yanzu ki tashi kiyi sallah in yaso sai ki samu Daddy kuyi magana".
Bata jira jin amsawar Farida ba ta haya sama don yin sallar magriba. Sai da ta fara shiga parlour Daddy ta dauki 'yanbiyu ta mika su wurin nannysu sannan ta wuce dakinta tayi sallah. Koda ta idar bata tashi ba sai bayan da tayi salkar isha sannan ta fito.
Ta samu su Zainab da Ruqaiya akan table suna jiransu don yin dinner amma har lokacin Daddy bai fito ba. "Zainab je ki kira Farida tazo taci abinci" Aisha tace mata. Tashi tayi ta nufi aiken da akayi mata, dawowa tayi tace mata wai tace ta koshi.
Cewa tayi da yaran suci abincinsu kawai ba tare da sun jira Daddy ba. Bayan sun gama cin abincin ne ta koma sama don ta tambayi Daddy ko akwai abinda yake son ci ta mishi don tunda taga bai sauko dinner ba tasan ba cin abincin zaiyi ba.
Koda ta shiga parlour ta iske shine tare da Farida tana zaune a kasa akan rug din tsakiyar kanta a sunkuye a kasa sai dai hakan bai hana kukanta fitowa ba. Juyawa tayi zata bar parlour Daddy ya tsaida tare da cewa "ya zaki fita ko ba wurina kika zo ba" yace yare da kashe mata ido daya😉.
Murmushi kawai tayi amma sosai Daddy ya bata kunya. Cewa tayi "na gani ne dama baka sauko kayi dinnwr ba shine zan tambayeka ko akwai wani abu da kake so na shirya maka kafin dare yayi". "Thanks for the gesture amma bana bukatar komai sai tea sai ki hada mini da cake, ai akwai ko?" tace "um akwai" ta juya ta bar parlour.
A lokacin da suka zo kwanciya ne Daddy ke fada mata dalilin zuwan Farida wai mijin ne ya korota saboda tana da matsala da matarshi da yaranshi yace bazai iya zama da matar da bata son 'ya'yanshi ba. Ita kuma Farida tace wai yaran ne keyi mata rashin kunya kuma wai uwarsu ke saka su ba kuma tayi magana ba sai yace ita fitinanniya ce bata son zaman lafiya shi yaranshi nada tarbiyya baza suyi mata rashin kunya ba.