← Book details Yayan Miji Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 15 OF 16

Sashe 15

Yayan Miji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Shiru kawai Aisha tayi bata ce komai ba sai dai cikin ranta cewa takeyi alhaki ai kwikwiyo ne hakanan kuma sharri dan aike ne duk inda yaje zai dawowa maishi. Tana tuna yanda Farida ta takura mata a zaman gidannan ta kuma yi sa'a komai tayi daidai ne a wurin Daddy bata laifi yanzu gashi abin ya dawo kanta.

Sai dai bazata iya fitowa ta gayawa Daddy hakan ba don haka tace mishi "to yanzu wanne mataki zaka dauka don kasan bazai yiwu ja yanke hukunci ba tare da kaji ta bakin maigidanta ba ko", yace "hakane nayi tunanin kiranshi muyi magana sai naga dare yayi amma In Sha Allahu gobe zan nemeshi don naji ta bakinshi amma idan har abinda tace mini gaskiya ne shima bai kyauta ba ai yaran yanzu ba abin yarda bane bazai yiwu ka bashi shaida ba farat daya".

Wannan rayuwar da abin mamaki take, shine kawai abinda Aisha ke cewa a cikin ranta don sosai Daddy ya bata mamaki jin cewar da yakeyi wai mijin Farida bai kyauta ba tunda yabi bayan yaranshi bayan shi dinma haka halinshi yake akan yaranshi sam su basa laifi sai dai kai ka saba musu amma badai su suyi maka ba.

Washegari ne bayan Daddy ya dawo daga office mijin Farida yazo. A parlourn bakinshi ya sauki surikinnashi. Sai bayan sun gama gaisawa ne sannan suka fara tattaunawa akan maganar inda yake shaidawa Daddy cewa Farida bata so ko yaya taga yaranshi sun rabeshi sai ta hau harare -harare tana zare musu ido shine yasa ma ko dakinta basa shiga haka nan kuma ta raina matarshi ko gaisheta batayi gashi sai tace wai bata yadda yayi hulda da matarshi ba shi kuma ya gaya mata cewa yana son matarshi bawai ya daina sonta bane yasa ya aureta shi kuma baiga diya macen da zai aura ya wulakanta Matarshi akanta ba, idan taga bazata iya zama da ita ba to sai dai ita ta fita ta bar mata gidanta.

Shiru Daddy yayi yana saurarenshi sai dai ranshi idan yayi dubu ya baci da rashin arzikin da Farida keyi a gidanta don kuwa shi ta zubarwa da mutunci don duk wanda yaji abinda takeyi a gidanta zaice ne bata samu tarbiyyar arziki ba a gidansu.

Hakuri ya bawa mijinnata yace mishi kuma In Sha Allah hakan bazai kuma faruwa ba don sosai zai ja mata kunne akan hakan. Sun rabu akan cewa sai gobe zata koma gidan.

*****

Kuyi hakuri da wannan wallahi kaina ciwo yakeyi dauriya kawai nayi nayi typing wannan, sannan kuyi hakurin rashin jina kwana biyu bana samun caji ne a wayata kusan kullum a kashe take yini lokacin dazan samu cajin kuma dare yayi.

UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): 👩‍👩‍👧‍👦👩‍👩‍👧‍👦👩‍👩‍👧‍👦👩‍👩‍👧‍👦👩‍👩‍👧‍👦👩‍👩‍👧‍👦👩‍👩‍👧‍👦👩‍👩‍👧‍👦👩‍👩‍👧‍👦👩‍👩‍👧‍👦
'YA'YAN MIJI
👩‍👩‍👧‍👦👩‍👩‍👧‍👦👩‍👩‍👧‍👦👩‍👩‍👧‍👦👩‍👩‍👧‍👦👩‍👩‍👧‍👦👩‍👩‍👧‍👦👩‍👩‍👧‍👦👩‍👩‍👧‍👦👩‍👩‍👧‍👦

Na Umm Asghar

24

Ranshi a bace ya shigo gidan. Tun daga kasa yake kwalawa Farida kira. Gaba daya jikinta ne ya dauki rawa jin yanayin da Daddy yake kiranta. Allah yasa dai ba wani laifin tayi ba don tun jiya dama a tsorace take da Daddy ganin bai wani bata goyin baya ba akan rikinsu da maigidanta.

A kasalance ta fito daga dakin don zuwa amsa kiran Daddy. Bata taba zaton akwai wata rana da zata ji tsoron haduwarta da Daddy ba irin yau don yanayin kiran da yake mata sosai ya kidimata. A bakin kofar dakin sukayi kacibis da Aisha da tazo kiranta. Ce mata kawai taje Daddy na kiranta ta wuce zuwa dakinta.

Da kyar Farida ta iya jan kafafunta ta wuce zuwa parlour Daddy. A hankali tamkar bata so tayi sallama, sai bayan daya amsa sallamar ne ta shiga cikin parlour. Durkusawa tayi tace "Daddy ina yini, gani ance kana kirana". Shiru ne ya ziyarci parlour tamkar babu kowa. Shi dai Daddy kallon Farida kawai yakeyi yana mamakin irin halayen yarinyar da abubuwan da mijinta yace tana yi mishi. Sai dai kuma yasan shine babban mai laifi a duk wani hali da Faridan ta kasance a ciki.

Tun tasowarta ya kasancevmai nuna bambanci tsakaninta da 'yanuwanta baya son laifinta ko kadan komai tayi a wurinshi daidai ne. Wani irin so yake yi mata da baya yiwa 'ya'yan daya haifa. Sosai yake tausayinta da maraicinta yana ganin duk duniya bata da sai shi tunda bata san ubanta ba. Kullum cikin nuna bambanci yake tsakaninta da 'yanuwanta don ko abu ne ya hadasu to baya taba bata laifi koda kuwa itace bata da gaskiya sai yace au aukw tsokanarta.

Akan haka sun sha samun sabani da Zainab don tana yawan gwada mishi cewa ba daidai bane abinda yakeyi. Bazai yiwu tayi tsokana ba sannan a bawa wanda t tsokana laifi ba wannan ba adalci bane amma sai ya rufe ido ya hau fada yana cewa don ba 'yarta bace yasa take ganin abin da yakeyi a kanta a matsayin rashin kyautawa amma da 'yarya ce yasan ko daga kai baza tayi ta kallesu ba.

A duk sanda irin haka ta faru sai tace mishi "wannan sangartawar fa da kake yiwa Farida ba gata ne kake yi mata ba domin kuwa ita din 'ya mace ce kuma wata rana gidan aure zata je, babu kuma mijin da zai dauki rashin da'a da rashin tarbiyyarta. Wannan wacce irin rayuwace ace yaro duk abinda yayi daidai ne baza'a mishi fada ba idan nayi magana kace na takura mata saboda ba 'yata bace nana tausayin maraicinta".

A yau ga wata rana din da Zainab ke yawan gaya mishi tazo gashi miji ya koro mishi Faridanshi akan halayenta marasa kyau. Allah ya jikan Zainab yayi mata Rahama, har kullum yana jin kewarta tana damunshi ya sani a zamansu bai kyuata mata ba don kuwa bai bata dama tayiwa yaranta irin tarbiyyar da take so ba. Dagowa yayi ya kalli Farida da jar lokacin take a durkushe tana sharar hawaye. A lokacin daya shigo daga ganawarsu da mijinta ranshi a matukar bace yake shine ma dalilim da yasa ya shigo yana kwala mata kira abinda ya fito da Aisha daga kitchen tana tambayarshi lafiya. Zaunar dashi tayi ta kawo mishi ruwa yasha sannan tace mishi bawai zai samu Farida da fada bane, nasiha zaiyi mata ya nuna mata cewa baya son munanan halayenta baiji dadin yadda take tafiyar da al'amuran gidanta ba a cikin nutsuwa ba wai da fada ba.

"Yanzu maigidanki ya bar nan mun kuma tattauna akan yanayin zamanki dashi da kuma iyalinshi. Banji dadi ba yanda yace wai bakya girmamashi bakya girmama matarshi sannan kuma bakya son 'ya'yansgi ba kyaso kiga yana kyakkyawar mu'amala dasu. Wanne irin sonkai ne dake Farida, yaya zakije gidan mata da 'ya'yanta kice wai mijinta bazai yi hulda da ita ba, to a ina aka taba irin haka.

Ai kema kinsan bakiso a zauna lafiya ba. Kin kuma dauki hanyar nesanta kanki ne da mijinki don ko ni nan bazan taba son matar da bata son iyalina ba. Don haka ina horonki da idan kin koma gidanki ki sake tsarin mu'amalarki da maigidanki da kuma iyalinshi.

Dole ne kiso 'ya'yanshi ki kuma yi kyakkyawar mu'amala dasu domin kuwa jema 'ya'yanki ne tunda kina auren ubansu kuma idan har son gaskiya kike yi mishi dole ne kiso duk wanda ke tare dashi don haka tsakaninki da matarshi girmamawa ne ban yarda naji ance kin raina ta ba.

Sannan kuma Farida dole ne ki kasance mai yin biyayya ga dukkan wani umarni na mijinki idan har bai kasance sabon Allah ba. Rashin da'a da tsiwa ba zai sa ki samu soyayyar mijinki ba sai dai ma ya nesanta ki dashi don haka inaso ki ajiye duk wani hali naki marar kyau ki aro kyawawan halaye ki yafa don kema ko zama tauraruwa a wurin mijinki.

Idan kinyi hakan kuma ba wani kika mutunta ba saini don wannan zai nuna cewa kin fito daga gida na tarbiyya tunda gashi kinyi ba daidai ba an gyara miki kuma kin dauka. Allah yayi miki albarka ya albarkaci rayuwar aurenki, tashi kije sai ki shirya gobe In Sha Allahu zaki koma gidanki".

Tunda Daddy ya fara magana Farida ke kuka har lokacin daya sallameta. Tashi tayi ta koma daki ta kwanta. Maganganun Daddy ne kawai suke dawo mata a ranta. Ta sani tana son mijinta sai dai kuma tana tsananin kishinshi da ko yaranshi bata so taga yana basu lokacinshi bare uwarsu.

Gashi kuma akayi dace yaran ba da'a ne dasu ba wannan ne yasa ta karaji yaran basuyi mata ba. Kasancewar ta saba a gidansu komai take sobshi take samu yasa tayi tunanin a gidan mijinta ma haka ne zai kasance sai taje ta tarar kwata-kwata rayuwar ba iri daya bace.

Mijinta wani irin mutum ne me son kanshi, bata usa tace anyi mata wani abu ba kama daga yaran har uwarsu sai ya rufe ido ya hau zazzaga mata masifa yana cewa bata isa ta rabashi da familynshi ba don sune rayuwarshi. Kuma fa sunayi mata abubuwa na rashin kirki amma kwata-kwata baya gani saima zuwa da yayi ya hadata da Daddy ya hada da laifinta da wanda ba nata ba duk yace nata ne.

Sai dai In Sha Allahu zata bashi mamaki don kamar yadda Daddy yace ne bada tsiya zata samo kanshi ba, ta kuma sha alwashin sai yaga canji a tare da ita sai ya sota ya mutunta ta a idon duniya kamar yadda yake yiwa matarshi. Zata zame mishi tamkar yadda Aisha ta zamarwa Daddy, zata zamanto mai sonshi mai tattalinshi da farin cikinshi. Zata yi hakuri da duk wani batanci da zata gani daga gareshi ne ko matarshi duk zata jure har sai ya sota tamkar koma fiye da matarshi don ta lura ba wani sonta yake yi ba tafi danganta shi da sha'awarta yakeyi, idan ma kuma akwai son to sha'awar ta rinjayeshi don haka zata koya mishi yadda zai sota ya kuma kaunaceta.

Dole ne ta sauke girman kai ta nemi taimakon Aunty Aisha (rana ta farko da Farida ta yardarwa zuciyarta cewa ta cancanci ta kirata da Aunty) wurin koyon girke-girke da yadda zata kula da muhallinta da mijinta dama wasu abubuwan. Don Ummie ta gaya mata irin problems din data fara fuskanta a wurin mijinta da taimakon Aunty Aisha komai ya zama normal.
Chapter 15 · 0% Book details