Sashe 10
Yayan Miji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yasan harda hakurinta da sanyin halinta wajen taimakawa wurin assasa mishi soyayyarta a zuciyarshi. Muryarta kawai yake so yaji ko zai samu nutsuwa sai dai kuma abin haushin shine ko numberta baya dashi.
To ko a wurin Khalifa zai nem number nata idan yaso sai ya fake da kira don jin lafiyarsu yaji muryarta. Kai a'a da kunya gaskiya ya nemi numberta wurin Khalifa sai dai ko a wurin Hajiya.
Kai yasan abu ne ma da bazai yiwu ba ya nemi numberta a wurin Hajiya idan dai baso yake ya bata mata rai ba. Kawai dai hakuri zaiyi har ya koma gida ai nan da kwan biyu ne babu wani dadewa. Sai dai kuma ganin kwanaki biyun yakeyi kamar watanni biyi koma shekaru don tsayi.
Ya dade a kwance yana juyi ba tare da ya iya yin bacci ba sai tunanin Aisha da ya sakashi a gaba. Da kyar bacci barawo ya lallabo ya saceahi, sai dai baccinnashi ma a cike yake da mafarkanta.
A safiyar alhamis ne Aisha ta tashi jikinta yayi matukar zafi zazzabi ya shigeta. Koda ta tashi ji tayi jiri yana dibanta, komawa tayi ta kwanta. Wayarta dake ajiye akan bedside drawer ta janyo ta kira Lami.
Ko mintuna biyar ba'a rufa ba Lami ta hayo, daga bakin kofa ta tsaya tana sallama. "Shigo Lami" Aisha tace bayan ta amsa mata sallamar. Karasowa ciki tayi sannan ta gaida Aisha.
Bayan sun gama gaisawa ne tace mata ta hadawa su Ruqaiya abincin makaranta sai kuma ta shirya breakfast saboda bata jin dadi bazata iya tashi ba.
Komawa tayi ta kwanta bayan fitar Lami daga dakin. Tana cikin bacci taji an yaye quilt din data rufa a jikinta. Koda ta bude ido Farida ta gani a tsaye a kanta tana huci. "Lafiya" shine abinda tace mata.
Cikin daga murya tacev"eh kin tambayi lafiya mana tunda kin samu wuri har kin nade akan gado kina bacci, idan banda kin samu wuri Lami zaki saka tayi mana abinci. Kevtunda kike a gidannan kin taba gani munci girkin 'yan aiki. To wallahi tun wuri gara ki tashi ki girka mana abinda zamuci idan ba haka ba na sanarwa Daddy".
Quilt dinta kawai taja ta rufa sannan tana daga ciki tace mata "idan kun ga bakwa son na Lamin sai ku shiga kitchen din ku girka amma ni yau bazan iya saukowa ba don kuwa bani da lafiya. Idan kin fita kija mini kofar".
Mamaki ne ya kama Farida don kuwa bata taba zaton Aisha zata iya maida mata martani ba. A nata tunanin shirun da Aishan keyi mata ta dauka tsoronta takeji bata san cewar tsabar rashin son fitina ne yasa take kyaleta.
Cikin sanyin jiki ta fita daga dakin. Dole hakanan abincin Lamin suka ci tundaha na safen har na rana dana dare. Da daren ne Farida ta dauki waya ta kira Daddy don ta kai mishi karar Aisha.
Yana daga wayar ko gaisheshi batayi ba ta fara mishi korafi tana cewa "Daddy karar matarnan na kawo maka yau throughout bata bamu abinci ba sai Lami ce ta girka mana kuma munyi mata magana tace idan baza muci ba mu barshi wai ita ta daina girka mana abinci".
Ajiyar zuciya ya sauke sannan yace "jinan Farida, hakanan Aisha bazata hanaku abinci ba ko dai akwai abinda kukayi mata, nasan halinku fa". Jin abinda abinda Daddy yace ne yasa ta fara matsar kwallar karya tana cewa "wallahi Daddy babu abinda mukayi mata kawai dai bata ga damar yin girkin bane kuma fa dama Daddy kaine bakasan halinta ba amma ba kirki ne da ita ba".
Har cikin ranshi yaji baiji dadin kalamin Farida akan Aisha ba. Hakuri kawai ya bata yace idan ya dawo zai tsawatar mata.
Washegari ma Aisha a kwance ta yini a ranar ma kuma sai Lami ta saka tayi mata girkin gidan. Kasancewar a ranar Daddy zai dawo ne yasa ta daure ta tashi duk da jiri dake dibarta amma a haka ta shiga dakinshi ta gyara ta wanke toilet sannan ta jona turaren wuta a burner.
Dakinta ta koma tayi wanka ta shirya a cikin atamfa super holland kalar blue da ratsin yellow a jiki. Mai kawai ta shafa sai turare data fesa a jikinta ta sauka kasa. Tea ta hada tasha sannan ta fito da naman kaza ta wanke ta dora duk a kokarinta na hadawa Daddy abinci sai dai kuma dauriya kawai takeyi don tsayuwa ma neman gagararta takeyi.
Kamshin tafasar naman ne ya bugeta a take taji amai ya taso mata. Kafin tayi wani yunkuri aman ya taho gaba daya. Anan wurin ta durkushe ta hau sheka amai. Lami dake wanke-wanke a sink ta taho da sauri ta riketa tana mata sannu.
Bayan ta gama aman ne ta kuskure bakinta Lami ta kamata ta maidata daki sannan ta koma ta gyara wurin. Komawa tayi dakin ta tambayeta me take da niyyar dafawa taje ta girka. Cewa tayi kawai tayi shinkafa da miya da salad. Sanin cewa ba lallai ne ya ci ba yasa tace tayi shinkafar don tasan baya cin abincin masu aiki.
Ya shigo gidan ne wajen karfe bakwai da rabi. Bai tarar da kowa ba a parlour kasa don haka ya wuce sama maybe kuma suna dakunansu. Dakinshi ya wuce, sai da yayi wanka yayi Sallah sannan ya fito don yaci abinci. Zuciyarshi fal da tunani Aisha yana mamakin abinda ya hana ta zuwa yi misgi sannu da zuwa. A take maganr da Farida tayi mishi jiya ta fado mishi a rai.
Baiyi wata-wata ba ya nufi dakinta don ganin lafiya. Tunda taje gidanshi a matsayin matarshi bai taba shiga dakinta ba sai yau. Tana kwance a kudundune cikin quilt. Da sallam a bakinshi ya shiga sai dai ganinta a kwance ta lulluba har kanta yasa bai san lokacin da ya karasa gaban gadon ba yana cewa "lafiya Aisha kika kudundune cikin bargo a zafinnan gashi ko fanka ko ac baki kunna ba".
Jin muryarshi ne yasa ta yaye rufarta bude idonta da suka kada suka yi jawur. Tsikar jikinshi ce yaji ta tashi hada idon da sukayi. Zama yayi a bakin gadon sannanyace "baki da lafiya ne, tun yaushe ne bakida lafiya" ya tambayeta yana mai kai hannu jikinta.
Da sauri ya janye hannunshi jin yadda jikinta yayi zafi. "Bari na canja kaya sai muje asibiti" yace a yayin da ya mike daga kan gadon. Baifi minti biyar da fita ba ya dawo yana sanye da shadda getzner kalar light brown dinkin tazarce.
Bargon ya janye sannan ya saka hannu ya dagota. Zaunar da ita yayi ya janyo hijabinta dake ajiye akan sallaya ya saka mata ya mika mata takalmi ta saka ya mikar da ita.
Tana rungume a jikinshi suka fita. Har sai da ya zaunar da ita a cikin mota sannan ya zagaya ya shiga ya tashi motar suka fice. Asibitin da suke da family folder suka je.
Ba wani bata lokaci suka sami ganin likita. Tambayr ta yayi abinda ke damunta tace mishi zazzabi ne sai jiri da take fama dashi sai kuma tashin zuciya. Test ya rubuta ta malaria da kuma ptegnancy test yace suje lab ayi yanzu su kawo mishi.
Bayan sunje sunyitest dinne sun kawo mishi result din ya duba yace "its as i suspected she's 12 wks pregnant sai dai kuma akwai malaria a jikinta. Wani irin farinciki ne ya ziyarci Daddy jin cewar zai samu Baby.
Gaba daya fuskarshi ta cika da annuri har mamaki ya dinga bawa Aisha don bata taba ganinshi a cikin farinciki kwatankwacin wannan ba. Bayan sun karbi magungunanta ne suka tashi suka tafi.
Motsi kadan idan Aisha tayi sai yayi mata sannu, mamakinshi ne kawai ya kamata don bata taba sanin wannan side din nashi ba.
UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): 👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
'YA'YAN MIJI
👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
Na Umm Asghar
17
Akan Aisha Daddy yayi watsi da policy dinshi na cewa iyalinshi bazasu ci abincin masu aiki ba don kuwa a yanzu kowa na gidan girkin Lami suke ci don laulayi ya sako Aisha a gaba komai taci sai ta amayar dashi.
Sosai take ganin kulawa da tarairaya a wurin Daddy abinda ya kara assasa wutar kiyayyarta a zuciyar yaran don sosai suke bakin cikin ganinta da ciki tun ma dai ba Farida ba.
Sai da cikinta yayi watanni hudu sannan ta samu saukin laulayin. A lokacin ne kuma ta karbi hidimar gidanta duk da dai Daddy yaso ta bari Lami ta cigaba da kulawa da komai amma ta dage akan zata iya don haka ya kyaleta.
A kwance take akan gadon Daddy sai shagwaba take zuba mishi wai jikinta na mata ciwo. Shi kuma ya biye mata yana mata tausa hade da yi mata mitar aikin da take yi ne ya saka mata ciwon jikin shine kuma dalilin da yasa tun farko ya hanata yin aikin taki ji.
Tun tana mamakin kulawar da take samu daga Daddy har ta dain don da farko ma kasa sakewa tayi dashi sai da taga dai da gaske yake janta ajikinshi sannan ta sake ta bar yin dari-dari dashi.
"Um Daddy kana jina" tace mishi cikin muryar shagwaba. Bata fuska yayi yaja kunnenta kadan yace "bana hana ki ce mini Daddy ba, ni ba Daddynki bane Daddyn baby ne" ya fada yana mai shafo cikinta. "Gara ma tun wuri ki daina kirana Daddy nan don banaso, kirani da sunana Ja'afar yafi mini, ok".
"Owch da zafi fa Dad... ow sorry, nifa gaskiya bazan iya kiran sunanka ba gatsau, haba ai babu ma tsari wallahi" ta fada tana mai cuno baki.
Sunkuyowa yayi yay kissing din lips dinta lightly sannan yace "to ki kirani da wani sunan amma ba Daddy ba". Tace to shikenan zanyi tunani, ni kasa na manta me ma zance maka, yauwa dama so nake nace'maka inason zuwa gidan Hajiya na gaisheta".
A take ya bata fuska yace "nifa bana son yawo, ke da baki da lafiya wane fita kuma zakiyi. Ina ce'kuma kusan sau uku Hajiyan tana zuwa dubaki bare kice kin dade baki ganta bane yasa kike son zuwa".
To ko a wurin Khalifa zai nem number nata idan yaso sai ya fake da kira don jin lafiyarsu yaji muryarta. Kai a'a da kunya gaskiya ya nemi numberta wurin Khalifa sai dai ko a wurin Hajiya.
Kai yasan abu ne ma da bazai yiwu ba ya nemi numberta a wurin Hajiya idan dai baso yake ya bata mata rai ba. Kawai dai hakuri zaiyi har ya koma gida ai nan da kwan biyu ne babu wani dadewa. Sai dai kuma ganin kwanaki biyun yakeyi kamar watanni biyi koma shekaru don tsayi.
Ya dade a kwance yana juyi ba tare da ya iya yin bacci ba sai tunanin Aisha da ya sakashi a gaba. Da kyar bacci barawo ya lallabo ya saceahi, sai dai baccinnashi ma a cike yake da mafarkanta.
A safiyar alhamis ne Aisha ta tashi jikinta yayi matukar zafi zazzabi ya shigeta. Koda ta tashi ji tayi jiri yana dibanta, komawa tayi ta kwanta. Wayarta dake ajiye akan bedside drawer ta janyo ta kira Lami.
Ko mintuna biyar ba'a rufa ba Lami ta hayo, daga bakin kofa ta tsaya tana sallama. "Shigo Lami" Aisha tace bayan ta amsa mata sallamar. Karasowa ciki tayi sannan ta gaida Aisha.
Bayan sun gama gaisawa ne tace mata ta hadawa su Ruqaiya abincin makaranta sai kuma ta shirya breakfast saboda bata jin dadi bazata iya tashi ba.
Komawa tayi ta kwanta bayan fitar Lami daga dakin. Tana cikin bacci taji an yaye quilt din data rufa a jikinta. Koda ta bude ido Farida ta gani a tsaye a kanta tana huci. "Lafiya" shine abinda tace mata.
Cikin daga murya tacev"eh kin tambayi lafiya mana tunda kin samu wuri har kin nade akan gado kina bacci, idan banda kin samu wuri Lami zaki saka tayi mana abinci. Kevtunda kike a gidannan kin taba gani munci girkin 'yan aiki. To wallahi tun wuri gara ki tashi ki girka mana abinda zamuci idan ba haka ba na sanarwa Daddy".
Quilt dinta kawai taja ta rufa sannan tana daga ciki tace mata "idan kun ga bakwa son na Lamin sai ku shiga kitchen din ku girka amma ni yau bazan iya saukowa ba don kuwa bani da lafiya. Idan kin fita kija mini kofar".
Mamaki ne ya kama Farida don kuwa bata taba zaton Aisha zata iya maida mata martani ba. A nata tunanin shirun da Aishan keyi mata ta dauka tsoronta takeji bata san cewar tsabar rashin son fitina ne yasa take kyaleta.
Cikin sanyin jiki ta fita daga dakin. Dole hakanan abincin Lamin suka ci tundaha na safen har na rana dana dare. Da daren ne Farida ta dauki waya ta kira Daddy don ta kai mishi karar Aisha.
Yana daga wayar ko gaisheshi batayi ba ta fara mishi korafi tana cewa "Daddy karar matarnan na kawo maka yau throughout bata bamu abinci ba sai Lami ce ta girka mana kuma munyi mata magana tace idan baza muci ba mu barshi wai ita ta daina girka mana abinci".
Ajiyar zuciya ya sauke sannan yace "jinan Farida, hakanan Aisha bazata hanaku abinci ba ko dai akwai abinda kukayi mata, nasan halinku fa". Jin abinda abinda Daddy yace ne yasa ta fara matsar kwallar karya tana cewa "wallahi Daddy babu abinda mukayi mata kawai dai bata ga damar yin girkin bane kuma fa dama Daddy kaine bakasan halinta ba amma ba kirki ne da ita ba".
Har cikin ranshi yaji baiji dadin kalamin Farida akan Aisha ba. Hakuri kawai ya bata yace idan ya dawo zai tsawatar mata.
Washegari ma Aisha a kwance ta yini a ranar ma kuma sai Lami ta saka tayi mata girkin gidan. Kasancewar a ranar Daddy zai dawo ne yasa ta daure ta tashi duk da jiri dake dibarta amma a haka ta shiga dakinshi ta gyara ta wanke toilet sannan ta jona turaren wuta a burner.
Dakinta ta koma tayi wanka ta shirya a cikin atamfa super holland kalar blue da ratsin yellow a jiki. Mai kawai ta shafa sai turare data fesa a jikinta ta sauka kasa. Tea ta hada tasha sannan ta fito da naman kaza ta wanke ta dora duk a kokarinta na hadawa Daddy abinci sai dai kuma dauriya kawai takeyi don tsayuwa ma neman gagararta takeyi.
Kamshin tafasar naman ne ya bugeta a take taji amai ya taso mata. Kafin tayi wani yunkuri aman ya taho gaba daya. Anan wurin ta durkushe ta hau sheka amai. Lami dake wanke-wanke a sink ta taho da sauri ta riketa tana mata sannu.
Bayan ta gama aman ne ta kuskure bakinta Lami ta kamata ta maidata daki sannan ta koma ta gyara wurin. Komawa tayi dakin ta tambayeta me take da niyyar dafawa taje ta girka. Cewa tayi kawai tayi shinkafa da miya da salad. Sanin cewa ba lallai ne ya ci ba yasa tace tayi shinkafar don tasan baya cin abincin masu aiki.
Ya shigo gidan ne wajen karfe bakwai da rabi. Bai tarar da kowa ba a parlour kasa don haka ya wuce sama maybe kuma suna dakunansu. Dakinshi ya wuce, sai da yayi wanka yayi Sallah sannan ya fito don yaci abinci. Zuciyarshi fal da tunani Aisha yana mamakin abinda ya hana ta zuwa yi misgi sannu da zuwa. A take maganr da Farida tayi mishi jiya ta fado mishi a rai.
Baiyi wata-wata ba ya nufi dakinta don ganin lafiya. Tunda taje gidanshi a matsayin matarshi bai taba shiga dakinta ba sai yau. Tana kwance a kudundune cikin quilt. Da sallam a bakinshi ya shiga sai dai ganinta a kwance ta lulluba har kanta yasa bai san lokacin da ya karasa gaban gadon ba yana cewa "lafiya Aisha kika kudundune cikin bargo a zafinnan gashi ko fanka ko ac baki kunna ba".
Jin muryarshi ne yasa ta yaye rufarta bude idonta da suka kada suka yi jawur. Tsikar jikinshi ce yaji ta tashi hada idon da sukayi. Zama yayi a bakin gadon sannanyace "baki da lafiya ne, tun yaushe ne bakida lafiya" ya tambayeta yana mai kai hannu jikinta.
Da sauri ya janye hannunshi jin yadda jikinta yayi zafi. "Bari na canja kaya sai muje asibiti" yace a yayin da ya mike daga kan gadon. Baifi minti biyar da fita ba ya dawo yana sanye da shadda getzner kalar light brown dinkin tazarce.
Bargon ya janye sannan ya saka hannu ya dagota. Zaunar da ita yayi ya janyo hijabinta dake ajiye akan sallaya ya saka mata ya mika mata takalmi ta saka ya mikar da ita.
Tana rungume a jikinshi suka fita. Har sai da ya zaunar da ita a cikin mota sannan ya zagaya ya shiga ya tashi motar suka fice. Asibitin da suke da family folder suka je.
Ba wani bata lokaci suka sami ganin likita. Tambayr ta yayi abinda ke damunta tace mishi zazzabi ne sai jiri da take fama dashi sai kuma tashin zuciya. Test ya rubuta ta malaria da kuma ptegnancy test yace suje lab ayi yanzu su kawo mishi.
Bayan sunje sunyitest dinne sun kawo mishi result din ya duba yace "its as i suspected she's 12 wks pregnant sai dai kuma akwai malaria a jikinta. Wani irin farinciki ne ya ziyarci Daddy jin cewar zai samu Baby.
Gaba daya fuskarshi ta cika da annuri har mamaki ya dinga bawa Aisha don bata taba ganinshi a cikin farinciki kwatankwacin wannan ba. Bayan sun karbi magungunanta ne suka tashi suka tafi.
Motsi kadan idan Aisha tayi sai yayi mata sannu, mamakinshi ne kawai ya kamata don bata taba sanin wannan side din nashi ba.
UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): 👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
'YA'YAN MIJI
👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
Na Umm Asghar
17
Akan Aisha Daddy yayi watsi da policy dinshi na cewa iyalinshi bazasu ci abincin masu aiki ba don kuwa a yanzu kowa na gidan girkin Lami suke ci don laulayi ya sako Aisha a gaba komai taci sai ta amayar dashi.
Sosai take ganin kulawa da tarairaya a wurin Daddy abinda ya kara assasa wutar kiyayyarta a zuciyar yaran don sosai suke bakin cikin ganinta da ciki tun ma dai ba Farida ba.
Sai da cikinta yayi watanni hudu sannan ta samu saukin laulayin. A lokacin ne kuma ta karbi hidimar gidanta duk da dai Daddy yaso ta bari Lami ta cigaba da kulawa da komai amma ta dage akan zata iya don haka ya kyaleta.
A kwance take akan gadon Daddy sai shagwaba take zuba mishi wai jikinta na mata ciwo. Shi kuma ya biye mata yana mata tausa hade da yi mata mitar aikin da take yi ne ya saka mata ciwon jikin shine kuma dalilin da yasa tun farko ya hanata yin aikin taki ji.
Tun tana mamakin kulawar da take samu daga Daddy har ta dain don da farko ma kasa sakewa tayi dashi sai da taga dai da gaske yake janta ajikinshi sannan ta sake ta bar yin dari-dari dashi.
"Um Daddy kana jina" tace mishi cikin muryar shagwaba. Bata fuska yayi yaja kunnenta kadan yace "bana hana ki ce mini Daddy ba, ni ba Daddynki bane Daddyn baby ne" ya fada yana mai shafo cikinta. "Gara ma tun wuri ki daina kirana Daddy nan don banaso, kirani da sunana Ja'afar yafi mini, ok".
"Owch da zafi fa Dad... ow sorry, nifa gaskiya bazan iya kiran sunanka ba gatsau, haba ai babu ma tsari wallahi" ta fada tana mai cuno baki.
Sunkuyowa yayi yay kissing din lips dinta lightly sannan yace "to ki kirani da wani sunan amma ba Daddy ba". Tace to shikenan zanyi tunani, ni kasa na manta me ma zance maka, yauwa dama so nake nace'maka inason zuwa gidan Hajiya na gaisheta".
A take ya bata fuska yace "nifa bana son yawo, ke da baki da lafiya wane fita kuma zakiyi. Ina ce'kuma kusan sau uku Hajiyan tana zuwa dubaki bare kice kin dade baki ganta bane yasa kike son zuwa".