Sashe 3
Yayan Miji Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
5
Ko da su Ummie suka dawo daga school sun iske Aisha ne a dakinsu. Farida ta rike kugu tare da kare mata kallo kafin tace "ke! Wacece ke kuma me kikeyi a dakinmu?" Farida kam akwai tsiwa ba kamar Ummie ba data kasance mai hakuri don sau tari idan Farida nayiwa Ummie tsiwa sai ka dauka itace babba. Aisha tayi murmushi sannan tace "sunana Aisha kuma yanzu a gidanku zan zauna so na zama 'yar gidanku kenan", cikin farinciki Ummie tace "kenan anan dakin zamu zauna dake, kai amma naji dadi wallahi, ko Farida?" "uhm" Farida tace tana yatsina fuska. Uniform ta cire ta zubar dasu a tsakiyar dakin sannan ta debi kaya ta saka ta fice daga dakin tana kwala kiran "Mami mun dawo". Ita kam Ummie ta saka Aisha a gaba tana ta mata tambayoyi, ita dai Aisha murmushi takeyi kasancewarta ba mai yawan magana ba. Shigowar Mami dakin ne yasa suka dago suka kalleta. "Ku taso kuci abinci ke Ummie kin saka Aisha a gaba da surutu ko, wai ko uniform din ma baki cire ba" tace bayan ta karaso cikin dakin sosai. Tashi Ummie tayi tana cewa "yanzu zan cire Mami". Tace "to maza ki cire ku fito kuci abinci don ku kadai ake jira" ta juya ta bar dakin.
Bayan Ummie ta canja kayan makarantarta dana gida ne suka sauka kasa don cin abincin. Ummie taja kujera ta zauna sannan tace Aisha tazo ta zaunaa kujerar kusa da ita. Tsaki Farida tayi don hakanan taji bakuwar da aka kira da Aisha bata kwanta mata ba. Ita kam Aisha duk a takure take jinta don bata saba cin abinci a table kuma a cikin mutane haka ba. Mu'azzam ne ya dago yana cewa "Mami wacece wannan kuma da zata zo ta zauna mana anan bata san nan duka family bane, me ya kawo bare cikinmu"
Cikin kakkausar murya Mami tace "Mu'azzam yi mini shiru anan, Aisha ba bare bace itama 'yar gida ce don haka kar na kara jin makamanciyar magana irin wannan a bakinka, kai gaba dayanku ma hope you understand?", gaba daya suka ce "eh Mami". Bayan gama cin abincinsu ne suka koma daki, suna shiga Aisha ta hau tattare kayan Farid data zubar a kasa. "Ina za'a saka wadannan" tace wa Ummie, "kai mata toilet ki saka a cikin kwandon kayan wanki" ta amsata.
Da daddare ne Mami suna zaune da Daddy a sittingroom dinshi na sama take ce mishi "dazu Hajiya tazo har ta kawo mini yarinyar da zata na tayani aiki tace 'yar wata kanwartace data rasu shine ta dauko yarinyar, to ina tunanin a sakata a school maimakon zamanta a haka ko ya ka gani". Shiru yayai bai amsata ba, ita kam wannan hali na J.B sau tari yana bata mata rai don idan baiso ba duk maganar da zatayi ba amsawa yakeyi ba shine ma ya saka idan ta mishi magana taga bai amsata ba bata maimaitawa sai ta kyaleshi, don kanshi kuma idan yaso saibya dauko maganar.
Yanzun ma ganin bazai amsata bane yasa ta mike don taje tayi shirin barci. Har ta kai wurin kofa taji yana cewa "duk yanda kikayi daidai ne". Murmushi kawai tayi sannan tace "nagode bari naje nayi shirin kwanciya don barci nakeji, akwai abinda kake bukata?" Cikin ginshira yace "yeah, only you". Wata kasalalliyar dariya tayi sannan tace "hmm Daddy kenan" ta juya ta bar parlour cikin rangwada. Hannu yasa ya shafa kwantacciyar sumarshi yana mai lumshe ido, murmushi dauke a fuskarshi. Shi kam Allah ya sani yana son Zainab sosai, after all these years yana jinta a ranshi tamkar yau ya fara sonta. Tashi yayi shima ya nufi dakin din yayi shirin kwanciya.
UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): 👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
'YA'YAN MIJI
Na Umm Asghar
7
A haka dai rayuwa taci gaba da tafiya. Ga Aisha dai ta dada kame kanta daga shiga harkar Farida da Mu'azzam don ta lura akansu zaman gidan zai iya gagararta. Ita kuwa a yanda takejin dadin zama da Mami ga kuma ingantaccen ilimi duka biyu wato na addini da boko da take samu baza taso tayi abinda zai rabata da zaman gaidannan ba.
Ga kuma baby Ruqaiya da sukayi wata irin shakuwa da ita don mafi yawan lokuta idan tana wurin Aisha ko Mami bata yarda ta dauketa sai da kyar. To shima Daddy a nashi bangaren bai kara maganar mayar da ita gidan Hajiya ba, kodayake a yanzu duk fitinar Farida da neman rigimarta ta kyale Aisha ganin bata shiga harkarta.
A yanzu haka Aisha tana ss1 ne yayin dasu Ummie suke jss3. Tun zuwan Aisha gidan sau daya taje garinsu tayi hutu na sati uku. A wannan lokacin ma hutun take son zuwa sai dai kuma kasancewar ciki ne da Mami tsohi yasa dole ta hakura. Ko babu komai tana taimakawa Mami da hidimar gidan don zuwa wannan lokacin babu wani abu da bata iya ba a kitchen.
Mafi yawan lokuta zaka sameta ne a kitchen tare da Mami da sauran ma'aikatan gidan, abinda bazaki taba ganin Ummie ko Farida sunyi ba. Yanzu ma aikin abincin dare sukeyi ita da Mami a kitchen. Yaya Khalifa ne ya shigo kitchen din yace "sannu Mami, mezan samu wallahi na gaji da yawa ga yunwa na kwaso, yau tunda muka fara lectures tun 12 sai six muka gama without any interval".
"Sannu Yay Khalifa ai kana kokari wallahi Allah dai ya bada sa'a". "Amin Aisha nagode, me kukayi ne da rana? Yace bayan ya zauna akan kujerar kitchen din. "Favourite dinka ne wato faten doya bari na zuba maka" tace bayan ta dauki plate ta zuba mishi abincin sannan tace mishi "anan zakaci ne ko na kai maka parlour". "Bari kawai na wuce dashi Aisha nagode" yace yana mai tashi daga kan kujerar. Karbar abincin yayi ya fita a kitchen din. Bayan sun gama hada abincin ne Mami ta fita ta barta a kitchen din ta karasa gyarawa. Sosai take tausayawa Mami ganin duk da tsufan cikinta hakan bai hanata yin hidimar gidanta ba.
A daren ranar suna kwance suna bacci Mami ta shigo dakinsu ta tashi Aisha. "Lafiya Mami?" tace bayan ta tashi zaune. "Saka hijabinki ki taso asibiti zamuje" tace mata a yayin da take barin dakin. A hanzarce ta tashi ta daura zani akan kayan baccinta ta dora hijabi ta fita zuwa dakina Mami. Akwatin da Mami ta hada don zuwa asibiti ta dauka suka fita. Koda suka fita harabar gidan tuni Daddy ya juyo da mota, gidan gaba ta budewa Mami ta shiga sannan ta koma baya ta zauna.
A lokacin da suka isa asibitin karfe daya da rabi ne na dare. Suna zuwa direct labour room aka wuce da Mami, su kuma suka samu wuri anan rwception din suka zauna. Nesa sosai da Daddy Aisha ta zauna, duk sai tana jinta a takure don ita dai hakanan take jin tsoron Daddy bata taba sakewa dashi ba shima kuma bai taba sakar mata fuska ba tsakaninta dashi gaisuwa ce kawai.
Basuyi zaman awa daya ba a wurin nurse ta fito ta fada musu Mami ta haihu diya mace. Gaba daya annurin farinciki ne ya sauka a fuskar Daddy, mamaki ne ya kama Aisha don kuwa bata taba ganin fara'arshi haka ba. Ba'a wani jima sosai ba aka fito da Mami da babynta zuwa wani dakin. Bin bayansu sukayi zuwa dakin da aka kwantar da ita. Daddy na rike da baby sai faman fara'a yakeyi yana ce mata "sannu Zainab", ya dade a asibitin kafin yayi sallama da Mami ya tafi gida don a lokacin kausan karfe uku da rabi ne na dare. Daga Mami har Aisha basu wani samu yin barci ba saboda baby bata barsu ba. Sauki daya suka samu ma shine da safe da likita yazo ya dubasu ya basu sallama. Anyi sallamar babu dadewa Daddy ya shigo dakin hannunshi rike da kwandon kayan abinci. Da sauri Aisha ta tashi ta karbi kwandon a hannunshi sannanta gaisheshi. Yana amsawa ya karasa kan gadon ya zauna yana yiwa Mami sannu tare da amsar baby a hannunta. Breakfast kawai sukayi suka koma gida kasancewar anyi discharging dinsu tun kafin zuwan Daddy. Da isarsu gida yaran gaba daya suka fito suna ihun Murna. Rige-rigen karbar baby sukeyi, Mu'azzam ne ya karbi babyn a hannun Aisha ita kuma ta fito da kayansu suka shiga cikin gidan. Cikin kankanin lokaci gidan ya cika da baki 'yan barka don haka nema hutun da Aisha take bukata bata sameshi ba saboda hidima da tayi mata yawa.
UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): 👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
'YA'YAN MIJI
Na Umm Asghar
Ko da su Ummie suka dawo daga school sun iske Aisha ne a dakinsu. Farida ta rike kugu tare da kare mata kallo kafin tace "ke! Wacece ke kuma me kikeyi a dakinmu?" Farida kam akwai tsiwa ba kamar Ummie ba data kasance mai hakuri don sau tari idan Farida nayiwa Ummie tsiwa sai ka dauka itace babba. Aisha tayi murmushi sannan tace "sunana Aisha kuma yanzu a gidanku zan zauna so na zama 'yar gidanku kenan", cikin farinciki Ummie tace "kenan anan dakin zamu zauna dake, kai amma naji dadi wallahi, ko Farida?" "uhm" Farida tace tana yatsina fuska. Uniform ta cire ta zubar dasu a tsakiyar dakin sannan ta debi kaya ta saka ta fice daga dakin tana kwala kiran "Mami mun dawo". Ita kam Ummie ta saka Aisha a gaba tana ta mata tambayoyi, ita dai Aisha murmushi takeyi kasancewarta ba mai yawan magana ba. Shigowar Mami dakin ne yasa suka dago suka kalleta. "Ku taso kuci abinci ke Ummie kin saka Aisha a gaba da surutu ko, wai ko uniform din ma baki cire ba" tace bayan ta karaso cikin dakin sosai. Tashi Ummie tayi tana cewa "yanzu zan cire Mami". Tace "to maza ki cire ku fito kuci abinci don ku kadai ake jira" ta juya ta bar dakin.
Bayan Ummie ta canja kayan makarantarta dana gida ne suka sauka kasa don cin abincin. Ummie taja kujera ta zauna sannan tace Aisha tazo ta zaunaa kujerar kusa da ita. Tsaki Farida tayi don hakanan taji bakuwar da aka kira da Aisha bata kwanta mata ba. Ita kam Aisha duk a takure take jinta don bata saba cin abinci a table kuma a cikin mutane haka ba. Mu'azzam ne ya dago yana cewa "Mami wacece wannan kuma da zata zo ta zauna mana anan bata san nan duka family bane, me ya kawo bare cikinmu"
Cikin kakkausar murya Mami tace "Mu'azzam yi mini shiru anan, Aisha ba bare bace itama 'yar gida ce don haka kar na kara jin makamanciyar magana irin wannan a bakinka, kai gaba dayanku ma hope you understand?", gaba daya suka ce "eh Mami". Bayan gama cin abincinsu ne suka koma daki, suna shiga Aisha ta hau tattare kayan Farid data zubar a kasa. "Ina za'a saka wadannan" tace wa Ummie, "kai mata toilet ki saka a cikin kwandon kayan wanki" ta amsata.
Da daddare ne Mami suna zaune da Daddy a sittingroom dinshi na sama take ce mishi "dazu Hajiya tazo har ta kawo mini yarinyar da zata na tayani aiki tace 'yar wata kanwartace data rasu shine ta dauko yarinyar, to ina tunanin a sakata a school maimakon zamanta a haka ko ya ka gani". Shiru yayai bai amsata ba, ita kam wannan hali na J.B sau tari yana bata mata rai don idan baiso ba duk maganar da zatayi ba amsawa yakeyi ba shine ma ya saka idan ta mishi magana taga bai amsata ba bata maimaitawa sai ta kyaleshi, don kanshi kuma idan yaso saibya dauko maganar.
Yanzun ma ganin bazai amsata bane yasa ta mike don taje tayi shirin barci. Har ta kai wurin kofa taji yana cewa "duk yanda kikayi daidai ne". Murmushi kawai tayi sannan tace "nagode bari naje nayi shirin kwanciya don barci nakeji, akwai abinda kake bukata?" Cikin ginshira yace "yeah, only you". Wata kasalalliyar dariya tayi sannan tace "hmm Daddy kenan" ta juya ta bar parlour cikin rangwada. Hannu yasa ya shafa kwantacciyar sumarshi yana mai lumshe ido, murmushi dauke a fuskarshi. Shi kam Allah ya sani yana son Zainab sosai, after all these years yana jinta a ranshi tamkar yau ya fara sonta. Tashi yayi shima ya nufi dakin din yayi shirin kwanciya.
UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): 👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
'YA'YAN MIJI
Na Umm Asghar
7
A haka dai rayuwa taci gaba da tafiya. Ga Aisha dai ta dada kame kanta daga shiga harkar Farida da Mu'azzam don ta lura akansu zaman gidan zai iya gagararta. Ita kuwa a yanda takejin dadin zama da Mami ga kuma ingantaccen ilimi duka biyu wato na addini da boko da take samu baza taso tayi abinda zai rabata da zaman gaidannan ba.
Ga kuma baby Ruqaiya da sukayi wata irin shakuwa da ita don mafi yawan lokuta idan tana wurin Aisha ko Mami bata yarda ta dauketa sai da kyar. To shima Daddy a nashi bangaren bai kara maganar mayar da ita gidan Hajiya ba, kodayake a yanzu duk fitinar Farida da neman rigimarta ta kyale Aisha ganin bata shiga harkarta.
A yanzu haka Aisha tana ss1 ne yayin dasu Ummie suke jss3. Tun zuwan Aisha gidan sau daya taje garinsu tayi hutu na sati uku. A wannan lokacin ma hutun take son zuwa sai dai kuma kasancewar ciki ne da Mami tsohi yasa dole ta hakura. Ko babu komai tana taimakawa Mami da hidimar gidan don zuwa wannan lokacin babu wani abu da bata iya ba a kitchen.
Mafi yawan lokuta zaka sameta ne a kitchen tare da Mami da sauran ma'aikatan gidan, abinda bazaki taba ganin Ummie ko Farida sunyi ba. Yanzu ma aikin abincin dare sukeyi ita da Mami a kitchen. Yaya Khalifa ne ya shigo kitchen din yace "sannu Mami, mezan samu wallahi na gaji da yawa ga yunwa na kwaso, yau tunda muka fara lectures tun 12 sai six muka gama without any interval".
"Sannu Yay Khalifa ai kana kokari wallahi Allah dai ya bada sa'a". "Amin Aisha nagode, me kukayi ne da rana? Yace bayan ya zauna akan kujerar kitchen din. "Favourite dinka ne wato faten doya bari na zuba maka" tace bayan ta dauki plate ta zuba mishi abincin sannan tace mishi "anan zakaci ne ko na kai maka parlour". "Bari kawai na wuce dashi Aisha nagode" yace yana mai tashi daga kan kujerar. Karbar abincin yayi ya fita a kitchen din. Bayan sun gama hada abincin ne Mami ta fita ta barta a kitchen din ta karasa gyarawa. Sosai take tausayawa Mami ganin duk da tsufan cikinta hakan bai hanata yin hidimar gidanta ba.
A daren ranar suna kwance suna bacci Mami ta shigo dakinsu ta tashi Aisha. "Lafiya Mami?" tace bayan ta tashi zaune. "Saka hijabinki ki taso asibiti zamuje" tace mata a yayin da take barin dakin. A hanzarce ta tashi ta daura zani akan kayan baccinta ta dora hijabi ta fita zuwa dakina Mami. Akwatin da Mami ta hada don zuwa asibiti ta dauka suka fita. Koda suka fita harabar gidan tuni Daddy ya juyo da mota, gidan gaba ta budewa Mami ta shiga sannan ta koma baya ta zauna.
A lokacin da suka isa asibitin karfe daya da rabi ne na dare. Suna zuwa direct labour room aka wuce da Mami, su kuma suka samu wuri anan rwception din suka zauna. Nesa sosai da Daddy Aisha ta zauna, duk sai tana jinta a takure don ita dai hakanan take jin tsoron Daddy bata taba sakewa dashi ba shima kuma bai taba sakar mata fuska ba tsakaninta dashi gaisuwa ce kawai.
Basuyi zaman awa daya ba a wurin nurse ta fito ta fada musu Mami ta haihu diya mace. Gaba daya annurin farinciki ne ya sauka a fuskar Daddy, mamaki ne ya kama Aisha don kuwa bata taba ganin fara'arshi haka ba. Ba'a wani jima sosai ba aka fito da Mami da babynta zuwa wani dakin. Bin bayansu sukayi zuwa dakin da aka kwantar da ita. Daddy na rike da baby sai faman fara'a yakeyi yana ce mata "sannu Zainab", ya dade a asibitin kafin yayi sallama da Mami ya tafi gida don a lokacin kausan karfe uku da rabi ne na dare. Daga Mami har Aisha basu wani samu yin barci ba saboda baby bata barsu ba. Sauki daya suka samu ma shine da safe da likita yazo ya dubasu ya basu sallama. Anyi sallamar babu dadewa Daddy ya shigo dakin hannunshi rike da kwandon kayan abinci. Da sauri Aisha ta tashi ta karbi kwandon a hannunshi sannanta gaisheshi. Yana amsawa ya karasa kan gadon ya zauna yana yiwa Mami sannu tare da amsar baby a hannunta. Breakfast kawai sukayi suka koma gida kasancewar anyi discharging dinsu tun kafin zuwan Daddy. Da isarsu gida yaran gaba daya suka fito suna ihun Murna. Rige-rigen karbar baby sukeyi, Mu'azzam ne ya karbi babyn a hannun Aisha ita kuma ta fito da kayansu suka shiga cikin gidan. Cikin kankanin lokaci gidan ya cika da baki 'yan barka don haka nema hutun da Aisha take bukata bata sameshi ba saboda hidima da tayi mata yawa.
UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): 👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
'YA'YAN MIJI
Na Umm Asghar