Sashe 5
Yayan Miji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
9
Tun bayan da Aisha tayi sallar asuba sai bata koma bacci ba sai ta shiga wanka ta fito ta shirya cikin atamfar mediym holland dinkin riga da zanu. Koda ta shirya sai ta hau gyaran gidan inda duk tasan ita ke gyarawa. Bayan ta gama ne ta shiga dakin Mami. Bata sameta a dakin ba don haka sai ta shiga gyaran dakin. Tana cikin yin shara ne Mami ta fito daga bandakin ga dukkan alamu wanka tayi.
"A'a Aisha har kin shirya" tace a lokacin da take zama a kan stool din dressing mirror. "Eh Mami, ina kwana" "lafiya lau, kin ma kuwa yi bacci irin wannan sakko haka" dariya tayi tace "nayi bacci Mami kawai dai tunda nayi sallah ban koma ba. Me za'ayi as breakfast naga kwana biyu ba'a bin timetable"? Mami tace ai kuwa dai, sabon timetable nakeso nayi har yanzu kuma ban samu lokaci na zauna ba. Ki bare doya a dafa sai ayi doya mai kwai hade da farfesun kayan cikin da mukayi jiya yana cikin fridge warming kawai za'ayi sai tea. Kije ki fara kafin na gama shiryawa na fito kitchen din".
Tattara sharar tayi sannan ta nufi kitchen don tayi aikin da Mami ta sakata. Sai dai ta kusa gama hada breakfast din sannan Mami ta shigo ta tayata suka karasa. Karfe goma batayi ba su Aisha suka dauki hanya ita da Mallam Adamu driver. Sosai Ruqaiya tayi kuka ganin Aisha zata fita babu ita. Ita kanta Aisha sai da ta zubar da hawaye ganin yadda Ruqaiya ke kuka.
Sun isa garinsu wurin karfe sha daya. Basu sami Babanta a gida ba har ya fita kasuwa sai Goggo kawai suka samu da 'yan jikokinta suna wasa. Karba sosai akayi mata. Ruwa kawai Mallam Adamu yasha ya juya ya bar Aisha sai bayan sati biyu zai dawo ya dauketa. Bayan taci abinci ta huta ne ta fita gidajen makwabta fon ta gaishesu. Duk gidan data shiga suna mamakin girmanta da wayewar da tayi. Ba ita ta koma gida ba sai goshin magriba, koda ta koma gida Babanta ya dawo. Sosai yaji dadin ganinta. Sai bayan anyi isha'i ne sannan ta fito musu da tsarabarsu suna ta murna tare da saka albarka. Bayan nanne suka zauna da Babanta suna hira, sai tambayoyi yakeyi mata akan zamanta dasu Mami ko tana da matsala duk da dai baiga alamar hakan a tare da ita ba amma zaiso yaji hakan daga bakinta. Sai da ta tabbatar mishi bata da wata matsala sannan suka shiga hirar duniya.
Anan nema yake ce mata shidai zaiso ace data gama secondary school idan har ta samu miji ta kawoshi gida ayi mata aure don mutuncin diya mace shine dakin mijinta don anan garinsu har an fara surutun rashin aurenta don ma ba ganinta akeyi ba.
Sosai Aisha taji dadin zuwanta gida don ta zagaya 'yanuwanta na wajen uwa da uba ta sada zumunci don haka ne ma taga sati biyun tayi saurin karewa. Koda safiyar da zata koma kano tayi ta gama shirinta tsaf kafin lokacin da Mallam Adamu yazo daukarta. Duk wani tsaraba da zata tafi dashi an hada mata shi wuri daya. Babanta ma bai fita kasuwa ba din yana so yaga tafiyarta kafin ya fita. Kafin karfe sha biyi Mallam Adamu har ya iso, babu bata lokaci tayi sallama da duk mutanen gidan ta fito tana sharar kwalla ta shiga mota suka dauki hanyar kano.
Suna hawa titi ta fara bacci wanda ba ita ta farka ba sai da suka iso gida taji Mallam Adamu nace mata ta tashi sun iso gida. Farkawa tayi da salati a bakinta ta kalli harabar gidan sai taga tamkar yaune ta bar gidan gashi har taje ta dawo. Da sallama ta shiga cikin parlour babu kowa a ciki don haka ta wuce kitchen don tasan a wannan lokacin acan zata samu Mami. Sosai Mami tayi murnar dawowarta. Bayan sun gaisa ne ta haya sama don ta ajiye kayanta. Data sauko ne take tambayar Mami inasu Ummie tace mata suna gidan Hajiya acan zasu yini. "Kuma Mami har Ruqaiya sukaje gidan Hajiya"? "A'a tana dakina tana bacci bata dade da kwanciya ba kika shigo".
Koda Ruqaiya ta farka taga Aisha ai sai ta makale mata ta hanata sakat duk inda ta saka kafa nan take maida tata. Ko gani takeyi zata kara tafiya ta barta ne. Su Ummie basu dawo gida ba sai wurin takwas na dare. A lokacin Aisha ce kadai a parlour don Mami tana sama tare da Daddy. Ganin Aisha a zaune da gudu Ummie tazo ta rungume ta tana murna cewa takeyi "Wallahi Aunty Aisha munyi missing dinki sosai kullum Ruqaiya sai tayi mana kuka ita akaita Aunty Aishanta gashi komai akayi mata sai tace sai ta gayawa Aunty Aisha idan ta dawo".
Ita kanta Aisha taji dadin ganinsu don kuwa tayi kewarsu sosai. Farida ce ta kalleta a sheke tace "huh lallai zaman kauye dai baiyi ba, Allah nagode maka da ban hada komai da kauye ba da ko yaya mutum yaje kauye ya dawo sai ya canja". Dariyar shakiyanci Mu'azzam ya saka sannan yace mata "ai wannan uwar kibar da kike narkawa kamata yayi a kaiki kauyen ko kya sabe, wuu wa yaga Farida a kauye" ya kyalkyale da dariya har yana rike ciki. "Amma dai wallahi Yaya Mu'azzam ka cuceni, aini ko ace daga kauye nake idan na samu na rabu da zaman kauye babu abinda zai maidani ballantana ma mi yayi gamin jirgi da mita" tace tana murguda mishi baki. Haka dai sukayi ta shakiyancinsu Aisha na jinsu tayi tamkar bata san ma sunayi ba.
UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): 👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
'YA'YAN MIJI
👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
Na Umm Asghar
10
A haka dai rayuwa taci gaba, gashi Aisha har ta gama secondary school ta samu cigaba a makarantar Sa'adatu Rimi college of Education tana karantar catering wato fannin girke-girke.
A yammacin wata alhamis ne Aisha na kitchen tana taya Mami hidimar abincin dare, Mamin ce ta shigo kitchen din tace "sannu Aisha na tafi na barki da aiki ko, wai ina wajen Daddy muna maganar tafiya Umrah da zamuyi tunda yara suna hutu, inaga ko wajen jibi sai ki shirya ki koma wajen Hajiya kafin mu dawo tunda tafiyar zata kama ranar lahadi ne".
"Ashe tafiyar tazo, Allah ya kaiku lafiya ya dawo daku lafiya. Mami ayi mana addu'a, In Sha Allahu zanyi shirin. Har kwana nawa zakuyi? "Inaga sati biyu ne" inji Mami.
Tunda Farida taji batun tafiyarsu Umrah taji kuma babu Aisha a tafiyar take ta faman yada mata da habaici. Ita kam Aisha ko kallonta batayi ba. Wani abu da Farida bata sani ba shine bata taba hada kanta dasu ba. Tasan matsayinta a gidan na 'yar cin arziki ta kuma san nasu matsayin na 'ya'yan gidan.
Wannan nema dalilin da yasa bata taba daga ido ta kalli wani abu da akayi musu da ba'ayi da itaba duk da dai Mami na kamantawa mawuyacin abu ne tayi musu wani abin batayi mata ba amma wasu lokutan tana yi din ita kuma Aisha hakan bai taba damunta ba.
A kowanne lokaci ta kasance mai godiyar Allah da bais ta zama mai kwadayin abin wani ba. Banda haka da tasha takacin Farida don kuwa sau tari Daddy yanayi musu kyauta ita da Ummie ba tare da ya hada da ita ba. Idan irin haka ta faru Farida ta dinga iyawa tana kafafa kenan duk don ta kular da ita.
Bata manta wani lokaci da Daddy yayi wata tafiya zuwa ingila ya kawowa su Ummie wayoyin hannu a matsyin tsarabarsu. Firirita da iyawar da Farida tayi mata a lokacin don ta kular da ita nada yawa. Ita kam ma dariya abn ya dinga bata don ganin ita dai wayar ma ba damunta tayi ba kuma ba wanda zata kira a waya gareta ba bare ta damu.
A yammacin asabar bayan ta gama hada kayanta zata tafi gidan Hajiya ne ta suka kasa don su kara yin sallama da Mami kafin ta wuce. Kowa na tambayarta abinda takeso su saya mata harda Zainab sai abinma ya bata dariya.
Da zata tafi ne Mami ta kawo kudi ta bata koda zata bukaci wani abu ba sai ta tambayi Hajiya ba. Godiya sosai tayi mata sannan ta dauki jakar kayanta ta kara yimata sallama ta fita. Har mota su Ummie suka rakata, ganin ta shiga mota sai Zainab ta fashe da kuka wai sai ta bita. Da kyar Ummie ta janyeta suka koma cikin gida.
Ta sani itama zatayi kewar Ruqaiya da Zainab sosai domin kuwa ta shaku da yaran ba kadan ba. Duk wata hidima tasu itace tun daga kan wankansu, cin abincinsu, shirinsu zuwa makaranta, kitsone da koya musu homework duk ita keyi. Mafi yawan lokuta ma tare suke kwana a dakin yaran.
Da sallama ta shiga cikin gidan tana janye da akwatinta. Baaba Indo mai aikin Hajiya na tsugune a bakin famfo tana wanke-wanke. Dagowa tayi tare da amsa sallamar tana cewa "maraba da takwara yanzu da yammannan kike tafe".
Cikin fara'ar da bata yankewa a fuskarta tace "eh Baaba Indo mun sameku lafiya" tace "lafiya lau hala dai zaki kwana mana biyu na ganki harda akwati". Aisha tace "eh sati biyu zanyi muku" tace "kai madalla kice muna da babbar bakuwa".
Murmushi kawai tayi ta wuce dakin Hajiya. Bata sameta a parlour ba sai ta wuce cikin dakin. A zaune akan sallaya ta tararda ita tana karatun AlQur'ani don haka akwatin kawai ta ajiye ta fito parlour ta zauna. Tayi kusan mintina goma a zaune kafin Hajiya ta fito daga dakin. Zamowa tayi daga kan kujerar ta gaisheta.
Bayan sun gama gaisawa ne Hajiya ke cemata taje kitchen ta debi abinci. "Wallahi na koshi Hajiya sai dai ko zuwa anjima" tace mata. Jefi-jefi suke hira da Hajiya har aka kira sallar magriba suka tashi don yin sallar.
Aisha dai bata tashi akan sallayar ba sai bayan da tayi sallar isha. Ko a gida ta saba bata tashi bayan magriba zama takeyi tayi tilawar karatun Alqur'ani har sai an kira sallar isha tukunna ta tashi tayi.
Tun bayan da Aisha tayi sallar asuba sai bata koma bacci ba sai ta shiga wanka ta fito ta shirya cikin atamfar mediym holland dinkin riga da zanu. Koda ta shirya sai ta hau gyaran gidan inda duk tasan ita ke gyarawa. Bayan ta gama ne ta shiga dakin Mami. Bata sameta a dakin ba don haka sai ta shiga gyaran dakin. Tana cikin yin shara ne Mami ta fito daga bandakin ga dukkan alamu wanka tayi.
"A'a Aisha har kin shirya" tace a lokacin da take zama a kan stool din dressing mirror. "Eh Mami, ina kwana" "lafiya lau, kin ma kuwa yi bacci irin wannan sakko haka" dariya tayi tace "nayi bacci Mami kawai dai tunda nayi sallah ban koma ba. Me za'ayi as breakfast naga kwana biyu ba'a bin timetable"? Mami tace ai kuwa dai, sabon timetable nakeso nayi har yanzu kuma ban samu lokaci na zauna ba. Ki bare doya a dafa sai ayi doya mai kwai hade da farfesun kayan cikin da mukayi jiya yana cikin fridge warming kawai za'ayi sai tea. Kije ki fara kafin na gama shiryawa na fito kitchen din".
Tattara sharar tayi sannan ta nufi kitchen don tayi aikin da Mami ta sakata. Sai dai ta kusa gama hada breakfast din sannan Mami ta shigo ta tayata suka karasa. Karfe goma batayi ba su Aisha suka dauki hanya ita da Mallam Adamu driver. Sosai Ruqaiya tayi kuka ganin Aisha zata fita babu ita. Ita kanta Aisha sai da ta zubar da hawaye ganin yadda Ruqaiya ke kuka.
Sun isa garinsu wurin karfe sha daya. Basu sami Babanta a gida ba har ya fita kasuwa sai Goggo kawai suka samu da 'yan jikokinta suna wasa. Karba sosai akayi mata. Ruwa kawai Mallam Adamu yasha ya juya ya bar Aisha sai bayan sati biyu zai dawo ya dauketa. Bayan taci abinci ta huta ne ta fita gidajen makwabta fon ta gaishesu. Duk gidan data shiga suna mamakin girmanta da wayewar da tayi. Ba ita ta koma gida ba sai goshin magriba, koda ta koma gida Babanta ya dawo. Sosai yaji dadin ganinta. Sai bayan anyi isha'i ne sannan ta fito musu da tsarabarsu suna ta murna tare da saka albarka. Bayan nanne suka zauna da Babanta suna hira, sai tambayoyi yakeyi mata akan zamanta dasu Mami ko tana da matsala duk da dai baiga alamar hakan a tare da ita ba amma zaiso yaji hakan daga bakinta. Sai da ta tabbatar mishi bata da wata matsala sannan suka shiga hirar duniya.
Anan nema yake ce mata shidai zaiso ace data gama secondary school idan har ta samu miji ta kawoshi gida ayi mata aure don mutuncin diya mace shine dakin mijinta don anan garinsu har an fara surutun rashin aurenta don ma ba ganinta akeyi ba.
Sosai Aisha taji dadin zuwanta gida don ta zagaya 'yanuwanta na wajen uwa da uba ta sada zumunci don haka ne ma taga sati biyun tayi saurin karewa. Koda safiyar da zata koma kano tayi ta gama shirinta tsaf kafin lokacin da Mallam Adamu yazo daukarta. Duk wani tsaraba da zata tafi dashi an hada mata shi wuri daya. Babanta ma bai fita kasuwa ba din yana so yaga tafiyarta kafin ya fita. Kafin karfe sha biyi Mallam Adamu har ya iso, babu bata lokaci tayi sallama da duk mutanen gidan ta fito tana sharar kwalla ta shiga mota suka dauki hanyar kano.
Suna hawa titi ta fara bacci wanda ba ita ta farka ba sai da suka iso gida taji Mallam Adamu nace mata ta tashi sun iso gida. Farkawa tayi da salati a bakinta ta kalli harabar gidan sai taga tamkar yaune ta bar gidan gashi har taje ta dawo. Da sallama ta shiga cikin parlour babu kowa a ciki don haka ta wuce kitchen don tasan a wannan lokacin acan zata samu Mami. Sosai Mami tayi murnar dawowarta. Bayan sun gaisa ne ta haya sama don ta ajiye kayanta. Data sauko ne take tambayar Mami inasu Ummie tace mata suna gidan Hajiya acan zasu yini. "Kuma Mami har Ruqaiya sukaje gidan Hajiya"? "A'a tana dakina tana bacci bata dade da kwanciya ba kika shigo".
Koda Ruqaiya ta farka taga Aisha ai sai ta makale mata ta hanata sakat duk inda ta saka kafa nan take maida tata. Ko gani takeyi zata kara tafiya ta barta ne. Su Ummie basu dawo gida ba sai wurin takwas na dare. A lokacin Aisha ce kadai a parlour don Mami tana sama tare da Daddy. Ganin Aisha a zaune da gudu Ummie tazo ta rungume ta tana murna cewa takeyi "Wallahi Aunty Aisha munyi missing dinki sosai kullum Ruqaiya sai tayi mana kuka ita akaita Aunty Aishanta gashi komai akayi mata sai tace sai ta gayawa Aunty Aisha idan ta dawo".
Ita kanta Aisha taji dadin ganinsu don kuwa tayi kewarsu sosai. Farida ce ta kalleta a sheke tace "huh lallai zaman kauye dai baiyi ba, Allah nagode maka da ban hada komai da kauye ba da ko yaya mutum yaje kauye ya dawo sai ya canja". Dariyar shakiyanci Mu'azzam ya saka sannan yace mata "ai wannan uwar kibar da kike narkawa kamata yayi a kaiki kauyen ko kya sabe, wuu wa yaga Farida a kauye" ya kyalkyale da dariya har yana rike ciki. "Amma dai wallahi Yaya Mu'azzam ka cuceni, aini ko ace daga kauye nake idan na samu na rabu da zaman kauye babu abinda zai maidani ballantana ma mi yayi gamin jirgi da mita" tace tana murguda mishi baki. Haka dai sukayi ta shakiyancinsu Aisha na jinsu tayi tamkar bata san ma sunayi ba.
UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): 👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
'YA'YAN MIJI
👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
Na Umm Asghar
10
A haka dai rayuwa taci gaba, gashi Aisha har ta gama secondary school ta samu cigaba a makarantar Sa'adatu Rimi college of Education tana karantar catering wato fannin girke-girke.
A yammacin wata alhamis ne Aisha na kitchen tana taya Mami hidimar abincin dare, Mamin ce ta shigo kitchen din tace "sannu Aisha na tafi na barki da aiki ko, wai ina wajen Daddy muna maganar tafiya Umrah da zamuyi tunda yara suna hutu, inaga ko wajen jibi sai ki shirya ki koma wajen Hajiya kafin mu dawo tunda tafiyar zata kama ranar lahadi ne".
"Ashe tafiyar tazo, Allah ya kaiku lafiya ya dawo daku lafiya. Mami ayi mana addu'a, In Sha Allahu zanyi shirin. Har kwana nawa zakuyi? "Inaga sati biyu ne" inji Mami.
Tunda Farida taji batun tafiyarsu Umrah taji kuma babu Aisha a tafiyar take ta faman yada mata da habaici. Ita kam Aisha ko kallonta batayi ba. Wani abu da Farida bata sani ba shine bata taba hada kanta dasu ba. Tasan matsayinta a gidan na 'yar cin arziki ta kuma san nasu matsayin na 'ya'yan gidan.
Wannan nema dalilin da yasa bata taba daga ido ta kalli wani abu da akayi musu da ba'ayi da itaba duk da dai Mami na kamantawa mawuyacin abu ne tayi musu wani abin batayi mata ba amma wasu lokutan tana yi din ita kuma Aisha hakan bai taba damunta ba.
A kowanne lokaci ta kasance mai godiyar Allah da bais ta zama mai kwadayin abin wani ba. Banda haka da tasha takacin Farida don kuwa sau tari Daddy yanayi musu kyauta ita da Ummie ba tare da ya hada da ita ba. Idan irin haka ta faru Farida ta dinga iyawa tana kafafa kenan duk don ta kular da ita.
Bata manta wani lokaci da Daddy yayi wata tafiya zuwa ingila ya kawowa su Ummie wayoyin hannu a matsyin tsarabarsu. Firirita da iyawar da Farida tayi mata a lokacin don ta kular da ita nada yawa. Ita kam ma dariya abn ya dinga bata don ganin ita dai wayar ma ba damunta tayi ba kuma ba wanda zata kira a waya gareta ba bare ta damu.
A yammacin asabar bayan ta gama hada kayanta zata tafi gidan Hajiya ne ta suka kasa don su kara yin sallama da Mami kafin ta wuce. Kowa na tambayarta abinda takeso su saya mata harda Zainab sai abinma ya bata dariya.
Da zata tafi ne Mami ta kawo kudi ta bata koda zata bukaci wani abu ba sai ta tambayi Hajiya ba. Godiya sosai tayi mata sannan ta dauki jakar kayanta ta kara yimata sallama ta fita. Har mota su Ummie suka rakata, ganin ta shiga mota sai Zainab ta fashe da kuka wai sai ta bita. Da kyar Ummie ta janyeta suka koma cikin gida.
Ta sani itama zatayi kewar Ruqaiya da Zainab sosai domin kuwa ta shaku da yaran ba kadan ba. Duk wata hidima tasu itace tun daga kan wankansu, cin abincinsu, shirinsu zuwa makaranta, kitsone da koya musu homework duk ita keyi. Mafi yawan lokuta ma tare suke kwana a dakin yaran.
Da sallama ta shiga cikin gidan tana janye da akwatinta. Baaba Indo mai aikin Hajiya na tsugune a bakin famfo tana wanke-wanke. Dagowa tayi tare da amsa sallamar tana cewa "maraba da takwara yanzu da yammannan kike tafe".
Cikin fara'ar da bata yankewa a fuskarta tace "eh Baaba Indo mun sameku lafiya" tace "lafiya lau hala dai zaki kwana mana biyu na ganki harda akwati". Aisha tace "eh sati biyu zanyi muku" tace "kai madalla kice muna da babbar bakuwa".
Murmushi kawai tayi ta wuce dakin Hajiya. Bata sameta a parlour ba sai ta wuce cikin dakin. A zaune akan sallaya ta tararda ita tana karatun AlQur'ani don haka akwatin kawai ta ajiye ta fito parlour ta zauna. Tayi kusan mintina goma a zaune kafin Hajiya ta fito daga dakin. Zamowa tayi daga kan kujerar ta gaisheta.
Bayan sun gama gaisawa ne Hajiya ke cemata taje kitchen ta debi abinci. "Wallahi na koshi Hajiya sai dai ko zuwa anjima" tace mata. Jefi-jefi suke hira da Hajiya har aka kira sallar magriba suka tashi don yin sallar.
Aisha dai bata tashi akan sallayar ba sai bayan da tayi sallar isha. Ko a gida ta saba bata tashi bayan magriba zama takeyi tayi tilawar karatun Alqur'ani har sai an kira sallar isha tukunna ta tashi tayi.