Sashe 11
Yayan Miji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Jikinta ne yayi sanyi jin abinda yace sai dai kuma bazata iya mishi musu ba don kuwa bata saba musu dashi ba komai yace da to take amsa mishi. Sai dai kuma har cikin ranta bata ji dadi ba don har fuskarta sai da ta nuna bacin ranta.
"Fushi kikayi don nace bazaki fita ba" tace "a'a me ka gani" yace "gashinan kin bata rai kin daina magana bayan da hira mukeyi". Yake kawai tayi tace "a'a ba fushi nayi ba ai nasan hakanan bazaka hanani zuwa wurin Hajiya ba dole kana da naka dalilin kuma ma ai ka fada cewar bani da lafiya. Babu komai wata rana sai naje idan na kara samun sauki".
Dole ba don taso ba ta ware take janshi da hira don ta kawar mishi da shakku a zuciyarshi sai dai har ga Allah bataji dadin hanata zuwa gidan Hajiya da yayi ba. Tunda aka kawota gidan a matsayin matarshi bata taba fita ba sai lokacin da sukaje asibiti kusan watanni bakwai.
Tana son zuwa gaya ma amma sanin cewar ba lallai ne ya barta ba yasa ta kasa tambayarshi bare kuma yanzu data samu cikinnan komai takeyi idonshi nakai, ita har mamakin son yaranshi takeyi.
Da safe ne bayan sunyi breakfast yake ce mata ta shirya taje gidan Hajiya amma karya dade don baya son kaiwa yamma a unguwa. To itama tasan policy dinshi ne tun lokacin Mami nada rai bata wuce karfe biyar a waje.
Kitchen ta nufa ta hada abincin rana. Alkubus tayi da miyar taushe sai farfesun kayan ciki. Bayan ta shirya warmers ne ta zuba wanda zata kaiwa Hajiya ta hada a cikin basket sai toma dkinta don ta shirya.
Kafin ta shirya dama sai da ta tura Zainab don ta fadawa Mallam Adamu cewa zasu fita. A sitting room dinshi na sama ta iske shi ta mishi sallama sannan ta fita.
Lokacin da ta isa harabar gidan sai ta iske babu Mallam Adamu babu motar kuma, cikin daurewar kai ta tsaya tana kallon wurin daya saba ajiye motar. To ko dai Zainab bata gaya mishi cewa zasu fita ba.
Komawa tayi cikin gidan, a zzaune a parlour Ruqaiya da Zainab ne suna kallo a tashar disney. "Zainab baki fadawa Mallam Adamu cewa zamu fita ba ne" ta tambayeta bayan ta zauna akan kujera.
Tace "na fada mishi, su Yaya Ummie da Yaya Farida ne suka ce ya kaisu gidan kawarsu kuma ya fada musu cewa tare zaku fita suka ce idan ya kaisu ya dawo ya kaiki".
Ok kawai tacewa Zainab. Tasan da gayya suka fita bayan sun sanccewa fita zatayi don a gabansu ta tura Zainab ta shaidawa Mallam Adamu zata fita shinw suka rigata ficewa ta kuma san ba lallai ne su barshi ya dawo yanzu ba.
Tashi tayi ta haya sama don ta sanarwa Daddy cewa bata tafi ba. Tana shiga sitting room din yace mata "ya kika dawo ko mantuwa kikayi", gyada kai tayi tace "a'a na samu su Farida sun fita tare da Mallam Adamun ne". "Baki gaya mishi zaki fita bane suka fita ba tare da sun jiraki ba", tace "na aika Zainab ta gaya mishi maybe sunyi zaton ba yanzu zan fita bane".
Cikin fada yace "zancen banza kenan yasan zaki fita amma ya biye tasu Farida ya fita dasu, wa ma ya basu izinin fita. Ko sun sanar dake zasu fita. Girgiza kai tayi tace "um-um maybe kuma ba nisa sukayi ba shi ya saka basu sanr ba".
Tashi yayi ya shiga daki ya canja kaya zuwa kaftan ya dauko kwy din mota ya fito. "Tashi mu tafi" yace mata. Tashi tayi tabi bayanshi suka sauka kasa. Suna shiga parlour ta cewa Ruqaiya da Zainab su dauko takalmi da gyale suzo su tafi.
Juyowa yayi ya kalleta jin abinda tace yace "dama dasu kika shirya tafiya" tace "a'a na gani ne gidan babu kowa sai su Lami kaga ai bai kyautu a barsu su kadai ba".
Bai kara cewa komai ba sai dai kuma har cikin ranshi yana Jin dadin yadda take kula mishi da yaranshi yasan hadda wannan yasa mishi sonta a zuciyarshi.
Suna saukowa suka fita, yaran na baya ita kuma ta kame a gaban mota. Jefi-jefi suna hira har suka isa gidan Hajiya. Yana tsaida motar yaran suka fita da gudu don ko motar basu rufe ba.
Murmushi kawai Aisha ta dauki basket dinta ta fita ta nufi hanyar cikin gidan. Horn din da yayi mata ne ya sakata juyowa. Fitowa yayi ya kulle motar sannan yace "ki jirani mana mu shiga tare".
Ita dai kunya takeji yanzu kawai sai Hajiya ta gansu sun jero, shine fa dalilin da yasa tayi saurin fita don ta rigashi shiga amma ya tsaida ita.
Gaba ya wuce ta bishi a baya. A tsakar gida suka iske Hajiya a zaune akan tabarma su Ruqaiya sunyi matashi da cinyarta. Haka nan yau sai taji tana kunyar hada ido da Hajiya.
Cikin sanyin jiki ta karaso ta zauna akan tabarmar tana gaida Hajiya ita kuma tana tambayarta jikinta. Sai da ya bri suka gam gaiswa sannan ya gaida Hajiya ya tashi yana mi kallon Aisha yace "zan tafi sai da yamma zan dawo, inasu Zanab ne suzomu tafi kunsan yau akwai islamiyya" tace mishi "to nagode Allah ya kiyaye".
Bayan tafiyarsu ne Hajiya tace mata "tashi ki shiga cikinima yanzu nima yanzu zan shigo, tashi tayi ta koma parlour ta zauna.
UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): 👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
'YA'YAN MIJI
👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
Na Umm Asghar
19
Yau kwanankin Aisha uku a asibiti kuma yau dinne ake saka ran za'a bata sallama. A cikin kwanakin nan gaba daya su Farida sai wasan buya suke yi da Daddy ko da wasa basu bari sun hadu dashi ba.
Shima kuma baibi takansu ba don a yanzu ba abinda ke gabanshi ba kenan. A yanzu ta lafiyar Aisha yakeyi, ya bari ne sai sun koma gida sannan ya zauna dasu dukkansu don yaji miye musabbabin hatsarin daya faru.
Baya so ya zurfafa zarginshi akan yaran sai dai kuma yanayinsu a lokacin ya nuna tabbas basu da gaskiya. Gashi kuma tun ranar bai kara sakasu a idanunshi ba abinda ya kara assasa zargin da yakeyi na cewar sune ke da alhakin kada Aisha har ta kusa tayi loosing yaranta.
Mutanen gaya ma sun samu labarin haihuwar Aisha don haka sukayita tururuwar zuwa dubata, Yakumbo Dije kuma ta zauna don ta kula da lafiyarta data jariran.
Koda aka sallameta gidanta aka wuce da ita duk da dai Hajiya taso ta tafi da ita gidanta amma Daddt yace a'a tunda dai ga Yakumbo Dije babu bukatar sai ta koma wurin Hajiya.
Koda suka dawo daga asibitin su Ummie basu je sun mata sannu ba bare suga babies, Khalifa ne kadai ya shiga ya dubata a daren ranar sai kuma su Ruqaiya da suka tare a dakinta basa motsawa ko nan da can.
Bayan kwana biyu da dawowarsu daga asibiti ne Daddy ya tara su a parlourshi na sama, tun daga kan Khalifa da ba ma ya nan abin ya faru har zuwa kan Farida. Ruqaiya da Zainab ne kawai babu.
Hatta da Hajia a ranar sai da tazo don tun suna asibiti ya gaya mata cewa yana so za suyi magana amma bai gaya mata akan miye ba sai kuma a yau yayi mata waya yace ya tura Khalifa ya daukota.
Gaba dayansu sun taru a parlourshi har Aisha. Ga Mu'azzam da Farida kuwa gaba daya sun rude don sun tabbatar da wannan zaman akansu akayi shi, hatta da Ummie a tsorace take.
Kallon wurin da suke Daddy yayi yaga yanda sukayi tsuru-tsuru kwata-kwata basa cikin nutsuwarsu.
Bayan wasu 'yan mintuna ne Daddy yayi gyaran murya yace "abinda yasa na taraku duka anan shine dan na sanar daku abinda ya faru kwanaki biyar da suka wuce na samun Aisha da nayi kwance a cikin jini bata cikin hayyacinta sai kuma wadannan da na samu a tsaye akanta wanda bana raba daya biyu sune sukayi sanadin dana sameta a halin dana tarar da ita" ya fada yana mai nuna su Mu'azzam.
Yaci gana da cewa "shine yasa na taraku anan don ina son sanin asalin abinda ya faru, Aisha ko zaki gaya mini yanda akayi kika fadi akan cikinki har yayi sanadin da sai da aka miki aiki aka ciro babies?"
Sunkuyar da kanta tayi ta kasa magana don sai yanzu da yayi maganar ne ma taji ciwon abin sosai. Bata taba sanin kin da suke yi mata har yakai yanda zasu yi mata lahani ba sai yanzu.
Tasan da gayya Mu'azzam ya cilla mata ball dinnan a cikinta abinda bata taba zaton zasu iya yi mata ba. Jin shirun nata yayi yawa ne yasa Daddy yace mata "Aisha kiyi magana mana, nace ko zaki iya fada mini abinda ya faru a ranar na tarar dake a kwance cikin jini".
Girgiza kanta tayi sannan tace "a gaskiya bazan iya tunawa ba na manta". Hajiya ce ta ce "wanne irin kin manta kina nufin baki san yadda akayi kika fadi akan cikinki ba da har yay sanadin da akayi miki aiki aka ciro yaran dake cikinki, kenan kin samu shafewar tunani da bazaki iya tuna rayuwarki ta baya ba".
Nanma Aisha cewa tayi "a'a Hajiya ban samu shafewar tunani ba kawai dai na manta abinda ya faru ne a ranar". Hajiya zata sake magana Daddy yayi hanzarin cewa "kyaleta Hajiya tunda tace ta manta shikenan saukinta ai ba ita kadai bace a wurin da abin ya faru don haka kai Mu'azzam kaine babba ko zan iya sanin abin d yaru da har nazo na iske Aisha a kwance yayinda kuke tsaye akanta kai da kannenka".
Mummunar faduwar gaba ce ta ziyarci Mu'azzam don har ga Allah yana tsoron Daddy yasan cewa shine ya cilla mata ball a ciki duk da dai yana tunanin Daddyn yasan cewa sune shine ma dalilin da yasa ya tara su duka anan wurin.
Ganin yayi shiru ya kasa magana ne yasa Daddy ya juya akalar tambayarshi wurin Ummie, itama shiru tayi ta kasa bashi amsa haka ma Farida.
Ranshi yayi mummunan baci, shirunsu ya kara tabbatar mishida zarginshi na cewa sune sukayi sanadin da Aisha ta kwanta a asibiti.
"Fushi kikayi don nace bazaki fita ba" tace "a'a me ka gani" yace "gashinan kin bata rai kin daina magana bayan da hira mukeyi". Yake kawai tayi tace "a'a ba fushi nayi ba ai nasan hakanan bazaka hanani zuwa wurin Hajiya ba dole kana da naka dalilin kuma ma ai ka fada cewar bani da lafiya. Babu komai wata rana sai naje idan na kara samun sauki".
Dole ba don taso ba ta ware take janshi da hira don ta kawar mishi da shakku a zuciyarshi sai dai har ga Allah bataji dadin hanata zuwa gidan Hajiya da yayi ba. Tunda aka kawota gidan a matsayin matarshi bata taba fita ba sai lokacin da sukaje asibiti kusan watanni bakwai.
Tana son zuwa gaya ma amma sanin cewar ba lallai ne ya barta ba yasa ta kasa tambayarshi bare kuma yanzu data samu cikinnan komai takeyi idonshi nakai, ita har mamakin son yaranshi takeyi.
Da safe ne bayan sunyi breakfast yake ce mata ta shirya taje gidan Hajiya amma karya dade don baya son kaiwa yamma a unguwa. To itama tasan policy dinshi ne tun lokacin Mami nada rai bata wuce karfe biyar a waje.
Kitchen ta nufa ta hada abincin rana. Alkubus tayi da miyar taushe sai farfesun kayan ciki. Bayan ta shirya warmers ne ta zuba wanda zata kaiwa Hajiya ta hada a cikin basket sai toma dkinta don ta shirya.
Kafin ta shirya dama sai da ta tura Zainab don ta fadawa Mallam Adamu cewa zasu fita. A sitting room dinshi na sama ta iske shi ta mishi sallama sannan ta fita.
Lokacin da ta isa harabar gidan sai ta iske babu Mallam Adamu babu motar kuma, cikin daurewar kai ta tsaya tana kallon wurin daya saba ajiye motar. To ko dai Zainab bata gaya mishi cewa zasu fita ba.
Komawa tayi cikin gidan, a zzaune a parlour Ruqaiya da Zainab ne suna kallo a tashar disney. "Zainab baki fadawa Mallam Adamu cewa zamu fita ba ne" ta tambayeta bayan ta zauna akan kujera.
Tace "na fada mishi, su Yaya Ummie da Yaya Farida ne suka ce ya kaisu gidan kawarsu kuma ya fada musu cewa tare zaku fita suka ce idan ya kaisu ya dawo ya kaiki".
Ok kawai tacewa Zainab. Tasan da gayya suka fita bayan sun sanccewa fita zatayi don a gabansu ta tura Zainab ta shaidawa Mallam Adamu zata fita shinw suka rigata ficewa ta kuma san ba lallai ne su barshi ya dawo yanzu ba.
Tashi tayi ta haya sama don ta sanarwa Daddy cewa bata tafi ba. Tana shiga sitting room din yace mata "ya kika dawo ko mantuwa kikayi", gyada kai tayi tace "a'a na samu su Farida sun fita tare da Mallam Adamun ne". "Baki gaya mishi zaki fita bane suka fita ba tare da sun jiraki ba", tace "na aika Zainab ta gaya mishi maybe sunyi zaton ba yanzu zan fita bane".
Cikin fada yace "zancen banza kenan yasan zaki fita amma ya biye tasu Farida ya fita dasu, wa ma ya basu izinin fita. Ko sun sanar dake zasu fita. Girgiza kai tayi tace "um-um maybe kuma ba nisa sukayi ba shi ya saka basu sanr ba".
Tashi yayi ya shiga daki ya canja kaya zuwa kaftan ya dauko kwy din mota ya fito. "Tashi mu tafi" yace mata. Tashi tayi tabi bayanshi suka sauka kasa. Suna shiga parlour ta cewa Ruqaiya da Zainab su dauko takalmi da gyale suzo su tafi.
Juyowa yayi ya kalleta jin abinda tace yace "dama dasu kika shirya tafiya" tace "a'a na gani ne gidan babu kowa sai su Lami kaga ai bai kyautu a barsu su kadai ba".
Bai kara cewa komai ba sai dai kuma har cikin ranshi yana Jin dadin yadda take kula mishi da yaranshi yasan hadda wannan yasa mishi sonta a zuciyarshi.
Suna saukowa suka fita, yaran na baya ita kuma ta kame a gaban mota. Jefi-jefi suna hira har suka isa gidan Hajiya. Yana tsaida motar yaran suka fita da gudu don ko motar basu rufe ba.
Murmushi kawai Aisha ta dauki basket dinta ta fita ta nufi hanyar cikin gidan. Horn din da yayi mata ne ya sakata juyowa. Fitowa yayi ya kulle motar sannan yace "ki jirani mana mu shiga tare".
Ita dai kunya takeji yanzu kawai sai Hajiya ta gansu sun jero, shine fa dalilin da yasa tayi saurin fita don ta rigashi shiga amma ya tsaida ita.
Gaba ya wuce ta bishi a baya. A tsakar gida suka iske Hajiya a zaune akan tabarma su Ruqaiya sunyi matashi da cinyarta. Haka nan yau sai taji tana kunyar hada ido da Hajiya.
Cikin sanyin jiki ta karaso ta zauna akan tabarmar tana gaida Hajiya ita kuma tana tambayarta jikinta. Sai da ya bri suka gam gaiswa sannan ya gaida Hajiya ya tashi yana mi kallon Aisha yace "zan tafi sai da yamma zan dawo, inasu Zanab ne suzomu tafi kunsan yau akwai islamiyya" tace mishi "to nagode Allah ya kiyaye".
Bayan tafiyarsu ne Hajiya tace mata "tashi ki shiga cikinima yanzu nima yanzu zan shigo, tashi tayi ta koma parlour ta zauna.
UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): 👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
'YA'YAN MIJI
👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦👩👩👧👦
Na Umm Asghar
19
Yau kwanankin Aisha uku a asibiti kuma yau dinne ake saka ran za'a bata sallama. A cikin kwanakin nan gaba daya su Farida sai wasan buya suke yi da Daddy ko da wasa basu bari sun hadu dashi ba.
Shima kuma baibi takansu ba don a yanzu ba abinda ke gabanshi ba kenan. A yanzu ta lafiyar Aisha yakeyi, ya bari ne sai sun koma gida sannan ya zauna dasu dukkansu don yaji miye musabbabin hatsarin daya faru.
Baya so ya zurfafa zarginshi akan yaran sai dai kuma yanayinsu a lokacin ya nuna tabbas basu da gaskiya. Gashi kuma tun ranar bai kara sakasu a idanunshi ba abinda ya kara assasa zargin da yakeyi na cewar sune ke da alhakin kada Aisha har ta kusa tayi loosing yaranta.
Mutanen gaya ma sun samu labarin haihuwar Aisha don haka sukayita tururuwar zuwa dubata, Yakumbo Dije kuma ta zauna don ta kula da lafiyarta data jariran.
Koda aka sallameta gidanta aka wuce da ita duk da dai Hajiya taso ta tafi da ita gidanta amma Daddt yace a'a tunda dai ga Yakumbo Dije babu bukatar sai ta koma wurin Hajiya.
Koda suka dawo daga asibitin su Ummie basu je sun mata sannu ba bare suga babies, Khalifa ne kadai ya shiga ya dubata a daren ranar sai kuma su Ruqaiya da suka tare a dakinta basa motsawa ko nan da can.
Bayan kwana biyu da dawowarsu daga asibiti ne Daddy ya tara su a parlourshi na sama, tun daga kan Khalifa da ba ma ya nan abin ya faru har zuwa kan Farida. Ruqaiya da Zainab ne kawai babu.
Hatta da Hajia a ranar sai da tazo don tun suna asibiti ya gaya mata cewa yana so za suyi magana amma bai gaya mata akan miye ba sai kuma a yau yayi mata waya yace ya tura Khalifa ya daukota.
Gaba dayansu sun taru a parlourshi har Aisha. Ga Mu'azzam da Farida kuwa gaba daya sun rude don sun tabbatar da wannan zaman akansu akayi shi, hatta da Ummie a tsorace take.
Kallon wurin da suke Daddy yayi yaga yanda sukayi tsuru-tsuru kwata-kwata basa cikin nutsuwarsu.
Bayan wasu 'yan mintuna ne Daddy yayi gyaran murya yace "abinda yasa na taraku duka anan shine dan na sanar daku abinda ya faru kwanaki biyar da suka wuce na samun Aisha da nayi kwance a cikin jini bata cikin hayyacinta sai kuma wadannan da na samu a tsaye akanta wanda bana raba daya biyu sune sukayi sanadin dana sameta a halin dana tarar da ita" ya fada yana mai nuna su Mu'azzam.
Yaci gana da cewa "shine yasa na taraku anan don ina son sanin asalin abinda ya faru, Aisha ko zaki gaya mini yanda akayi kika fadi akan cikinki har yayi sanadin da sai da aka miki aiki aka ciro babies?"
Sunkuyar da kanta tayi ta kasa magana don sai yanzu da yayi maganar ne ma taji ciwon abin sosai. Bata taba sanin kin da suke yi mata har yakai yanda zasu yi mata lahani ba sai yanzu.
Tasan da gayya Mu'azzam ya cilla mata ball dinnan a cikinta abinda bata taba zaton zasu iya yi mata ba. Jin shirun nata yayi yawa ne yasa Daddy yace mata "Aisha kiyi magana mana, nace ko zaki iya fada mini abinda ya faru a ranar na tarar dake a kwance cikin jini".
Girgiza kanta tayi sannan tace "a gaskiya bazan iya tunawa ba na manta". Hajiya ce ta ce "wanne irin kin manta kina nufin baki san yadda akayi kika fadi akan cikinki ba da har yay sanadin da akayi miki aiki aka ciro yaran dake cikinki, kenan kin samu shafewar tunani da bazaki iya tuna rayuwarki ta baya ba".
Nanma Aisha cewa tayi "a'a Hajiya ban samu shafewar tunani ba kawai dai na manta abinda ya faru ne a ranar". Hajiya zata sake magana Daddy yayi hanzarin cewa "kyaleta Hajiya tunda tace ta manta shikenan saukinta ai ba ita kadai bace a wurin da abin ya faru don haka kai Mu'azzam kaine babba ko zan iya sanin abin d yaru da har nazo na iske Aisha a kwance yayinda kuke tsaye akanta kai da kannenka".
Mummunar faduwar gaba ce ta ziyarci Mu'azzam don har ga Allah yana tsoron Daddy yasan cewa shine ya cilla mata ball a ciki duk da dai yana tunanin Daddyn yasan cewa sune shine ma dalilin da yasa ya tara su duka anan wurin.
Ganin yayi shiru ya kasa magana ne yasa Daddy ya juya akalar tambayarshi wurin Ummie, itama shiru tayi ta kasa bashi amsa haka ma Farida.
Ranshi yayi mummunan baci, shirunsu ya kara tabbatar mishida zarginshi na cewa sune sukayi sanadin da Aisha ta kwanta a asibiti.