← Book details Yankan Kauna Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 8 OF 23

Sashe 8

Yankan Kauna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da sauri Kuma Khalid ya ɗauki wayar shi Allah yasa bata tarwatse ba ya shiga Kiran Doctor wanda shike Duba Anwar Idan ciwon shi ya tashi Doctor ya tabbatar wa da Khalid ya bashi Minti Goma sabida yana kusa dasu ne Gidan shi Khalid ya kashe wayar ya janyo Anwar saman Jikinshi gaba ɗaya Hankalin Khalid a tashe yake A haka Doctor Yazo ya same su wanda Shigowar Doctor ce ta fargar da Ma'aikatan Gidan Sanin Halin da Anwar yake ciki sabida Kowa yasan in kaga Doctor yazo Gidan to ciwon Anwar ne ya tashi Ma'aikatan gidan Sune Suka sanar da Mama abin da yake faruwa da sauri ta zari mayafi Jikinta har rawa yake ta nufi Part Ɗin Anwar Sedai koda ta ƙarasa Khalid ne a bakin Ƙofar gadan gadan ta nufi Buɗe Ƙofar Khalid ya hanata ta hanyar zira key.

"Marar kunya tsohon munafuki ka barni na wuce naga halin da yake ciki kodan bani ce na haife shiba in uwar shice Ni zaka Hanani shiga ne?"

Khalid ya kawar da kanshi bai tanka wa Mama ba wadda hakan ya ƙara fusata ta seta hau masifa Khalid yayi mata banza har Doctor ya fito yana yarfe zufa hannun shi da kayan aikin shi mama bata daina masifar da take yiba seda Doctor yayi gyaran murya kafin ya kalleta "Hajiya kamata yayi Ki fita sabida Maganar ki zata iya Janyo masa matsala" mama tahau Sosa kai tana cewa Doctor "To ai abinne da ciwo Ƙiri ƙiri nazo zanga halin da yake ciki wannan Munafukin ya hanani sabida Ni ba uwar shi bace ba to duk dai tsiya ba ku isa kun raɓa alaƙar ƴaƴana dashi ba" Likita ya mayar da hankali wajan Khalid yana bashi takardar magani tare da yi masa gargaɗin kula da lafiya Anwar sabida zuciyar shi tana cikin hatsari.

Khalid ya amsa Still Rufe ƙofar ya kuma yi yabi bayan doctor yabar Mama a tsaye cike da mamaki Haka halin Khalid yake Shi baya son Ƙunbiya Ƙunbiya yadda Halin Anwar yake haka halin shi yake shine ma yasa zaman su yazo daidai bambancin su kaɗai Anwar baya da yawan Magana Kuma yana da Miskilanci saɓanin Khalid mai Yawan magana da son shiga hurɗar Jama'a.

Khalid bai gigin shedawa innah ba ya shiga Mota ya nufi pharmacy ya siyo maganin da Doctor ya rubuta tare da yi masa takeaway ya dawo Gida har Lokacin Anwar yana bacci sabida alluran da Doctor yayi mishi A gefen shi Khalid ya zauna yana jiran ya tashi Har bayan Isha a lokacin Kiran Innah ya shigo wayar shi tashi yayi ya fita a wannan Lokacin bai Rufe Ƙofar ba yabar ta a buɗe ya nufi part Ɗin su.

Tun daga Ƙofar falo Mama take bambamin bala'i "Sabida bani na haifi Anwar ba yasa ake nunan fifiko akan shi fisabilillahi mai nake wa Anwar da har Khalid zai hanani ganin shi?"

Khairat ce ta tintsire da dariya har tana bugewa da Kujera "Kema mama mai ya kaiki Ni wallahi ban ga amfanin baka son Mutum ba kuma ka dinga Nuna wa kana son shi a gaban idanun shi Tunda bakya Son Ya Anwar why note ba zaki Nuna masa zahirin Ƙiyayyar da kike masa ba seki dinga pretending Kina son shi a gaban idanun shi To ina zaton Sun gane ki"

Ihsan ma dariya take Yi jin maganar da Khairat tayi a daidai wannan Lokacin kuma Hanan ta fito daga Bedroom Ɗinta Babbar Yarinyar Mama ce tuni ta kammala degree ɗinta Hanan tana masifar Son Anwar duk da Mama bata son Anwar ko kaɗan Hanan agolar mama ce data zo da ita gidan su Anwar saɓanin Husna da Khairat da Ihsan da suke Ƴaƴan Mama acikin Gidan su Anwar dan mama bata da ɗa namiji matanta Uku a gidan har Hanan Huɗu kenan.

Husna tayi aure tana zaune a garin Abuja Mijinta ma'ikacin banki ne tana nan da ciki tsoho haihuwa ko yau ko gobe shirin dawowa gida take ta haihu kamar yadda mama ta buƙaci hakan, Husna ce babba acikin ƴaƴan mama A gidan su Anwar

Inkiya mama taiwa su Khairat akan suyi shuru gudun kada Hanan taji abin da ya sami Anwar ta ɗaga hankalinta bayan tarin wulaƙanci da take sha a wajan sa amman ita zuciyarta kamar kare ya cinye Komai zai mata bata ganin Laifin shi akan shi bata Kula kowa duk ta Kori maneman ta wannan dalilin ya ƙara hassasa ƙiyayyar mama da Anwar wadda bata yarda ta fito fili ta Nuna masa ba ta ƙaunar tashi.

Duk yadda mama a farko taso Taja hankalin Anwar akan Hanan tayi amman da yake kamar Dutse yake Ko gezau shi kuma Abba yaƙi ɗaukar mataki akan soyayyar Anwar da Hanan kasancewar Abba yace ba ze wa yaron shi Auren dole ba duk wadda yake so yana da ƴancin aura wannan kalamin na Abba ya tunzura mama dan taso yayi wa Anwar dole ya amshi auren Hanan ganin duk wata hanya tabi batai nasara ba yasa ta ƙara Jin wutar Ƙiyayyar Anwar acikin zuciyarta sedai Mama ƙarshen Makira ce bata yarda ko a fuska ta Nuna wa Anwar bata son shi wanda Tuni Khalid shi ya gama karantar wacece mama shima Anwar ɗin Ko ya karanceta Oho badai ya nuna mata yasan mai take ciki kasancewar shi Mutum marar son magana bare hayaniya.

Hanan tabi su Khairat da kallo tana Ƙoƙarin Yin magana ne Mai aikin su ta shigo da kayan Abinci a saman tray ta nufi dining maganar mai aikin ce tasa Hanan miƙewa da sauri inda mai aikin take tambayar mama ta gano Jikin Alhaji ƙaramin yaya Jikin nashi yake.

Zumbur Hanan ta Miƙe tana dafe Ƙirjinta.
"Mama Yaya ne babu lafiya amman baki gaya mini ba?"
Mama Yaƙe taiwa mai aikin tana cewa da sauƙi Mai aikin tana fita mama tace "To marar zuciya ubanki zaki masa yama Mutu mana wani nada asara ne" Hanan bata tsaya Jin ƙarashen maganar da mama take yiba ta fita daga Part Ɗin nasu Direct Hanyar part Ɗin Anwar ta nufa duk da yana yawan yi mata gargaɗin shigar masa part amman haka ta faɗa Cikin part Ɗin nashi direct Kuma bedroom ɗin sa ta shiga Duk Fuskarta ta Jiƙe da ruwan hawaye.............
*YANKAN ƘAUNA…I! littafin kuɗi ne 500 naira zuwa wannan asusun bankin 0078174806 Sterling bank, idan kuma kati ne Mtn ko Airtel card na 500 hoton sa za'a ɗauka a turo,shaidar biya 09022260850*

*ZAINTUNA MULTI TRADE KANO*🔥🔥

*KOMAI DA RUWAN KA SHINE TAKEN MU MUNA ARHA MUNA RAHUSA GA DUKKAN KAYAN MU DOMIN SAUƘAƘAWA MASU SIYA*

*A ZAITUNA MULTI TRADE MUNA SIYAR DA*

*KAYAN GWANJO*
*KAYAN KITCHEN*
*KAYAN ELECTRONIC*
*GADAJE*
*KUJERU*
*KAYAN SAKAWA NA YARA DA MANYA DA JARIRAI*

_A WANI ƁANGARAN MUNA YIN_
*GRAN JIKI*
*ƘUN SHI DA BABU IRIN SA*
*MUNA DA TURARUKAN WUTA HUMRA*
*MUNA DA MAGUNGUNAN MATA*
*GUMBAR UKU BALA'I*
*GUMBAR TABAJE*
*GUMBAR BUJENTA JAGAB*
*GUMBAR SAKA MAI GIDA IHU*
*MUNA DA ZAFAFAN KAYAN MATAN DA BABU IRIN SU*🔥🔥
*MUNA DA SUPLEMENTS*
_ZAITUNA MULTI TRADE MUNA YIN_
*MAKE UP NA AMARE DAMA WAÆŠANDA BA AMAREN BA*
*MUNA YIN SALOON*
*MUNA DA YADIDDIKAN MATA DA TAKALMAN SU*
_A ƁANGARAN ƘWALAMA KUMA MUNA_
*SIYAR DA ÆŠANYUN KAJI MASU ARHA DA GIRMA*
*MUNA YIN PEPPER CHICKEN MAI DAÆŠIN GASKE*
*MUNA SIYAR DA KAJIN BIKI SUNA*
*MUNA DA EXCLUSIVE KAYAN SAWA DON AURE KO SHA'ANI NA FITA KUNYA KU NEMEMU*
*KADA KU MANTA AKWAI KAYAN GWANJO MASU AMINCI MUNA FASA DEALER DAGA NAN HAR SALLAH*

*MUNA DELIVERY NATION KO INA A FAƊIN ƘASAR NAN*

*ADIRESHINMU NA NAN A GARIN KANO MARMARA OPPOSITE ASIBITIN YARA NA MARMARA TITIN NAGODA KU NEME MU A WAÆŠANNAN NUMBOBIN WAYAR KAMAR HAKA*
08136259679 / 07067338694/ 08036426589/08067336110/08060235089/07048985018 MUNA MARABA DA MASU SIYAN ÆŠAIÆŠAI KO SARI AKWAI RAGI NA MUSAMMAN GA WAÆŠANDA SUKA SAI KAYAN GWANJO MUTUM BIYAR NA FARKO

*MULTI TRADE KANO*🔥🔥
*YANKAN ƘAUNA..!!*🌹
        
         *NA*
*AUTAR MANYA*

ADABI WRITTER'S ASSOCIATION

                     *009*

Kwance yake samɓal a saman gadon Numfashin sa yana sauka a hankali, Idanunshi a rufe ruf duk Zara zaran gashin idanun shi sun rufe masa Idanu ruf, Ƙarasawa tai wajan Ac control ta ƙara mai ƙarfin AC'n kafin ta nufi gadon jikinta duk a sanyaye wani Irin tausayi rayuwar shi take bata wadda take Jin Ninkin soyayyar shi acikin Zuciyarta fiye da ƙima Fiye da zaton mai zato.
Guntun hawayen dake Zubo mata take sharewa a fili ta furta "Wai kai baka jin Yadda nake jine wai kai wace Irin zuciya gare ka ban taɓa Jin ka furta kalmar kana soba sedai naji kalmar ana son ka a bakin mata da yawa daga Ciki harda ƙawaye na Dan Allah ka cire tsanar soyayya a zuciyarka kazo ka tallafi wadda take maitar son ka" Hanan ta furta kalmar tana tsira masa ido shima kuma adaidai nan ya buɗe idanun shi da suka ɗan Kumbura kaɗan suka ƙara Girma Yawun tsoro ta haɗiye ga kuma wani irin fitsari daya ke Ƙoƙarin zubo mata a hankali take ja da baya tana Ƙoƙarin sauka daga saman gadon sedai hakan bai samu ba sakamakon hannunta da Anwar ya cafke yayi wa Riƙon tsauri wanda har ƴar ƙara ta saki sabida zafi.

Rintse idanu tayi ta buɗe su har lokacin kallonta yake ba ko Ƙiftawa yana so yasan yaya son ta zai shiga zuciyar shi Kodan nacin ta gare shi amman ya kasa Gaba ɗaya zuciyar shi a bushe take kamar Dutse Bai taɓa furta kalmar soba hasalima in aka ce ana son shi haushi yake Ji shiyasa yake mamakin Yadda yake Jin Khalid na waya da ƴammata shikam yayi ƙoƙarin gwada Saka soyayya aran shi amman hakan ya gagara sabida kallon mata yake duka halin su ɗaya wani abune yake taso masa tina wani mikin da yajima a zuciyar shi da sauri ya saki hannunta ya Jingine kanshi da Pillow wani irin hawaye mai zafi ya soma gudu a saman Fuskar Jarumin namiji kamar Anwar Da sauri Hanan ta Tashi har tana tuntuɓe garin saurin barin ɗakin dan tana hango Tashin hankaline a cikin Idanun shi wanda inta zauna kusa dashi Komai na iya samunta.
Chapter 8 · 0% Book details