← Book details Yankan Kauna Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 23

Sashe 21

Yankan Kauna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Gidan nasu kamar babu kowa ɗaki suka buɗe suka shiga Hajiya duk ta ɓata Jikinta sabida haka basu zauna ba saida suka gyara Hajiya tas sannan Suka Shiga sabgar gabansu.

Saadah ta kasa gayawa Ummi abin da Anwar yayi mata ta dai ce mata shine ya kawo ta Jiya ya nemi ta daina aiki agidan su yau kuma yace mata auren ta zeyi yadda Ummi ta shiga Murna ne ya bawa saadatu mamaki.

Har dare saadah tana zuba ido ko Anwar zai dawo ya dubata amman shuru babu shi babu Ɗuriyar sa wasa wasa har tsayin kwanaki Uku babu Anwar Babu labarin sa suna samun abinci wajan Aunty Murja sannan Kamalu yana basu ɗari biyar Kullum Tunda ta dawo Gida Kamalun daya zo Taga yanayin sa kamar yaɗan sauko Har faɗa yay ma Abbati na dukan daya mata to wannan Rufin asirin ne yake riƙe dasu saboda har zuwa wannan kwanaki Anwar bai kuma zuwa wajanta ba Tun tana shiga ɗaki tai kuka har ma abin ya zame mata Jiki Dan wani Bin ko zama tai sai taita tunanin shi A yanzu ta yarda da soyayyar shi ta shiga zuciyarta tun ranar data ganshi taji Tana yi masa wata irin soyayya mai wuyar a fassarata.

Yau Kimanin kwanaki Biyar rabonta da Anwar Aunty Murja ce ta shigo Gidan da yamma sabida Aunty Murja bata shakkar Umma kai tsaye take Shigowa gidan.

Zama Aunty Murja tayi a kusa da Saadah taÉ—an kalleta kaÉ—an.

"Ni kam saadah kina fama da zazzaɓin dare ne?"
Saadah tai Murmushi mai ciwo tare da cewa.
"Mai kika gani wallahi lafiya ta ƙalau"
Ummi ta kalli Aunty Murja tana cewa.
"Nima na rasa me yake damun ta Kullum sai ta Ɓoye kanta taita Kuka nasha kamata tana Kuka to amman naga kamar bata son nasan damuwarta ne shiyasa nai mata shuru"

Saadah ƙasa tai da kanta bata Iya cewa komai ba saboda ita kaɗai tasan yadda take ji acikin zuciyarta game dashi.

"Saadah meke damun ki? sannan ina wanda ya É—auko mu daga asibiti ina maganar ku ta tsaya?"
Ƙirjin saadah ne yaɗan Buga kaɗan ta ɗago ta kalli Aunty Murja sai ga hawaye na zuba daga idanunta anan Aunty Murja ta gano bakin zaren Damuwar saadah Cikin Hikima Aunty Murja tace mata.

"Kodai tun daga ranar bai Kuma zuwa ba?" saadah ta É—aga mata kanta alamun "Ehh"

Aunty Murja tace "Shine kika rame haka lallai soyayyar taki da gaske ne Hajiya saadah an faɗa soyayya ai maganin ki yayi Ko nine haka zan Miki haba ai Nima kaina naga alamun ranshi ya ɓaci Ƙiri ƙiri Kika ƙi shiga motar shi fa Kuma Shine ya biya Miki Komai na asibiti dan da Mijina ne zai Biya zuwan shi yaje wajan likita ya biya Komai amman dan baki da Kirki agabanmu Kika dinga Nuna halin taurin kanki zuciya yayi ina ga baki da Number shi da se Ki masa waya"

Saadah ta É—an zaro ido tana cewa.
"Ni bani da Number shi Aunty Murja ina ganin fa dama Yaudarata zeyi Ina shi ina Aure na ÆŠan Gidan Alhaji Sule Kurfi ne fa naji Wadda ta kaini aiki gidan tana gaya Min To Aunty ina wannan mai KuÉ—in ina ni"

Ta faÉ—a cikin karaya.
Murmushi Aunty Murja tayi.
"Ni kuma gaskiya banga yanayin shi yayi kama da mayaudari ba, sabida daga gani ba yaro bane Kuma yana da Nutsuwa nafi zaton Fushi yayi ko wani uzirin kin san manya fa sai an Musu uziri Ko kuma Hidimar Gida"
Murmushi Saadah tai.
"Bashi da mata gaskiya ni dai ban san mai ya hana shi zuwan ba"
Aunty murja ta zaro ido.
"Bai da mata tabb Allah yasa rabonki ne wannan ai Kika aure shi zaki Shagwaɓarki son ranki dan naga yana da shekaru kawai dai bamai Kule Kule bane amman ai yaci ace yana da ƴaƴa ma Kita addu'a kuma ki kwantar da hankalinki Kinji"
Aunty murja ta dinga kwantar mata da hankalinta.
Har ta É—an sami Nutsuwa sallama sukai Aunty Murja ta koma Gida daran ranar Saadah labarin Anwar taita bawa Ummi wadda Ummin ta lura Anwar yayi wa Æ´ar uwarta Shigar sauri cikin zuciyarta.

*************

Yana tunanin anya bai shiga haƙƙin taba baya son takurawa Mutum sabida haka sai ya yanke shawarar rabuwa da ita Ko hakan zai sa ta samu Nutsuwa sabida haka koda yaje Gida ya tarar da Ɓacin ran Abba sosai na sallamar da yayiwa Alhaji jamilu haƙuri ya bawa Abba wanda ya Umarce shi akan lallai lallai ya mayar da Alhaji jamilu kan Kujerar shi.

Daga cikin Gida Duban Duniya Kande tayi wa Saadah bata ganta ba, sabida ko kaɗan bata kawo cewar Da Anwar suka Fita ba Ganin har dare yayi babu Saadah yasa ta sanar da Mama wadda mama ta kira Hadiza tace mata ba'aga Yarinyar data kawo ba Hadiza tace bata nan tana ƙauye amman In ta dawo zata Je Gidansu Yarinyar da haka Suka bar maganar sabida Hidimar Sunan Husna da suka Shiga Ita ta ɗauke hankalinsu daga Bibiyar Ina saadah tayi.
Kuɗin data bari ma Da kande ta kaiwa Husna cewa tayi ta Riƙe Kande taita Godiya Hanan kuwa data ji Saadah ta tafi har Rawar Murna tayi sabida dama bata ƙaunar yarinyar Ko kaɗan.

Anwar ya shiga sabgar gabanshi sai dai duk yadda yaso ya cire saadah a zuciyarshi abin ya faskara ko Rufe idanunshi yayi Hotonta yake gani Gaba É—aya jiyay ya shiga damuwar rashinta.

Yau kimanin sati rabon shi da ita dafe yake da ƙirjinshi dake yi masa zafi Yana kwance a saman Doguwar Kujera a falon shi.
Khalid ya shigo cikin shirin fita.
"Lafiya na ganka a kwance ba zaka fita Office bane?"
Khalid ya faÉ—a masa yana zama a gefen shi.
Tashi yayi tare da yamutsa fuskar shi kaÉ—an.
"Bana jin daÉ—i yau ba zan fita ba"
Khalid yaÉ—an tsira masa ido.
"Innah ma tai min Complain na yadda ka sauya kwana biyu Zamu iya shearing Matsalar ka?"
Anwar ya jingine kai da Jikin Kujerar yana sakin numfashi.
Khalid ya miƙe a zuciye.
"Ka mayar dani soko Ni ko meye ina sanar dakai Anwar akwai abin da ke damunka Ko wannan yarinyar ce?"
Da sauri ya É—ago yace.
"Wa kenan?"
Khalid yayi Murmushi tare da cewa.
"Ban sani ba kafini sanin ta ay wadda na zo na tarar dakai da ita ban san dai alaƙarku ba amman nasan matsalar baze wuce daga wajan taba"
Anwar yayi Murmushi.
"Yes ita ce kasan Ni bana yaudara ban taɓa yin soyayya ba bare na yaudari ƴammata wallahi Auren ta zanyi sabuwar mai aikin gidan ce..........
A takaice ya gayawa Khalid Komai dake faruwa.
Khalid yay dariyar shaƙiyanci.
"lallai ka shiga da yawa akanta zaka fasa zuwa Office daÉ—i na da Gobe saurin zuwa da kana ganin kamar bani da abinyi Ko kadai Ji yadda soyayyar take Ko?"
Anwar ya harari Khalid cikin wasa tare da cewa.
"Ni dai ka bani shawara raini ne bana so gaskiya Kuma ban iya rarrashin mace ba bare na lallaɓata"
Khalid dan dariya har da ƙwarewa.
"Aifa shiyasa naga kana kwance ka dafe Ƙirji kaga tashi Muje Office daga nan sai Muje wajanta Ko?"
Tashi yayi ya shirya suka fita har suka kai Office labarin saadah yake bawa Khalid yana jaddawa Khalid yadda yake Jin tausayin ta.
Khalid ya dire Anwar a office ya wuce shima wajan la'asar suka tashi ya Kuma Biyowa suka tafi tare don Anwar bai fita da Mota ba.

A ƙofar Gidan su saadah sukai Parking Khalid ne ya fita ya sami yaro yace yaje ya kira Musu saadah acikin wancan Gidan Sanda yaron yaje saadah tana bacci Ummi ta tasheta Fuskarta duk ta Kumbura idanunta ya ƙara Girma ta sa Hijabi ta fita Ido Huɗu sukai da Khalid wanda ta ɗan shaida shi sabida haka sai ta ƙarasa wajansu ta ɗan tsaya daga Nesa batare data yi magana ba...........*YANKAN ƘAUNA...I! littafin kuɗi ne 500 naira zuwa wannan asusun bankin 0078174806 Sterling bank, idan kuma kati ne Mtn ko Airtel card na 500 hoton sa za'a ɗauka a turo,shaidar biya 09022260850*
​

*ZAINTUNA MULTI TRADE KANO*🔥🔥

*KOMAI DA RUWAN KA SHINE TAKEN MU MUNA ARHA MUNA RAHUSA GA DUKKAN KAYAN MU DOMIN SAUƘAƘAWA MASU SIYA*

*A ZAITUNA MULTI TRADE MUNA SIYAR DA*

*KAYAN GWANJO*
*KAYAN KITCHEN*
*KAYAN ELECTRONIC*
*GADAJE*
*KUJERU*
*KAYAN SAKAWA NA YARA DA MANYA DA JARIRAI*

_A WANI ƁANGARAN MUNA YIN_
*GRAN JIKI*
*ƘUN SHI DA BABU IRIN SA*
*MUNA DA TURARUKAN WUTA HUMRA*
*MUNA DA MAGUNGUNAN MATA*
*GUMBAR UKU BALA'I*
*GUMBAR TABAJE*
*GUMBAR BUJENTA JAGAB*
*GUMBAR SAKA MAI GIDA IHU*
*MUNA DA ZAFAFAN KAYAN MATAN DA BABU IRIN SU*🔥🔥
*MUNA DA SUPLEMENTS*
_ZAITUNA MULTI TRADE MUNA YIN_
*MAKE UP NA AMARE DAMA WAÆŠANDA BA AMAREN BA*
*MUNA YIN SALOON*
*MUNA DA YADIDDIKAN MATA DA TAKALMAN SU*
_A ƁANGARAN ƘWALAMA KUMA MUNA_
*SIYAR DA ÆŠANYUN KAJI MASU ARHA DA GIRMA*
*MUNA YIN PEPPER CHICKEN MAI DAÆŠIN GASKE*
*MUNA SIYAR DA KAJIN BIKI SUNA*
*MUNA DA EXCLUSIVE KAYAN SAWA DON AURE KO SHA'ANI NA FITA KUNYA KU NEMEMU*
*KADA KU MANTA AKWAI KAYAN GWANJO MASU AMINCI MUNA FASA DEALER DAGA NAN HAR SALLAH*

*MUNA DELIVERY NATION KO INA A FAƊIN ƘASAR NAN*

*ADIRESHINMU NA NAN A GARIN KANO MARMARA OPPOSITE ASIBITIN YARA NA MARMARA TITIN NAGODA KU NEME MU A WAÆŠANNAN NUMBOBIN WAYAR KAMAR HAKA*
08136259679 / 07067338694/ 08036426589/08067336110/08060235089/07048985018 MUNA MARABA DA MASU SIYAN ÆŠAIÆŠAI KO SARI AKWAI RAGI NA MUSAMMAN GA WAÆŠANDA SUKA SAI KAYAN GWANJO MUTUM BIYAR NA FARKO

*MULTI TRADE KANO*🔥🔥
*YANKAN ƘAUNA..!!*🌹

*NA*
*AUTAR MANYA*

ADABI WRITTER'S ASSOCIATION

*20*

Idanunta ya zubawa ido yaga yadda suka kumbura sukai wani irin Girma Fuskarta tayi jajir gaban shi ne yaɗan faɗi kaɗan cikin wani irin yanayi yake Ƙureta da kallon shi, Kafin yaja ajiyar zuciya Tunda ta fito ta Tsaya a wajan bata ƙaraso wajan suba sai Khalid ne yayi masa Inkiya wadda tasa Dole shi ɗin ne ya fito daga Mota yazo Inda take.

"Mata masu Mulki, Nayi Laifi ne?" ya faÉ—a yana É—age mata Girarshi Guda É—aya.

Hararar shi tayi tana Juya masa baya da sauri yakai hannu zai Juyo da ita sai Kuma ya fasa ta hanyar mayar da hannunshi yana yarfewa.
"Kinga É—an juyo kalle ni kaÉ—an"
Ya faÉ—a a rarrabe.
Chapter 21 · 0% Book details