← Book details Yankan Kauna Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 18 OF 23

Sashe 18

Yankan Kauna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bayan sun kammala Saadatu tukunya ƙarama ta samu ta zuba ruwa da kayan haɗin shayi ta Ɗora tana tsaye ya tafasa ta juye ta haɗa komai cikin Dogon tray ta fita dashi zuwa ɗakin su sai da aka yi sallar Isha'i ta miƙe bayan ta watsa ruwa gami da sauya kaya ta ɗauki tray ɗin ta nufi wajan shi tana tunanin koya ci abinci Gaba ɗaya tausayi rayuwar shi take bata tana Jin ina ma zata ji labarin shi koda kaɗan ne domin daga gani akwai abubuwan dake tare dashi.

Raɓewa tayi ajikin ƙofar falon shi sabida jin sautin maganganun dake fita daga cikin falon nashi Allah ya gani ba laɓe tayi ba dalilin tsayawar tata gudu take in ta Koma da kayan shayin Wani zai iya ganinta acikin ahalin gidan shiyasa ta zaɓi ta dakata har baƙin nashi su Fito sai ta shiga takai masa.
"Anwar karfa kai wa rayuwarka Illah shekaran Jiya Likita ya gama faÉ—a akan ciwon ka yau gashi ka Kuma kwanciya Ni bana son wannan yawan damuwar taka tunda ba cikakkiyar lafiya gare kaba"
Muryar mace ke tashi acikin falon.
Shi kam ba'a jin abin da yake faɗa sabida ƙaramin sauti da yake amfani dashi maganganu suke waɗanda suka danganci ban haƙuri da Nasiha da matar ke masa kafin ta gama ta fito Ɗauke Numfashi Saadatu tayi Lokacin da matar ta gama maganar ta fito daga falon, Wuff saadatu ta faɗa cikin falon tana raba ido yana kwance a saman Sopa jikinsa sanye da Singlet da Dogon wando yana ganinta yaɗan sauya fuska yay kamar bai ji daɗi a yadda ta same shiba.
Ƙasa tayi da kanta bayan tai sallama ya amsa mata a taƙaice.

"Yaya jikin naka dan Allah kayi haƙuri"
Ta faɗa kanta ƙasa tana ajiye Tray ɗin hannunta.
"Ke ni wannan ban haƙurin naki ya isa tashi kije"
Jitai gwiwarta ta saki a ranta take ayyana Saadatu kin zaƙe da yawa tunda bai neme kiba meye zaki kawo kanki Gurin wanda yafi ƙarfin ki.
Tashi tayi zata tafi.
"Zoki É—auke wannan abun"
Ya nuna tray É—in da hannun shi mai lafiyar.
Hawaye ne ya wanke mata fuska ta sunkuya zata É—auka yabi fuskarta da kallo.
"Kukan na menene Tell me?"
Bata yi magana ba domin in da amsar da zata biyo bakinta kuka ne mai ƙarfi ta yaya ta Ƙona shi ya kwanta Ciwo ta kawo masa shayi dan ta duba shi ya gwaleta Ji take kamar ita ce silar Komai na ciwon shi shiyasa taji hankalinta ya gaza kwanciya.
"Mami Come here"
Ya faÉ—a yana kallonta.
Ta fahimci me yake nufi sabida haka zuwa tayi gabanshi ta zauna.

A hankali ya kalleta.
"Ke sunan mahaifiyata gareki, Aikin me kika zo gidannan sannan ke a ina kike?"
Da nutsuwa ta É—ago taÉ—an kalle shi.
"Ina layin É—orawa nazo ne ina wa Wadda ta haihu anan gidan aiki ne..........
TaÉ—an bashi labarin dalilin zuwanta gidan nasu.
"Ina baki kuÉ—in maganin mama zaki koma gida ina nufin ki koma ku cigaba da Jinyar mahaifiyarku sabida duk wata Æ´a mace Mutuncin ta gidan su ko gidan Mijinta yanzu haka kowa da irin kallon da zai Miki"
Tunda ya soma mata maganar taji girman shi yana ƙara ƙaruwa cikin idanunta shine Mutum Na farko a duniya daya soma taimakon ta a maza batare daya nemi komai daga wajanta ba.
Hawaye ya wanke mata fuska.
"Nagode Allah ya jiƙan mahaifa in sun mutu in suna raye Allah yaja kwana, amman na riga na amshi Kudin wannan watan"
Ya tsareta da girman idanunshi.
"Miye kikai da kuÉ—in?"
Ya faÉ—a cikin hausarshi wadda take Nuna Ainihin harshen shi wato na katsinanci.
"Dama zan kai wa Ummi ne sabida kula da Hajiya"
Shuru yayi Kamar baze yi mata magana ba can yace mata.
"I understand you, zaki iya tafiya Ki shirya kayan ki"
Daga haka ya Mayar da kanshi ya kwantar.
Tashi tayi Jikinta duk yayi sanyi harta kai Ƙofar fita ta kuma dawowa.
"Me zan ce wa Hajiya?"
Shuru yayi mata sai da ta kuma nanatawa.
Sannan yace mata.
"Kice mata Anwar yace zai mayar dake Gidan ku, Ki basu kuÉ—in da suka baki"
Jimm tayi tare da sakin Ajiyar zuciya kafin ta fita daga Falon nashi.
Daran ranar Saadatu bata rintsa ba, Ta rasa ina maganganun sa suka dosa amman ta bawa zuciyar ta amsa da Taimakonta yake so yayi.
Washe gari Sabgarta ta shiga ganin bai mata magana ba.
Shima a nasa ɓarin Ayyuka ne suka taru akan shi a office, Ga Binciken daya tsaurara akan Fitar da kuɗin da akai bawai Biyan Kuɗin ne yayi Mishi ciwo ba A,a zafin Zargin da Abba ke masa shine ya ƙara tunzura shi akan dole ma sai ya Gano yaya akai Kuɗin suka fita wannan dalilin yasa a wannan rana ya dakatar da Alhaji Jamilu ya kuma dakatar da Chief Information Officer lamarin daya Girgiza zuƙatan mutane Biyun wato Alhaji jamilu yayan Mama matar Mahaifin Anwar da Amininshi wanda suke haɗa ka wajan cuta da handama acikin Kamfanin.
Anwar bai shigo gidan ba sai yamma Lis part Ɗin Innah ya wuce yaci abinci sannan ya fito zuwa nashi part Ɗin Lokacin daya shiga ana kiran sallar magariba alwala yayi ya fita masallaci sai da yayi sallah sannan ya Watsa ruwa Cikin shiga Black Jeans da white shirt ya fito yana ta baza ƙamshin turaren shi na Tom ford Oud wood, Babban falon su ya Nufa Baba kande tana ta hidimar haɗa Girki da sauri ta russuna tana gaishe dashi ya dakatar da ita.
Dan baya so babba kamarta tana rissuna mai.
"Baba kiramin wannan yarinyar mana"
Bata fahimta ba.
Yanayin yadda take yine ya nuna masa hakan.
"Wadda aka kawo sabuwar nan"
Da sauri baba kande ta juya ta shiga ɓarin su ta kirawo saadatu data ke zaune ta idar da sallah dan Lokacin ta sami tsarki sabida dama bata wani Jimawa.
Gaban sa'adah ya faɗi sanda Baba kande ke sanar da ita Alhaji ƙarami na kiranta.
Tashi tayi ta biyo bayan Baba kande zuwa falon.
Baba kande ta wuce Kitchen ita kuma ta Nufi inda yake tsaye ya harɗe hannayen shi a saman Ƙirjin shi.......
*YANKAN ƘAUNA...I! littafin kuɗi ne 500 naira zuwa wannan asusun bankin 0078174806 Sterling bank, idan kuma kati ne Mtn ko Airtel card na 500 hoton sa za'a ɗauka a turo,shaidar biya 09022260850*

*ZAINTUNA MULTI TRADE KANO*🔥🔥

*KOMAI DA RUWAN KA SHINE TAKEN MU MUNA ARHA MUNA RAHUSA GA DUKKAN KAYAN MU DOMIN SAUƘAƘAWA MASU SIYA*

*A ZAITUNA MULTI TRADE MUNA SIYAR DA*

*KAYAN GWANJO*
*KAYAN KITCHEN*
*KAYAN ELECTRONIC*
*GADAJE*
*KUJERU*
*KAYAN SAKAWA NA YARA DA MANYA DA JARIRAI*

_A WANI ƁANGARAN MUNA YIN_
*GRAN JIKI*
*ƘUN SHI DA BABU IRIN SA*
*MUNA DA TURARUKAN WUTA HUMRA*
*MUNA DA MAGUNGUNAN MATA*
*GUMBAR UKU BALA'I*
*GUMBAR TABAJE*
*GUMBAR BUJENTA JAGAB*
*GUMBAR SAKA MAI GIDA IHU*
*MUNA DA ZAFAFAN KAYAN MATAN DA BABU IRIN SU*🔥🔥
*MUNA DA SUPLEMENTS*
_ZAITUNA MULTI TRADE MUNA YIN_
*MAKE UP NA AMARE DAMA WAÆŠANDA BA AMAREN BA*
*MUNA YIN SALOON*
*MUNA DA YADIDDIKAN MATA DA TAKALMAN SU*
_A ƁANGARAN ƘWALAMA KUMA MUNA_
*SIYAR DA ÆŠANYUN KAJI MASU ARHA DA GIRMA*
*MUNA YIN PEPPER CHICKEN MAI DAÆŠIN GASKE*
*MUNA SIYAR DA KAJIN BIKI SUNA*
*MUNA DA EXCLUSIVE KAYAN SAWA DON AURE KO SHA'ANI NA FITA KUNYA KU NEMEMU*
*KADA KU MANTA AKWAI KAYAN GWANJO MASU AMINCI MUNA FASA DEALER DAGA NAN HAR SALLAH*

*MUNA DELIVERY NATION KO INA A FAƊIN ƘASAR NAN*

*ADIRESHINMU NA NAN A GARIN KANO MARMARA OPPOSITE ASIBITIN YARA NA MARMARA TITIN NAGODA KU NEME MU A WAÆŠANNAN NUMBOBIN WAYAR KAMAR HAKA*
08136259679 / 07067338694/ 08036426589/08067336110/08060235089/07048985018 MUNA MARABA DA MASU SIYAN ÆŠAIÆŠAI KO SARI AKWAI RAGI NA MUSAMMAN GA WAÆŠANDA SUKA SAI KAYAN GWANJO MUTUM BIYAR NA FARKO

*MULTI TRADE KANO*🔥🔥
*YANKAN ƘAUNA..!!*🌹
        
         *NA*
*AUTAR MANYA*

ADABI WRITTER'S ASSOCIATION

                     *18*

Tunda ta doso wajen shi yake binta da kallo ta ƙasan idanunshi wanda ba lallai itan ta gane irin kallon ƙurullar da yake yi mata ba.
A hankali ta ƙaraso gabanshi ta tsaya daga nesa dashi ta sunkuyar da kanta a ƙasa tana wasa da yatsun hannunta.
"Wuce muje"
Ya faɗa mata a taƙaice.
ÆŠago idanunta tayi tare da yin raurau da su kamar zatai kuka! kafin tai magana cikin sakarci kaÉ—an tace masa.
"Nifa ban gama shirya wa ba"
Tsira mata kaifin idanunshi yayi wanda yasa ta yi saurin Kauda kanta tana jin wata irin faÉ—uwar gaba.
Cikin ƙaramin sauti ya furta.
"Muje ko"
Ya faɗa lokacin daya juya domin fita daga falon bata da wani zaɓi face na bin bayan shi ko Kuɗin bata mayar wa da Husna ba haka zalika bata ɗauki kayanta ba, Bare tai wa Baba kande sallama.
Sai da ta ƙara da Gudu sannan ta cimmasa sabida saurine dashi ba ɗan kaɗan ba a bakin wata farar Mota ta tarar dashi sai da ta ƙaraso sannan ya shiga ɓangaren driver ya sa hannu ya buɗe mata kusa dashi sannu a hankali ta shiga cikin Motar ta zauna.

Ya kunna ya tashi Motar suka bar wajan a bakin gate ya danna Horn masu gadi suka BuÉ—e masa suna É—aga mai hannu ya fita daga harabar Gidan gaba É—aya saman kwalta ya cilla hancin Motar tashi.
Tafiya ce suke kamar ta Kurame yana sane daya zo layin yaÉ—an wuce da sauri tace.
"Ga layin namu fa"
YaÉ—an kalleta yana cewa.
"Nina É—auka Kurma ce ay"
Dariya ta saki kaÉ—an tana sa hannunta tana rufe fuskarta.
Cikin layin nasu ya shiga yana tafiya a hankali har yakai daidai inda ta Nuna masa ya kashe Motar ya É—an kalleta.

"Ki shiga gida to sai da safe"
Magana take son yi masa amman kwarjinin shi ya hana ta furta abin da take son gaya masan.

"Ko na rakaki?"
Ya faÉ—a yana É—age girar shi guda É—aya.
Sunkuyar da kanta tayi tare da kama Murfin Motar zata buÉ—e ta fita.
Da sauri ya kamo hannunta.
Itama da sauri ta ɓamɓare hannun nata daga Cikin nashi.
"Ashhh kin fama min Ƙunata"
Ya faÉ—a mata a hankali.
Chapter 18 · 0% Book details