← Book details Yankan Kauna Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 4 OF 23

Sashe 4

Yankan Kauna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Mijin Aunty Murja yaji ransa ya ɓaci Amman bai nuna wa baffa ba yace.
"To in sha Allahu zanyi Mata magana kayi haƙuri ba zata kuma shiga ba In banda abin Murja babu mai son hurlɗa da ɗan iska"

Baffa yayi masa sallama ya tafi dama da ire iren waɗannan zantukan Baffa yabi ya ɓata su Sa'adah a layin Shiyasa kowa yake Musu kallon baibai se wanda Allah yasa yasan halin da suke ciki ne yake Musu Uziri.

Mijin Aunty Murja ya shiga gidan kallo É—aya tai masa tasha Jinin Jikinta.

Seda suka Nutsu a falo Sannan ya dube ta.
"Mai ya haÉ—aki da Æ´ammatan can Gidan Kina kallon Baffan suma yana kuka da halin su bare ke ina ruwan ki dasu har Kike basu abinci ba tare da sanina ba to ni ina rayuwata Cikin Rufin asiri ba zaki ja min surutun layi ba"
Murmushi Aunty Murja tayi tare da tsira masa idanu har ya gama maganganun sa cikin faÉ—a.

"Wallahi Allah Bai gaya maka gaskiya ba Nima ada yadda ya gaya maka haka nake Musu kallo sabida Ina jin yadda ake yi dasu Inna je Kitso can Gidan se yau da Babbar ta fito tana Kukan neman agaji akan Yayanta yana Dukan ƙanwarta shine na shiga Abun babu daɗin faɗi rayuwar yaran abin tausayi ce nai kuka ba ɗan kaɗan ba dama jira nake kazo mu san abin yi"

Ya fuskanci matar tashi tiryan tiryan ta shiga gaya masa halin data ga su sa'ada aciki sanin wacece matar shi yasa bai musalta mata ba amman seya Kalleta da kulawa yace.
"To ta yaya kike ganin zamu tallafa Musu sabida Mutum mai sharri abin tsoro ne na fahimci kamar da baki suke aibata yaran"
Aunty Murja ta jinjina kai tare da cewa.
"Dama shine matsalar Amman kayi shawara se Muga wani taimako zamu basu wanda zai Riƙe su dan ina gudun kada babu tasa su fara harkar banza Tunda babu laifi yaran suna da kamun kansu daidai misali"

Ce mata yayi zeyi shawara abin da ya yanke ze sanar da ita da haka suka shiga wata Hirar ta daban.

Jikin Hajiya ne ya rikice ta dinga wasu irin surutai tana zubar da Miyau abin daya ɗaga wa su Sa'adatu hankali kenan ga maganin Hajiya ya ƙare dama wani bin Ciwon nata kamar shigar Jinnu yake amman dai Likitan ta ya shaida masu wani bin masu lalurar suna haka, ga Hajiya babu baki bare tace ga inda ke mata ciwo yadda suka ga dare haka suka ga rana da sassafe Sa'adatu taje shagon kamalu babban yayan su don ta sheda masa ga halin da Hajiya take ciki dan yazo Ko zasu kaita asibiti Abin mamaki dubu ya cillo mata yace suyi kuɗin Mota shi bashi da kuɗi ta sunkuya ta ɗauka bata koma gida ba titi taje ta kira mai napep Ita da Ummi suka tallafo Hajiya zuwa napep Ɗin Direct asibitin Murtala suka wuce da ita Koda mai napep ɗin ya sauke su bai karɓi kuɗin suba yace su barshi sukai yi masa Godiya suka kama Hajiya zuwa CIkin asibitin in da suka zauna Zaman Jiran yankar katin ganin Likita Koda layi yazo kansu Sun sami nasarar Ganin Likitan masifa yahau yi Musu akan sakacin da sukai Har Jinin Hajiyar tasu yakai Maƙurar hawa Ita dai Sa'adatu Haƙuri take bawa Likitan magani ya rubuta Musu Tare dayi Musu Gargaɗin lallai su Nemo shi su bata sabida Komai yana iya faruwa Jikin sa'adah har rawa yake bayan sun fito tana tafe tana haɗawa da Gudu zuwa pharmacy dan ta siyo maganin Da dubu ɗayan hannunta gani take In bata sai maganin ba Hajiya ƙila ma ta Mutu...........Autar manya 09022260850

*ZAINTUNA MULTI TRADE KANO*🔥🔥

*KOMAI DA RUWAN KA SHINE TAKEN MU MUNA ARHA MUNA RAHUSA GA DUKKAN KAYAN MU DOMIN SAUƘAƘAWA MASU SIYA*

*A ZAITUNA MULTI TRADE MUNA SIYAR DA*

*KAYAN GWANJO*
*KAYAN KITCHEN*
*KAYAN ELECTRONIC*
*GADAJE*
*KUJERU*
*KAYAN SAKAWA NA YARA DA MANYA DA JARIRAI*

_A WANI ƁANGARAN MUNA YIN_
*GRAN JIKI*
*ƘUN SHI DA BABU IRIN SA*
*MUNA DA TURARUKAN WUTA HUMRA*
*MUNA DA MAGUNGUNAN MATA*
*GUMBAR UKU BALA'I*
*GUMBAR TABAJE*
*GUMBAR BUJENTA JAGAB*
*GUMBAR SAKA MAI GIDA IHU*
*MUNA DA ZAFAFAN KAYAN MATAN DA BABU IRIN SU*🔥🔥
*MUNA DA SUPLEMENTS*
_ZAITUNA MULTI TRADE MUNA YIN_
*MAKE UP NA AMARE DAMA WAÆŠANDA BA AMAREN BA*
*MUNA YIN SALOON*
*MUNA DA YADIDDIKAN MATA DA TAKALMAN SU*
_A ƁANGARAN ƘWALAMA KUMA MUNA_
*SIYAR DA ÆŠANYUN KAJI MASU ARHA DA GIRMA*
*MUNA YIN PEPPER CHICKEN MAI DAÆŠIN GASKE*
*MUNA SIYAR DA KAJIN BIKI SUNA*
*MUNA DA EXCLUSIVE KAYAN SAWA DON AURE KO SHA'ANI NA FITA KUNYA KU NEMEMU*
*KADA KU MANTA AKWAI KAYAN GWANJO MASU AMINCI MUNA FASA DEALER DAGA NAN HAR SALLAH*

*MUNA DELIVERY NATION KO INA A FAƊIN ƘASAR NAN*

*ADIRESHINMU NA NAN A GARIN KANO MARMARA OPPOSITE ASIBITIN YARA NA MARMARA TITIN NAGODA KU NEME MU A WAÆŠANNAN NUMBOBIN WAYAR KAMAR HAKA*
08136259679 / 07067338694/ 08036426589/08067336110/08060235089/07048985018 MUNA MARABA DA MASU SIYAN ÆŠAIÆŠAI KO SARI AKWAI RAGI NA MUSAMMAN GA WAÆŠANDA SUKA SAI KAYAN GWANJO MUTUM BIYAR NA FARKO

*MULTI TRADE KANO*🔥🔥
*YANKAN ƘAUNA..!!*🌹
        
         *NA*
*AUTAR MANYA*

ADABI WRITTER'S ASSOCIATION

                     *005*

Sedai ƙafafun ta sun sage ne Lokacin data ji Zunzurutun Kuɗin maganin Yawu ta haɗiya muƙut tana share Gumin Fuskarta duk da akwai sanyin Safiya iska tana kaɗawa Amman Hakan bai hana Gumi ya wanke sa'ada ba Ta ina zasu sami Kuɗin maganin Hajiya wanda ayau jikin nata yakai maƙurar wajan rikicewa Zaman dirshan sa'adah tayi tana Rusa kuka hannunta riƙe da Katin maganin Idanunta yayi jajir Fuskarta ta kumbura sabida Kuka.

"Ƴammata Dafatan dai lafiya kike wannan kuka?"
Cewar wata mace baƙa tana tsaye a saman kan Sa'ada Ɗago idanu tayi tana kallon Matar fuskarta tai dumu dumu da hawaye da majina.
"Babarmu aka rubuto wa magani Mu Kuma bamu da KuÉ—in maganin gashi Kuma Likita yace lallai se Mun bata in ba haka ba komai na iya faruwa"
Matar ta ƙarewa sa'adatu kallo a fili tace.
"Madallah da Ubangijin daya halicci wannan sura mai kyau Ina fatan Allah ya kare Miki Mutunci ki dama Ƴammata zasu yi koyi da Halin ki gaki dai babu Namijin da baze ganki ya ƙyasa ba amman Kin kare martabar ki dan Kina da surar da waje ma za'a iya fitar da mahaifiyarki amman Baki banzatar da kanki ba Muje naga Babar taku"
Sa'adatu ta share hawaye tayi gaba matar na binta a baya Suka je wajan su Ummi wadda Hajiya ke Jikinta duk Yawu ma ya ɓatawa Ummi Kayanta wanda Hajiya ke zubar dashi.

Suka gaisa da Ummi da matar.
"Allah sarki Ni zan taimaka Muku Yanzu dai Kuzo Muje Ku kai mahaifiyarku Gida ke Kuma seki Biyoni a Janguza Gidana yake Sana'ata kai yara gidan aiki to akwai Gidan da suke son Masu aiki a rijiyar zaki sena kaiki"
Godiya sukai wa matar Suka kama Hajiya suka fita suka shiga napep har Gida matar ta rakasu wadda tace Sunanta Hadiza Gudun magana yasa Sa'adah ta dakatar da Hadiza a waje Bayan sun kai Hajiya Gida Ta fito tabar Ummi tare da Hajiya.

Tafiya sukai Hadiza tana cewa sa'ada ashema basu da Nisa Har Suka tsallaka Titi wani katafaran Gida suka Shiga mai gadi ya buɗe Musu Ƙofa Yana tsokanar Hadiza A wani ƙaton falo suka zauna seda Suka jima a zaune sannan matar Gidan ta fito Sa'ada tabi matar da kallo wadda take ma sha Allah ƙatuwa da ƙyar take tafiya sabida Jikin da Allah ya bata gata baƙa Ƙirin se Uban ƙaton Hanci a ɗage take kallon su Kafin ta zauna da ƙyar aikuwa seda Kujerar ta Loɓa sabida Ƙibarta.

"Hadiza se yau kika ga damar kawo Mini mai aikin gashi jibi zan bar ƙasar?" Hadiza ta fara fadanci tana ƙasa da kai tana cewa.
"Tuba nake uwar ɗakina Ƴammatan ne sunyi wahala"
Se Lokacin Sa'ada ta gaishe da matar wadda ta zuba mata idanu na wasu Lokuta kafin ta kalli Hadiza tana ce mata "Badai wannan yarinyar kika kawon na É—auka aiki ba?" Hadiza ta sosa kanta.
"Eh ita ce Hajiya anan ma Kusan ku take"
Dariyar yaƙe matar tayi tare da cewa "Ina Hadiza bazan iya ɗaukar wannan yarinya ba ai seta ƙwacen Mijina Gaskiya kuma fita dan Lokacin dawowar shi ya kusa"

Sa'ada ta matsa Jikin Matar ta kama ƙafafunta "Dan Allah Kimin alfarma Nai kona wata ne Mamana zan samawa Kuɗin magani"
Cikin rashin Imani irin na wasu masu haunu da shunin matar taja tsaki tana cewa "Dallah Ku fita bazan ɗauki jaraba da kuɗina ba wannan kyan naki na halaka ai sena Halaka kaina na ɗaukeki" Daga haka ta tashi tabar su a falon Hadiza ta kama Hannun Sa'a suka bar Falon Har suka Fita titi Sa'ada na kuka Hadiza tayi Matiƙar tausayawa Sa'ada sabida haka rarrashinta tayi tare da bata tabbacin zata cigita mata wani Gidan aikin In sha Allahu har naira ɗari Biyu ta bawa sa'ada wadda ta damƙe Kuɗin tayi Gida Koda taje babu yadda Hajiya take Sabida haka hankalinta ƙara tashi yayi Fiye dana farko Saka Hajiya tai a gaba tana Kuka wajan La'asar Aunty Murja ta kawo Musu abinci da Kuɗi tace Inji Mijinta Da murna sa'ada ta Ɗauki naira dubu Biyun Da Mijin Aunty Murjar ya aiko Musu dashi ta fita wajan siyo wa Hajiya magani wani ƙaton Chemist ta je a bakin Titi ta bashi katin tare da Kuɗin ya zuba mata ido kamar maye mai chemist Ɗin kenan, Bayan ya karanta.
Chapter 4 · 0% Book details