← Book details Yankan Kauna Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 15 OF 23

Sashe 15

Yankan Kauna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

_A WANI ƁANGARAN MUNA YIN_
*GRAN JIKI*
*ƘUN SHI DA BABU IRIN SA*
*MUNA DA TURARUKAN WUTA HUMRA*
*MUNA DA MAGUNGUNAN MATA*
*GUMBAR UKU BALA'I*
*GUMBAR TABAJE*
*GUMBAR BUJENTA JAGAB*
*GUMBAR SAKA MAI GIDA IHU*
*MUNA DA ZAFAFAN KAYAN MATAN DA BABU IRIN SU*🔥🔥
*MUNA DA SUPLEMENTS*
_ZAITUNA MULTI TRADE MUNA YIN_
*MAKE UP NA AMARE DAMA WAÆŠANDA BA AMAREN BA*
*MUNA YIN SALOON*
*MUNA DA YADIDDIKAN MATA DA TAKALMAN SU*
_A ƁANGARAN ƘWALAMA KUMA MUNA_
*SIYAR DA ÆŠANYUN KAJI MASU ARHA DA GIRMA*
*MUNA YIN PEPPER CHICKEN MAI DAÆŠIN GASKE*
*MUNA SIYAR DA KAJIN BIKI SUNA*
*MUNA DA EXCLUSIVE KAYAN SAWA DON AURE KO SHA'ANI NA FITA KUNYA KU NEMEMU*
*KADA KU MANTA AKWAI KAYAN GWANJO MASU AMINCI  MUNA FASA DEALER DAGA NAN HAR SALLAH*

*MUNA DELIVERY NATION KO INA A FAƊIN ƘASAR NAN*

*ADIRESHINMU NA NAN A GARIN KANO MARMARA OPPOSITE ASIBITIN YARA NA MARMARA TITIN NAGODA KU NEME MU A WAÆŠANNAN NUMBOBIN WAYAR KAMAR HAKA*
08136259679 / 07067338694/ 08036426589/08067336110/08060235089/07048985018 MUNA MARABA DA MASU SIYAN ÆŠAIÆŠAI KO SARI AKWAI RAGI NA MUSAMMAN GA WAÆŠANDA SUKA SAI KAYAN GWANJO MUTUM BIYAR NA FARKO

*MULTI TRADE KANO*🔥🔥

​*YANKAN ƘAUNA..!!*🌹

*NA*
*AUTAR MANYA*

ADABI WRITTER'S ASSOCIATION

*15*

Jikinta a matiƙar sanyaye wanda yayi kama da wanda aka tsoma ta acikin ƙanƙara haka ta buɗe Ƙofar falon nashi ta shiga, wawiyar ajiyar zuciya ta saki Lokacin data ƙarasa shiga Cikin Falon Sanyi ne da ƙamshi suka cika ta, Kamar mai tsoron wani abun haka tai saurin aje tray ɗin hannunta tana Ƙoƙarin Juyawa domin ta koma sabida bata Ji alamun da Mutum cikin falon ba sai kawai taji sautin Muryar shi ta fita a hankali.
"Kawo mini shi nan matsoraciya kamar wani zai kamaki"
Gabanta ne yayi wata irin faɗuwa harda dafe Ƙirji tayi kafin ta ɗan zaro idanunta kaɗan wanda hakan yayi matiƙar yi mata kyau.
Ɗauka tayi ta ƙarasa gabanshi yana zaune ya miƙe ƙafafun shi ya ɗora ƙafar shi ɗaya akan ɗaya.
Ta ajiye a gaban shi.
"Zuba min ki miƙo min"
Ya faÉ—a a dake.
Sosa idanunta tayi tana hamma! kafin ta ɗauki Cup ta tsiyaya masa aciki Ta miƙa masa Tsirawa hannun shi ido tayi kaɗan, Abin ya birgeta ko ina gashi ne kwance hatta a saman yatsun shi.
Tana miƙa masa ta Miƙe zata tafi.
"Zauna har na gama sai ki tafi da kayan" ya faÉ—a yana Kurbar shayin batare daya tsaya firfita shi ba.
Wani irin haɗaɗɗan Ƙamshi da daɗi mai ratsa zuciya ne ya shiga Kwanyar shi ya Lumshe ido yana kurɓar shayin cike da mamaki dama ance yawanci ƴaƴan da suka taso Cikin rashin wadata sunfi Ƙoƙarin iya komai saɓanin ƴaƴan da iyayensu keda hannu da shuni waɗanda Suna kwance ake Musu komai

Jingina kanta tayi da Jikin Kujera duk jinta take a takure ita gaskiya hakan ya zama takura a gareta sai dai bata da damar yi masa Musu Ya É—auki wajan Minti Goma sha biyar kafin ya sallameta tana tafe tana haÉ—a hanya tsoro fall zuciyarta sabida yadda Ko ina yayi tsit a gidan.

Tana aje kayan a kitchen ta Rufo Ƙofar part ɗin Maman ta nufi nasu Koda taje Baba kande tayi bacci Ƙwan ɗakin ta kashe ta kwanta ba jimawa bacci ya ɗebe ta cike da Wani irin yanayi a tare da ita.

Anwar sai wajan 2 na dare bayan ya kammala nafilolin shi ya shiga Bedroom ya kwanta bacci washe gari ranar Sunday babu Office sabida gaba É—aya ma'aikatan Kurfi Tex basa fita ranar Sunday Hutu suke Baccin shi yasha dan sai wajan 12 ya farka shima Khalid ne ya shigo ya tashe shi daga baccin suka fito falo suna kallon Ball.

Baccin Saadatu rabi da rabine a ranar sabida rashin sabo ta saba kwanciyar ƙasan tabarma yau gata a lafiyayyen gadon daya sha katifa wai a haka ma gadon mai aikine ina ga kuma masu Gidan Da asubahi baba Kande ta tayar da saadatu akan ta tashi tayi sallah Miƙewa tayi sabida bata sallah tana fashi wanka tayi da ruwan ɗumi ta gyara Jikinta sosai Ta koma tayi kwanciyarta wajan ƙarfe Goma suka tashi daga ita har Baba kande Bayan sun gaisa Baba kande ta fita Ɓangaren su Mama ita kuma ta zauna gyara Musu ɗakin da wanke Musu bayin su da yake bata da saurin aiki sai wajan 11 ta kammala sannan ta fita ɓangaren maman ita ma tuno Wannan Budurwar ta jiya taji gabanta na faɗuwa addu'ar Neman tsari daga sharrin abin tsoro ta shiga yi taɗan sami Nutsuwa kaɗan kai tsaye ɗakin Husna ta Shiga suna zaune su Huɗu acikin ɗakin Husna tana bawa Bassam Nono sauran ukun kuma ko wacce ta miƙe ƙafa da waya a hannunta a ɗarare Saadatu ta ƙarasa gaban Husna ta rissuna har ƙasa Muryarta a sanyaye tace.
"Maman Bassam ina kwana?"
Da murmushi akan saman Fuskar Husna tace mata.
"Lafiya lau nanny Bassam, yaya kwanan baƙon waje amman Kin ɗan makara Bassam yayi Kashi da tumbuɗi Suna toilet suna jiranki"
Lokacin ɗaya daga cikin Ƴammatan taɗan Juyo tana kallon Saadah kafin tace.
"Ke baki ga mutane bane a wajan Husna wannan wace Irin mai aiki kika samu marar tarbiya ni bamma ga amfaninta ba tunda muna da washing machine a gidannan wankin me zata yi?"
Husna ta É—an haÉ—e ranta.
"Ni bana buƙatar Inji ya wanke Mini kayan yaro na sabida Masu kyau da tsada ne Zasu lalace wankin hannun Mutum yafi, Ke kuma Saadah baki ga mutane bane karki yarda a ƙara kawo Min ƙarar rashin gaisuwar Ki dan Jiya Aunty Hanan tace kin ture ta sanda zaki fita daga nan da yamma dan Allah Ki lura"
Saadatu tai ƙasa da kanta.
Tare da cewa.
"In sha Allahu, Suyi haƙuri hakan baze ƙara faruwa ba"
Sannan ta juya ta na gaishe dasu.
"Wow Saadatu ko ma sha Allah dama nice da kyanki Gaskiya kina da kyau" Cewar É—aya daga cikin Æ´ammatan wannan ta jiyan ce ta aje wayar hannunta tana kallon wadda ke yabon kyan saadah tsaki taja tare da cewa.
"Kedai anyi banza ina wani kyau anan aba kamar Nunar rana dallah tashi ki bani waje" da sauri Budurwar ta fita tana Gunguni Ita dai saadah tashi tayi tabar wajan ta shiga Toilet Ɗin sai da takai zuciyarta nesa wajan wanke kayan sabida harda panties ɗin Husna da suka ɗan ɓaci da Jini Aikuwa tana wankin tana tara Miyau acikin bakinta zuciyarta na wani Irin tashi haka ta kammala da ƙyar ta wanke toilet ɗin tass sannan ta fito Husna ta shiga wanka ita kuma ta soma gyara ɗakin Bassam ne ya ke Kuka sosai Husna ce ta fito Jikinta duk Kunfa tana wa Saadatu faɗan tabar mata yaro yana kuka "To naji Kince karna taɓa shine shiyasa ban yi Gigin taɓa shi ba amman Kiyi haƙuri" Ta ɗauki yaron tana Jijjigashi, Husna kuma ta koma wankan sai da ta fito sannan ta miƙa mata shi ta fita Kitchen ta shiga wajan Baba kande ta taimaka mata wajan kammala girkin tana Miƙa kayan zuwa dining.

Bayan sun kammala komai suka Ɗibi nasu zuwa ɓangarensu Suna Karyawa baba kande tana Yi mata nasihar kwantar da kai tare da yin biyayya ga ƴaƴan gidan baba kande ta ƙara da cewa.
"Duk ƴaƴan mama basu da matsala sosai su kawai Ka basu Girmansu in kana binsu zaka ji daɗin zama dasu, Mai bala'in matsala Hanan Ita ce babba a ƴaƴan Mama kuma ba ƴar Gidannan bace a golace Fiƙe ake gaya Miki kafi ƙaya tsini, Nima kaina bata ganin ƙimata amman Husna Khairat Ihsan Gaskiya ba sosai Suke da damuwa ba sabida haka Ki kula sosai Saadatu naga Kina da hankali"
Saadatu tai wa baba godiya anan suka cigaba da zama Baba kande ta kawo Musu ƙarshen zaman nasu ta hanyar kamo Musu tashar Arewa 24 Suna kalla Ga kuma sauran Ƙwai da farfesun da suka rage nan Saadah tana kallon Ragowar abin karin Hajiya da ummi suka Faɗo mata wanda Tun Jiya ta shiga damuwar rasa wayarta bare ta Kira Ummi taji yaya suka kwana ƙwalla ce ta taru a idanun saadah tashi tayi ta fita kai tsaye ɓangaren Sa ta nufa tana Tunanin Ko zata ga wayar tata Jin sautin muryoyi na tashi daga cikin falon nashi yasa ta Juya zata Koma wanda adaidai nan taji sautin Muryar shi.
"Wacece anan wajan?"
Tai tsuru Har zufa na karyo mata.
"Zonan ina zaki tafi bayan na kamaki"
Gabanta yana faɗuwa ta Juyo shi kuma lokacin har ya buɗe Ƙofar falon ya koma to tayaya ya gano ta bayan Ƙofar falon tana rufe.
Ta jima tana kokonton binsa tare dajin faɗuwar gaba kafin tai Shahadar Bin bayanshi wanda shi tuni har ya Koma cikin falon Taja ƙofar ta buɗe ta shiga a Lokacin taga wani farin namiji ya shiga Cikin wata Ƙofa da waya a kunnen shi tai saurin ɗauke idonta daga kallon shi tare da mayar da akalar Idanun nata zuwa ga Masifaffan Jiya wanda yake kwance a saman Doguwar Kujera Jikinshi sanye da Baƙar jallabiya.

"Ina kwana"
Ta faɗa bayan tai ƙasa da ƙwayar idanunta.
"Mai ya kawo ki nan ko yanzun ma ɓatan kai kika yi?"
Anwar ya jefa mata tambayar.
Girgiza kanta tayi.
"Tom ina jinki"
Tayi masa shuru.
"Okay ba zaki magana ba? Ko Abin break kika kawo Mini dama kin barni da kewar baƙin shayin ki"
Ta maimaita maganar a zuciyarta.

Da sauri ta Kuma girgiza kanta.
"Tab duk rashin maganata yau naga wadda ta fini yaya sunanki ma?"
A hankali ta furta.
"Sa'adatu"
Ya É—an sauke ajiyar zuciya yana Lumshe ido.
"Wow Nice name Mamina!"
Ita dai shuru tayi masa.
"Yanzu ina so ki kawo Min irin wannan shayin na jiya amman ki tafi da wancan Flask É—in sai ki zubo man aciki"
Ta maimaita hausar tashi a bakinta tabbas hausar bata ba kano bace hausar tai kama da katsinanci.
Ta tashi kamar wadda ƙwai ya fashe acikinta wurga ido take ko zata ga wayarta amman bata gani ba.

Ta gefen shi ta wuce ta fita daga falon Ba tare data bari wata maganar ta Kuma haÉ—a suba.
Chapter 15 · 0% Book details