← Book details Sauyin Yanayi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 8 OF 14

Sashe 8

Sauyin Yanayi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kamar zata tafi sai kuma ta tsaya tana cewa "ni ko Mama a cikin book baki ganin akwai inda ake cewa bin Bokaye da Malamai babu kyau kuma masu yin hakan kina jin yadda k'arshen su yake kasancewa. Mi yasa baza....... D'aga mata hannu Mama tayi tana zare mata ido kamin ta ce "Kinga duk nasan wannan tunkan a haifeki nake jin wa'azi, dan haka babu abunda zan fasa, indai hakan wancar matar ce da y'ay'anta dan haka tunkan waje ya k'ure miki kama hanya ki tafi inda zaki"

Da sauri Khadija ta fice daga gidan gaba d'aya tana d'aga k'afad'arta irin ko a jikinta d'in nan.

A waje kuwa Jafar ne tsaye yana waya da wani abokinsa yana cewa "haba abokina kasanfa motar nan maido maka da abunka zanyi ba wani dad'ewa zanyi ba zan dawo"

Daga cikin wayar aka ce "kaga Jafar ya kamata wannan k'aryar ace yanzu ka daina ta. Tunda kana da mata da y'ay'a har uku, ace kuma hakan bai isa ba sai ka k'ara yin wata k'aryar ka auro wata kuma. Kana ganin rayuwa zata tafi a hakane?"

Jafar ya murtuke fuska kamar yana gaban wadda suke wayar dashi kamin ya ce "kaga Baffa please ka rik'e gaskiyarka bana so. Amma aure saifa na k'arasa, idan ba haka kake ma matan yanzu ba tofa ko kallonka basayi, yo akan mi? ai wallahi kamar yadda na auri Hafsat ta gama haukanta wai bazata zauna a gidan k'asa ba, bazata ci tuwo ba, ta gama haukanta ba gashi dole tayi hakuri ta rungume kaddara ba. To itama haka wannan dole ne zatayi hakuri kota k'i kota so".

"Ka dai rink'a sassauta k'arya a rayuwarka wallahi Jafar"

"Kaga bawan Allah naji rik'e wa'azinka zaiyi anfani amma fa wata ran"

Yana fad'in hakan ya tsinke kiran ganin Khadija na tahowa inda yake tsaye.

Tana k'arasowa ya sakar mata murmushi yana cewa "Ohh My Khady wannan kyau haka?"

Dariya ta saki tana sa tafin hannunta ta rufe fuskarta kamin kuma ta sauke tana cewa "ai duk kaine akai mawa"

"Wow duk ni d'aya"

"Eh man"

"To yanzu dai da ina da ina kike so muje yau?"

D'an fari tayi da ido kamin ta ce "eh ina so muje shopping da wajan cin abinci haka"

Dariyar yak'i Jafar ya saki, danma yana da y'an kud'insa daya rantab'o ma kansa bashi, kullum cikin cin bashi yake da aron kayan jama'a, shine aro mota can, shine aro kayan sawa can shine kaza shine kaza.

Bud'e mata mota yayi yana k'ara washe baki ya ce "Bismillah ki shiga"

Shiga kawai motar Khadija tayi ta zauna, shima ya rufe motar ya shiga ya zauna.

Ya data ita suka fice daga unguwar taso.

*Gurbi K'aramar Hukumar Jibia Katsina State Nigeria*

"Nanah kizo ku wuce Islamiya fa ko, gashi har shidda tayi safiya ta farayi, naga alamar baki son zuwa Islamiyar asubar nan"

Nanah data fito daga d'aki tana faman murmuza idonta dake cike da bacci, ta kalli Inna dake bakin murhu tana dama Koko, ta ce "Inna wai Baba bai dawo bane?"

Gaban Inna ne ya d'an fad'i har sai da ta d'an dafe k'irjinta kamin kuma ta samu kanta da addu'a a ranta, sai kuma ta dawo da dubanta wajan Nanah data k'araso inda take yanzu.

Ta ce "bai dawo ba, nima nayi mamaki anayin sallar Asuba fa yake dawowa gida, indai sukai kwanan dajin nan"

Murmushin yak'i kawai Nanah ta saki, dan itama taji irin fad'uwar gaban da Inna taji kawai ta d'aure ne dan kar Inna ta fahimci hakan.

Auta ta jawo yasha Kokon kamin ta kama hannunsa zasu fice daga gidan taji Inna ta tsaida ita tana cewa "ke kuma fa bazaki sha kokon bane?"

Wani abu Nanah ta had'e a mak'oshinta kwata-kwata yau bata jin dad'i, bawai rashin jin dad'i na jiki ba, a'a kwata-kwata yanayin yau bata jin dad'insa.

Da kyar ta ce "a'a Inna na k'oshi, idan na dawo naci wani abu kawai"

Itama Innar bata sake magana ba, har su Nanah suka fice daga gidan. Kawai saita samu kanta da tagumi hannu biyu-biyu ta rasa mike mata dad'i itama.

Tafe suke kan hanya ita da Auta zasu dawo gida bayan an taso daga Islamiyar, Auta sai tsaida ita yake yana y'an wasanninsa.

Tsawa ta daga masa tana cewa "wai kai Auta mi yasa baka da natsuwa ne?, muna tafe kan hanya ka natsu mana muje gida"

Auta daya firgita da tsawar da Nanah tayi masa, yasa ba shiri ya natsu yana binta da kallo kamar ba itama ba, bata tab'a masa irin wannan tsawar ba. Kodai bata da lafiya ne?.

Sai kuma ta kamo hannunsa suka cigaba da tafiya.

Sun shawo kwanar gidansu kawai taji Auta na cewa "lahhh Nanah dubi k'ofar gidanmu cike da mutane"

Kan Nanah a k'asa yake ai da sauri ta waiga inda k'ofar gida nasu yake. Wata wawar bugar zuciya ce lokaci d'aya ta riski Nanah had'e da wata fad'uwar gaba. Tunkan ace mata mike faruwa ta fara hawaye kawai domin jikinta ya bata ba lafiya ba.

Da gudu Auta ya warce hannunsa da Nanah ta rink'e yayi cikin gida.

Nanah ma ta tsakiyar mutanan ta rab'a ta wuce yadda taga sai binta suke da kallon tausayi, an shinfid'a tabarma ga Liman yazo wasu na alwala duk jikin mutane a sanyaye.

Da sassarfa ta idasa shigewa cikin gidan. Tana shiga abunda idonta yayi mata tozali dashi shine Gawar Baba shinfid'e a har an gama shiryata duk jini ya b'ata jikin likafanin. Wata irin razananinyar k'ara Nanah ta saki a haukace ta nufi inda gawar Baba take wata irin wawar runguma tayi masa, kawai ta fashe da wani irin kuka mai zuma zuciyar mai saurare.

Auta dake jikin Inna shima sai kuka yake duk da bai san mutuwa ba amma yasan idan aka tafi ba'a dawowa shikenan kaida mutum har abada.

Da kyar aka b'anb'are Nanah da har sumewa tayi a jikin Gawar Baba sai da aka shafa mata ruwa bayan an fita dashi.

Matsuwa Nanah tayi jikin Inna tasa kanta akan k'afad'ar Inna tana hawaye tana magana cikin muryar kuka ta ce "Inna miya faru da Baba?",

"Nanah y'an Ta'addar nan ashe dajin dasu Babanku suke b'uya sun gane cewa dama b'uya suke subar matansu. Wani d'an lek'en asiri suka turo ya kwana a garin shine yaje ya sanar dasu komai har inda su Babanku suke. A daran sukai ma wajan dirar mikiya sun kashe da yawan mazan dake wajan hatta Balah shima sun kashe sa Ibro ne kad'ai ya tsira shima sunji masa mugun ciwo"

Kuka kawai Nanah ta saki tana tsinema y'an Ta'addar nan a zuciyarta yafi a k'irga sai tsine masu take tana jawo masu bala'in duniya dana lahira.

Gaba d'aya garin Gurbi ya zama shuru da yawan mutane a ranar basu k'ara kwana a garin ba, a hankali garin ya fara zama kamar ba gari ba. Duk wadda ka kalla a cikin garin bashi da natsuwar zuciya kullum da tashin hankali suke kwana suke tashi. Dan yanzu har tsakiyar rana y'an Ta'addar shigowa suke.

Tsaye Inna take yau kusan wata d'aya da mutuwar Baba tana shirin saida gidan da suke ciki ta tattara y'ay'anta su koma cikin garin Jibia da zama, ko sun samu kwanciyar hankali, duk da taji Jibiar ma shiga suke idan sunyi niyya, amma ai gara can da yawan mutane a garin.

"Yanzu Inna waye zai siya wannan gidan da daraja a garin nan?"

Inna ta kalli Nanah dake mata magana. Inna ta nisa ta ce "na dai aika Auta gidan Saminu dallali, yaji idan zai iya siyan gidan nan, dan bana ma so mu k'ara wasu kwanaki a garin nan gaskiya"

"To Allah yasa ya siya d'in, kin san yanzu tsoron siyan gida ake a garin nan ma"

"Yo Nanah ba dole aji tsoron siyan gida a garin nan ba. Ai dan a zauna ake siyan gida, to k'iri-k'iri idan ka siya zai gagareka zama indai a cikin garin nan ne.........

*SAUYIN YANAYI*

Share Fisbilillahi
*©ZAHRA ROYAL STAR 🌝*

*ROYAL STAR WRITERS ASSOCIATION*

*EPISODE* 6

*Unguwar Dubantu Hadejia Jigawa State Nigeria*

"Kaiii Ismail tsaya na ce"

Juyowa Ismail yayi yana duban Hajara data masa tsawa, rik'e k'ugunsa yayi yana kallon Hajara kawai.

Wani duba take mai cike da mamakin yaron ta cije baki kamin ta ce "kai dan ubanka, ni ce zan aike ka kaje kayo min shirme?"

"Mama bafa shirme nayo miki ba, haka kike ce na sayo miki Sigari"

Dafe k'irjinta Mama tayi ido a waje take nuna Ismail tana cewa "na shiga uku Sigari?, ni ce nace ka sayo min Sigari?"

Wani irin kuka ta fashe dashi na makirci. Tana matse hawaye

Da sauri Maryam ta fito daga d'aki tana kallon Mama cike da mamaki take cewa "Mama lafiya na ganki tsaye da yaron nan dangin marassa kunya?"

Mama ta dubeta ta ce "bari y'ar nan, yanzu ni wannan yaron zaima shirri?, wai ni ce zance yaje ya sayo min Sigari ni?, yanzu kamar wannan yaron d'an haka dashi ya iya k'ulla shirri?".

Wani kukan kura Maryam tayi sai gata agaban Ismail batai wata-wata ba, ta tsinka masa mari. Wani ihu Ismail ya saki yana dafe kumatunsa.
Duk da haka Maryam sai da taci kwalar rigarsa tana zare masa ido, a tsawa ce take masa magana.

"Kaii dan ubanka, uban waye ya had'a maka wannan tuggun da har ka iya had'a munafurci, dan kaja ma Mama shirri kana yaro da kai?. Zaka fad'a min ko sai na faffasa maka baki?, ka tab'a ganin Mama nashan tab'a dan uwarka?"

Hajiya ce da Salma suka fito a hargitse jin kukan Ismail.

Ganin yadda Maryam taci kwalar rigarsa yasa Salma zuwa da k'arfi tajawo Ismail tana bin Maryam da kallo na mamakin miye yayi mata haka?.

Mama ganin Hajiya ta fito, yasa dan d'aukar magana ta saki wata shewa tana cewa "yo idan banda abunki Maryam, ai uwarsa ce zata gaya masa yaje ya sayo Sigari domin kawai ya b'ata min suna, dama bata san zamana a gidan nan. Tota Allah bata mutum ba wallahi, duk wani munafurci uwarsa ya gadu ai".
Chapter 8 · 0% Book details