Sashe 14
Sauyin Yanayi Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Wani dogon tsaki Tajo yaja yana shafa sumar kansa, ya d'an daga kansa sama, sak'on d'aya biyu....... Kawai ya kaima Auta wani bugu a saman kai, nan take Auta ya zube a sume.
Wani sab'on kuka ne ya kufce ma Nanah tana kiran sunan Auta iya k'arfinta, duk tunaninta ko mutuwa yayi.
Cikin muryar kuka take magana tana kallon Tajo cike da tsana ta ce "ku sani Allah bazai tab'a kyale ku ba, Allah saiya isar mana akan zaluncin da kuke mana. K'aramin yaro ma baku kyale ba, tsabar baku da imani, Allah ya isarmu wallahi bamu yafe ba".
Dariya Tajo ya saki yana matsowa inda Nanah take, ya damko wuyanta yana cewa "au ashe kina magana y'an mata?, na d'auka ai kurma muka d'akko. Dama mu ai bamu ce ku yafe ba. Ya ishe mu da kukan banza ne, shine na sashi yin baccin dole, kin gane?, zai farka ai ba mutuwa yayi ba, amma ki sani ya sake mana irin haka, to zaibar duniya ne gaba d'aya. Ya kamata ki kula, bama son damuwa ne".
Wani abu mai d'aci Nana ta had'iye a mak'oshinta tana bin Tajo da kallo. Ji take inama tana da dama data shak'e masa wuta shima harsai ya daina numfashi.
Cikin dare Nanah tajiyo kukan Auta daya farka, sanyin dake cikin dajin ne ya farkar dashi, ga kuma inda yake kwance tsinnaku duk sun cijeshi a jiki. Da sauri Nanah ta kira sunansa a hankali. Da lalube ya k'araso inda Nanah take, yana zuwa ta rufe masa baki da tafin hannunta data samu Tajo ya kwance mata shi, d'azo daya gama gaggaya mata magana.
A hankali Nanah ta ce "dan Allah Auta kayi shuru, kayi hakuri kaji?, zuwa safiya za'a baka wani abu kaci, kana kallo mutanan nan basu da imani fa, kana so ka mutu ne?".
Da sauri Auta ya girgiza mata kai.
Ta ce "to yawwa ka daina kuka idan baka so kaji?".
Ba yadda Auta yayi dole tasa yayi shuru ya mak'ale a jikin Nanah.
Suna haka, sukaji ihun wata matashiyar yarinya, daga jin yadda take ihun tana neman taimako, zaka san cewa so ake a keta mutumcinta ne.
Yadda Nanah ke jin yarinyar na cewa "wayyo Allah, ku taimaka min zai kashe ni, na shiga uku ina zan kai wannan mutunin, zai lalata min rayuwa dan Allah ku ceceni".
Waro idonta Nanah tayi tana kallon wata ruffa da abun ke faruwa hasken fitila ta gani a wajan, ihun yarinyar na fitowa daga cikin rufar. Tana iya jiyo yadda suke kokowa da yarinyar, tana son kwance kanta. Tana jin shi kuma yadda yake ta kai mata maruka ba k'ak'k'autawa.
Allah sarki yarinyar duk da irin dukan da yake kai mata so kawai take ta kwaci kanta, sai kuka take tana kiran azo a taimaketa.
Ganinfa tana son b'ata masa lokaci, gashi duk ta ji masa ciwo yasa ya harzuk'a bai san sadda ya d'akko bindiga ba ya sakar mata harsashi.
A mugun rud'e Nanah ta toshe kunnuwanta had'e da k'ara rungume Auta daya fasa wata gigitacciyar k'ara yana sumewa a jikin Nanah, domin harga Allah ya mugun tsorota sosai. Nanah tama rasa wane hali take ciki, duk ta rud'e ta fice daga yaccinta. Ga Auta da bata jin motsinsa a jikinta, ga yarinyar da tana da tabbacin ita ce aka halba. Tana iya jiyo yadda D'an Ta'addar ke ta'asarsa saman kan yarinyar duk da halbinta da yayi, amma tsabar mugunta da rashin imani a haka ya afka mata.....
_________________________
Mike shirin faruwa ne da Salma wai?, ya rayuwar Salman zata kasance a nan gaba ne wai?, shin Momy wacce irin zuciya ce da ita ne ta rashin imani?, kaiii wannan Mama ma akwai y'ar kwal uba fa🤭. Shin wai tsaya ma Hajiya zata amince da aurar da ake son d'aura ma d'iyarta wadda bata san dashi ba?, Yaya Salma zata ji idan taji an d'aura mata aure da wani, waninma wadda bata tab'a gani ba?...*KAIII JAMA'A AKWAI CAKWAKIYA A BOOK D'INGA, NA TSAYA A NAN DOMIN NIMA INA SON SANIN DUK AMSOSHIN NAN*
_________________________
*To a nan na kawo k'arshen Free pages*
*Game son ci gaban book d'in nan zai biya D'ARI BIYAR NE KACAL*
Ta wannan account number d'in.
8130479973 Fatima Rabi'u Opay bank
Saika turo shaidar biya ta wannan number d'in 08130479973
Wani sab'on kuka ne ya kufce ma Nanah tana kiran sunan Auta iya k'arfinta, duk tunaninta ko mutuwa yayi.
Cikin muryar kuka take magana tana kallon Tajo cike da tsana ta ce "ku sani Allah bazai tab'a kyale ku ba, Allah saiya isar mana akan zaluncin da kuke mana. K'aramin yaro ma baku kyale ba, tsabar baku da imani, Allah ya isarmu wallahi bamu yafe ba".
Dariya Tajo ya saki yana matsowa inda Nanah take, ya damko wuyanta yana cewa "au ashe kina magana y'an mata?, na d'auka ai kurma muka d'akko. Dama mu ai bamu ce ku yafe ba. Ya ishe mu da kukan banza ne, shine na sashi yin baccin dole, kin gane?, zai farka ai ba mutuwa yayi ba, amma ki sani ya sake mana irin haka, to zaibar duniya ne gaba d'aya. Ya kamata ki kula, bama son damuwa ne".
Wani abu mai d'aci Nana ta had'iye a mak'oshinta tana bin Tajo da kallo. Ji take inama tana da dama data shak'e masa wuta shima harsai ya daina numfashi.
Cikin dare Nanah tajiyo kukan Auta daya farka, sanyin dake cikin dajin ne ya farkar dashi, ga kuma inda yake kwance tsinnaku duk sun cijeshi a jiki. Da sauri Nanah ta kira sunansa a hankali. Da lalube ya k'araso inda Nanah take, yana zuwa ta rufe masa baki da tafin hannunta data samu Tajo ya kwance mata shi, d'azo daya gama gaggaya mata magana.
A hankali Nanah ta ce "dan Allah Auta kayi shuru, kayi hakuri kaji?, zuwa safiya za'a baka wani abu kaci, kana kallo mutanan nan basu da imani fa, kana so ka mutu ne?".
Da sauri Auta ya girgiza mata kai.
Ta ce "to yawwa ka daina kuka idan baka so kaji?".
Ba yadda Auta yayi dole tasa yayi shuru ya mak'ale a jikin Nanah.
Suna haka, sukaji ihun wata matashiyar yarinya, daga jin yadda take ihun tana neman taimako, zaka san cewa so ake a keta mutumcinta ne.
Yadda Nanah ke jin yarinyar na cewa "wayyo Allah, ku taimaka min zai kashe ni, na shiga uku ina zan kai wannan mutunin, zai lalata min rayuwa dan Allah ku ceceni".
Waro idonta Nanah tayi tana kallon wata ruffa da abun ke faruwa hasken fitila ta gani a wajan, ihun yarinyar na fitowa daga cikin rufar. Tana iya jiyo yadda suke kokowa da yarinyar, tana son kwance kanta. Tana jin shi kuma yadda yake ta kai mata maruka ba k'ak'k'autawa.
Allah sarki yarinyar duk da irin dukan da yake kai mata so kawai take ta kwaci kanta, sai kuka take tana kiran azo a taimaketa.
Ganinfa tana son b'ata masa lokaci, gashi duk ta ji masa ciwo yasa ya harzuk'a bai san sadda ya d'akko bindiga ba ya sakar mata harsashi.
A mugun rud'e Nanah ta toshe kunnuwanta had'e da k'ara rungume Auta daya fasa wata gigitacciyar k'ara yana sumewa a jikin Nanah, domin harga Allah ya mugun tsorota sosai. Nanah tama rasa wane hali take ciki, duk ta rud'e ta fice daga yaccinta. Ga Auta da bata jin motsinsa a jikinta, ga yarinyar da tana da tabbacin ita ce aka halba. Tana iya jiyo yadda D'an Ta'addar ke ta'asarsa saman kan yarinyar duk da halbinta da yayi, amma tsabar mugunta da rashin imani a haka ya afka mata.....
_________________________
Mike shirin faruwa ne da Salma wai?, ya rayuwar Salman zata kasance a nan gaba ne wai?, shin Momy wacce irin zuciya ce da ita ne ta rashin imani?, kaiii wannan Mama ma akwai y'ar kwal uba fa🤭. Shin wai tsaya ma Hajiya zata amince da aurar da ake son d'aura ma d'iyarta wadda bata san dashi ba?, Yaya Salma zata ji idan taji an d'aura mata aure da wani, waninma wadda bata tab'a gani ba?...*KAIII JAMA'A AKWAI CAKWAKIYA A BOOK D'INGA, NA TSAYA A NAN DOMIN NIMA INA SON SANIN DUK AMSOSHIN NAN*
_________________________
*To a nan na kawo k'arshen Free pages*
*Game son ci gaban book d'in nan zai biya D'ARI BIYAR NE KACAL*
Ta wannan account number d'in.
8130479973 Fatima Rabi'u Opay bank
Saika turo shaidar biya ta wannan number d'in 08130479973