← Book details Sauyin Yanayi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 14

Sashe 3

Sauyin Yanayi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Computers guda biyu ya d'auka sai wasu y'an abubuwa yana shirin barin wajan yaji Henry na cewa "yawwa kaga nama manta babbar mawak'iyar nan tazo nemanka wai tana so tayi wak'a da kai"

"Wa kenan?"

"Enisa mana"

"Ohhh, but I'm just singing, I don't release the video of the song, but some people sing my song if we sing normal, but honestly I won't sing, I can't sing"

"Faruk na fad'a mata wannan duk da taso ku hau wak'ar tare amma ta amince zaku rera wak'ar kawai"

"Okay yayi ba bamuwa ita ce ta rubuta wak'ar ne?".

"Eh ita ce yanzu hakama taban wak'ar a rubuce zuwa gobe zata dawo domin ganinka.Then decide when you think you will sing the song"

"Ba damuwa zuwa goben ma idan aiki bai min waya ba, zamu iyayinta kawai".

Ficewa yayi daga studion yana fata yasa face mask ya rufe fuskarsa, gudun mutane suyo kansa, duk da dare ya tsala amma garin kamar safiya ce. Dan duk inda ya shiga a k'asar Canada to ansan sa ansan waye Faruk Galadima shahararran mawakin dake tashe a duniya. Ya fara wak'a tun yana k'araminsa da sun cikar burinsa na son zamowa mawaki. Kuma Amma ta basa goyin baya, sai dai duk da haka baisa ya manta shi d'in waye ba. Mahaifiyarsa kad'ai ta rage masa a duniya. Sunsha wahalar rayuwa acan baya amma wak'ar daya ke tasashi d'aukaka, d'aukakar da zato bai zata ba. Shi kansa baiyi tunanin zai zama wadda duniya take alfahari dashi kamar haka ba, it's a good thing for everyone to join him wherever he goes or where he goes.
Abunda ya maido sa zama Canada shida Amma bayan wak'a yana aiki a wani kanfani na k'era wayoyi da computers da dai sauran na'oruri daya danganci electric. Yasan takan waya da computers duk idan sun samu matsala zai iya gyara maka a d'an k'ank'anin lokaci. All companies are proud of Faruk Galadima.

Katse tunaninsa yayi dai-dai yazo gaban wata Mota mai d'aukar ido. Bud'e gidan baya yayi yasa abubuwan dake d'auke a hannunsa, bayan yasa ya rufe bayan ya dawo ya shiga ya tada motar yabar cikin studion, da shima mallakinsa ne yanzu, mawak'a wadda basu kaisa ba suna zuwa sosai domin su buga wak'arsu a studionsa ba tare da ka bada ko sisi ba. Da yawan mutane abunda ke k'ara sawa su soshi kenan sunansa yayi zarra a k'asar Canada, kai harma da makwaftan k'asashe.

Wani ma dai-daicin gida wadda ya gaji da had'uwa yayi parkin d'in motar tasa kamin ya bud'e ya fito yana danna wani madanni dake hannunsa nan take get d'in gidan ya bud'e, shi kuma ya koma cikin motar ya data ita, ya idasa shigewa harabar gidan. Wajan aje motoci yayi parking.

Fito yayi daga motar ya d'auki kayansa dake bayan motar ya nufi cikin gidan.

Yana shiga babban parlon gidan ya iske Amma dake zaune zaman jiransa.

Ganinsa ya dawo k'alau yasa Amma sauk'e ajiyar zuciya. Har saida Faruk yaji yadda ta sauk'e ajiyar zuciyar.

Murmushi ya saki yana ajiye kayan dake hannunsa yazo kusa da Amma ya rungumeta yana cewa "Ohhh Amma idan na fita sai kace wani k'aramin yaro, wadda idan ya fita akesa ran bazai iya gane gida ba?. Amma nafa girma yanzu"

Kumatunsa Amma taja tana cewa "kaci gidanku Faruk, yaushe aka haifeka ma da zaka wani ce ka girma yanzu?, ni a waje na kai yaro ne".

Murmushi ya sakar mata ya ce "hakane fa Amma, ai kin san ina kan hanya gashi na dawo kuma lafiyata lau".

"Kaji ja'iri baccin ka gama tada min hankali, ka kalli k'arfe nawa ne yanzu kuwa?"

Da sauri Faruk ya kai dubansa akan tsintsiyar hannunsa dake d'aure da agogon hannu. Waro ido waje yayi yana cewa "Ohhhh sorry Amma sha biyu saura ashe na dare. Mi yasa baki kwanta ba?, aiki ne yau yayi min yawa wallahi"

Shafa kansa tayi tana cewa "nayi tunanin hakan, amma kasan idan ba dawowarka na gani ba bazan iya bacci ba. Kaida kota ina mutane nemanka suke ya za'ai kullum hankalina bazai tashi ba idan zaka fita?".

"Amma nemana mutane suke amma ai soyayya ce tasa hakan ba wai cutar dani zasuyi ba"

Murmushi Amma ta saki irin na manya ta ce "har yanzu kai yaro ne Faruk, ai cikin hakan ake samun mak'iya, wad'anda basa son ci gabanka, kai dai kawaii Allah yayi mana tsari da su. Allah kuma ya k'ara k'are min kai a duk inda kasa gaba"

Kiss ya kai mata a goshi yana amsawa da amin.

Yana niyar tashi Amma ta ce "abinci fa?"

"Bana jin abincin nan zai shiga yanzu Amma"

"To miye kaci yau?".

"Na d'anci wani abu a studio"

"A'a bazan yarda ba saifa kaci abinci, nasan ba wani abinci kaci ba, yanzu haka Chacolate d'in daka saba ci kayan zak'i sune kayita sha. Kazo ga abinci nan akan darning table kaci"

D'an tab'a cikinsa Faruk yayi sai yanzu nema yaji lallai yana jin yinwa, dan rabonsa da abinci tun safe da zai fita aiki. Sai Chacolate d'in da sha.

Shigewa yayi d'akinsa dake sama. Yana shiga toilet ya fad'a ya watsa ruwa, bayan ya fito yasa wasu k'ayan bacci. Yana d'aukar wayarsa dake ta aikin ringing tun d'azo.

Wayarsa ta gida wacce y'an uwansa na kusa da friend's nasa ne kad'ai ke kira ta cikinta yaji ta fara k'ara.

D'aukan kiran yayi yana k'arawa a kunne.

Cike da kulawa yake yin wayar wani lokacin yayi dariya daka gani kasan da abokinsa yake waya.

Can ya ce "Okay kuna gaf shiga jirgi?. Ni banso ka koma Nigeria ba yanzu friend, miye zakai a Nigeria ne?, kasan kuma ciwonka yafi tashi idan kana can".

Daga cikin wayar aka ce "to ya zanyi ina son k'asata kuma Daddy ya kirani yana son gani na nima nayi kewarsa sosai kasanfa rabona da Nigeria zanyi shekara biyu, tun sadda naje Momy ta matsa nayi aure, akayi a daran aka samu matsala dole na saki matar tun lokacin na bar k'asar"

Faruk cike da kulawa ya ce "Salman ya kamata fa asan miye asalin mike damunka gaskiya ba yadda za'ai ka zauna ba aure"

"Abunda bana so kana min maganarsa kenan Faruk ka sani. Nigeria is the only thing I don't want to come to where I went and Daddy pressured me to get married, kuma bayan yasan bazan iya zama da kowacce mace ba a haka"

"Insha Allahu Salman komai zai wuce zamuyi waya idan ka sauka. Wai ina Jasmin ne taka?"

"Kai ko? Bana son wannan zancan, ko kasan Jasmin bata da kamun kai?, kai kwata-kwata ma bata cikin jerin matan da nake so. Kuma duk fad'a take duk sadda a gaban idonta ciwo na ya tashi wallahi a ranar guduwa zatai"

"Hakane aboki ai da yawansu badan Allah suke son mutane irinku ba"

"Harda kai ma ai Faruk kaifa sele ne"

Dariya Faruk ya saki yana cewa "kai Salman na kaika ne nifa wak'a ce ta d'aukaka ni kaifa tsaye kake da k'afafunka kaine ka kafa kanka da kanka, ai matsiyin da dabanne"

"Ka cika wasa Faruk wallahi"

Sun dad'e suna waya kamar kar su daina sai da jirgin su Salman zai tashi tukunna sukai sallama..........
*SAUYIN YANAYI*

Share Fisbilillahi *©ZAHRA ROYAL STAR 🌝*

*ROYAL STAR WRITERS ASSOCIATION*

*EPISODE* 3

*Gurbi K'aramar Hukumar Jibia Katsina State Nigeria*

"Ance wai ana sallama da Babansu Auta"

Inna dake tsakar gida ta dubi yaron daya shigo ta ce "kaje kace gashi nan zuwa"

Juyawa yaron yayi ya fice daga gidan.

Inna ta kalli Nanah dake cin abinci ta ce "Nanah shiga d'akin Babanku kice ana sallama dashi k'ofar gida"

Tashi kawai Nanah tayi ta shiga d'akin Baba ta sanar dashi.

Ba'a jima ba Baba ya fito ya fice daga gidan ya nufi waje.

Nanah ta kalli Inna ta ce "wallahi Inna gidan su D'an Liti mai shigo tashi fa zasuyi daga garin nan"

Inna ta aje redion dake hannu wacce take shirin kunnawa ta kalli Nanah, kamin ta d'an nisa ta ce "ai banga laifin su ba wallahi"

"Da mukaje da Auta yi masu jaje wallahi sai had'a kaya suke gaba d'ayansu gidan wai zasu koma katsina"

"Allah sarki ni kinga tun ranar dana je masu jajen ban gani ba, ashe barin Gurbi zasuyi. Kai wa'innan mutanan suna d'aukar alhakin al'umma. Haka kawai kana son garinka amma ya gagareka zama".

A k'ofar gida Baba yana fitowa ya iske su Ibro da Balah duk abokansa ne. Ganinsu hankali a tashe yasa Baba k'arasowa da sauri yana mik'a masu hannu, gaisawa sukai kamin Balah ya ce "Baban Nanah akwai fa matsala a garin nan"

Cikin Baba saida ya bada wani sauti kulululuuuu da kyar ya had'e miyau ya ce "ban gane ba Balah?"

"To yanzu dai y'an Dabar nan dake yawan shigo mana gari masu satar mutane had'e da kashe su, sana su d'ibi dukiyarmu da muke nomawa sun waiwayo kanmu"

"Subhanallahi wai kana nufin wadda suka so data garin nan baki d'aya?"

Ibro ya sauk'e lumfashi yana mik'a masa wata farar takarda ya ce "kaga wannan takadar sak'o ne daga wajansu suka aiko wai suna nan shigowa garin muma shirya. Sana sunce duk abunda muka noma mu tabbatar mun barsa a gonakinmu domin suna zuwa zasu d'ibesa su k'ara gaba, kai harda kud'in haraji ma suka sama kowa dake cikin garin nan"

Baba dake kallonsu ido a zare ya ce "wai wa'innan mutanan miye suke sone damu?, so suke su maida mu bayinsu kenan?".

Balah ya nisa ya ce "kuma abunda ke k'ara tada min hankali ma shine, Gwamnati ta kasa kawo mana d'auki. Kun tab'a ganin wani shugaban Gwamnati ya k'ara zuwa cikin garin nan da sunan yazo yaji miye yake damun talaka?".

"Inafa muka sake jin d'uriyarsu, ai tun gabannin zab'e da suke so muje mu dangwala masu k'uru'a. Sunci zab'en sun manta damu. Daga su sai iyalansu, ai wata shara'ar sai dai a lahira wallahi"

Cewar Baba da duk jikinsa yayi sanyi.

Baba ya sake kallonsu ya ce "to yanzu miye abunyi?"

Ibro ya ce "nidai gaskiya yanzu haka naba matata kud'in mota ita da yara na ce taje garinsu, mugani kamin garin yayi lafiya. Dan yanzu haka dangin D'an Liti mai shigo suma, sun tashi daga garin nan gaba ki d'ayansu"
Chapter 3 · 0% Book details