Sashe 11
Sauyin Yanayi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai dai duk da abunda tasa rayuwarsa a ciki hakan baisa Allah yak'i basa sa'ar rayuwa ba. Tunda ya fara karatu bai tab'a samun matsala ba, gashi da farin jinin jama'a. Kota ina ana ji dashi, komai zai tab'a sai Allah yasa masa albarka a ciki. School d'in dayayi da kansu suka d'au nauyin karatunsa aka turasa k'asar waje ya ci gaba da karatunsa.
Yana gama karatunsa, bai jira wani aikin Gwamnati ba, kona Daddynsa, ya kama sana'ar saida motoci da gidaje, da kud'in da aka basa kyautar su a school d'in daya gama, yaci kyaututuka kala-kala iri-iri daban-daban. Hatta k'asar daya gama karatu sunso d'aukarsa aiki amma ya ce shi so yake ya tsaya da k'afafunsa.
Cikin ikon Allah nanma Allah yasa masa albarka dandanan ya bud'e kanfanin k'era motoci. Companynsa kusan biyar a k'asar waje, harda na k'era Abayoyi irin na K'asar Dubai, da atanfofi da dai sauran su.
Momy abunda ya k'ara sa mata tsanar yaron kenan, bata da wani buri yanzu saina ganin bayansa....
Sauk'e lumfashi Momy tayi tana zama akan gadonta bayan ta gama tuno gaba d'aya rayuwar data wuce baya....
*SAUYIN YANAYI*
Share Fisbilillahi
*©ZAHRA ROYAL STAR 🌝*
*ROYAL STAR WRITERS ASSOCIATION*
*EPISODE* 8
*Unguwar Dubantu Hadejia Jigawa State Nigeria*
"Wallahi Abbansu Maryam k'iri-k'iri yaron nan Ismail, ya nemi min rashin kunya, saboda uwarsa ta d'aure masa gindin yayi ma mutane rashin kunyar"
Mama ta idasa maganar tana hararar Hajiya dake gefe, sai Ismail dake gaban Abba. Dawowar Abba kenan gidan, Mama ta kai k'arar Ismail.
Abba da b'acin rai ya aika a kira masa Ismail, shine Hajiya tajawo hannunsa suka shigo a tare d'akin Abban.
Abba ya kalli Hajiya yana cewa "wato na ce yazo shi d'aya shine ke mai d'a, zaki kwaso k'afa ki biyosa ko?"
"Amma Mlm abunda kake fa bai dace ba ko kad'an"
Cewar Hajiya tana kallon Abba, dake masifa an tab'a masa mata.
Rik'e baki yayi yana kallon Hajiya, sai kuma ya kama kunnan Ismail ya murd'e. K'ara Ismail ya saki yana ba Abban hakuri.
Abba ya k'ara murd'e kunan Ismail yana cewa "dan k'aniyarka, miye ya had'aka da ita?"
Ismail cikin muryar kuka ya ce "wallahi Abba, ita ce ta ce naje na sayo mata Sigari, shine fa dana dawo take cewa ita ba itace ta ce na sayo mata ba"
Dafe k'irji Mama tayi ai kawai saita fashe da kuka tana nuna Ismail tana cewa "kaji irinta ko?, yanzu haka ita ta jashi d'aki saida ta shirya masa abunda zai fad'a, idan an kawo k'ararsa wajanka dama. Wallahi wannan maganar fad'a masa ita akai, wannan d'an yaron dai bazai iya shirya magana har haka ba. Yanzu tsakani da Allah Abbansu Maryam na tab'a sha maka Sigari a gida fisbilillahi?".
Kamin ma ta rufe baki Abba ya kaima Ismail wani mangari a k'eyarsa. Yana cewa "bata hakuri dan ubanka, kuma ka tashi kabar wajan nan, marar kunya kawai"
Zuciyarsa Ismail na zafi ya duk'a har k'asa yaba Mama hakuri, ciki-ciki ta amsa tana binsa da mugun kallo.
Duk abunda ke faruwa Hajiya na kallo bata sa baki ba, zuciyarta na zafi, ta taushi zuciyarta ne kawai dan a zauna lafiya.
Ismail na fita Mama ta kalli Abba ta ce "yawwa dama ina son magana da kaine, akwai maganar da nake so mu tattaunawa mai mahimmanci"
Abba ya kalli Hajiya da bata da niyar tashi ya ce "maganar tamu kad'ai ce ko kuwa?, sai an bamu waje?".
Murmushin jin dad'i Mama tayi ganin yadda Abba ke gayama Hajiya magana.
Cike da makirci ta ce "a'a kowaye zan iya fad'a a gabansa, tunda mutum baida wuta baida Aljanna bare ya saka ni".
Gyara zama Abba yayi yana bata hankalinsa, domin indai maganar samu ce ta kud'i to Abba yana gaba-gaba a wajan.
Mama ta gyara zama itama tana cewa "yawwa abun arzik'i ne yazo har gida. Khadija dai ta samu miji, kuma da alama mai kud'i ne, baya ma so bikin ya d'auki lokaci da yawa, tunda kaga ta kusa gama karatun ta, yana son shigowa gida ne asan dashi, idan yaso akasa ranar auran sai asa dai-dai lokacin da zata gama karatunta. Koya kake gani Mlm?"
Cike da farin ciki Abba ya washe baki yana cewa "kai Masha Allahu, haka ake so, kinga ita ta tsaya tayi karatunta kuma ga miji ta samo dai-dai ita, ba irin su O'a ba"
Murmushin Hajiya dake gefe ta saki, batayi niyar tsoma masu baki ba, amma jin abunda Abban ke cewa ne, yasa Hajiya bazata iya hakura ba ta ce "karka manta Mlm dukansu fa Y'ay'anka ne, kuma komai lokaci ne dashi. Itama baccin kak'i ai da yanzu Salma ta dad'e da yin auranta"
Girar Abba ce ta had'e waje d'aya, kamin ya dubi Hajiya yana cewa "Hajiya kima daina wannan maganar, domin kuwa Salma gata can ma tayi karatu, ke wai wani ya hanaki yin karatun ne?, ba da iliminki na ganki ba, miye karatun bokon baiyi miki ba, hatta aikin hajji da kika je, ba ta dalilin karatun bane?".
Ganin maganar naso tayi tsayi yasa Hajiya tashi domin tasan ko kwana zatai tana gaya masa gaskiya tofa ba yarda zaiyi ba.
Tashi tayi tana cewa "Allah ya baka hakuri, amma gaskiya ka rink'a kamanta adalci a cikin y'ay'anka"
Tana idasa fad'ar haka ta fice daga d'akin.
Wani tsaki Mama taja tana cewa a zuciyarta "kinyi ki gama Hajiya, amma Salma ba ita ba auran wani wadda zata huta a rayuwa, sai nasa ta auri wadda zai ida nakasa mata rayuwa, wannan al'k'awari ne wadda na d'aukarma kaina"
Abba ne ya katse mata tunani, suka ci gaba da maganar Khadija da Jafar yadda komai zai kasance.
Washe da safe. Salma ce ta fito daga d'akinsu tana k'ok'arin shiga babban kitchen d'in gidan. Fitowarta ta hangi su Maryam da Mama dake zaune k'ofar nasu d'akin.
Fitowarta taji tsakin da sukai mata. Mama ce ta kunna redio, kawai taji suna karanto wani littafi waishe KADDARA CE, abunda ya k'ara hargitsa ma Mama da Maryam kwakwalwa shine yadda sukaji wacce ta rubuta book d'in.
Salma duk da taji abunda yasa su firgita sai tayi shigewarta kitchen d'in ta nuna kamar bata ji ba. Duk da tasan book d'inta ne, to amma cikin gidan nasu babu wadda yasan tana rubuta book's daga ita sai y'an d'akinsu. Ita kanta bata san gidan redio na karanta book nata ba, amma taji dad'in haka.
A rud'e Maryam ta ce "wai baku ji wane suna naji ana kira bane?"
Dariyar rainin wayo Khadija ta saki tana cewa "naji mana, zai wuce wata ce can sabuwar marubuciya akai, dan naji wani book ma abokiyar hira ta karanta na marubuciyar yadda kaddara taso, duk ita tayi shi".
Maryam ta ce "to amma ya akai sunan marubuciyar yake kama dana wancar Salman"
Mama ta tab'e baki ta ce "ke kuwa Maryam da abun dariya kike, idan banda abunki ina Salma ina iya rubuta wani littafi, yarinyar da bata san komai ba, sai jakanci kwakwalwata babu komai ciki sai dusa"
Dariya suka saki tare Maryam da Khadija har suna tab'awa. Dai-dai lokacin da Salma ta fito daga kitchen d'in.
Duk taji abunda suke cewa, sai kawai ta girgiza kanta tana murmushi ta shige d'aki.
Tana shigewa Mama tabi bayanta da harara tana cewa "yo yama za'ai hakan ta kasance, ai da nayi kukan bak'in ciki kuwa, ai insha Allah haka zaki k'are a gantale Salma keda uwarki"
Bayan kwana biyu Mama na zaune kan gadonta taji Maryam ta tab'a ta, ba shiri ta tashi zaune tana kallonta.
Ganin kamar gulma ta kawo mata yasa ta tashi da sauri tana cewa "ke lafiya na ganki haka?, kamar wacce aka biyo tayi sata"
Maryam tama kasa zama, ta had'e hannayenta waje d'aya, sai kuma ta kama baki cike da tsananin mamakin abunda kunnuwanta suka jiyo mata a k'ofar d'akinsu Salma, sakin bakin tayi ta dafe kanta. Mama ganin cewa kamar fa Maryam d'in a kid'ime take yasa ta jawota ta zaunar da ita a kusa da ita.
A hankali Mama ta waiga k'ofar d'aki wai ko wani abu ne ya biyo Maryam d'in, daya sa ta zama Haka.
Ganin babu alamar komai yasa Mama cewa "wai minene naga fuskarki ta cika da mamaki?"
Sauk'e wani goran lumfashi Maryam tayi kamin ta ce "yo ba dole Mama ki ganni a haka ba, ashe duk littatafan da muke ji a redio da You tub channel, wadda abokiyar hira take Karantawa, ashe duk na Salma ne, mu duk d'aukarmu ai suna ne kawai yazo d'aya ba ita ba ce, ashe kuwa Salmar gidanmu ce ba wata ba"
A zabure Mama ta mik'e tana cewa "keeee Maryam bana son maganar banza kinji"
"Na rantse miki Mama ita ce"
"Ke ta gidan Ubanwa kika sani to?"
"Mama ki natsu dan Allah kaji"
Jawota Maryam tayi ta zaunar da ita tana cewa "Mama nazo shiga ban d'aki ne, kawai kamar ance na matsa k'ofar d'akin su Salma, sai naji Hajiya na cewa. "Salma ya kamata fa ki aje typing d'in nan haka nan, ki d'an huta, idan kika gama littafin nan, ki d'an huta, kamin ki d'ora wani"
Sai kuma na sake jin Salma ta ce "Hajiya ai hutu ba yanzu ba, tunda ina da lokaci yanzu so nake sai nayi littafi kusan goma ko biyar tukunna zan huta. Dan har gasar Hikayata nake so na shiga shekarar nan"
A haukace Mama ta mik'e tana cewa "kutumar Ubancan, ai ko bazai tab'a yiwuba wallahi, dole na d'au mataki, dole ne gobe naje garin Hayin fari, wajan Mlm, dole ne sai Salma ta nemi wannan basirar rubutu littafin ta rasa, dani suke zancan wallahi".
Maryam ta sake kamo hannun Mama tana cewa "Mama kiyi a hankali dan Allah, kar wani yaji, nasan dama zaki d'au mataki ai, shi yasa zuciyata ta kasa yarda ba Salma bace tunda naji sunanta, na ce ni ko saina binciko, ashe-ashe b'oye mana ake dankar mu gane",
"Hmm dole zasu b'oye mana, amma yanzun ma ba makara nayi ba wallahi".
*Gurbi K'aramar Hukumar Jibia Katsina State Nigeria*
Tagumin da Nanah ta zafga ne, tun fitar Saminu take jin wata fad'uwar gaba, Allah ya sani tunda Baba ya rasu take jin irin haka, kuma har yanzu bata sake ta ba.
Yana gama karatunsa, bai jira wani aikin Gwamnati ba, kona Daddynsa, ya kama sana'ar saida motoci da gidaje, da kud'in da aka basa kyautar su a school d'in daya gama, yaci kyaututuka kala-kala iri-iri daban-daban. Hatta k'asar daya gama karatu sunso d'aukarsa aiki amma ya ce shi so yake ya tsaya da k'afafunsa.
Cikin ikon Allah nanma Allah yasa masa albarka dandanan ya bud'e kanfanin k'era motoci. Companynsa kusan biyar a k'asar waje, harda na k'era Abayoyi irin na K'asar Dubai, da atanfofi da dai sauran su.
Momy abunda ya k'ara sa mata tsanar yaron kenan, bata da wani buri yanzu saina ganin bayansa....
Sauk'e lumfashi Momy tayi tana zama akan gadonta bayan ta gama tuno gaba d'aya rayuwar data wuce baya....
*SAUYIN YANAYI*
Share Fisbilillahi
*©ZAHRA ROYAL STAR 🌝*
*ROYAL STAR WRITERS ASSOCIATION*
*EPISODE* 8
*Unguwar Dubantu Hadejia Jigawa State Nigeria*
"Wallahi Abbansu Maryam k'iri-k'iri yaron nan Ismail, ya nemi min rashin kunya, saboda uwarsa ta d'aure masa gindin yayi ma mutane rashin kunyar"
Mama ta idasa maganar tana hararar Hajiya dake gefe, sai Ismail dake gaban Abba. Dawowar Abba kenan gidan, Mama ta kai k'arar Ismail.
Abba da b'acin rai ya aika a kira masa Ismail, shine Hajiya tajawo hannunsa suka shigo a tare d'akin Abban.
Abba ya kalli Hajiya yana cewa "wato na ce yazo shi d'aya shine ke mai d'a, zaki kwaso k'afa ki biyosa ko?"
"Amma Mlm abunda kake fa bai dace ba ko kad'an"
Cewar Hajiya tana kallon Abba, dake masifa an tab'a masa mata.
Rik'e baki yayi yana kallon Hajiya, sai kuma ya kama kunnan Ismail ya murd'e. K'ara Ismail ya saki yana ba Abban hakuri.
Abba ya k'ara murd'e kunan Ismail yana cewa "dan k'aniyarka, miye ya had'aka da ita?"
Ismail cikin muryar kuka ya ce "wallahi Abba, ita ce ta ce naje na sayo mata Sigari, shine fa dana dawo take cewa ita ba itace ta ce na sayo mata ba"
Dafe k'irji Mama tayi ai kawai saita fashe da kuka tana nuna Ismail tana cewa "kaji irinta ko?, yanzu haka ita ta jashi d'aki saida ta shirya masa abunda zai fad'a, idan an kawo k'ararsa wajanka dama. Wallahi wannan maganar fad'a masa ita akai, wannan d'an yaron dai bazai iya shirya magana har haka ba. Yanzu tsakani da Allah Abbansu Maryam na tab'a sha maka Sigari a gida fisbilillahi?".
Kamin ma ta rufe baki Abba ya kaima Ismail wani mangari a k'eyarsa. Yana cewa "bata hakuri dan ubanka, kuma ka tashi kabar wajan nan, marar kunya kawai"
Zuciyarsa Ismail na zafi ya duk'a har k'asa yaba Mama hakuri, ciki-ciki ta amsa tana binsa da mugun kallo.
Duk abunda ke faruwa Hajiya na kallo bata sa baki ba, zuciyarta na zafi, ta taushi zuciyarta ne kawai dan a zauna lafiya.
Ismail na fita Mama ta kalli Abba ta ce "yawwa dama ina son magana da kaine, akwai maganar da nake so mu tattaunawa mai mahimmanci"
Abba ya kalli Hajiya da bata da niyar tashi ya ce "maganar tamu kad'ai ce ko kuwa?, sai an bamu waje?".
Murmushin jin dad'i Mama tayi ganin yadda Abba ke gayama Hajiya magana.
Cike da makirci ta ce "a'a kowaye zan iya fad'a a gabansa, tunda mutum baida wuta baida Aljanna bare ya saka ni".
Gyara zama Abba yayi yana bata hankalinsa, domin indai maganar samu ce ta kud'i to Abba yana gaba-gaba a wajan.
Mama ta gyara zama itama tana cewa "yawwa abun arzik'i ne yazo har gida. Khadija dai ta samu miji, kuma da alama mai kud'i ne, baya ma so bikin ya d'auki lokaci da yawa, tunda kaga ta kusa gama karatun ta, yana son shigowa gida ne asan dashi, idan yaso akasa ranar auran sai asa dai-dai lokacin da zata gama karatunta. Koya kake gani Mlm?"
Cike da farin ciki Abba ya washe baki yana cewa "kai Masha Allahu, haka ake so, kinga ita ta tsaya tayi karatunta kuma ga miji ta samo dai-dai ita, ba irin su O'a ba"
Murmushin Hajiya dake gefe ta saki, batayi niyar tsoma masu baki ba, amma jin abunda Abban ke cewa ne, yasa Hajiya bazata iya hakura ba ta ce "karka manta Mlm dukansu fa Y'ay'anka ne, kuma komai lokaci ne dashi. Itama baccin kak'i ai da yanzu Salma ta dad'e da yin auranta"
Girar Abba ce ta had'e waje d'aya, kamin ya dubi Hajiya yana cewa "Hajiya kima daina wannan maganar, domin kuwa Salma gata can ma tayi karatu, ke wai wani ya hanaki yin karatun ne?, ba da iliminki na ganki ba, miye karatun bokon baiyi miki ba, hatta aikin hajji da kika je, ba ta dalilin karatun bane?".
Ganin maganar naso tayi tsayi yasa Hajiya tashi domin tasan ko kwana zatai tana gaya masa gaskiya tofa ba yarda zaiyi ba.
Tashi tayi tana cewa "Allah ya baka hakuri, amma gaskiya ka rink'a kamanta adalci a cikin y'ay'anka"
Tana idasa fad'ar haka ta fice daga d'akin.
Wani tsaki Mama taja tana cewa a zuciyarta "kinyi ki gama Hajiya, amma Salma ba ita ba auran wani wadda zata huta a rayuwa, sai nasa ta auri wadda zai ida nakasa mata rayuwa, wannan al'k'awari ne wadda na d'aukarma kaina"
Abba ne ya katse mata tunani, suka ci gaba da maganar Khadija da Jafar yadda komai zai kasance.
Washe da safe. Salma ce ta fito daga d'akinsu tana k'ok'arin shiga babban kitchen d'in gidan. Fitowarta ta hangi su Maryam da Mama dake zaune k'ofar nasu d'akin.
Fitowarta taji tsakin da sukai mata. Mama ce ta kunna redio, kawai taji suna karanto wani littafi waishe KADDARA CE, abunda ya k'ara hargitsa ma Mama da Maryam kwakwalwa shine yadda sukaji wacce ta rubuta book d'in.
Salma duk da taji abunda yasa su firgita sai tayi shigewarta kitchen d'in ta nuna kamar bata ji ba. Duk da tasan book d'inta ne, to amma cikin gidan nasu babu wadda yasan tana rubuta book's daga ita sai y'an d'akinsu. Ita kanta bata san gidan redio na karanta book nata ba, amma taji dad'in haka.
A rud'e Maryam ta ce "wai baku ji wane suna naji ana kira bane?"
Dariyar rainin wayo Khadija ta saki tana cewa "naji mana, zai wuce wata ce can sabuwar marubuciya akai, dan naji wani book ma abokiyar hira ta karanta na marubuciyar yadda kaddara taso, duk ita tayi shi".
Maryam ta ce "to amma ya akai sunan marubuciyar yake kama dana wancar Salman"
Mama ta tab'e baki ta ce "ke kuwa Maryam da abun dariya kike, idan banda abunki ina Salma ina iya rubuta wani littafi, yarinyar da bata san komai ba, sai jakanci kwakwalwata babu komai ciki sai dusa"
Dariya suka saki tare Maryam da Khadija har suna tab'awa. Dai-dai lokacin da Salma ta fito daga kitchen d'in.
Duk taji abunda suke cewa, sai kawai ta girgiza kanta tana murmushi ta shige d'aki.
Tana shigewa Mama tabi bayanta da harara tana cewa "yo yama za'ai hakan ta kasance, ai da nayi kukan bak'in ciki kuwa, ai insha Allah haka zaki k'are a gantale Salma keda uwarki"
Bayan kwana biyu Mama na zaune kan gadonta taji Maryam ta tab'a ta, ba shiri ta tashi zaune tana kallonta.
Ganin kamar gulma ta kawo mata yasa ta tashi da sauri tana cewa "ke lafiya na ganki haka?, kamar wacce aka biyo tayi sata"
Maryam tama kasa zama, ta had'e hannayenta waje d'aya, sai kuma ta kama baki cike da tsananin mamakin abunda kunnuwanta suka jiyo mata a k'ofar d'akinsu Salma, sakin bakin tayi ta dafe kanta. Mama ganin cewa kamar fa Maryam d'in a kid'ime take yasa ta jawota ta zaunar da ita a kusa da ita.
A hankali Mama ta waiga k'ofar d'aki wai ko wani abu ne ya biyo Maryam d'in, daya sa ta zama Haka.
Ganin babu alamar komai yasa Mama cewa "wai minene naga fuskarki ta cika da mamaki?"
Sauk'e wani goran lumfashi Maryam tayi kamin ta ce "yo ba dole Mama ki ganni a haka ba, ashe duk littatafan da muke ji a redio da You tub channel, wadda abokiyar hira take Karantawa, ashe duk na Salma ne, mu duk d'aukarmu ai suna ne kawai yazo d'aya ba ita ba ce, ashe kuwa Salmar gidanmu ce ba wata ba"
A zabure Mama ta mik'e tana cewa "keeee Maryam bana son maganar banza kinji"
"Na rantse miki Mama ita ce"
"Ke ta gidan Ubanwa kika sani to?"
"Mama ki natsu dan Allah kaji"
Jawota Maryam tayi ta zaunar da ita tana cewa "Mama nazo shiga ban d'aki ne, kawai kamar ance na matsa k'ofar d'akin su Salma, sai naji Hajiya na cewa. "Salma ya kamata fa ki aje typing d'in nan haka nan, ki d'an huta, idan kika gama littafin nan, ki d'an huta, kamin ki d'ora wani"
Sai kuma na sake jin Salma ta ce "Hajiya ai hutu ba yanzu ba, tunda ina da lokaci yanzu so nake sai nayi littafi kusan goma ko biyar tukunna zan huta. Dan har gasar Hikayata nake so na shiga shekarar nan"
A haukace Mama ta mik'e tana cewa "kutumar Ubancan, ai ko bazai tab'a yiwuba wallahi, dole na d'au mataki, dole ne gobe naje garin Hayin fari, wajan Mlm, dole ne sai Salma ta nemi wannan basirar rubutu littafin ta rasa, dani suke zancan wallahi".
Maryam ta sake kamo hannun Mama tana cewa "Mama kiyi a hankali dan Allah, kar wani yaji, nasan dama zaki d'au mataki ai, shi yasa zuciyata ta kasa yarda ba Salma bace tunda naji sunanta, na ce ni ko saina binciko, ashe-ashe b'oye mana ake dankar mu gane",
"Hmm dole zasu b'oye mana, amma yanzun ma ba makara nayi ba wallahi".
*Gurbi K'aramar Hukumar Jibia Katsina State Nigeria*
Tagumin da Nanah ta zafga ne, tun fitar Saminu take jin wata fad'uwar gaba, Allah ya sani tunda Baba ya rasu take jin irin haka, kuma har yanzu bata sake ta ba.