Sashe 10
Sauyin Yanayi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Rayuwarta ta can baya take tunowa, da abunda ya maida ita muguwa, abunda yasa ta tsani Salman shida uwarsa, wacce tana kawosa duniya Momy tayi sanadiyar barinta duniya.
*Shekarun baya da suka wuce*
"Yanzu Didi Alhaji Bin Muhammad aure zaiyi?, kuma yasan ina bala'in sonsa, haba Didi kiyi wani abu mana"
Didi ta kalli Aysha dake kuka bil hakki da gaskiya. Duk da tasan Alhaji Bin Muhammad d'an uwa ne a garesu to amma tunda yaje ya d'akko bare yaya zatai dashi?, tunda yak'i y'ar uwarsa k'iri-k'iri ma ya nuna Hakan.
"Kinga ki kwantar da hankalinki, indai ina da rai to sai kin auri Alhaji, kima sama kanki ruwan sanyi"
Share hawayenta Aysha tayi, duk da taji dad'in maganar Dad'i tayi, to amma idan ta tuna dole fa su biyu zai aura koda ya amince da auran nata, sai taji zuciyarta tayi bak'i wani irin kishi na rufe mata ido.
Tashi tayi ta shiga d'akinta tana zarya so take ta samu mafitar ruguza auran Alhaji da waccar Hafsa d'in, ta tsane ta, ita ba y'ar gidan kowa ba, amma tana son bata matsala. Ji take ko wuk'a aka bata zata iya yanka Hafsa wallahi.
"My hayat ka tsaya mana tun d'azo nake fa faman gwala maka kira fa"
Tsayawa Alhaji yayi yana bin Aysha da kallo, shi harga Allah bata birgesa. Yanzu ma abunda ya kawosa gida yazo wajan Dad'i ne shine take masa maganar dole ya had'a auran Aysha ya auri mata biyu, idan ba haka ba kuma bata yafe masa ba. Sun kasance Dad'i ita ce Kakarsu kuma ita ce kad'ai ta rage masu a duniya daga shi har Ayshar, itama Iyayenta sun dad'e da rasuwa, a wajan Dad'i take zaune, kuma tun tana k'arama take dak'on son Bin Muhammad.
Ita kam Aysha dake kallonsa kamar zata cinyesa. Tun shigowarsa taji, ta sakko da gudu domin ganinsa kawai da jin muryarsa yana sata farin ciki.
Ganin ta tsaya ita bata ce masa komai ba yasa shi cewa "kefa nake jira ina inda zani, kuma waje ne mai mahimmanci a rayuwata"
Bakinta bata san sadda ya furta cewa "wajan wa zaka daya fi nan mahimmanci?"
"Hmm wajan My Hafsa mana"
Ya fad'i hakan yana shigewa Motarsa ya data yabar mata saurin k'urar motar a fuskarta.
Rufe idonta tayi tana jin wani tuk'uk'un bak'in ciki na tokare mata wuya.
Fad'awa tayi kan gadonta bayan ta shigo d'akinta da gudu. Tana fashewa da kuka.can Kuma saita tsayar da kukan tana tuno k'awarta kuma Aminiyata Asiya.
Da sauri tajawo wayarta ta dannama mata kira.
"K'awata yau kune da kanku kuke nemanmu?"
Bayan Asiya ta d'auki wayar ta ce haka.
"Kinga akwai matsala wallahi ina cikin damuwa ne"
"Subhanallahi mike faruwa ne haka?"
"Kinga maganar bata waya bace kawai kizo ina son ganinki"
Daga haka ta katse kiran.
Zuwa can da yamma Asiya tazo gidan. Zaune suke a d'akin Aysha. Asiya ta kama hannun Aysha bayan ta gama jin duk abunda ke damun k'awar tata.
Ta nisa ta ce "tabbas idan baki d'au mataki ba, haka za'ayi auran, ki koma y'ar kallo, ki koma yi masu shara da wanke-wanke"
A zabure Aysha ke kallon Asiya, cikin b'acin rai Aysha ta ce "ai wallahi hakanma bazai tab'a yiwuba ba, kin san wacece ni ai?"
"Na sani duk da haka saifa kin mik'e tsaye kin kwato ma kanki y'anci"
"Ban gane miye kike son cewa ba Asiya"
"Kawo kunnanki kaji"
Wani abu Asiya ta rad'a ma Aysha, wata dariya suka saki a tare had'e da tafa hannu. Aysha ta tashi tsaye cike da murna ta ce "kin tabbata idan muka je wajan Malamin nan zai min aiki Alhaji yaso ni kamar Hafsa?".
"Harma yafi na Hafsa, ai aiki yake kamar yankan wuk'a wallahi"
Duk wata hidimar biki cike da kuzari Aysha da k'awarta Asiya suke yinsa.
Hatta Dad'i ganinta saki ranta itama ta d'auka ko Alhaji ne ya fara nuna ma jikar tata kulawa.
Bayan an d'aura aure har yanzu basu je wajan Malamin ba, Asiya ta ce mata ta bari sai bayan bikin tukunna da kanta zataje mata kuma za'ayi aiki yadda ya dace.
Bayan biki da wata d'aya, Dad'i ta rasu, abunda ya dakatar da Aysha kenan zuwa wajan Malaminsu danta ce da kanta zataje Asiyar ta raka ta. Domin kuwa har yanzu babu abunda yake shiga tsakaninsu da Alhaji sai kallo kawai, amma a wajan Hafsat kuwa soyayya take ganin yana nuna mata sosai.
Aysha tasha kukan rashin Dad'i dan har saida aka kwantar da ita asibiti. Amma duk da haka mutuwar Dad'i bata sa Aysha saduda da duniya ba, domin tana samun sauk'i suka wuce wajan Malamin da Asiya ke fad'a mata.
Bayan Malamin ya koro masu jabin cewa Hafsa na d'auke da cikin Alhaji na tsawon sati uku. Yasa Aysha rud'ewa zuciyarta a bushe ta ce "Mlm babu yadda za'ai cikin ya zube?"
"Akwai yadda za'ai mana. Ga wannan maganin ki tabbatar kinsa mata shi a cikin abinci, sana wannan k'ullin kuma ki tabbatar Alhaji ya tsallaka sa, to komai sai abunda kika ce shine za'ai a gidan".
Sosai Aysha taji dad'in hakan, ta zube masa kud'i masu yawa wadda bata sanma iya adadin nawa taba Malamin ba.
Kamar yadda Mlm ya ce haka komai ta aiwatar dashi yadda ya dace.
Kuma an samu nasara Hafsa taci abincin, Alhaji zaije kiran Aysha ganin yadda Hafsa ke juye-juye tana rik'e da cikinta, ga jini sai zuba yake mata duk ya b'ata mata jiki. Suna zaune daga cin abinci yaga ta fara haka.
A rud'e ya nufi sama inda d'akin Aysha yake, a nan wajan ya tsallaka maganin, dama kuma tasan zaiyi wuya baizo sanar da ita ba, kawai saita yanke shawarar sasa a hanyar d'akinta.
Ai ko yana tsallaka maganin yaji kansa ya juya kamar wani abu ya shige masa tunani.
Yadda taga Alhaji ke mata magana cike da kulawa da soyayya tasan aikinta yayi, hak'arta ta cimma ruwa.
Itama cike da makirci ta sakko k'asa hannunta cikin na Alhaji.
D'aukar Hafsa sukai aka nufi Asibiti da ita.
A sadda Doctor ke sanar da Alhaji cewa cike ne da Hafsa na tsawon sati uku, cikin yaso zubewa ne, kuma kamar wani abu tasha shine ya kawo mata hakan, amma Allah ya tak'aita abun, domin cikin na nan bai fita ba.
A lokacin Aysha ji tayi kamar ta shak'e Doctor d'in nan. Tun lokacin duk wani makirci ta rink'a had'ama Hafsa. Hafsa tayi bak'i ta lalace ga cikin jikinta na matuk'ar bata wahala, haka ta d'aure ta cije take zaune a gidan. Yanzu ita da Alhaji sai dai kallo domin ko d'akin kwananta Aysha sai taga dama zata ce yaje ya kwana.
Babu irin abunda Aysha bata yi ba, domin dai cikin jikin Hafsa ya fita amma ina Allah yayi al'k'awarin sai yazo duniya.
A ranar da zata haihu a ranar Aysha ta koma wajan bokanta, a ranar aka had'a wani mugun asiri data dawo gida a bayan gidan ta binnesa. Asiri kuma shine wasu bak'ak'e aljanu aka turama Hafsa su shafi jariran data haifa, ita kuma su kasheta.
A dai-dai lokacin data binne asirin a dai-dai lokacin kuma nak'udar Hafsa ta tashi gadan-gadan, gashi ita d'aya ce a d'aki sai wahala take tun d'azo.
Koda Aysha ta shigo gidan tana iya jiyo ihun Hafsa da neman taimako da take, saima ta samu waje akan kujerun parlo tayi zamanta.
Hafsa tasha bak'ar wahala ta shafe awanni kamin Allah yasa ta haifo d'anta namiji, sai dai tana haihuwa bata ga abunda ma ta haifan ba, taji kamar an shake mata wuya tana shure-shure har rai yayi halinsa.
Sai da Aysha taji kukan jariri ya karad'e gaba d'aya gidan, ta daina jin matsin Hafsa, hakan yasa da gudu tayi cikin d'akin da Hafsa take.
Wani mugun farin ciki ne ya lullub'e Aysha ganinfa Hafsa an tafi, tafiyar da babu dawowa.
Cike da makirci, ta kira Alhaji tana wani irin kuka tana sanar dashi Hafsa ta haihu amma ita Allah yayi mata rasuwa.
Shima hankali a tashe duk da dama an kauda hankalinsa daga gareta kwata-kwata, amma mutuwar ta shigesa dan har kuka yayi a sadda yaga za'a fita da ita.
Tun lokacin ya dawo da soyayyar da yake ma Hafsa akan abunda ta haifa. Tun lokacin da Hafsa ta haihu Aysha taga namiji ne, nanma ji tayi kamar ta shak'e jaririn, amma wata zuciyar na gargad'inta da hakan, tunda ta tuna shima fa ta gama da rayuwarsa, zai taso ne kamar mahaukaci, ba mai cikakkar lafiya zai taso ba.
Aysha taso ta kauda hankalin Alhaji daga Salman tun yana k'arami amma hakan ya gagara. Dole tasa ta yada makaman yak'inta, ta rink'a jawo yaron a jiki kamar wacce take sonsa Dan Allah. Shi kuma Alhaji ganin yadda take basa kulawa yasa ya k'ara jin sonta a ransa. Dan har idan zatai wani abu ko tana son amsar kud'i a hannun Alhajin sai kiga tana k'ara ririta Salman kamar ta maida sa ciki.
Tunda Salman ya tashi ya bud'e ido ya gansa tare da Momy Aysha duk zatonsa ita ce ta haifesa. Sai dai ita da kanta ta fad'a masa cewa Mamarsa ta rasu wajan haihuwarsa. Domin Allah ya sani ta tsani yaron kamar yadda ta tsani uwarsa. Koda rab'arta yayi ji take kamar ta shak'e sa ya mutu haka nan take danne zuciyarta tana nuna masa soyayyar k'arya.
Tun yana shekara goma, abunda Momy ta masa tun yana ciki ya fara tashi. Haka kawai sai aga yaro ya fad'i kamar mai farfad'iya, yayita fashe-fashen abubuwa, duk da k'ananun shekarunsa idan mutane sunzo rik'esa duk sai ya watsar dasu, ko kuma ya kama mutum saiya ji masa ciwo ko ya sumar da mutum.
Alhaji ya shiga tashin hankali, ba inda baije ba domin neman magani har k'asar waje ansha fitar da Salman, amma abun yak'i sakinsa. Momy kuwa ita tak'i bari aje wajan Malaman Addini bare har a gano miye yake damun Salman d'in na ainafi.
*Shekarun baya da suka wuce*
"Yanzu Didi Alhaji Bin Muhammad aure zaiyi?, kuma yasan ina bala'in sonsa, haba Didi kiyi wani abu mana"
Didi ta kalli Aysha dake kuka bil hakki da gaskiya. Duk da tasan Alhaji Bin Muhammad d'an uwa ne a garesu to amma tunda yaje ya d'akko bare yaya zatai dashi?, tunda yak'i y'ar uwarsa k'iri-k'iri ma ya nuna Hakan.
"Kinga ki kwantar da hankalinki, indai ina da rai to sai kin auri Alhaji, kima sama kanki ruwan sanyi"
Share hawayenta Aysha tayi, duk da taji dad'in maganar Dad'i tayi, to amma idan ta tuna dole fa su biyu zai aura koda ya amince da auran nata, sai taji zuciyarta tayi bak'i wani irin kishi na rufe mata ido.
Tashi tayi ta shiga d'akinta tana zarya so take ta samu mafitar ruguza auran Alhaji da waccar Hafsa d'in, ta tsane ta, ita ba y'ar gidan kowa ba, amma tana son bata matsala. Ji take ko wuk'a aka bata zata iya yanka Hafsa wallahi.
"My hayat ka tsaya mana tun d'azo nake fa faman gwala maka kira fa"
Tsayawa Alhaji yayi yana bin Aysha da kallo, shi harga Allah bata birgesa. Yanzu ma abunda ya kawosa gida yazo wajan Dad'i ne shine take masa maganar dole ya had'a auran Aysha ya auri mata biyu, idan ba haka ba kuma bata yafe masa ba. Sun kasance Dad'i ita ce Kakarsu kuma ita ce kad'ai ta rage masu a duniya daga shi har Ayshar, itama Iyayenta sun dad'e da rasuwa, a wajan Dad'i take zaune, kuma tun tana k'arama take dak'on son Bin Muhammad.
Ita kam Aysha dake kallonsa kamar zata cinyesa. Tun shigowarsa taji, ta sakko da gudu domin ganinsa kawai da jin muryarsa yana sata farin ciki.
Ganin ta tsaya ita bata ce masa komai ba yasa shi cewa "kefa nake jira ina inda zani, kuma waje ne mai mahimmanci a rayuwata"
Bakinta bata san sadda ya furta cewa "wajan wa zaka daya fi nan mahimmanci?"
"Hmm wajan My Hafsa mana"
Ya fad'i hakan yana shigewa Motarsa ya data yabar mata saurin k'urar motar a fuskarta.
Rufe idonta tayi tana jin wani tuk'uk'un bak'in ciki na tokare mata wuya.
Fad'awa tayi kan gadonta bayan ta shigo d'akinta da gudu. Tana fashewa da kuka.can Kuma saita tsayar da kukan tana tuno k'awarta kuma Aminiyata Asiya.
Da sauri tajawo wayarta ta dannama mata kira.
"K'awata yau kune da kanku kuke nemanmu?"
Bayan Asiya ta d'auki wayar ta ce haka.
"Kinga akwai matsala wallahi ina cikin damuwa ne"
"Subhanallahi mike faruwa ne haka?"
"Kinga maganar bata waya bace kawai kizo ina son ganinki"
Daga haka ta katse kiran.
Zuwa can da yamma Asiya tazo gidan. Zaune suke a d'akin Aysha. Asiya ta kama hannun Aysha bayan ta gama jin duk abunda ke damun k'awar tata.
Ta nisa ta ce "tabbas idan baki d'au mataki ba, haka za'ayi auran, ki koma y'ar kallo, ki koma yi masu shara da wanke-wanke"
A zabure Aysha ke kallon Asiya, cikin b'acin rai Aysha ta ce "ai wallahi hakanma bazai tab'a yiwuba ba, kin san wacece ni ai?"
"Na sani duk da haka saifa kin mik'e tsaye kin kwato ma kanki y'anci"
"Ban gane miye kike son cewa ba Asiya"
"Kawo kunnanki kaji"
Wani abu Asiya ta rad'a ma Aysha, wata dariya suka saki a tare had'e da tafa hannu. Aysha ta tashi tsaye cike da murna ta ce "kin tabbata idan muka je wajan Malamin nan zai min aiki Alhaji yaso ni kamar Hafsa?".
"Harma yafi na Hafsa, ai aiki yake kamar yankan wuk'a wallahi"
Duk wata hidimar biki cike da kuzari Aysha da k'awarta Asiya suke yinsa.
Hatta Dad'i ganinta saki ranta itama ta d'auka ko Alhaji ne ya fara nuna ma jikar tata kulawa.
Bayan an d'aura aure har yanzu basu je wajan Malamin ba, Asiya ta ce mata ta bari sai bayan bikin tukunna da kanta zataje mata kuma za'ayi aiki yadda ya dace.
Bayan biki da wata d'aya, Dad'i ta rasu, abunda ya dakatar da Aysha kenan zuwa wajan Malaminsu danta ce da kanta zataje Asiyar ta raka ta. Domin kuwa har yanzu babu abunda yake shiga tsakaninsu da Alhaji sai kallo kawai, amma a wajan Hafsat kuwa soyayya take ganin yana nuna mata sosai.
Aysha tasha kukan rashin Dad'i dan har saida aka kwantar da ita asibiti. Amma duk da haka mutuwar Dad'i bata sa Aysha saduda da duniya ba, domin tana samun sauk'i suka wuce wajan Malamin da Asiya ke fad'a mata.
Bayan Malamin ya koro masu jabin cewa Hafsa na d'auke da cikin Alhaji na tsawon sati uku. Yasa Aysha rud'ewa zuciyarta a bushe ta ce "Mlm babu yadda za'ai cikin ya zube?"
"Akwai yadda za'ai mana. Ga wannan maganin ki tabbatar kinsa mata shi a cikin abinci, sana wannan k'ullin kuma ki tabbatar Alhaji ya tsallaka sa, to komai sai abunda kika ce shine za'ai a gidan".
Sosai Aysha taji dad'in hakan, ta zube masa kud'i masu yawa wadda bata sanma iya adadin nawa taba Malamin ba.
Kamar yadda Mlm ya ce haka komai ta aiwatar dashi yadda ya dace.
Kuma an samu nasara Hafsa taci abincin, Alhaji zaije kiran Aysha ganin yadda Hafsa ke juye-juye tana rik'e da cikinta, ga jini sai zuba yake mata duk ya b'ata mata jiki. Suna zaune daga cin abinci yaga ta fara haka.
A rud'e ya nufi sama inda d'akin Aysha yake, a nan wajan ya tsallaka maganin, dama kuma tasan zaiyi wuya baizo sanar da ita ba, kawai saita yanke shawarar sasa a hanyar d'akinta.
Ai ko yana tsallaka maganin yaji kansa ya juya kamar wani abu ya shige masa tunani.
Yadda taga Alhaji ke mata magana cike da kulawa da soyayya tasan aikinta yayi, hak'arta ta cimma ruwa.
Itama cike da makirci ta sakko k'asa hannunta cikin na Alhaji.
D'aukar Hafsa sukai aka nufi Asibiti da ita.
A sadda Doctor ke sanar da Alhaji cewa cike ne da Hafsa na tsawon sati uku, cikin yaso zubewa ne, kuma kamar wani abu tasha shine ya kawo mata hakan, amma Allah ya tak'aita abun, domin cikin na nan bai fita ba.
A lokacin Aysha ji tayi kamar ta shak'e Doctor d'in nan. Tun lokacin duk wani makirci ta rink'a had'ama Hafsa. Hafsa tayi bak'i ta lalace ga cikin jikinta na matuk'ar bata wahala, haka ta d'aure ta cije take zaune a gidan. Yanzu ita da Alhaji sai dai kallo domin ko d'akin kwananta Aysha sai taga dama zata ce yaje ya kwana.
Babu irin abunda Aysha bata yi ba, domin dai cikin jikin Hafsa ya fita amma ina Allah yayi al'k'awarin sai yazo duniya.
A ranar da zata haihu a ranar Aysha ta koma wajan bokanta, a ranar aka had'a wani mugun asiri data dawo gida a bayan gidan ta binnesa. Asiri kuma shine wasu bak'ak'e aljanu aka turama Hafsa su shafi jariran data haifa, ita kuma su kasheta.
A dai-dai lokacin data binne asirin a dai-dai lokacin kuma nak'udar Hafsa ta tashi gadan-gadan, gashi ita d'aya ce a d'aki sai wahala take tun d'azo.
Koda Aysha ta shigo gidan tana iya jiyo ihun Hafsa da neman taimako da take, saima ta samu waje akan kujerun parlo tayi zamanta.
Hafsa tasha bak'ar wahala ta shafe awanni kamin Allah yasa ta haifo d'anta namiji, sai dai tana haihuwa bata ga abunda ma ta haifan ba, taji kamar an shake mata wuya tana shure-shure har rai yayi halinsa.
Sai da Aysha taji kukan jariri ya karad'e gaba d'aya gidan, ta daina jin matsin Hafsa, hakan yasa da gudu tayi cikin d'akin da Hafsa take.
Wani mugun farin ciki ne ya lullub'e Aysha ganinfa Hafsa an tafi, tafiyar da babu dawowa.
Cike da makirci, ta kira Alhaji tana wani irin kuka tana sanar dashi Hafsa ta haihu amma ita Allah yayi mata rasuwa.
Shima hankali a tashe duk da dama an kauda hankalinsa daga gareta kwata-kwata, amma mutuwar ta shigesa dan har kuka yayi a sadda yaga za'a fita da ita.
Tun lokacin ya dawo da soyayyar da yake ma Hafsa akan abunda ta haifa. Tun lokacin da Hafsa ta haihu Aysha taga namiji ne, nanma ji tayi kamar ta shak'e jaririn, amma wata zuciyar na gargad'inta da hakan, tunda ta tuna shima fa ta gama da rayuwarsa, zai taso ne kamar mahaukaci, ba mai cikakkar lafiya zai taso ba.
Aysha taso ta kauda hankalin Alhaji daga Salman tun yana k'arami amma hakan ya gagara. Dole tasa ta yada makaman yak'inta, ta rink'a jawo yaron a jiki kamar wacce take sonsa Dan Allah. Shi kuma Alhaji ganin yadda take basa kulawa yasa ya k'ara jin sonta a ransa. Dan har idan zatai wani abu ko tana son amsar kud'i a hannun Alhajin sai kiga tana k'ara ririta Salman kamar ta maida sa ciki.
Tunda Salman ya tashi ya bud'e ido ya gansa tare da Momy Aysha duk zatonsa ita ce ta haifesa. Sai dai ita da kanta ta fad'a masa cewa Mamarsa ta rasu wajan haihuwarsa. Domin Allah ya sani ta tsani yaron kamar yadda ta tsani uwarsa. Koda rab'arta yayi ji take kamar ta shak'e sa ya mutu haka nan take danne zuciyarta tana nuna masa soyayyar k'arya.
Tun yana shekara goma, abunda Momy ta masa tun yana ciki ya fara tashi. Haka kawai sai aga yaro ya fad'i kamar mai farfad'iya, yayita fashe-fashen abubuwa, duk da k'ananun shekarunsa idan mutane sunzo rik'esa duk sai ya watsar dasu, ko kuma ya kama mutum saiya ji masa ciwo ko ya sumar da mutum.
Alhaji ya shiga tashin hankali, ba inda baije ba domin neman magani har k'asar waje ansha fitar da Salman, amma abun yak'i sakinsa. Momy kuwa ita tak'i bari aje wajan Malaman Addini bare har a gano miye yake damun Salman d'in na ainafi.