Sashe 5
Sanadin Soyayyar Shan Minti Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Zaunawa Mama tayi sannan tace. "Bintu mai zance? Aje ayi Allah yasa a gama lafiya." Tana gama fadin haka ta tashi ai take Mama ta wanke jiki ta fadi kasa tana amain jini, da gudu sukayi kanta suna kiran suna ta.
Daukarta Yaya yayi suka wuce asibiti, gado aka bata sannan aka sama mata drip dan temper dinta ce ta hau sannan Yaya ya cike takadar da za'ayi man aiki, sai wajen mangrid Mama ta farko haka ta matsa aka sallamaita ni kuma aka barni da Dija, duk da nima na farko amman ba sosai nike yin magana ba.
Washe gari da safe Doctor ya shigo ya duba jikina, hana bani komai yayi yace 10am za'a shiga dani ayi man wankin ciki, sanann ya tafi wajen 9 na safe Yaiyane duk sunzo sun cika asibitin suna duba lafiya, goma nayi aka zo tafiya dani za'a yi man aiki haka na bar yan'uwana suna kuka, dan bansan wani hali nike ba nidai naga suna kuka.
Wajen Mama kuwa tunda ta koma gida take kuka, dan tanajin ciwon abunda ya faru dani sosai, dan ma anbar mata Yaya Amina a gida ita ta kama kwantar mata da hankali tana gaya mata maganganu masu dadi wanda zai sa taji sanyi a zuciyar ta.
Kallon Yaya Amina tayi sannan tace. "Amina bakisan abunda nike ji ba shiyasa, amman na yafema Khadija Allah yasa ta dauki darasin duniya, daman ita duniya haka take tafi bagaruwa jifa, na yafe mata Allah yasa iyakar kaddararta kenan kinga ta biye ma san zuciya ta lalata rayuwar ta a banza."
Haka aka kirasu waya aka gaya mata anshiga dani dan yi man aiki, tayi man fatan fitowa lafiya.
*Allah Sarki, rayuwar Khadija da ban tausayi sosai wallahi nan bakuji komai ba😭, nima lokacin da take gaya man nayi kuka har na godema Allah, fatan dai Allah ya kara tsaremana imanin mu Amin, ya karemu da aikata aikin da na sani*
Share
Comment
And
Vote
[12/31/2020, 11:02 PM] Jamila writar: *A SANADIN SOYAYYAR MINTI*
_na ɓata rayuwata😭_
Na
*Jameey yar'mutan kankia ce❣️*
*MANAZARTA WRITERS ASSOC📚🖊️*
https://www.facebook.com/107980080946102?referrer=whatsa
_________________
https://chat.whatsapp.com/BS0N4RFqbe6LFqlXZZ9vxD
*Wannan page din nakane Yayana na kaina Muhammad Kareem MK, Allah ya kara daukaka da lafiya Amin*
*Gaisuwa ban girma gareki Maryam Majitapha lawal My Maryam ina maki fatan alkhairy ta wajena*
_Haba my real fans, ya ban ganin ruwan vote and comment a wattpad😢, pls show me ur love a wattpad mana😍_
*Wattpad JameelarhSadiq*
Page 5⏩6
Kallon Mama Yaya Amina tayi sanann ta dafa ta tace. "Mama dan Allah ki kwantar da hankalin ki insha Allah za'a shiga lafiya kuma a fito da Auta lafiya." Kallonta Mama tayi sannan tace. "Amina ba wannan ke tada man hankali ba, yanzun ace Auta za'ayi ma wankin ciki? Karki manta Yarinya ce fa, bata wace shekara sha takwas ba, ina lisafi wata mai kamawa take cika shekara ta sha tara, amman har za'ayi mata wanki ciki, idan za'ayi mata aure mai za'a cema wanda zata aura? Ce mashi zamuyi tayi cikin shegen? Ko kuma muce mashi har wankin ciki an taɓa yi mata Amina."?
Numfasawa Yaya Amina tayi sannan tace. "Hakane Mama amman nasan na Allah basu kyarewa mudai muyi mata fatan samun miji na gari wanda zai rike ta amana ba tare da yayi mata gori ba watan watarana."
Dariya Mama tayi sannan tace. "Ai ba wanda zai iya aurenta Amina, dan haka tana samun sauki wallahi zan aura mata Alhaji Salahu, fatan dai Allah yasa a dace."
Cikin ruɗewa Yaya Amina tace. "Haba Mama ya kikeso ki bada gudumuwa wajen lalacewar rayuwar Auta, a rasa wanda za'a daura ma Auta sai Alhaji Salahu koni ya haifeni balle Auta, kuma matan shi uku dan ma ta hudu ta rasu, har ƙawa nike da ita a gidan fa."
Wurga mata harara Mama tayi sannan tace. "Wallahi ba wanda ya isa ya hanani aura ma Khadija Salahu , idan ba shi ba wa zai aureta? Yarinyar da ta zubdar da mutuncinta a waje ai Alhaji Salahu rufa mata asiri zaiyi ya aureta."
Cikin kuka Yaya Amina tace. "Dan Auta tayi ciki shine yasa zakiyi mata haka? Maiyasa kika kasa yarda da kaddara ne Mama? Mama kinsan kaddara tana cikin cikon imani amman ke kin ki yarda da hakan, yanzun baki gudun tace zata gudu tabar maki gidan? Dan nayi imani ga Allah Auta ba zata yarda da auren wannan mutun min ba, Mama karki ce nayi maki rashin kunya a matsayinki ba mahaifiya ta, amman ko nice kika ce na auri shi wallahi ba zan aureshi balle Auta da take budurwar wannan zamanin, kum... Tas Mama ta wanke Yaya Amina da mari tana cewa. "Dan ubanki har kin isa ki hanani abunda nayi niya? Ko kin fini son Khadija ne? Ai nasa nice na dauki cikinta nayi rainonshi har na tsawan wata tara da kwana tara sannan na haifeta ko? Kuma na bata nonona tasha, ai gata nike nema mata da zaki kama challenge dina dan nace zan aura mata Salahu, yanzun ma zani nayi mashi maganar ta tana gama jini za'ayi bikinsu ko kuna so ko baku so, dan nasan bakinku daya da yan'uwanki to ku sani ba wanda ya isa ya hanani wallahi."
Mama na gama fadin haka ta dauki hijab dinta ta tafi gidan Alhaji Salahu dan yin magana dashi, haka ta bar Yaya Amina zaune tana kuka ganin kukan baiyi mata maganin komai ta shiga kitchen ta dafa abinci tasa a cooler sannan ta fito ta shiga motarta ta wuce asibiti , lokacin da ta shigo hospital din aka fito dani angama yi man wankin cikin.
Fitowa tayi da abincin ta nufo wajen su, duk da suma sun danyi kuka amman ba sosai ba dan Yaya Jamilu hakuri ya basu sosai ya kuma kwantar masu da hankali shiyasa sukayi shiru kallo daya Yaya Jamilu yayi mata ya ganne akwai matsala dan tasha kuka sosai, kunsan ace babban uba daman Babana ya rasu ne tun ina cikin ciki bansan Babana ba, shine dai Ubanmu mu dukanmu daman duk matane shi kadaine babba, baice komai ba tana ijiye abincin yace tazo yana son ganinta a waje, aiko suka fito suka samu waje su dukansu akabar Dija ta cigaba da kula dani.
Office din Doctor Dikko suka je suka zauna sannan Yaya Jamilu yace. "Amina gaya man maike faruwa ya jikin Mama ko jikin tane har yanzun."!? Cikin tsoro yayi mata maganar dan daman hankalinshi ba kwance yake ba yana tunanin halin da Mama take ciki.
Share hawayenta Yaya Amina tayi sannan tace. "Yaya wallahi Mama tana son ta ɓata rayuwar Auta duk da ta kasance uwa a gareta, wallahi bansan yaushe Mama ta chanza hali ba Yaya." Ta karasa maganar cikin kuka, kallonta Yaya Fatima tayi sannan tace. "Amina kiyi mana bayani mu fahimta kin yi mana magana a dabarbarce bamu gane ina maganarki ta dosa ba."
Shidai Yaya kasa cewa komai yayi yana jiran yaji abunda Yaya Amina zatace, balle Yaya Aisha take kuka har yanzun dan ta kasa yafema kanta akan abunda sukayi man ita da Mama, cewa tayi. "Yaya Amina dan Allah ki gaya mana abunda ke faruwa da Mama wallahi hankalina ya tashi sosai."
Cikin kuka tace. "Mama tace ana sallamo Auta aure zatayi mata, kuma da Alhaji Salahu ba yanda banyi ba akan tayi hakuri taƙi daga karshe ma har marina tayi kuma tace ba wanda ya isa ya hanata aurar da Auta ba."
Tashi Yaya Jamilu yayi yana girgiza kai sanann yace. "Ina wallahi ba zamu yarda ba, mu zuba ido muna kallo Mama ta ɓata ma Auta future ba, ya kamata Mama ta gane wannan fa kadddarace wanda ba wanda ya isa ya kauce mata harta ku masu aure dan ba'a fatan haka fisabillahi, kuma ta rasa wa zata aura mata sai wannan tsohon wanda baisan darajar dan'adam ba, kuma kullun gidanshi sai matanshi sunyi fada yanzun haka yaranshi talatin a duniya ai ko sa'ana yayi ma Auta zufa a aure yanzun ko nike da shekara tallatin biyar balle Alhaji Salahu da yayi shekara saba'in yana hanyar mutuwa ku bari naje nayi magana da ita."
Su kuwa kasa cewa komai sukayi dan lamarin ya girmi tunaninsu, haka suka fito tare suka tafi gida wajen Mama dan Yaya Fatima cewa tayi su tafi su dukansu.
Niko cikin ikon Allah na farfado har nayi brush naci abincin da Yaya Amina ta kawo, an bani magani nasha, nidai ba bacci nike ji ba balle nayi, zaunawa nayi na jingina da gado ina tunani da tarin nadamar abunda na aikata, Dija ce tace. "Aunty Khady dan Allah kiyi hakuri, ki dauki wannan abun a matsayin kaddaraki duk da sakakinki a ciki ammn haka Allah ya kaddara kuma ba yanda zakiyi inba ki yarda da kaddara ki kuma godema Allah."
Mai neman kuka angaya mashi mutuwa, aiko na fashe da kuka ina kallonta na girgiza nace. "Dija dan Allah ki daina bani hakuri ki barni nayi kuka ko naji saukin abunda nikeji a cikin zuciya ta, Dija nasan duk abunda ke faruwa dani cikin jikina ya zube sannan anyi man wankin ciki kuma babu tabbacin zansake haihuwa a duniya, ba dole nayi kuka ba Dija? Ni yanzun joya za'a ringa kirana ko? Wanda bata haihuwa bani ganin jinina a dorajaran kasa? Idan na mutu bani da maiyi man Addu'a a koda yaushe sai yan'uwana kenan? Dan Allah ki daina bani hakuri ki barni nayi kukan na rokeki wannan alfarmar."
Shiru itama Dija tayi ta dukar da kanta kasa tana aikin kuka dan maganganuna sunyi mata tasiri sosai a zuciya, tabbas banda maiyi man addu'a ko yaiyaine ba kullun ne zasuyi man ba, inba sun tuna dani ba, amman haka Allah yaso muna cikin kukanmu sai Doctor Dikko ya shigo lailashemu yayi sannan yayi ma Dija fada akan tana daina wannan kukan hakuri ya dace ta bani,ƙara duba lafiyata yayi ya tambayeni idan yake man ciwo sannan ya tafi cikin tausayi na.
Daukarta Yaya yayi suka wuce asibiti, gado aka bata sannan aka sama mata drip dan temper dinta ce ta hau sannan Yaya ya cike takadar da za'ayi man aiki, sai wajen mangrid Mama ta farko haka ta matsa aka sallamaita ni kuma aka barni da Dija, duk da nima na farko amman ba sosai nike yin magana ba.
Washe gari da safe Doctor ya shigo ya duba jikina, hana bani komai yayi yace 10am za'a shiga dani ayi man wankin ciki, sanann ya tafi wajen 9 na safe Yaiyane duk sunzo sun cika asibitin suna duba lafiya, goma nayi aka zo tafiya dani za'a yi man aiki haka na bar yan'uwana suna kuka, dan bansan wani hali nike ba nidai naga suna kuka.
Wajen Mama kuwa tunda ta koma gida take kuka, dan tanajin ciwon abunda ya faru dani sosai, dan ma anbar mata Yaya Amina a gida ita ta kama kwantar mata da hankali tana gaya mata maganganu masu dadi wanda zai sa taji sanyi a zuciyar ta.
Kallon Yaya Amina tayi sannan tace. "Amina bakisan abunda nike ji ba shiyasa, amman na yafema Khadija Allah yasa ta dauki darasin duniya, daman ita duniya haka take tafi bagaruwa jifa, na yafe mata Allah yasa iyakar kaddararta kenan kinga ta biye ma san zuciya ta lalata rayuwar ta a banza."
Haka aka kirasu waya aka gaya mata anshiga dani dan yi man aiki, tayi man fatan fitowa lafiya.
*Allah Sarki, rayuwar Khadija da ban tausayi sosai wallahi nan bakuji komai ba😭, nima lokacin da take gaya man nayi kuka har na godema Allah, fatan dai Allah ya kara tsaremana imanin mu Amin, ya karemu da aikata aikin da na sani*
Share
Comment
And
Vote
[12/31/2020, 11:02 PM] Jamila writar: *A SANADIN SOYAYYAR MINTI*
_na ɓata rayuwata😭_
Na
*Jameey yar'mutan kankia ce❣️*
*MANAZARTA WRITERS ASSOC📚🖊️*
https://www.facebook.com/107980080946102?referrer=whatsa
_________________
https://chat.whatsapp.com/BS0N4RFqbe6LFqlXZZ9vxD
*Wannan page din nakane Yayana na kaina Muhammad Kareem MK, Allah ya kara daukaka da lafiya Amin*
*Gaisuwa ban girma gareki Maryam Majitapha lawal My Maryam ina maki fatan alkhairy ta wajena*
_Haba my real fans, ya ban ganin ruwan vote and comment a wattpad😢, pls show me ur love a wattpad mana😍_
*Wattpad JameelarhSadiq*
Page 5⏩6
Kallon Mama Yaya Amina tayi sanann ta dafa ta tace. "Mama dan Allah ki kwantar da hankalin ki insha Allah za'a shiga lafiya kuma a fito da Auta lafiya." Kallonta Mama tayi sannan tace. "Amina ba wannan ke tada man hankali ba, yanzun ace Auta za'ayi ma wankin ciki? Karki manta Yarinya ce fa, bata wace shekara sha takwas ba, ina lisafi wata mai kamawa take cika shekara ta sha tara, amman har za'ayi mata wanki ciki, idan za'ayi mata aure mai za'a cema wanda zata aura? Ce mashi zamuyi tayi cikin shegen? Ko kuma muce mashi har wankin ciki an taɓa yi mata Amina."?
Numfasawa Yaya Amina tayi sannan tace. "Hakane Mama amman nasan na Allah basu kyarewa mudai muyi mata fatan samun miji na gari wanda zai rike ta amana ba tare da yayi mata gori ba watan watarana."
Dariya Mama tayi sannan tace. "Ai ba wanda zai iya aurenta Amina, dan haka tana samun sauki wallahi zan aura mata Alhaji Salahu, fatan dai Allah yasa a dace."
Cikin ruɗewa Yaya Amina tace. "Haba Mama ya kikeso ki bada gudumuwa wajen lalacewar rayuwar Auta, a rasa wanda za'a daura ma Auta sai Alhaji Salahu koni ya haifeni balle Auta, kuma matan shi uku dan ma ta hudu ta rasu, har ƙawa nike da ita a gidan fa."
Wurga mata harara Mama tayi sannan tace. "Wallahi ba wanda ya isa ya hanani aura ma Khadija Salahu , idan ba shi ba wa zai aureta? Yarinyar da ta zubdar da mutuncinta a waje ai Alhaji Salahu rufa mata asiri zaiyi ya aureta."
Cikin kuka Yaya Amina tace. "Dan Auta tayi ciki shine yasa zakiyi mata haka? Maiyasa kika kasa yarda da kaddara ne Mama? Mama kinsan kaddara tana cikin cikon imani amman ke kin ki yarda da hakan, yanzun baki gudun tace zata gudu tabar maki gidan? Dan nayi imani ga Allah Auta ba zata yarda da auren wannan mutun min ba, Mama karki ce nayi maki rashin kunya a matsayinki ba mahaifiya ta, amman ko nice kika ce na auri shi wallahi ba zan aureshi balle Auta da take budurwar wannan zamanin, kum... Tas Mama ta wanke Yaya Amina da mari tana cewa. "Dan ubanki har kin isa ki hanani abunda nayi niya? Ko kin fini son Khadija ne? Ai nasa nice na dauki cikinta nayi rainonshi har na tsawan wata tara da kwana tara sannan na haifeta ko? Kuma na bata nonona tasha, ai gata nike nema mata da zaki kama challenge dina dan nace zan aura mata Salahu, yanzun ma zani nayi mashi maganar ta tana gama jini za'ayi bikinsu ko kuna so ko baku so, dan nasan bakinku daya da yan'uwanki to ku sani ba wanda ya isa ya hanani wallahi."
Mama na gama fadin haka ta dauki hijab dinta ta tafi gidan Alhaji Salahu dan yin magana dashi, haka ta bar Yaya Amina zaune tana kuka ganin kukan baiyi mata maganin komai ta shiga kitchen ta dafa abinci tasa a cooler sannan ta fito ta shiga motarta ta wuce asibiti , lokacin da ta shigo hospital din aka fito dani angama yi man wankin cikin.
Fitowa tayi da abincin ta nufo wajen su, duk da suma sun danyi kuka amman ba sosai ba dan Yaya Jamilu hakuri ya basu sosai ya kuma kwantar masu da hankali shiyasa sukayi shiru kallo daya Yaya Jamilu yayi mata ya ganne akwai matsala dan tasha kuka sosai, kunsan ace babban uba daman Babana ya rasu ne tun ina cikin ciki bansan Babana ba, shine dai Ubanmu mu dukanmu daman duk matane shi kadaine babba, baice komai ba tana ijiye abincin yace tazo yana son ganinta a waje, aiko suka fito suka samu waje su dukansu akabar Dija ta cigaba da kula dani.
Office din Doctor Dikko suka je suka zauna sannan Yaya Jamilu yace. "Amina gaya man maike faruwa ya jikin Mama ko jikin tane har yanzun."!? Cikin tsoro yayi mata maganar dan daman hankalinshi ba kwance yake ba yana tunanin halin da Mama take ciki.
Share hawayenta Yaya Amina tayi sannan tace. "Yaya wallahi Mama tana son ta ɓata rayuwar Auta duk da ta kasance uwa a gareta, wallahi bansan yaushe Mama ta chanza hali ba Yaya." Ta karasa maganar cikin kuka, kallonta Yaya Fatima tayi sannan tace. "Amina kiyi mana bayani mu fahimta kin yi mana magana a dabarbarce bamu gane ina maganarki ta dosa ba."
Shidai Yaya kasa cewa komai yayi yana jiran yaji abunda Yaya Amina zatace, balle Yaya Aisha take kuka har yanzun dan ta kasa yafema kanta akan abunda sukayi man ita da Mama, cewa tayi. "Yaya Amina dan Allah ki gaya mana abunda ke faruwa da Mama wallahi hankalina ya tashi sosai."
Cikin kuka tace. "Mama tace ana sallamo Auta aure zatayi mata, kuma da Alhaji Salahu ba yanda banyi ba akan tayi hakuri taƙi daga karshe ma har marina tayi kuma tace ba wanda ya isa ya hanata aurar da Auta ba."
Tashi Yaya Jamilu yayi yana girgiza kai sanann yace. "Ina wallahi ba zamu yarda ba, mu zuba ido muna kallo Mama ta ɓata ma Auta future ba, ya kamata Mama ta gane wannan fa kadddarace wanda ba wanda ya isa ya kauce mata harta ku masu aure dan ba'a fatan haka fisabillahi, kuma ta rasa wa zata aura mata sai wannan tsohon wanda baisan darajar dan'adam ba, kuma kullun gidanshi sai matanshi sunyi fada yanzun haka yaranshi talatin a duniya ai ko sa'ana yayi ma Auta zufa a aure yanzun ko nike da shekara tallatin biyar balle Alhaji Salahu da yayi shekara saba'in yana hanyar mutuwa ku bari naje nayi magana da ita."
Su kuwa kasa cewa komai sukayi dan lamarin ya girmi tunaninsu, haka suka fito tare suka tafi gida wajen Mama dan Yaya Fatima cewa tayi su tafi su dukansu.
Niko cikin ikon Allah na farfado har nayi brush naci abincin da Yaya Amina ta kawo, an bani magani nasha, nidai ba bacci nike ji ba balle nayi, zaunawa nayi na jingina da gado ina tunani da tarin nadamar abunda na aikata, Dija ce tace. "Aunty Khady dan Allah kiyi hakuri, ki dauki wannan abun a matsayin kaddaraki duk da sakakinki a ciki ammn haka Allah ya kaddara kuma ba yanda zakiyi inba ki yarda da kaddara ki kuma godema Allah."
Mai neman kuka angaya mashi mutuwa, aiko na fashe da kuka ina kallonta na girgiza nace. "Dija dan Allah ki daina bani hakuri ki barni nayi kuka ko naji saukin abunda nikeji a cikin zuciya ta, Dija nasan duk abunda ke faruwa dani cikin jikina ya zube sannan anyi man wankin ciki kuma babu tabbacin zansake haihuwa a duniya, ba dole nayi kuka ba Dija? Ni yanzun joya za'a ringa kirana ko? Wanda bata haihuwa bani ganin jinina a dorajaran kasa? Idan na mutu bani da maiyi man Addu'a a koda yaushe sai yan'uwana kenan? Dan Allah ki daina bani hakuri ki barni nayi kukan na rokeki wannan alfarmar."
Shiru itama Dija tayi ta dukar da kanta kasa tana aikin kuka dan maganganuna sunyi mata tasiri sosai a zuciya, tabbas banda maiyi man addu'a ko yaiyaine ba kullun ne zasuyi man ba, inba sun tuna dani ba, amman haka Allah yaso muna cikin kukanmu sai Doctor Dikko ya shigo lailashemu yayi sannan yayi ma Dija fada akan tana daina wannan kukan hakuri ya dace ta bani,ƙara duba lafiyata yayi ya tambayeni idan yake man ciwo sannan ya tafi cikin tausayi na.