Sashe 3
Rayuwar Rayhana Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Ajiyar zuciya ta sake yi ta kasa ce da Ibraheem komai, la shakka ta yi kuskure, anya ma ita ce? Ta maida kanta jahila haka? Ina zurfin tunaninta ina kwalayen iliminta? Ta maida kanta irin matan bakin- kasuwa?
Nadama ce take shigarta sosai, a kasalce ta ce da Himun.
“Komai ya canza daga yau insha Allahu, tunda na yi maganin matsalar. Kai min addu’a ka ba shi hakuri..... Himu don Allah.......”
Tausayi da kaunar Mamin suka kara kama shi. A take ya ce,
“Mami komi ya wuce, na ari bakin Daddyn na ci masa albasa, komi ya wuce, sai na iso”.
Ya kashe wayar da sauri don zuciyarsa ba za ta iya jurar sauraron kukan mahaifiyar ba. Wanda ke tada tsigar jikinsa har ya sanyawa jikinsa tsuma.
Ibraheem kenan, shi da Khalipha ban san wa ya fi kaunar Mamin nan ba (Takori).
Allah ka barmu da iyayenmu, mu rayu tare har karshen rayuwarmu. Ka bamu iko da karfin zuciyar yi musu biyayya, albarkarsu ta zama mayafinmu kuma bango abar jinginarmu. Sannan abin tinkahonmu gobe kiyama.
******
A FARM CENTRE
“Halan waken nan sai da aka barza shi aka fidda dusar, kafin ayi faten nan?”
Dr. Mansur kenan, ke tambayar Inna Juma. Rahane ta dau pillow na kujera ta tura bayan Daddy. Bai lura da shakiyancin da ta yi masa ba ya sake tambayar Juma.
“Kuma kifin nika shi kika yi a blander kafin ki zuba?”
Ai sai Rayha ta kwashe da dariya. Inna Juma ta zuba mata duka a cinyarta ta ce,
“Uban naki kikewa shakiyanci ko ya yi kama da Malam Hudu? (Kakanta wanda ya haifi Yalwati).
Sai a lokacin Dr. Mansur ya ankara da abinda ke faruwa, ya karashe lomarsa ta karshe ya mike ya kora da lemun safari cikin tambulan, ya dauki mukullin motarsa ya yi hanyar kofa yana murmushi ya ce,
“kyaleta Inna Juma, ta mai dani kakan nata ya fiye min da ta rikeni a matsayin siriki ta dinga nuku-nuku dani, ta kasa gaya mun damuwarta. Bayan nine uwarta, nine ubanta, nine abokinta, kuma kawarta. Ke kuma kakarta.
Bari in wuce gida yamma ta yi, yanzu zan yi tuki da kuzari tunda hanjina ya warware. Go-slow ne dai na san sai ya kai ni magariba a titin nan idan ma na yi sauri kenan, Kano is full, alhamdulillah Kanon Dabo ta yi zarrah a jihohin Nigeria gaba daya, wajen albarkar Al’ umma”.
Rayhanah ce ta bude masa kofar motar ya shiga ta rufe,
“Sleep well Daddy.....”
Ta fada tana daga masa hannu har ya bar get dinsu yana daga mata shima. Maigadi ya kulle, ita kuma ta koma cikin gida.
Nan ta ga wayar Daddyn a nan inda ya tashi santin faten waken Inna Juma ya mantar da shi. Ta ce,
“Lah! Inna kinga Daddy ya manta wayarsa”.
Inna ta ce,
“Sai ki adana gobe ya karba”.
Ta ce, “Ba lallai ya zo gobe ba, karshen wata ne zai je Takai. Bari dai na ajiye din”.
Ta yi dakinta da ita ta sanya a kan lokar gadonta, ta fada bayan gida don ta yi alwalar sallar magariba.
Kafin lokacin magariba ya cika, Rayhanah na zaune kan sallaya da carbinta a hannu cikin kyakkyawar shiga da ta ware musamman don yin ibada, doguwar Abaya ce kirar Kuwait da farin Hijab wanda ya tsaya iya gwiwoyinta, tana yiwa Ubangiji tazbihi.
Har aka kira magariba ta tada sallah, a lokacin da wayar Daddy dake kan lokar gadonta ta soma dan kida ba mai cika kunnuwa da gigita mutum ba.
Don haka a nutse ta ci gaba da sallarta har ta idar, mai kiran bai hakura ya daina kiran ba sai kira yake akai-akai-akai. Yana yi yana karawa.
Ta mike ta kwanta a gefen gadonta ta dauki wayar Daddy don ta kashe, a ranta tana kunkuni cikin fadin “these so-called AKTH emergency unit, will not leave my Dad to live in peace ........haba! Ko inji ai yana son (service) kafin ya ci gaba da aiki balle mutum dan-Adam.
Amma shi Daddyn baya gajiya, ko ya kwana da an kira shi komin dare zai tafi. Ni gara ma da ya bar wayar, yau daya dai ya huta”.
Amma ga mamakinta sai ta kasa kashewa, ta zubawa lambar ido, domin ba ta yi kama da normal lambobin da ta saba gani ba. Lambobi ne rankacau (International).
Haka nan ta samu kanta da faduwar gaba, mutuwar jiki da sanyin gwiwa, wanda suka dage da cewa lallai suna son amsa wannan wayar, ta gayawa mai su Daddy baya tare da wayar, don ganin yawan kiran mai nuna mai ita a matse yake da son magana da Daddyn daga kololuwar duniya ba kiran asibiti bane.
A dai-dai lokacin da kiran ya kara shigowa, sai ta kishingida ta amsa.
“Dacta baya tare da wayar fa! Be patient mana!!”.
Wata irin sassanyar murya ce mara amo da karsashi, sannan kuma mai taushi, yarinyar ta yi amfani da ita wajen yi masa wannan kalamin, wadda ta tsirga har cikin kwakwalwarsa, ta haifar masa da macewar jiki, at the same time, ta tada tsigogin jikinsa.
Da ta ji anyi shiru kawai sai ta katse wayar ta ajiye. Ta dau remote ta kunna A.C ta soma addu’ar kwanciya barci.
Ibraheem ya yi shiru yana kallon wayar hannunsa, tsaye yake a balcony din gidansa (terrace) a saman bene yana kallon yadda ruwa ke tsiri, yana zuba cikin furanninsa korra sharr.
Akwai wani abu extraordinary cikin muryar yarinyar da bai taba ji a muryar wata diya mace ba, mai sanya sanyin jiki da kasala.
Me ya hada Daddy da budurwa har wayarsa ta je hannunta? Yana da kyakkyawan zato a kan mahaifinsa, amma wannan ba Abida ba ce ba Jawahir ba, ba kuma Azizah ba.
Idan ma sune ba yadda za ai wayar Daddy ta zo hannunsu. Don haka ya ji yana so ya tambayeta ita wace ce? Me ya hadata da wayar mahaifinsa?
Don haka ya sake kira, ta kuwa sake amsawa don yau cikin nishadi take, don Daddy ya ce za ta tafi Singapore jibi in Allah ya kaimu ta dora karatunta kafin Ibraheem ya nemi gida.....
“Wace ce ke?”
Abinda ya tambaya kenan a gintse, da makalalliyar hausarsa mai fita a doron harshe, cikin tsananin takaitawa.
Ita ma a takaicen ta samu kanta da amsawa.
“Sunana Juma”.
“Juma? What kind of name is this?”
Ta amsa da cewa, “Sunan da iyayena suka rada min kenan”.
A muryarta kamar ta ji zafin tambayar da ya yi mata, shi kuma a rayuwarsa bai iya muzanta dan adam ba. Sai ya yi saurin cewa,
“Ki gafarce ni plz, ina so in san yadda akai wayar Dr. Mansur ta zo hannunki ne?”
“Am the Nurse on duty, and he left it at the ward”.
Ibraheem ya gamsu da bayaninta har ga Allah, ita kuma kawai cikin nishadi take kan wannan albishir mai dadi da Daddy yayi mata na tafiya Singapore (Informatics-Singapore) ta rasa da wanda za ta yi sharing nishadin nata, sai ya fada a kan Ibraheem.
Ya ce, “Alright, zan kira zuwa gobe. Thank you”
“Don’t mind”. In ji ta.
Nadama ce take shigarta sosai, a kasalce ta ce da Himun.
“Komai ya canza daga yau insha Allahu, tunda na yi maganin matsalar. Kai min addu’a ka ba shi hakuri..... Himu don Allah.......”
Tausayi da kaunar Mamin suka kara kama shi. A take ya ce,
“Mami komi ya wuce, na ari bakin Daddyn na ci masa albasa, komi ya wuce, sai na iso”.
Ya kashe wayar da sauri don zuciyarsa ba za ta iya jurar sauraron kukan mahaifiyar ba. Wanda ke tada tsigar jikinsa har ya sanyawa jikinsa tsuma.
Ibraheem kenan, shi da Khalipha ban san wa ya fi kaunar Mamin nan ba (Takori).
Allah ka barmu da iyayenmu, mu rayu tare har karshen rayuwarmu. Ka bamu iko da karfin zuciyar yi musu biyayya, albarkarsu ta zama mayafinmu kuma bango abar jinginarmu. Sannan abin tinkahonmu gobe kiyama.
******
A FARM CENTRE
“Halan waken nan sai da aka barza shi aka fidda dusar, kafin ayi faten nan?”
Dr. Mansur kenan, ke tambayar Inna Juma. Rahane ta dau pillow na kujera ta tura bayan Daddy. Bai lura da shakiyancin da ta yi masa ba ya sake tambayar Juma.
“Kuma kifin nika shi kika yi a blander kafin ki zuba?”
Ai sai Rayha ta kwashe da dariya. Inna Juma ta zuba mata duka a cinyarta ta ce,
“Uban naki kikewa shakiyanci ko ya yi kama da Malam Hudu? (Kakanta wanda ya haifi Yalwati).
Sai a lokacin Dr. Mansur ya ankara da abinda ke faruwa, ya karashe lomarsa ta karshe ya mike ya kora da lemun safari cikin tambulan, ya dauki mukullin motarsa ya yi hanyar kofa yana murmushi ya ce,
“kyaleta Inna Juma, ta mai dani kakan nata ya fiye min da ta rikeni a matsayin siriki ta dinga nuku-nuku dani, ta kasa gaya mun damuwarta. Bayan nine uwarta, nine ubanta, nine abokinta, kuma kawarta. Ke kuma kakarta.
Bari in wuce gida yamma ta yi, yanzu zan yi tuki da kuzari tunda hanjina ya warware. Go-slow ne dai na san sai ya kai ni magariba a titin nan idan ma na yi sauri kenan, Kano is full, alhamdulillah Kanon Dabo ta yi zarrah a jihohin Nigeria gaba daya, wajen albarkar Al’ umma”.
Rayhanah ce ta bude masa kofar motar ya shiga ta rufe,
“Sleep well Daddy.....”
Ta fada tana daga masa hannu har ya bar get dinsu yana daga mata shima. Maigadi ya kulle, ita kuma ta koma cikin gida.
Nan ta ga wayar Daddyn a nan inda ya tashi santin faten waken Inna Juma ya mantar da shi. Ta ce,
“Lah! Inna kinga Daddy ya manta wayarsa”.
Inna ta ce,
“Sai ki adana gobe ya karba”.
Ta ce, “Ba lallai ya zo gobe ba, karshen wata ne zai je Takai. Bari dai na ajiye din”.
Ta yi dakinta da ita ta sanya a kan lokar gadonta, ta fada bayan gida don ta yi alwalar sallar magariba.
Kafin lokacin magariba ya cika, Rayhanah na zaune kan sallaya da carbinta a hannu cikin kyakkyawar shiga da ta ware musamman don yin ibada, doguwar Abaya ce kirar Kuwait da farin Hijab wanda ya tsaya iya gwiwoyinta, tana yiwa Ubangiji tazbihi.
Har aka kira magariba ta tada sallah, a lokacin da wayar Daddy dake kan lokar gadonta ta soma dan kida ba mai cika kunnuwa da gigita mutum ba.
Don haka a nutse ta ci gaba da sallarta har ta idar, mai kiran bai hakura ya daina kiran ba sai kira yake akai-akai-akai. Yana yi yana karawa.
Ta mike ta kwanta a gefen gadonta ta dauki wayar Daddy don ta kashe, a ranta tana kunkuni cikin fadin “these so-called AKTH emergency unit, will not leave my Dad to live in peace ........haba! Ko inji ai yana son (service) kafin ya ci gaba da aiki balle mutum dan-Adam.
Amma shi Daddyn baya gajiya, ko ya kwana da an kira shi komin dare zai tafi. Ni gara ma da ya bar wayar, yau daya dai ya huta”.
Amma ga mamakinta sai ta kasa kashewa, ta zubawa lambar ido, domin ba ta yi kama da normal lambobin da ta saba gani ba. Lambobi ne rankacau (International).
Haka nan ta samu kanta da faduwar gaba, mutuwar jiki da sanyin gwiwa, wanda suka dage da cewa lallai suna son amsa wannan wayar, ta gayawa mai su Daddy baya tare da wayar, don ganin yawan kiran mai nuna mai ita a matse yake da son magana da Daddyn daga kololuwar duniya ba kiran asibiti bane.
A dai-dai lokacin da kiran ya kara shigowa, sai ta kishingida ta amsa.
“Dacta baya tare da wayar fa! Be patient mana!!”.
Wata irin sassanyar murya ce mara amo da karsashi, sannan kuma mai taushi, yarinyar ta yi amfani da ita wajen yi masa wannan kalamin, wadda ta tsirga har cikin kwakwalwarsa, ta haifar masa da macewar jiki, at the same time, ta tada tsigogin jikinsa.
Da ta ji anyi shiru kawai sai ta katse wayar ta ajiye. Ta dau remote ta kunna A.C ta soma addu’ar kwanciya barci.
Ibraheem ya yi shiru yana kallon wayar hannunsa, tsaye yake a balcony din gidansa (terrace) a saman bene yana kallon yadda ruwa ke tsiri, yana zuba cikin furanninsa korra sharr.
Akwai wani abu extraordinary cikin muryar yarinyar da bai taba ji a muryar wata diya mace ba, mai sanya sanyin jiki da kasala.
Me ya hada Daddy da budurwa har wayarsa ta je hannunta? Yana da kyakkyawan zato a kan mahaifinsa, amma wannan ba Abida ba ce ba Jawahir ba, ba kuma Azizah ba.
Idan ma sune ba yadda za ai wayar Daddy ta zo hannunsu. Don haka ya ji yana so ya tambayeta ita wace ce? Me ya hadata da wayar mahaifinsa?
Don haka ya sake kira, ta kuwa sake amsawa don yau cikin nishadi take, don Daddy ya ce za ta tafi Singapore jibi in Allah ya kaimu ta dora karatunta kafin Ibraheem ya nemi gida.....
“Wace ce ke?”
Abinda ya tambaya kenan a gintse, da makalalliyar hausarsa mai fita a doron harshe, cikin tsananin takaitawa.
Ita ma a takaicen ta samu kanta da amsawa.
“Sunana Juma”.
“Juma? What kind of name is this?”
Ta amsa da cewa, “Sunan da iyayena suka rada min kenan”.
A muryarta kamar ta ji zafin tambayar da ya yi mata, shi kuma a rayuwarsa bai iya muzanta dan adam ba. Sai ya yi saurin cewa,
“Ki gafarce ni plz, ina so in san yadda akai wayar Dr. Mansur ta zo hannunki ne?”
“Am the Nurse on duty, and he left it at the ward”.
Ibraheem ya gamsu da bayaninta har ga Allah, ita kuma kawai cikin nishadi take kan wannan albishir mai dadi da Daddy yayi mata na tafiya Singapore (Informatics-Singapore) ta rasa da wanda za ta yi sharing nishadin nata, sai ya fada a kan Ibraheem.
Ya ce, “Alright, zan kira zuwa gobe. Thank you”
“Don’t mind”. In ji ta.