Sashe 14
Rayuwar Rayhana Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read
“Mene ne sunanki......?”
“Rahane”.
“Rayhanatu kenan ko?”
“A’a, Rahane.......”
“To ni ba zan iya kiranki Rahanen ba, don baida ma’ana at all sam-sam....... Rayhanah....!!!”
Ya tuno tattaunawar farko da mahaifinsa ya yi da ita a ranar da ta fara samun kanta daga hatsarin da suka yi, a kuma ranar da Baban da abokinsa Dr. Imam suka makala mata ‘hearing aid’. As soon as da suka fahimci she's hearing impaired!
Kafin Rayhanah ta ankara Ibraheem ya kai hannu gareta ya cire hijabinta yana duba kunnenta da bayan kunnen, babu komai sai dan karamin dan kunne mai barima na farin dutse. Ta saki ledodi da jakar hannunta kasa saboda razana.
“Where's your hearing aid?”.
Abin da ya tambayeta kenan da wata murya mai sanyi, harshensa da accent dinsa (American), wato na Amurka ba na Birtaniya da ya fi saukin furtawa ba.
Hannuwanta biyu ta kai kan nata tana son rufe gashinta da ya tsiraita. Sai ya russuna yana kwashe mata ledodin ta da jakarta da ta zubar ya bata hanya tareda yi mata alamar ta wuce, sai ta rabe ta gefensa ta shige ciki.
Babu kowa a falon, Inna da Baba Dacta sun shige kicin tun sanda Ibraheem ya cizge hijabin Rahane.
Ai ganin ba kowa a falon sai ta kara da gudu ta yi dakin barcinta ta rufo kofar ta jingina da ita tana numfarfashi kamar wadda ta yi gudun mita duba. Idanunta ta lumshe tana ambaton
“Yaa Wahhabu......... Yaa jamilal munzarrr (Ya mafi kyawun masu gani)!”
Ya Himu ne, tabbas shine....Daddy ya kinkimo ya kawo mata tana zaman-zamanta lafiya, ita ina ruwanta da wani Ibraheem. Tun can bai son ta, kyankyaminta yake, kalma wannan ba ta taba shiga tsakaninsu ba tun saninta da shi a gidan Dacta Mansur, kawo barinsa gidan don ba ta ishe shi ko da kallo ba.
Ita fa wannan auren kawai ta dauke shi suna ne, biyan bukatar ran Daddy bata taba tunanin zai zama reality ba.
Ta yi zaton haka za ta kare rayuwarta cikin kwanciyar hankali da neman ilmi da taimakon Babanta Mansur da Innarta Juma. Ba ta taba kawowa ranta Ibraheem din zai shigo cikin rayuwarta ba.......
Ta shiga uku....... wannan gundamemen Ba-amurken ne mijin nata da har Inna da Baba Dacta za su fita su barta da shi a gida akan saninsu? To tace masa me? Ko tayi masa me? Tayi yaya da shi?
Watakila ma dubawa ya yi in da hearing aid ya ce baya son ta. Duk Khalipha shi ya janyo mata....... da sunyi aurensu na so da kauna da ganin mutunci da kimar juna ai da Daddy bai yi mata AUREN HUCE HAUSHI da Ibrahim ba.
Sai ji ta yi hawaye na bin fuskarta. Bokon nashi har ya zarta misali, tsoro yake bata, kwarjinin shi razanata yake, ba ta san inda Daddy ke nufi ta kai shi a matsayin life-partner ba. Wannan gandamemen baqin bature haka wanda zai iya hadiyeta baki dayanta?
Ya yi biyun Yaya Khalipha a girma da tsayi, ba wai kiba ce da shi ba (physique).
Kuma ita bata taba yiwa kanta sha’awar rayuwa da wani Da namiji ba bayan Khalipha, shine dai-dai ita, domin ta kowanne bangare bai tsaurara ba...... ga boko ga addini, ga simplicity bai dauki kansa a bakin komai ba.
Rana daya wannan iftila’i ya ratsa, ta karbi zabin Daddy don biyayya da yakinin da take da shi na cewa a haka za su kare rayuwar tasu ita da Innarta da Daddy Ibrahim ba zai zo ba. Yau gata ga IBRAHIM MANSUR TAKAI.
Kokarin bude kofar ake, kofar da take jingine a jikinta. Ai da ta yi wata zabura guda daya sai ganinta ta yi a toilet dinta na bedroom ta kulle kanta.
Inna ta shigo tana cewa,
“Yau na ga abin da ya isheni ni Juma, mijin kike gudu haka? Lallai kin hada kanki da aiki.
Fito ki ci abincin da kika siyo shi Ibraheemu ma ya dade da fita a gidan nan.......”
Ai kuwa ta bude kofar ta fito idanunta sun ci kuka sunyi jawur. Haka Inna ta yi ta lallamin ta don ta ci abincin, amma ta kasa cin abin kirki duk soyayyarta da ‘wontonmee’ da ‘chili crab’. Ga Inna ba ta iya cin wannan cakudedeniyar ba, barta dai a KFC (Kentucky Fried Chicken).
Sai ta tattara ta zuba mata a firij tana ta mita.......
[12/27/2019, 11:51] Takori: “Kuma shi kenan don Allah ya amsa addu’armu Ibraheem ya zo, sai ki kuntatawa kanki?
Tun safe baki yi karin kumallon kirki ba kika fita, na kuma tabbata a can baki ci ba, kin sayo abin dadin ki rimi-rimi sai ki ki ci Rahane?
Haba Rahane, an Rahane na! ‘yar gidan BABANTA!! Kina son Uba kina gudun Dan sa, anya an taba yin haka?!!!”
Hawaye suka fitowa Rahane surrrrr...! Har daga cikin hanci, cikin dakushewar murya mai cike da kuka ta ce,
“Inna ni dai na fi son Yaya Khalipha.......”
Sai bammm! Inna ta buge bakinta da hannun ta,
“Kina auren wani kina cewa wani kike so? Maza-maza ki yi istigfari. Wanene Yaya Khalipha kuma? Shashashar banza, irin wannan zabgegen miji haka na likawa a goshi?
To ni ina son sa ki bar mini, ki ga yadda zan killace abina a daki kada wata ta tayi min kwace...... idan baki godewa Allah kin godewa Baba Likita ba, to za ki ga ba dai-dai ba a rayuwarki wallahi Allah ki dawo cikin nutsuwarki.
Haba an Rahane na? Ibraheem mai kyau da shi? Mai tarin ilmi. Daga yi min allura ya bani kwayoyi na sha na nemi ciwon bayan dake damuna na rasa.
Ubangiji ya ce idan bamu godewa rahamarsa ba, la-shakka zamu godewa azabarsa.
Ki nutsu, ki manta da wani Khalipha Rahane ki karbi mijin da Allah ya baki.
Shi bai ce baya son ki ba, bai kamata ke ki fadi hakan ba. SO na Allah ne, shi ke sanya shi a tsakanin bayinSa.
Je ki ki yi wanka Rahane, ki yi kwalliya ki tarbi mijinki, ki yi kwalliyarki ta ‘ya’yan Hausawa ya san cewa tushensa ya aura. Tashi maza ki cire shirmen nan na jikinki ki yi wanka.....”
Rahane ta katseta cikin kuka,
“Ni wallahi babu wankan da zan yi, da can bana wanka sai don ya zo? Kuma ai gidan nan babu dakin da zai sauka in ba naki za a ba shi ba ina zai je?”
Inna dai lallami take don haka ta gintse dariyar da ta cika mata ciki, ta ce,
“Na ji na ba shi nawan ni zan kwana a falo, ai ko wadannan lausasan kujerun sun isheni in yi barcina har da saleba. To canza kayan tunda ba za ki yi wankan ba.......”
Ai kuwa ta rantse ba abin da za ta yi a ciki. Ran Inna ya soma baci, ta tashi ta rabu da ita ta shiga kicin don yin abincin da Daddy ya ce ta yi musu kafin su dawo, ta barta nan ta sanya kai cikin kafafu tana ta kuka.
Ta gama kular da Inna, don haka ta fita sha’anin ta har ta gama girkinta ta jera a dining dan karami na mutum biyu (mai kujeru biyu kacal) dake can gefe a falon. Duk shiga da ficen da take sai ta ganta yadda ta barta, zuwa lokacin kuma ta gaji da kukan ta yi shiru, sai ajiyar rai take.
“Rahane”.
“Rayhanatu kenan ko?”
“A’a, Rahane.......”
“To ni ba zan iya kiranki Rahanen ba, don baida ma’ana at all sam-sam....... Rayhanah....!!!”
Ya tuno tattaunawar farko da mahaifinsa ya yi da ita a ranar da ta fara samun kanta daga hatsarin da suka yi, a kuma ranar da Baban da abokinsa Dr. Imam suka makala mata ‘hearing aid’. As soon as da suka fahimci she's hearing impaired!
Kafin Rayhanah ta ankara Ibraheem ya kai hannu gareta ya cire hijabinta yana duba kunnenta da bayan kunnen, babu komai sai dan karamin dan kunne mai barima na farin dutse. Ta saki ledodi da jakar hannunta kasa saboda razana.
“Where's your hearing aid?”.
Abin da ya tambayeta kenan da wata murya mai sanyi, harshensa da accent dinsa (American), wato na Amurka ba na Birtaniya da ya fi saukin furtawa ba.
Hannuwanta biyu ta kai kan nata tana son rufe gashinta da ya tsiraita. Sai ya russuna yana kwashe mata ledodin ta da jakarta da ta zubar ya bata hanya tareda yi mata alamar ta wuce, sai ta rabe ta gefensa ta shige ciki.
Babu kowa a falon, Inna da Baba Dacta sun shige kicin tun sanda Ibraheem ya cizge hijabin Rahane.
Ai ganin ba kowa a falon sai ta kara da gudu ta yi dakin barcinta ta rufo kofar ta jingina da ita tana numfarfashi kamar wadda ta yi gudun mita duba. Idanunta ta lumshe tana ambaton
“Yaa Wahhabu......... Yaa jamilal munzarrr (Ya mafi kyawun masu gani)!”
Ya Himu ne, tabbas shine....Daddy ya kinkimo ya kawo mata tana zaman-zamanta lafiya, ita ina ruwanta da wani Ibraheem. Tun can bai son ta, kyankyaminta yake, kalma wannan ba ta taba shiga tsakaninsu ba tun saninta da shi a gidan Dacta Mansur, kawo barinsa gidan don ba ta ishe shi ko da kallo ba.
Ita fa wannan auren kawai ta dauke shi suna ne, biyan bukatar ran Daddy bata taba tunanin zai zama reality ba.
Ta yi zaton haka za ta kare rayuwarta cikin kwanciyar hankali da neman ilmi da taimakon Babanta Mansur da Innarta Juma. Ba ta taba kawowa ranta Ibraheem din zai shigo cikin rayuwarta ba.......
Ta shiga uku....... wannan gundamemen Ba-amurken ne mijin nata da har Inna da Baba Dacta za su fita su barta da shi a gida akan saninsu? To tace masa me? Ko tayi masa me? Tayi yaya da shi?
Watakila ma dubawa ya yi in da hearing aid ya ce baya son ta. Duk Khalipha shi ya janyo mata....... da sunyi aurensu na so da kauna da ganin mutunci da kimar juna ai da Daddy bai yi mata AUREN HUCE HAUSHI da Ibrahim ba.
Sai ji ta yi hawaye na bin fuskarta. Bokon nashi har ya zarta misali, tsoro yake bata, kwarjinin shi razanata yake, ba ta san inda Daddy ke nufi ta kai shi a matsayin life-partner ba. Wannan gandamemen baqin bature haka wanda zai iya hadiyeta baki dayanta?
Ya yi biyun Yaya Khalipha a girma da tsayi, ba wai kiba ce da shi ba (physique).
Kuma ita bata taba yiwa kanta sha’awar rayuwa da wani Da namiji ba bayan Khalipha, shine dai-dai ita, domin ta kowanne bangare bai tsaurara ba...... ga boko ga addini, ga simplicity bai dauki kansa a bakin komai ba.
Rana daya wannan iftila’i ya ratsa, ta karbi zabin Daddy don biyayya da yakinin da take da shi na cewa a haka za su kare rayuwar tasu ita da Innarta da Daddy Ibrahim ba zai zo ba. Yau gata ga IBRAHIM MANSUR TAKAI.
Kokarin bude kofar ake, kofar da take jingine a jikinta. Ai da ta yi wata zabura guda daya sai ganinta ta yi a toilet dinta na bedroom ta kulle kanta.
Inna ta shigo tana cewa,
“Yau na ga abin da ya isheni ni Juma, mijin kike gudu haka? Lallai kin hada kanki da aiki.
Fito ki ci abincin da kika siyo shi Ibraheemu ma ya dade da fita a gidan nan.......”
Ai kuwa ta bude kofar ta fito idanunta sun ci kuka sunyi jawur. Haka Inna ta yi ta lallamin ta don ta ci abincin, amma ta kasa cin abin kirki duk soyayyarta da ‘wontonmee’ da ‘chili crab’. Ga Inna ba ta iya cin wannan cakudedeniyar ba, barta dai a KFC (Kentucky Fried Chicken).
Sai ta tattara ta zuba mata a firij tana ta mita.......
[12/27/2019, 11:51] Takori: “Kuma shi kenan don Allah ya amsa addu’armu Ibraheem ya zo, sai ki kuntatawa kanki?
Tun safe baki yi karin kumallon kirki ba kika fita, na kuma tabbata a can baki ci ba, kin sayo abin dadin ki rimi-rimi sai ki ki ci Rahane?
Haba Rahane, an Rahane na! ‘yar gidan BABANTA!! Kina son Uba kina gudun Dan sa, anya an taba yin haka?!!!”
Hawaye suka fitowa Rahane surrrrr...! Har daga cikin hanci, cikin dakushewar murya mai cike da kuka ta ce,
“Inna ni dai na fi son Yaya Khalipha.......”
Sai bammm! Inna ta buge bakinta da hannun ta,
“Kina auren wani kina cewa wani kike so? Maza-maza ki yi istigfari. Wanene Yaya Khalipha kuma? Shashashar banza, irin wannan zabgegen miji haka na likawa a goshi?
To ni ina son sa ki bar mini, ki ga yadda zan killace abina a daki kada wata ta tayi min kwace...... idan baki godewa Allah kin godewa Baba Likita ba, to za ki ga ba dai-dai ba a rayuwarki wallahi Allah ki dawo cikin nutsuwarki.
Haba an Rahane na? Ibraheem mai kyau da shi? Mai tarin ilmi. Daga yi min allura ya bani kwayoyi na sha na nemi ciwon bayan dake damuna na rasa.
Ubangiji ya ce idan bamu godewa rahamarsa ba, la-shakka zamu godewa azabarsa.
Ki nutsu, ki manta da wani Khalipha Rahane ki karbi mijin da Allah ya baki.
Shi bai ce baya son ki ba, bai kamata ke ki fadi hakan ba. SO na Allah ne, shi ke sanya shi a tsakanin bayinSa.
Je ki ki yi wanka Rahane, ki yi kwalliya ki tarbi mijinki, ki yi kwalliyarki ta ‘ya’yan Hausawa ya san cewa tushensa ya aura. Tashi maza ki cire shirmen nan na jikinki ki yi wanka.....”
Rahane ta katseta cikin kuka,
“Ni wallahi babu wankan da zan yi, da can bana wanka sai don ya zo? Kuma ai gidan nan babu dakin da zai sauka in ba naki za a ba shi ba ina zai je?”
Inna dai lallami take don haka ta gintse dariyar da ta cika mata ciki, ta ce,
“Na ji na ba shi nawan ni zan kwana a falo, ai ko wadannan lausasan kujerun sun isheni in yi barcina har da saleba. To canza kayan tunda ba za ki yi wankan ba.......”
Ai kuwa ta rantse ba abin da za ta yi a ciki. Ran Inna ya soma baci, ta tashi ta rabu da ita ta shiga kicin don yin abincin da Daddy ya ce ta yi musu kafin su dawo, ta barta nan ta sanya kai cikin kafafu tana ta kuka.
Ta gama kular da Inna, don haka ta fita sha’anin ta har ta gama girkinta ta jera a dining dan karami na mutum biyu (mai kujeru biyu kacal) dake can gefe a falon. Duk shiga da ficen da take sai ta ganta yadda ta barta, zuwa lokacin kuma ta gaji da kukan ta yi shiru, sai ajiyar rai take.