← Book details Makaho Ne Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
CHAPTER 7 OF 11

Part ɗin sa ya kai kayan bayan ya nuna wa Mama da Inna kayan kafin ya kai part ɗin sa.

Makaho Ne Part 1 Complete Hausa Novel · about 36 min read

Inna ta fara fadar cewa tsabar almubazzaranci ga kayan lefe ne zai je ya kifi wasu kayan.

Bai kula ta ba ya fita don yin sallar magrib.

Text message ya tura wa Nadra ganin ta tare a dakin mama.

*Ƙarfe goma na dare na yi ki yi ma su sallama ki koma part ɗina tare za mu kwana kafin gobe idan na tafi za ki iya kwana a dakin da kika ga dama.*

Tana kwance a gadon Mama bayan ta yi sallar isha'i ne ta ga message ɗin nasa.

Tura baki ta yi tana cewa.

"Ni ba ƴar iska ba ce da zan je kwana dakinka bayan abun da ka yi ma ni da safe."

Kamar ya san me take cewa sai ga wani message.

*Idan ba ki zo ba zan biyo ki ne ko a gaban Mama ne ba ruwana da kunya.*

Bayan ta karanta tana hawaye ta ce.

"Na shiga uku. Wallahi zai aikata bai da kunya."


Yana gama tura ma ta messages ɗin. Ya siye gasashshen kaza ya siye fresh milk ya bar wajen.


_Makaho_

Yana dawowa daga wajan da yake gyaran takalmin daidai kan kwanar da zai sada shi da hanyar unguwarsu wata baƙar motar ta tsaya a gabansa.

Wasu maza masu ƙirar samudawa ne suka fito su biyu, suka ɗauke shi suka saka shi a bayan motar bayan sun toshe ma sa baki da hannu kafin ya yi wani yunkuri, a guje motar ta bar layin .

Wata mota dake can gefe ta mara ma su baya a guje.


*Maman Ihsan ce*


09065327995

Follow the MAKAHO NE channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029Vb7CzOoIXnljBnIJjp2z


*MAKAHO NE*


*NA*

Maman Ihsan ce ✍️


https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️


page3️⃣8️⃣


Wasu maza ma su ƙirar samudawa suka fito su biyu. Suka ɗauke shi suka saka shi a bayan motar bayan sun toshe ma sa baki da hannu kafin ya yi wani yunkuri, a guje motar ta ta bar layin.

Wata mota dake can gefe ta mara ma su baya a guje.


Motar da ta fahimci ana binta ne sai Direban ya ce wa mutanen nan guda biyu da suke rike da Makaho cewa.

"Wancan me motar na fahimci bin mu yake yi fa?"

Ɗaya daga cikin mutane biyun ya ce.

"Ka san yadda za ka yi ka ɓace wa ganinsa."

Ya yi maganar yana shaƙawa Khalifa hankaci a hancinsa. Wan da ya ya sa Khalifa ya a yi luu ya zube a kan kujerar."

Sai suka sake shi suna kallon motar da aka ce yana bin su. Daidai lokacin ne kuma wayar ɗaya daga cikinsu ya yi ringing.

Suna dubawa suka ga uban gidansu ne yake kiran wayar.

Amsawa ya yi yana cewa .

"Sai oga, aiki ya kammala muna hanya, sai dai mun fahimci wata baƙar mota tana nan tana bin mu, tun da muka dauke shi take bin mu ina kyautata zaton sun ga lokacin da muke dauke shi ne suka bi mu?"

Daga can ɓangaren ya ce .

"What's? Ta ya za ku yi sakaci haka bayan na faɗa ma ku yadda za ku gudanar da komai, to bari ku ji ku tabbatar kun tsere ma su domin idan har kuka yi sakaci aka kama ku to har da kanku kuka yi wa don ba zan taɓa bari miliyoyin da aka biyani akan aikin makahon nan ya tafi a kansa ba na rasa su."

Cikin tabbatarwa ya ce .

"Kafa ka damu boss ba mu taba ma ka matsala ba kuma ba za mu fara kan wannan ba."

Ogan na jin haka sai ya ce.

"Good job."

Ya katse kiran wayar.


Gudu suke ya kamar za su tashi dama don sun kama hanyar barin unguwannin da ke da mutane.

Yayin da su ma motar da take bayansu dai ƙara gudu suke yi don su ga sun tarar da su.

Su biyu ne a cikin motar wanda yake zaune mazaunin direba sai kuma ɗayan yana zaune gefen wajen me zaman banza.

Wanda ke zaune gefen wajen me zaman banza ya kira wata lamba, sannan ya kara a kunnensa.

Bayan an ɗaga ne ya ce .

"Hello sir"

Ta cikin wayar ya ji an ce .

"Hello ya ake ciki ne ina fatan ba wata matsala ko?"

"Akwai matsala yallaɓai."

Ɗan jim ya yi kafin ta ce .

"Meke faruwa?"

"Wallahi wasu ne suka ɗauke shi suka saka shi a motarsu suka bar wajen a guje."

Tsawa ya daka ma su yana cewa .

"Meye amfanin ku da har za ku yi sakaci da wasu za su samu damar ɗauke shi ba ku dakatar da su ba?"

"Wato abu ne da ba mu yi zato ba, ya dawo daga inda ya saba zuwa ya dauki hanyar gidan da yake zaune kenan sai suka ritsa shi suka tura shi a cikin motar da karfi wanda Kafin mu yi wani yunƙuri tuni sun bar wajen. Amma muna biye da su in sha Allah dai mun cin ma su"

"Ita yarinyar da kuka kuna ganinsu tare da ita fa?"

"Ita tana gida shi kaɗai ne suka kama."

"Okay me ya alaƙarsa da yarinyar ne?"

"Abun da har yanzu ba mu tabbatar ba kenan, amma bayan kuɓutar da shi za mu iya gano dangantakar da ke tsakaninsu da ita ."

Yana fadar haka sai ya ji an katse kiran wayar.

Daidai lokacin ne kuma suka nemi motar gabansu suka rasa. Sakamakon sun zo mararraba ce, hanayar ta rabu hudu suka rasa in za su bi , dan ba su san in da za su bi ba, mikewa ne ko kuma damar su za su bi ki hagu.

Gabaɗaya sun rasa in da za su tafi, ga shi mota daya suka fito da ita ballantana ace su rabu wani zai iya hangen su.

Sai dai kawai suka mike ba tare da sanin Ina motar gabansu ta yi ba


_Ma'eesha_

Ganin har na kira sallar magrib makaho bai dawo ba ne hankalin ta ya fara tashi.

Domin ta san baya taɓa kai wa magrib bai shigo ba. Don haka sai ta kira wayarsa. Tana jin yans riginging amma ba'a ɗaga ba. Sai ta dake kira a karo na biyu ta ji wata baƙuwar murya da ba ta taɓa jin sa baya ɗaga kiran wayar yana ka ta sallama. Gaban ta ne ya yi mummunan faduwa amma sai ta dake ta amsa sallamar.

"Wa'alaika Salam, ina mai wayar."

Hajiya tafiya nake yi akan hanya na ji ƙarar wayar, ko da na duba sau na ga kina kira,kafin na daga ta katse sai yanzu da kika sake kira."

Cikin tashin hankali ta ce.

"Ba ka ga wani makaho a wajan wayar ba?"

"Ba kowa sai kayan gyaran takalmin da suke watse a Wajen."

Hawaye ne ya wanke ma ta duka ta ce .

"Innalillahi wa'inna ilahir raji'un. Bawan Allah kana ina ne yanzu?"

Ya yi ma ta kwantancen farkon layin ta ce.

Ita matar me wayar da kayan gyaran takalmin ne ga ta nan fitowa .

Katse wayar ta yi ta daki hijabi ta saka sannan tana fita gudan sauri -sauri gudu-gudu. Har ya karasa wajan.


Tun daga nesa ta hango mutane za su kai biyar a waje ɗaya, ga kayan gyaran takalmin Khalifa nan na a waje ɗaya.

Tana ƙarasowa ta ce

"Don Allah ina kuka ga ya bi da ya zubar da kayansa a nan."

Ta yi tambayar tana kallonsu, wanda ya ba ta wayar ne yake cewa.

"Ga wayar da kayan ki tafi gida zai dawo."

Ta karaɓa tana kallonsa kamar wata sokuwa."

Ɗaya daga cikinsu ne ya ce.

"Kada ka ɓoye ma ta komai matasa ce fa. Hajiya ki yi addu'a Allah ya bayyanar ma ki mijinki, domin wasu ne suka zo da mota suka saka sa ciki da karfin tafiya


Kanta ta dafe tana cewa.

"Innalillahi wa'inna ilahir raji'un, ina suka kai shi?"

"Allah masani sai dai duk yadda aka yi wadannan mutanen criminals ne dan ba su yi kama da jami'ai ba."

Goge hawayenta ta yi ta ce.

"Na gode Allah ya saka ma ku da alkhairi."

Tana gama fadar haka ta nufi gida rike da kayan aikinsa da wayarsa a hannunta.

Tana zuwa gidan ta ajiye kayan aikinsa ta fito dan zuwa police station ta kai report. Duk da ta san ba ta da kudin da zai kai ta ya dawo da ita, ɗari biyun da makaho ya ba ta ne wadanda aka cuce shi aka ba shi a matsayin ɗari biyar.

Jin kiran sallar isha'i ya sa ta dakata sai da ta gabatar da sallar isha'i kafin ta wuce bayan ta yi ma sa addu'o'i.

Sannan ta rufe gidan ta kama hanyar zuwa Ofishin ƴan sandan. Sai da ta kai bakin titi sannan ta tsaya.

Mai keke nape ta tare da sanar da shi ya ƙai ta police station ya sanar da ita kudin ta ɗari uku za ta biya, amma sai ta roke shi ya taimaka ɗari biyu take da shi. Ya ha kekensa ya tafi wai shi ba zai iya zuwa a dari biyu ba. Haka ta dinga tare ma su keke kusan su uku ba su dauke ta a ɗari biyu ba.

Hawaye ne ya dinga ambaliya a saman fuskarta kamar an bude famfo.

Bayan hannunta ta sa tana goge hawayenta kafin wani tunani ya fado ma ta a rai.

"A.S.P."

ASP Nasir Yusuf Wani tsohon saurayinta ne wanda ya taba nuna yana son ta a baya ita kuma ta nuna ba ta son sa. Saboda nacin son da yake yi ma ta ne har ta yi blocking nasa a waya, sakamakon yawan kira da messages. A gidan ma ta ce wa Maigadi idan ya zo ya ce ta bar ƙasar. Da haka ya hakura da ya fahimci ba ta son sa.

Tana tsaka da tunanin sai wani mai nape ya tsaya yana cewa.

"Hajiya tafiya ne?"

Ta sanar da shi police station da zai kai ta ta kuka roke shi ya kai ta dari biyu take da shi.

Ganin tana cikin tashin hankali ya sa ya kai ta a haka nan.

Bayan ya sauke ta ne sai ta ba shi kudin ta ciri wayar ta ta yi unblock ɗin A.S.P

Sannan ma sa kira ta yin sai ta ji ringing ɗin wayar a bayanta. Ta waiga ta gan shi sanye da kakinsa na aiki yana kokarin shiga motarsa.

Wayar ya ciro ya duba yana kallon sunan da mamaki, a hankali ya furta.

"Ma'eesha."

Katse kiran ta yi ta karasa wajensa daidai lokacin da yake kokarin bin kiran nata.


_Fahad_


Bayan ya siye kaza da fresh milk park ya nufa in da suka saba zama su shaƙata su da abokansa.

Suna zaune su biyu Sadik da mukhatar suna ganin motarsa suka taso suka ƙarasa wajan , kasancewar ya sanar da su ba zai zauna ba.

Sadik ya shiga gaban motar yayin da Mukhatar ya shiga baya.

"Ya aka yi ne Ɗab America har an gama cin amarcin ne?"

Cewar Sadik yana kallon Fahad. Mukhtar dake baya ya ce .

"Wai kamshin me nake ji ne a cikin motar nan, har da tsaraba ka kawo ma na ne?"

Ya yi maganar yana kallon kazar.

"Ba sai ka ci ba tunda da kudinka na siya."

Mukhtar ya yi dariya yana cewa .

"Wai amarya ana siyo wa wannan kazar? Shegen sama ashe za ka sauko da wuri haka? Ai da cewa ka yi ba ka so har kana fushi da mutane shi ya sa yanzu na ga an..."

"Ya isa haka nan Mallamai, ba ruwanku, sallama na zo mu yi ba na da lokacin ɓatawa."

"Da Nadra za ka tafi ne?"

Cewar Sadik yana kallon fuskar Fahad."

"Why not ka je da ita ? Amma ka ce bayan kun yi aure can za ka zauna da matarka."

"Eh lokacin Ban san ita ba ce a lokacin Sidra ce zan aura kuma ita ta ce can za ta zauna ita da Nigeria sai ta zo ziyara. Ita kuma wannan da yake akwai duhun kai a tattare da ita cewa ta yi ba za ta je ba."

Nam suka ɗan taɓa fira Kafin suka yi sallama da juna suka fito ya bar wajen su ma kowa ya shiga motarsa suka bar wajen kowa ya kama hanyar gidansa.


_Nadra_

Tana zaune a dinning table suna cin abinci ita da iyalan gidan.

Duk wani motsi nata akan idanun Sidra take yin sa. Musamman ganin irin wayar da Nadra ke amfani da shi ya tashi. Musamman da ta ga lokaci lokaci tana duba wayarta.

Ita kuma Nadra sakon Fahad ne ke sake ba ta mamaki.

Bayan sun kammala cin abinci lokacin karfe tara ne sai Sidra ta ja hannun Nadra suka shiga ɗakinta.

Suna shiga ta tura ƙofar tana cewa.

"Ƙanwata wayarki sabuwa ce ko?"

Tana Murmushi take maganar yadda za ta bugu cikin Nadra ta faɗa ma ta.

"Eh sabuwa ce Yaya Fahad ya siya ma ni ita."

Sai da ta ji wani abu ya soki ƙrjinta kafin da daidaita kanta ta ce.

"Na ki ya ɓace ne?"

"A'a shi ya karba ya siyo ma ni wannan ."

"Okay amma dai ya kamata a ce kina kiran masoyinki a waya Ya Sayyadi kuna gaisawa, saboda ya san da cewa kuma jiransa shi ma ya jira ki."

Zaro idanunta waje ta yi ta ce.

"Rufa ma ni asiri ranar da Ya Sayyadi ya kira ni a waya sai da Yaya Fahad ya masa gargaɗi mai haɗe da barazana na tabbata ba zai sake waiwaya ta ba. Amma kin ga da zaran Yaya Fahad ya sake ni shi kenan sai ja je na sanar da shi, amma yanzu ba daidai bane na kira shi."

Harararta ta yi a fakaice ta ce.

"Okay to yaushe zai sake ki?"

"Ya ce kada na sake yi ma sa zandan saki, idan lokacin ya yi da kansa zai sake ni. Wai idan na sake maganar sai ya ba ni mamaki."

"Ba ana ba ki shawara ba ki dauka ba, kina masa sanyi da yawa dole ya raina ki. Muga wayarki."

Ta shiga wajen kira ta ga ba su taba magana da Fahad a waya ba kamarsa ma ba ta yi servin ba, sai dai ya kira ta yau ba ta ɗaga ba. Sai ta shiga wajen message ta ga messages da ya tura wa Nadra. Nan ne hankalin Sidra ya tashi sosai.

"Kina nufi ɗakinsa ya ce ki ki kwana tare da shi?"

"Eh Ni ma haka na message ɗin ."

"Kuma ba ki taɓa kwana daki daya da shi ba ko?"

Kai Nadra ta daga ma ta kafin ta ce.

"Ɗazu da ya karbi kayan Rumaisa ya kai ma ki ne ya yi ma ki?"

Shiru ta yi kafin ta ce .

"Ba abinda ya yi Mani?"

"To shine zai zo karɓar ma ki kayan? Sannan kika dinga noƙewa kuna jin kunya sai da ya dauke ki?"

Ta yi maganar kamar za ta dake ta, kafin ta kwantar da murya tana cewa .

"Kin ga Fahad ba son ki yake yi ba, wayau zai ma ki ya cuce ki ya kwashe albarkatun jikinki sai ya mayar da ke fanko ya wulakanta ki ya ce ki je ki auri ya Sayyadi. To shi Sayyadin wawa ne?"

Shiru dai ta yi ba ta ce komai ba.

"Yanzu ki tashi ki je ɗakin Mamansa ki kwanta ki yi barci a dakin, kuma ki kashe wayarki."

Sallama ta yi ma ta ta fito don zuwa dakin Mama. A hanya ta kashe wayarta sannan ta shiga ɗakin da sallama.

Turus ta yi ganinsa tsaye a ɗakin yana magana da Mama yayin da ita kuma take yanke Fruits.

Hanyar fita ta nufa Mama ta ce ma sa.

"Ba za ka sha Fruits din ba ne?"

Kallon Nadra ya yi kafin ya ce .

"Mama ki ba Nadra ta kawo mani, idan zan kamata zan sha. Good night."

"Okay to Allah ya tashe mu lafiya."


*Wata kila na kara ma ku page ɗaya zuwa dare, idan ban samu dama ba to sai dai na ce mu hadu bayan sallah idan Allah yasa muna cikin ma su yawancin rai, don ba na posting cikin azumi fatan alkhairi*🤗


*Maman Ihsan ce*✍️


09065327995

*MAKAHO NE*


*NA*

Maman Ihsan ce ✍️


https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️


page3️⃣9️⃣

Ba za ka sha Fruits ɗin ba ne?"

Kallon Nadra ya yi kafin ya ce.

"Mama ki ba Nadra ta kawo Mani idan zan kwanta zan sha. Good night."

"Okay Allah ya tashe mu lafiya?"

Mama na gama fadar haka ya fice daga cikin ɗakin. Kallon Nadra mama ta yi kafin ta ce.

"Daughter lafiya kuwa?"

Ƙokarin ƙaƙaro murmushi take yi kafin ta ce.

"Ba komai Mama."

Kallon ta take yi tare da nazartar yanayin ta kafin ta ce .

"Na ga ba walwala a tare da ke ne, idan akwai wata matsala ki faɗa ma mahaifiyarsa ce ni, ina da ikon da zan saka shi ya canza."

"Ba komai Mama."

Ta yi maganar tana zama ƙasa saman carpet. Mama ta kalle ta ta ce.

"Bari na gama yankaa ku fruits ɗin sai ki wuce ma ku da shi."

Shiru ta yi gabanta na faɗuwa kafin ta ce.

"Mama zan kwana a ɗakinki?"

"Ɗakina kuma Nadra?"

Kai ta ɗaga alamar eh tana wasa da yatsun hannunta.

"Kar ki damu in dai kwana a ɗakin nan ne sai ya ishe ki. Amma ba yau ba sai gobe idan mijinki ta tafi America. Na so a ce tare kuka tafi amma kika ce ba za ki je ba, duk da cewar akwai rashin sabo da rashin shaƙuwa a tsakanin ke da shi sakamakon yadda auren ya zo ba yadda muka yi tsammanin sa ba. Amma duk da hakan ki saki jiki da mijinki a haka za ku shaƙu da juna ku saba, idan da wani abu da yake yi ma ki wanda bai dace ba ko ba ki so to kada ki ɓoye ma ni komai, ko yana hantarar ki ko wani abu da bai dace yana yi ma ki ba a tsakanin ki na matarsa to ki sanar da ni in sha Allah zan yi wa tufkar hanci.

Nisawa ta yi kafin ta ce.

"Rayuwar aure dai da mutunta juna, Idan aka rasa mutunta juna a cikin kowace irin alaƙa, alaƙar soyayya ce ko abota, hatta alaƙar zumunta, za ta mutu ne. ta koma tamkar gangan jiki bayan an zare rai. Koda a zahiri ana tare, amma kowa zuciyarsa ta ware."

Sosai Mama ta yi ma ta nasiha da bada shawarwari kafin ta ce.

"Tashi ki tafi wajen mijinki sai da safe."

Jinjina kai ta yi cikin sanyin jiki ta mike ta karbi bowl ɗin fruit ɗin ta fita tana yi wa Mama sai da safe.

Murmushi Mama ta yi cike da ƙaunar Nadra ta ce.

"Allah ya tashe mu lafiya."

Da haka ta fita daga dakin zuciyarta cike da fargaba da kullum abun da zai iya biyo wa baya.

A hankali take tafiya kamar kazar da ƙwai ya fashewa a cikin ciki haka take tafiya.

Matattakalar ma a hankali take taka step ɗin har ta isa ƙofar shiga falo.

Nan ta tsaya cak ta kasa taɓa ƙofar tana rike da bowl ɗin fruits ɗin a hannun ta


Har tsawon mintuna biyar kenan take tsaye wanda a karshe ta san ba ta da wani zaɓi da ya wuce ta shiga ko don Fruits ɗin da Mama ta ba ta don ta kai ma sa.

Knocking ɗin ƙofar t fara yi amma sai ta ji shiru tsawon lokaci bai ba ta izinin shiga ba.

Fahad kam yana zaune yana aiki a system ɗin sa. Kum yana jin tana knocking amma y share ta. Ɗin shi a ganinsa ya kamata a ce ta shigo kai tsaye ne ba sai ta jira ya ba ta izinin ba.

Sai da ta gaji ne ta yi sallama tana tura ƙofar ɗakin. Ganinsa zaune da ta yi jan kujera yana danna system ɗin sa ya ba ta mamaki.

Wato yana zaune kum yana ganin ita ce amma ya share ta.

Tura ƙaranin bakinta gaba ta yi daidai lokacin da ya ɗago kai ya kalle ta.

Rufe system ɗin ya yi tare da kallonta wanda ita ma ya yi daidai da lokacin da ta kalle shi.

Tashi ya tsaye ya yi daidai lokacin da ta ajiye bowl ɗin kan Centre table dake gabansa.

"Ina wuni lafiya."

Ta gaishe shi tana mai ɗan durƙusawa.

Bai amsa ba kamar kullun da idan ta gaishe shi dama baya amsawa.

Ledojin da ya shigo da su ne ya ɗauko ya ajiye saman Centre carpet

Zama ya yi yana mai ce ma ta.

"Kawo mun Fruits ɗin nan."

Ta dauki bowl ɗin ta karasa gabansa ta ajiye.

"Zauna."

Ya umarce ta yana ciro kaza ɗaya daga cikin ledar. Nan ya baje ma su ita yana mai furta.

"Bismillah."

Gabanta ne ta ji ya fadi sai sai ya dinga nanata kalmar innalillahi wa'inna ilahir raji'un a zuciyarta.

Ganin ba ya da niyyar saka sannu ya saka ya yago cinyar kazar yana nufar bakinta da shi.

Girgiza kai ta yi tana kallon ƙasa.

"Kada ki yi ma ni gardama akan komai a wannan daren kin ji."

Ɗago kai ta yi tana kallonsa ba tare da ta ce komai ba.

"Ina son ki kasance mai biyayya a gare ni matukar dai ban saɓon Allah na umarce ki da ki aikata ba, don haka duk yadda na so ko na yi da ke ki kasance mai biyayya a gare ni kamar yadda na san an yi ma ki nasiha akan biyayya ga umarnin miji ko?

Kai ta jinjina ba tare da ta yi magana ba, cikin sanyin jiki ta jinjina kai.

Sake ba ta kazar ya yi ta kasa ci sai sai ta saka hannu ta karba sannan ta ci , tun da ta ci cinya ɗaya ba ta ƙara ci ba ta ce ta ƙoshi. Fresh milk ya zuba a cup ya ba ta ta karɓa ta shanye.

Shi ma bai wani ci ba ya tattara kayan ya nufi kitchen dake cikin part ɗin nasa.

Bayan ya dawo ne ta ji ya kama hannunta ya miƙar da ita tsaye, ƙokarin zame hannunta take yi amma ta kasa.

"Mu je mu yi wanka ko?"

Gabanta ya faɗi wanda sai da ta kalle shi ba shiri.

"Na yi wanka."

"Eh mu sake yi."

Ƙwalla ya cika idanunta ta kalle shi ta ce.

"Ni fa zan iya yin wanka tare da kai ba."

"Okay ki je ki fara yi ."

Ya yi maganar yana jan hannunta har zuwa cikin bathroom. Da kansa ya hada ma ta ruwan wank sannan ya fito ya janyo ma ta kofar.

Set ɗin akwatin kayanta da ya siyo ma ta ya buɗe.

Sanin halinta ba ta sun saka kananan kaya ya sa ya fito mata da riga da wando sai dogon Hijabi da za ta yi sallah.

Bayan ta gama ne sai ga ta ta fito ɗaure da babban towel da da kuma wani ta lulluɓe da wani towel ɗin.

Tsaya wa ta yi ta kasa ƙarasawa tsakiyar ɗakin.

Kallon ta ya yi tare da kau da kansa gefe ɗaya kafin ya ce.

"Kin ɗauro alwala?"

"Eh."

Ta bashi amsa a taƙaice.

"Okay ki shirya ga kayan barci nan na fito ma ki da shi."

Ya fadi haka yana nufar ƙofar bathroom ɗin ya shiga.

Kamar tana jiran ya shiga bathroom don haka cikin sauri ta shirya cikin kayan barcin da ya ajiye ma ta, don dogon wando ne har ƙasa, duk da dai bai fito ma ta da underwears ba amma gudun ya fito ya same ta haka nan ta saka kayan da sauri.

Dogon Hijabin da ya ajiye ma ta shi ta ɗauka ta saka.


_Ma'eesha_

Tana ƙarasawa gaban A.S.P Nasir Yusuf kiran wayar ta ya shigo wayarsa. Kallon wayarta ya yi kafin ya kalli fuskarta kasancewar akwai hasken fitilu a Wajen.

Da mamaki yake kallonta daga sama har ƙasa mamaki bayyane akan fuskarsa.

"Ma'eesha?"

Ya kira sunan ta da alamar sigar tambaya. Kasa amsa ta yi hawaye na sintiri a idanunta. Wanda hakan ya ɗan tashi hankalinsa ganin yadda take kuka kuma da dukkan alama tana cikin tashin hankali.

"What's happening with you?"

Kukan ta ci gaba ta yi kafin ta durƙusa a gabansa akan guiwoyinta . Ganin haka ya sa ya kai hannu zai riko ta ya tayar da ita tsaye, sai ta yi saurin janye hannunta tana watsa ma sa wani kallo wanda hakan ya saka ya mike tare da mayar da hannayensa a cikin aljihun wandonsa.

"Kin tayar ma ni da hankali matuƙa ganin halin da kike ciki, ko dai an yi garkuwa da ke ne kika kuɓuto kika fara zuwa wajen mu?"

"Nasir don Allah ka taimake sa ka ceci rayuwarsa makaho ne shi baya gani, kuma baya da gata idan ba Allah ba."

"Kin ga ki kwantar da hankalinki ki yi ma ni bayanin komai yadda zan fahimta. Shin wane makaho daga ina kike kuma su waye suka kama Makahon?"

"Mijina ne makahon ban san su waye suka ɗauke shi ba, amma bayan na kira wayarsa sakamakon jin sa shiru da na yi. Sai wani ya dauki wayar yake sanar da ni Inda ya tsinci wayar. To bayan na je wajen ne shi ne ake sanar da ni wata mota ce ta ɗauke shi ta gudu da shi ana zaton criminals ne."

A.S.P Nasir Yusuf sagale ya yi yana kallon ta, don tun kalmar farko da ta ce mijinta ne ya saki ƙirjinsa duk da ya san cewa ba wai tana son sa ba ne, amma muna kalmar bai ji daɗinsa ba kamar yadda kowane mai rai da numfashi yake ji idan wacce take so ya ji ta ji aure. Amma sai ya dake bai nuna damuwa ko wani abu ba, hasalima ya ƙaƙaro murmushi yana cewa.

"Ma sha Allah, ashe yanzu matar aure ce ke. Yanzu na ji bayanin ki mu shiga ciki ki shigar da report na ɓatar nasa."

Yana fadar haka ya nufi hanyar komawa cikin station. Bin bayansa ta yi ta goge hawaye dake idanunta.


Bayan sun shiga ne ya sa aka ɗauki report nata, kafin Asp ya ce ta je gida za su yi bincike in sha Allah.

Kuka ta saka ma sa tana cewa.

"Ta ina zan koma gida bayan ban san halin da mijina yake ciki ba?"

Kin ga ki kwantar da hankali in sha Allah za mu yi bincike za mu gano shi. Yanzu dare ya yi ki koma gida in sha Allah a daren nan za mu fara bincike."

Sai da ya yi fama da ita sannan ta yarda za ta tafi kan gobe sai ta dawo ta ji halin da ake cik.

Amma kafin ta tafi ya nemi ta bayar da photon makaho, ƙaramar wayarta ta bayar bayan ta lalubo ɗaya daga cikin hotunan da take ɗaukarsa wanda bai na san tana yi ba. Don wannan yana zaune ne akan tabarma bayan ya cire bakin glass dake idanunsa ya lumshe idanunsa yana jingine da bango.

Bayan sun cire tura photo cikin na'urarsu ce suka ba ta wayar .

Tana fitowa waje ta fara tunanin abun yi don, don ko sisi ba ta d shi da za ta hau motsa ya koma gida.

Tsawon mintuna biyar tana tsaye cikin rashin sanin madafa ta fara tafiya ta nufi hanyar komawa gida, duk da ta san ba lallai ta iya yin doguwar tafiya a ƙafa ba.

Ta yi tafiya kamar na mintuna goma sai ta ji horn ɗin mota a gefenta, sai ta waiga ta ga motar ASP Nasir Yusuf ne ya tsaya.

Sai ta karasa wajan motar yayin da yake dauke glass ɗin motar.

"Ya na ga kina tafiya a ƙafa ina motarki take?"

"Ban zo da ita ba."

"Okay idan ba damuwa ki zo ba sauke ki a gida ko?"

"A'a ka bar shi kawai na gode."

"No kada mu yi haka da ke, ki shigo kin ga dare ya yi ko?"

"LBa tare da ta sake wata magana ba ta buɗe gaban motar wajen me zaman banza ta shiga.

Ba ta yi magana ba

"Wace unguwa kuke?"

Ta fada ma sa sa sunan unguwar.

Bayan sun kai unguwar kasancewar ASP Nasir bai taɓa shiga cikin unguwar ba ya yi mamaki ganin yanayin unguwar na marasa ƙarfi, wanda bai kamata a ce kamar Ma'eesha Ibrahim Khalil ƴa ɗaya tilo ga attajirin irin Alhaji Ibrahim Khalil ke rayuwa a ciki ba. Wanda ko da a ce Direban ko mai gadinsa ne zai iya ba su lafiyayyan gidan da za su zauna ballantana a ce ƴarsa ce ke rayuwa a unguwar.

Daƙyar motar je bin hanayar yayin da mamaki fal a zuciyar ASP Nasir amma ya kasa magana.

Sai da suka kai kofar gidan zuwa lokaci n karfe sha ɗaya na dare ne.

Bayan ta sanar da shi sun iso ne ta ɗan kalle shi ta ce .

"Na gode Yaya Nasir Allah ya saka da alkhairi ya sa ka fi haka."

"Ina ne gidan mijin naki?"

Da hannu ta nuna ma sa kofar gidan, ya kalli gidan da mamaki ya ce .

"Anya ke ce kuwa Ma'eesha da na sani?"

"Eh ni ce ɗin dai da ka sani ikon Allah kenan ya fi gaban mamaki. Alhamdulillah ala kulli halin."

"To amma me ya...?

Ɗaga ma sa hannu ta yi alamar dakatarwa kafin ta ce.

"Don Allah kada ka tambaye ni komai, sai da safe."

Ta buɗe murfin motar ta fita ya bi ta da kallo har ta shige cikin gidan.


_Nadra_

Tana nan tsaye a har Fahad ya fito daga cikin bathroom ɗin.

Ɗaure yake da towel a ƙugunsa sai wani karamin yana tsane ruwan kansa.

Kallo ɗaya ta yi masa ya kau da kai da sauri gabanta na tsananta faɗuwa.

Closet ɗin sa ya shiga ciki.

Tana nan tsaye har ya fito sanye da farar jallabiya sai zuba ƙamshi yake yi.

Sallaya ya shimfida ma su sannan ya zuba ma ta rikitatun idanunsa.

"Bismillah."

"Na yi sallah ni."

"Ni ma na yi wanann nafila ce za mu yi."

Take gabanta ya tsananta faɗuwa sai yanzu ta fara gane manufarsa.

Narai-narai ta fara yi da idanu tana shirin yin kuka.

Bai kalli fuskarta ba cikin bayar da umarni ya ce .

"Ke nake jira ki zo mu yi sallar."

A hankali ta karasa wajen sallayar tana hawaye.

Sallah raka'a biyu suka gabatar bayan sun idar ya yi masu addu'a sanan ya rike goshinta ya yi addu'a.


*Maman Ihsan ce.*


09065327995

*MAKAHO NE*


*NA*

Maman Ihsan ce ✍️


https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️


page4️⃣0️⃣


Sallah raka'a biyu suka gabatar bayan sun idar ya yi ma su addu'a sannan ya riƙe goshinta ya yi addu'a.

Bayan ya gama ya cire hannunsa tare da nazartar yanayin ta. Jikinta har rawa ya fara yi kuma zuciyarta cike da tsoro take a wajan .

"Zan tafi ɗakin Mama na kwana a can."

"Ko saboda me za ki je can ki kwana?"

"Kawai dai zan tafi ne."

"Ba ki da hujjar zuwa dakin Mama ki kwana bayan ga ɗakin mijinki nan ya fi cancanta ki kwana. Ita ma Mama da ace Baba na ƙasar part ɗin sa za ta kwana tare da shi."

Hawaye ne ya fara zarya a saman fuskarta wanda hakan ya saka ta sunkuyar da kanta ƙasa .

"Me na yi ma ki na kuka ne kuma?"

Kai ta girgiza alamar a'a kafin ta cigaba da cewa.

"Ni dai ba zan kwana tare da kai ba tsoro nake ji."

Wani dariya ya yi kafin ya ce.

"Tun yanzu har kin fara jin tsoro na, to za ki huta ai ƙasar zan bari gobe in sha Allah. Amma kafin nan sai na more."

Kafin ta yi magana ya ɗaga ta cak ya nufi tangamemen gadonsa da ita a hannu.

Kuka mai sauti ta sakar ma sa tana cewa .

"Yaya Fahad Please kada ka yi ma ni komai ba zan iya ba."

"Calm down ba abun da zan yi ma ki kina ji na ko? Ki kwantar da hankalinki. Idan kuma ba haka ba ke ce za ki sha wahala."

Da sauri ta goge hawayenta tana cewa.

"Za ka bar ni na yi barci ."

"Eh amma sai kin nutsu."

Jin haka ya sa ta sake ƙudundune jikinta cikin Hijabin dake jikinta.

Juyawa ya yi ya nufi closet ɗin sa. Tana nan tana raba idanu ta gan shi ya dawo babu riga a jikinsa sai wando three-quarter fari. Har ta ɗauke idanunta daga kallonsa sai ta yi sairin dawo da idanun ta gefen ƙirjinsa zuwa damtsen hannunsa an yi zanen Tattoo har da sunan Sidra da hoton butterfly.

Tsaya wa ta yi tana kallon Tattoo ɗin da sunan Autyn nata.

Rage hasken ɗakin ya yi bayan ya haura saman gadon.

Janyo ta jikinsa ya yi ya haɗa ta da jikinsa. Sannan ya zare ma ta hijabin dake jikinta ya sake manna ta da jikinsa.

Buɗe ba ki ta yi da niyyar yin ihu hakan ya ba shi damar saka bakinsa cikin nata ya fara kissing ɗin ta. Hawaye kawai ke ambaliya a idaninta, tsawon mintuna biyar ya ɗauka yana tsotson bakinta kafin ya zare bakinsa a hankali.

Ya mayar da fuskarsa cikin wuyanta yana shinshina, hannunsa ɗaya kuma ya zira cikin rigarsa yana shafa fatar jikinsa. Nan hankalin sa ya kara tashi saboda laushin fatarta.

A kiɗime ya raba ta da kayan barci da ke jikinta.

Shafar ta yake yi ta ko ina tun daga saman ta har ƙasanta, dukiyar Fulaninta a tsaye ƙyam ƙyam kamar an hura balloons. Hankalinsa ya kara tashi cikin rawar jiki ya kai bakinsa ya fara tsotson dukiyar Fulaninta kamar jaririn da ya kwana biyu bai sha nono ba. Yana tsotson ɗaya yana murza ɗaya .

Sarrafa ta yake yi ta ko'ina tun daga samanta har ƙasanta.

Lokaci ɗaya ya ƙara gigicewa ya fita hayyacinsa, sai wani gurnani yake yi kamar wani zaki.

Duk yadda Nadra ta so kwatar kanta a hannun Fahad kasa wa ta yi, don ganin ba za ta ba shi hadin kai ba ne ya sa ya sakar ma ta nauyin jikinsa. Ta yadda ba za iya iya tashi ba.

Kuma har lokacin kuka take yi tana roƙonsa kada ya kasance ta ba ta so amma baya jin ma tana magana .

Tsoro da fargabar ta ya kara tsananta ne lokacin da ta ji ya fara karanto addu'ar saduwa da iyali.

Duk da cikin duhu ne amma hakan bai hana ta girgiza kai alamar a'a ba. Hawaye duk ya gama wanke ma ta fuska ya jiƙa filon ta take kai.

Wani gigitaccen ƙara ta saki na azaba, ture shi ta dinga yi da hannayenta duka biyu iya ƙarfinta amma ta kasa. Wani ƙarar ta sake saki wanda ya fi na farkon saboda lokacin ne ya sake ratsa wa cikin jikinta.

Ihun da ta yi na biyu shi ne ya karaɗe ilahirin gidan. Sai dai babu wanda hankalinsa ya kawo wajen sai Sidra.


A figice ta mike tsaye daga kwancen da take cikin tashin hankali ta ɗora hannu akai tana cewa.

"Shi kenan na shiga uku ni Sidra, me kunne na ya ji yo ma ni ne?"

Kamar yanda wacce aka zabura ta mike ta fice daga dakin a guje.


_Makaho_

Bayan sun shaƙa ma sa powder da ya sa ya fita hayyacinsa bai sake sanin kansa ko in da suke ba.

Don a hankali ya ji kansa na juyewa yana ganin duniyar na juya ma sa .

Doguwar tafiya suka yi ba wanda ya yi magana kafin wani ya yi magana ya ce.

"Wai su waye suke bin mu a baya ne?"

Wanda ke zaune a baya da suka saka makaho tsakiya ne ya yi maganar.

Direban ya ce .

"Ban san su waye ba, sai dai ina fatan ba jami'an tsaro ba ne, don idan su ne akwai matsala babba."

Matsalar me bayan mun ɓacewa ganinsu, ai ba wata matsala.

"To idan ba wata matsala me zai saka take muna ɗaukarsa muka saka a motar take su ma suka ma ta ma na baya ko wajan ba mu bari ba sun bi mu, idan ba jami'an tsaron ba ne hakan yana nufin waɗan nan mutanen suna ba wa makaho kariya kenan."

Direban ne ya yi maganar yana jinjina kai, kafin ya dora da cewa

"Ko su waye tabbas kariya suke ba shi ba tare da saninsa ba."

"Haba dai wani irin kariya za su ba shi wanann makahon da ba shi da gata bai da wani tsayayyen mutum da zai tsaya ma sa ne za'a sami ma su ba shi kariya?"

Direban ya ci gaba da cewa.

"Abun da yake ba ni mamaki kenan amma ko ka mene ne ta faru dai ta kare."

Sauka suka yi daga saman titin suka dauki wata hanya. Bayan gari n don ba gine-gine a wajan ko alamar mutane.

Daidai wani gidan gona suka yi parking motar a wajen gate ɗin.

Suna gama parking wani mutum dogo yana da ƙiba ya fito daga gida gidan gonar.

Kai tsaye motar ya nufa wanda ganinsa ya sa duk suka fito sai makaho dake kwance a bayan motar.

Buɗe ma sa murfin motar aka yi ya kalli Makaho, sannan ya sune yaran nasa ɗaya bayan ɗaya ya ce.

"Aikin ku ya yi kyau."

Ya yi ma su alamar jinjina da hannunsa. Sannan ya ciro wayarsa a cikin aljihunsa, wata lamba ya danna wa kira kafin ya kara wayar a kunnensa.

Bayan sakanni ya ji murya daga cikin wayar ana cewa.

"Ya ake ciki ne sun iso?",

"Eh sun iso."

"Okay Ina son ka ɓatar da shi ya bar duniyar gabaɗaya. Zan tura maka cikon Naira miliyan goma."

Daga haka ya katse kiran wayar daidai lokacin da wata mota ta iso wajen a guje.

Kallo ɗaya suka yi wa motar nan suka gane ita ce wacce ta bi bayansu bayan sun ɗauki makaho, sai dai bayan suna ganin kamar sun tsere ma ta ne ashe ba haka ba.

Wasu gardawa ne guda biyu suka fito daga cikin motar. Yayin da ogan wadanda suka sato Makaho yake kokarin ciro bindiga daga cikin aljihun wandonsa.

Cikin ƙwarewa da zafin nama wannan da suka zo ƙwatar makaho ya yi saurin Harbin hannun wando ya ciro bindiga wanda hakan ya saka ya saki bindigar ya durƙusa a Wajen.

Sauran mutane biyun kuwa suna ganin an karbi ogan nasu sai suka ruga a guje, sai dai dukkannin su biyun ba wanda ya tsere domin sai sa aka harbi kowa a ƙafa. Take suka zube suka kasa tafiya sai ihu. Shi kuma ogan ya yi saurin ɗaukar bindiga da niyyar harbi sai aka dayan hannun kuma wanda ya ɗauko bindigar da shi.

Nam ya saki ƙara ya kwanta don suka hannun akwai harbi ƙafarsa ma .

Take ya fara ihu yana roƙon taimaka ma sha a bar su da kansu kar su kashe su.

Wajen motar da makaho ke ciki suka nufa. Nan suka gan shi kwance a bayan motar.

Suka ɗauko su sannan suka saka shi a cikin motarsu suka bar wajen.

Suna barin wajen kira ya shigo wayar ogan sai sai ba hannun da zai ɗauki kiran wayar da shi.

Sau uku ana kira ba hannun ɗaga wayar, shi sauran yaran nasa kuma duk an harbi ƙafarsu.


Makaho na kwance a bayan motar amma ya kasa ko da motsi ne, sai barci kawai da yake aikin yi.

Su biyu suna gaba yayin da shi kadai ke kwance a bayan motar .

Wanda ke zaune a kujerar me zaman banza ne ya kalli wanda ke driving ya ce.

"Na kira sir na faɗa ma sa ko?'

Kai ya jinjina ba tare da ya yi magana ba, sai bayan wasu sakanni kafin ya ce .

"Sam na kasa gane dalilin da ya sa waɗan nan abubuwan."

Ya yi maganar cike da takaici.

Daidai lokacin wanda aka kira a wayar ya ɗaga tare da cewa.

"Assalamu alaikum."

"Wa'alaika salam, sir mun samu kuɓutar da shi amma yanzu baya cikin hayyacinsa."

Ɗan jim ya yi kafin ya ce .

"Ina fatan ba su cutar da shi ba ko?"

"No sun dai bugar da shi ne kawai, kuma Allah ya sa muka je akan lokaci ba tare da wani abu ya faru da shi ba ko sun yi ma sa wani abu."

"Gud job."

"Thank you sir."

Ya faɗa yana kallon wanda ke driving ko zai yi Magana, girgiza ma sa kai ya yi alamar a'a kafin ya ce .

"Sir mu mayar da shi gida ne yanzu?"

"No ku bari ya dawo cikin hayyancinsa zuwa gobe sai a kai shi."

"Okay sir."

Daga haka ya katse kiran wayar yana sauke ajiyar zuciya .


_Ma'eesha_

Bayan ASP Nasir ya kai ta kofar gidan ta shiga gida sai ta ga gidan ya ma ta ƙunci da duhu. Wani irin kewar makaho take yi, duk da ba ta ci komai ba amma ba ta cikinta take yi ba.

A hankali ta mayar da kofar gidan ta kulle bayan ta saka sakata.

Tsaya wa ta yi tana kallon gidan na wasu mintinan kafin ta shiga cikin dakin bakinta ɗauke da sallama. Kayan jikinta ta cire ta je fito waje bayan ta ɗaura towel ta kuma daka hijabinta.

Kasancewar akwai wutar nepa gidan da haske.

Ta dauka bokiti ta ɗebi ruwa ta shiga banɗaki don yin wanka.

Ba jimawa sai ga ta daga wankan, ta dauki buta ta yi alwala sannan ya shiga ɗaki.

Bayan ta saka kaya ne ta ɗauki hijabinta ta hau kan sallaya .

Sallolin nafila ta yi tare da yi wa mijinta addu'ar Allah ya kuɓutar da shi ya ƙare shi a duk in da yake .

Sannan ta yi karatun Alkur'ani mai girma. Ba ita ta kwanta ba sai karfe biyun dare sannan ta kwanta .

Ga wani tsoron gidan da take ji.

A ranar ba ta iya lashe haske ba ta bar shi a kunne. Sannan kuma ba ta yi barcin kirki ba har asuba ta yi .

Kewar makaho ne fal a zuciyarta, don pilow da take kwance a kai duk ya jike da hawayenta.

Kuka take yi na tausayin mijinta da rashin sanin halin da yake ciki.

Da asuba ta tashi da ciwon kai sakamakon kuka da rashin isasshen barci da suka hadu ma ta .

"Adaddafe ta tashi ta kunna gas, ruwan ɗumi kadan ya yi wutar gas din ta yi low. Sakamakon ƙsraewar da gas din ya yi .

"Innalillahi wa'inna ilahir raji'un."

Shi ne kalmar da ta furta sakamakon ta san ba ta da ko Naira biyar a hannunta. Ballantana ta zuba gas, dai dai gawayin da take da shi wanda ba ta san ma yadda ake kunna murhun gawayi ba.


*Maman Ihsan ce*✍️


09065327995

*MAKAHO NE*


*NA*

Maman Ihsan ce ✍️


https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️


page4️⃣1️⃣

Shi ne kalmar da ta furta sakamakon ta san ba ta da ko Naira biyar a hannunta. Ballantana ta zuba gas , ga dai gawayin da take da shi wanda ba ta san ma yadda ake kunna murhun gawayi y.

Kashe gas din ta yi ta juye ruwan a bokiti sannan ta shiga banɗaki don yin wanka.

Bayan ta fito ne ta ɗaura alwala ta shiga ɗaki, dai dai lokacin ne nepa suka dauke wuta.

Duhu ya mamaye ɗakin, sai ta tuno da zancen makaho da yake ce ma ta shi ba wani banbanci a wajan sa da akwai wutar NEPA da idan babu, saboda duhu yake gani duka ko wani lokaci.

Wayarta ta laluba ta kunna torchlight sannan ta saka kaya ta yi sallar raka'atanil fijri.

Kafin aka kira sallar assalatu ta gabatar da sallar asuba.

Tana idar da sallar asuba ta zauna tana karatun Alkur'ani mai girma. Kafin gari ya waye sannan ta yi azkar din safiya ta .

Addu'a sosai ta yi wa mijinta kafin ta tashi ta fita.

Wanke-wanke ta fara yi bayan ta gama ne ta fara gyaran ɗaki. Daga nan ta fito ta gyara gidan.

Mutun hawayi Ta ɗauka tana kunnawa amma bai kama ba. Kamar za ta yi kuka da kasa takaici ga shi duk kayan jikinta sun yi baƙin ha88i8wayi duk sun ɓaci da gawayi


Dole ya saka ya je ta canza kayan jikinta, hijabi ya saka. Ka tsaye gidan da aka kai ta ta ƙi zama kafin suka kama haya.


_Nadra_


Ba ƙaranin wuya ta sha a hannun Fahad ba a wannan daren. Shi ma kansa ya ji a jikinsa. Don Nadra ba abinda ba ta yi ba don ta ƙwaci kanta a hannun Fahad. Ganin Fahad bai ba san tana yi ba gabaɗaya ya gigice akanta sai sambatu yake yi ma ta har da daka ma ta albarka yake yi tare da godiya na tsare mutuncinta na ƴa mace.

Nadra jin azabtar ta yi yawa ne ya saka ta kai ma sa duka da cizo har da yagushi don duk ta ji ma sa ciwo a fatarsa ta ji na sa ciwo har da cizo ya sha. Amma hakan bai sa ya saurara ma ta ba.

Tsabar azaba sai da Nadra ta sume ma sa a wannan daren . Don bai yi la'akari da cewa ita budurwa ce ba. Yai ne karo na farko da ta taɓa sanin Ɗa namiji, sannan kuma shi za ɗauki tsawon lokaci yana wahalar da rayuwarta.

Sai da ya samu natsuwa sosai kafin ya bar ta ta mirgina gefe yana mayar da numfashi.

Zuwa lokacin karfe uku na dare ne.

Shi a tunaninsu Nadra ta gaji da kukan ne ya saka ta yi shiru bai yi tunanin cewa sumewa ta yi ba.

Da sauri ya shiga bathroom ya yi wanka ya tsarkake jikinsa

Ba tare da ɓata lokaci ba ya yi wanka ya tsarkake jikinsa ya fito. Ka yi tsaye closet ɗin kayansa.

Fitowa yayi daga cikin closet ɗin ya kunna hasken ɗakin, kwance ya gan ta ba ta motsi kuma ba alamar numfashi. Ga jini nan a jikinta.

Dafe goshinsa ya yi tare da cewa.

"Ya Allah."

Ya ma rasa me zai yi lokacin da ta karasa baƙin gadon.

Ɗan girgiza ta ya yi ya ga ba ta numfashi. Ga shi irin jinin da ya gani ya tayar ma sa da hankali. Dole ya nemi taimako Don bai san yadda zai yi da ita ba.

Ruwa ya yayyafa ma ta amma ina ba ta farfaɗo ba, don haka hankalinsa ya kara tashi ya nufi ƙofar fita.

Downstairs ya nufa wanda tun kafin ya karasa sauka yake ji yo sautin kukan Sidra.

Tana zaune a kan sofa sai kuka take yi ta haɗa kanta da guiwa
.

Kin motsi an saukowa ta ɗaga kai ta kalle shi da idanun ta da suka rine suka yi ja.

Kallo daya ya yi ma ta ya dauke kai ba tare da ya ce komai ba .
Chapter 7 · 0% Book details