← Book details Makaho Ne Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
CHAPTER 2 OF 11

Part ɗin Fahad ta nufa don ta tabbatar ya shirya ganin karfe biyar ya kusa yi.

Makaho Ne Part 1 Complete Hausa Novel · about 56 min read

Da sallama ta shiga cikin falon, Sautin waƙar da bikin kawai ke tashi wasu na rawa yadda wakar ke ma su dad'i.

Hanyar bedroom ɗin Fahad ɗin ta nufa sai suka haɗu a corridor.

Shi ma angon ya yi dressing White and black. Yana sanye cikinsu tsadadden Suit ɗin sa baƙi, da farin shirt a ciki, ya sanya farin glass a idanunsa. Ƙafarsa sanye cikin cikin takaninsa cover shoe mai baƙi ƙirar Louis Vuitton mai ƙamshinsa mai dadi ke tashi daga jikinsa.

Hannunsa ɗaure da tsadadden agogonsa, ya yi masifar kyau wanda ya kara fito da ajinsa da kwarjininsa.

"Tabarakallah ma sha Allah, tsarki ya tabbata ga uban gijin da ya halicci wannan kyakkyawan angon."

Sai a lokacin ya lura da ita,kallonta ya yi fuska ba walwala .

"Na gaji da ganin wannan murtuƙewar taka haka, har yanzu kana tunanin Sidra ko?"

Bai ce komai ba ya kau da Kai gefe yana kallon wani wajen daban. Don haushin kowa ka yake ki a cikin Rayuwarsa


"Ka rungumi ƙaddararka a yadda ta zo maka Fahad. Don Allah ka yi kokarin cire Sidra daga cikin rayuwar ka, ka ɗauka ita ba matarka ba ce Nadra ce matarka. Dama can hakan Allah ya tsara, wata ba ta auren mijin wata, haka kuma wani baya auren matar wani. Ka rungumi Nadra ka yi irin rayuwar da ka tsara yi da Sidra da ita, ka ba ya kulawar da kake ba wa Sidra ka ƙunace ta kamar yadda ka ƙauna ci Sidra."

Girgiza kansa ya yi yana cewa.

"Ba na iya tunanin zan yi haka Sunyi Rahama."

Saboda ba ka son ta ko?"

Shiru ya yi ba tare da ya ce komai ba. Sai ya ji muryar ta tana sake cewa.

"Saboda ita ba fara ba ce iya ɓaka ce ya saka ba ka son ta masai Sidra baƙa ko?"

"Ba wannan ne kawai matsalar ba, ita wanann yarinyar sam ba ta waye ba, ta cika sanyi da yawa ga ta da zubin munafukai, ta dinga sunkuyar da kai wai ita mai kunya ni ba na son mace mai kunya, yadda kina san wata mutumiyar da can baya haka take sam ba ta waye ba. Wallahi ba na jin zan iya rayuwa da ita ba."

Murmushi Aunty Rahama ta yi tana cewa.

"Wannan ba matsala ba ne, kai za ka iya canz ta ta koma yadda kake so? Kai za ka koya ma ta son ka da irin rayuwar da kake so matukar bai sabawa addini ba. Don haka ka saki ranka don Allah ka daina wanann haɗe rai da kake yau rana ta musamman ce a wajanka ba ka ga yadda kowa ke farin ciki saboda kai ba, to kai me zai sa ka kasace cikin bakin ciki?"

Murmushi ya yi wanda iya fatar bakinsa ta tsaya sannan ya yi wa Zahrah Baby alamar ta zo.

Da sauri ta saki mahaifiyar tata ta nufi wajen uncle Fahad ɗin ta ta rungume shi.

Hannunta ya rike suka nufi falon Sunyi Rahama n jaddada ma sa wasu sun wuce ya je su dauki Amarya su tafi. Da to kawai ya amsa har ya karasa suke gaisawa da sauran wadanda suka zo ma sa .

Daga nan ne kuma aka fara fita don zuwa wajen Dinner party.

Shi ma fitowa ya yi suna tafiya yayin da Zahrah Baby ta nufi mahaifiyarta ganin za ta shiga wani motar.

Fahad kuwa wajen sabuwar motarsa wacce ya siya bai fara hawa ba sai yau, da burin yau ne zai fara hawanta shi da Sidra ashe ba haka ba ne shi da Nadra zai hau ta.

Wasu daga cikin abokan ango motarsu na cikin gidan suka shishshiga wasu kuma na su na waje ne suka dinga fita zuwa wajen motocin.


Wata galleliyar mota ƙirar Lamborghini urus ya nufa wanda yana ƙarasawa wajan motar sai ga diraba ya bude ma sa bayan motar, bayan ya shiga sannan ya rufe da hanzari direba ya nufi mazauninsa ya yi wa motar key suka bar gidan.

Jingina bayansa ya yi da jikin motar sit ɗin motar ya lumshe idanunsa ƙamshinsa da sanyin ac ke ratsa kowane sashe na motar.

A ƙofar gidansu Nadra direban ya yi parking don ya san inda za su fara zuwa kafin su tafi Dinner party.

Yana ƙarasawa ya ga motoci na barin wajen.


_Nadra_

Bayan an gama yi ma ta wani kwalliyar ne aka fito da kayan da za ta saka.

Karɓa ta yi ta warware kayan ta juya gaba da baya ta kalle shi da kyau sannan ta ce.

"Yanzu Wai wannan kayan kuke tunanin ni Nadra zan saka?"

Gwaggo Laraba da mai kwalliyar sai wata ƙanwar Umma daje ɗakin suka kalle ta. Kafin su yi magana ta ce .

"Ku duba fa ku gani kayan ko hannun arziki bai da shi hannun ƙarani ne ga shi gaban rigar irin mai bayyanar da ƙirar halittar mace ne, wato shape ɗin ƙirjinta, don an yi ma sa gidan breast .

Yanzu dama ranar da Aunty Sidra suka fita da Yaya Fahad ta ce za su je siyan rigar da za su yi Dinner party da shi wannan kayan suka siyo? A yanzu a matsayin ta na matar aure ne za ta saka wannan kayan ta fita cikin jama'a ana kallonta? Shi ma Yaya Fahad da suka fita zaɓen kayan ya san wannan kayan suka zaɓo zai bar matarsa ta saka ta shiga cikin jama'a maza da mata?"

Ƙawar Umma mai suna Hajiyayye ta kalli Nadra ta ce.

"Daughter ki yi hakuri ki saka ku tafi ga angon can a mota yana zaman jira da?"

Kwaɓe fuska ta yi tare da cewa .

"Ba zan iya saka wannan kayan ba?"

Yar Abba Gwaggo Maimuna ce ta daka wa Nadra tsawa ta ce.

"Za ki saka ku tafi ana jiran ki ko sai na ɓata ma ki rai yanzu?"

Kasancewar Gwaggo Maimuna tana da zafi sosai ko Abba shakkarta yake yi, family ba wanda baya tsoron ta.

Gwaggo Laraba dai ba ya ce komai ba, don ita ma ta ga rashin dacewar kayan a wajen mace mai kunya wacce ta saba shigar mutunci da kamala ba za ta iya saka kayan nan. Kuma ta ga laifin Fahad wanda aka ce shi da Sidra suka zaɓo kayan, wani irin rashin sanin ya kamata ne ya bari matarsa ta shiga jama'a da wannan kayan, idan Sidra ba ta da hankali ai shi yana da wannan ai ba wayewa ba ne, tana tsaka da wannan tunanin ta ji muryar Gwaggo Maimuna na cewa.

"Nadra idan ba ki saka kayan nan kun tafi ba wallahi yanzu zan saka a danne mani ke na saka ma ki kayan nan ta karfin tsiya, ita Sidra da za ta saka me kika fi ta ne, ko ita ma ta san ciwon kanta ba sai ke ce mai sanin ya kamata, to sannu uztaziyya."

Gwaggo Laraba za ta yi magana kenan sai Gwaggo Maimuna ta ce .

"Ki yi Mani shiru Laraba idan aka biye ma ki yarinyar nan ba za ta saka kayan nan ba, don ba zan iya lallaɓa ta da kike yi ba, tun dazu sai bata wa mutane lokaci take yi ana ta jiranta."

Ba yadda Gwaggo Laraba ta iya saboda Gwaggo Maimuna yayarta ce, kuma ko mahaifun Nadra ne idan ta yi magana baya yi ma ta gardama don haka ta jinjina wa Nadra kai tana ma ta murmushi alamar ƙwarin guiwa.

Don haka Nadra ta saka kayan wanda ya yi masifar yi ma ta kyau, sai dai sun kama ta duk shape ɗin ƙirjinta ya fito da hips ɗin ta ma su ɗaukar hankali.

Dogowar rigar irin wanda bayansa je sharar ƙasa ne idan tana tafiya.

Kuka take son yi sai Gwaggo Maimuna ta ce.

"Ki haɗiye kukan nan kar ki kuskura ya fito waje."

Jin haka ya fasa kukan ta haɗiye shi mai kwalliya ta gyara ma ta in da hawayen ya zubo.

Ita ma kayan nata white and black ne, don rigar dari da baƙi ne sai mayafin kamar net da ka daura ma ta ne fari zalla.

Sarƙar gold ɗin ta aka saka mata a kunne da wuya sai hannu da yatsu wato warwaro da zobe. Da aka saka ma ta. Sai wani takalmi mai tsawo sosai da tsini ta saka. Wanda tsinin takalmin ya yi yawa. Kuma dama ita ba ma'abiciyar saka dogon takalmi ba ne duk, takalmi mai tsawo ba ne flat shoe take saka wa.

Haka ba yadda ta iya ta zira ƙafa tana kallon su yayin da mai kwalliyar ke yi ma ta hoto.

"To sai ki fita ki je ga angon nake can yana jiran ki."

"Ango na muka Gwaggo?".

Sai a lokacin Gwaggo Maimuna ta san cewa ta saki layi.

"Au angon Sidra nake son cewa fa."

"Ni wallahi da ta dawo na yanzu na huta da wannan masifar, ga shi wani gyaran jiki ne tun safe har yamma ba ta dawo ba?"

"Za ki wuce ko sai na ɓata ma ki rai?"

Tafiya take yi a hankali kasancewar ba ta iya tafiya da irin takalmimin nan ba.

Salma ƴar Gwaggo Laraba ke bin bayanta za ta taka ta wajan motar, don ƙawar ta A'isha Humaira ta wuce gida bayan ta yi sallar la'asar.


Yana zaune a bayan motar har lokacin idanunsa a lumshe suke.

Kamar an za ce ya biɗu lumtsatstsun idanunsa ya sauke su akan ta ta jikin mirror ya hago ta tana tafiya kamar wacce take tausayin ƙasa ta nufo motar .


_Makaho_

Bayan fitar Ma'eesha da ne ya samu ya kwanta a saman zanin da ta shimfida ma sa, sakamakon rashin rarcin da bai yi ba, don ko na mintuna biyar bai yi ba, ta sakamakon kwana da ya yi a zaune yana aiki. Yi wa Ma'eesha tare da kore ma ya sauro.

Yana kwance a saman zanin yana tunani sabuwar rayuwar da za su yi da Ma'eesha. Lallai dole ya tashi ya nemi abun yi saboda ya rike ta duk da ya san cewa ba zai iya ɗauka ɗawainiyar ta ba bisa la'akari da irin rayuwar da ta ta so ta saba da shi, da kuma abincin da ta saba ci da irin ruwar da ta saba sha da makwancinta da suturarta da mayyukan shafawarta da turarruka da ta saba amfani da su. Ta ya Ma'eesha za ta zauna da shi.

A tunaninsa ba za ta yarda ta zauna da shi ba, ya ɗauka za ta ci mutuncinsa ne ta wulakanta shi ta sa ya sake ta amma sai ya ga ba ta dauki rayuwar da zafi ba ta rungume kundin ƙaddararta, ta yarda tare za su yi karatun tare za su yi hadda sannan kuma tare zasu koka. Tabbas samun mace irin Ma'eesha a wanann zamanin sai an bincika.

Yana ta tufka da warwara har barci ya yi awon gaba da shi nan kwance akan zanin da ta shimfida ma sa .


_Ma'eesha_

Tana fita daga cikin gidan ta tari mai keke nape, bayan ya tsaya ya kalle ta ya ce

"Hajiya ina zuwa?"

"Mallam ka san in da ake siyen waya na hannu?"

"Eh na sani Hajiya, sai sai gaskiya ba su siye da daraja ba, yadda kika san ɓarayi haka suke, za ki siye waya da tsada amma su siye shi a wulaƙance. Amma idan kika je siye a wanensu tsada za su yi Maki."

"Mu je ka kai ni lalura ce ta saka zan siyar."

"To mu je amma ba lallai sun fito ba don sai karfe tara zuwa goma suke fitowa ."

"To mu je idan sun fito na siyar za ka kai ni kasuwa na yi soyayya sai mu kwashi kayan ka kai ni gida."

"To Bismillah."

Ta shiga suka ɗauki hanyar zuwa kasuwar.


Cikin ikon Allah suna ƙarasawa sai ga wani yana kokarin bude shago, da alama shi kadai ne ya fara fitowa .

Kashe kake nape ya yi ya yi ma ta jagora yana cewa.

"Mu je Hajiya."

Tana bin sa a baya suka shiga shagon da sallama.

Mai shagon ya amsa yana kallon su.

"Me kuke so?"

Ma'eesha ta ce

"Waya zan siyar Mallam?"

"Wace irin ce?"

"Iphone 15 ne."

Sai da ya tsaya ya kalle ta da kyau daga sama har ƙasa ya kare ma ta kallo ya tabbata ba ta yi kama da wacce za ta kawo ma sa wayar sata ba.

"Kawo mu gani."

Handbag ɗin ta ta buɗe ta ciro wayar ta ba shi sannan ya karba ya duba da kyau. Kafin ya kalle ta ya ce.

"Na gaji zan siye ta Naira dubu dari huɗu 400k."

Wani kallo ta yi ma sa ta ce.

"Mallam ka san nawa aka siya mun wayar nan kuwa? Ko wata biyu ba'a cika ba da mahaifina ya siya ma ni ita miliyan daya da dubu ɗari biyar na kawo ta yanzu za ka siye ta a wulaƙance?"

"To Hajiya ai ma na siye da daraja idan wasu na Naira dubu dari uku da hamsin za su siye ta, waya ko yau kika siye gobe kika kai kasuwa sai ta karye kin sani."

"Ban sani ba don ban taɓa siyar da waya ba sai sai na kyautar, wanan karon ma ƙaddara ce da ba za ka ganni a nan ba."

"To gaskiya zan siye ta dubu ɗari huɗu da hamsin."

"Don Allah ka kara Mallam wallahi matsala ce ta saka na siyar da wayar ba komai ba, lalura ce."

"Na sani don daga ganin ki kina cikin matsala, don haka zan tausaya ma ki na dutse dubu ɗari biyar 500k idan bai yi ma ki ba ki dauki wayarki ki tafi ."

Shiru ta yi tana mamakin wannan son zuciya a ce a cikin wata biyu ka yi asarar miliyan ɗaya ko rabin kudin ba za'a baka ba."

"Ka siye ko 700k ne mana."

"Ba wanda zai siye wayar nan a haka don sai a daɗe ba'a samu mai siye ba."

Sanin ba ta da wani zaɓi kuka tana bukatar kuɗi don ba ta da shi ya saka ta ce.

"Kawo kuɗin."

"Me nape ya yi saurin cewa.

"Hajjya kada ki siyar da wayar nan ki koma da abun ki gida ki yi hakuri."

Murmushin takaici ta yi tana cewa.

"Dole ne na siyar da wayar ba na da wani zaɓi ne."

"To ki jira wasu su zo sai ki yi ma su tallah."

"Ko sun zo farashi daya muke siyan kaya."

"Gaskiya ba ku da imani."

"Kar ka faɗa mani maganar banza akan sana'a ta, daga ganin ka ma kai karere ne.Hajiya iya dubu ɗari biyar idan ba ki siyar ba sai Anjima."

"Kawo kuɗin."

Ta fada kamar za ta yi kuka.

Ta cire sim da memory card, sannan ta sauke email ɗin ta dake kan wayar, ta goge komai sannan ta bashi wayar?"

"Cash zan baki ko na yi na ki transfer?"

"Cash za ka bani."

Ya ba ta bandir na dubu ɗari guda biyar ta karba ta zuba a handbag suka fice da mai nape

Bayan ya tayar da nape ya ce

" ina za mu je."

"Kasuwa za ka kai ni?"

"Wace kasuwa?"

"In da zan samu kayan ɗaki ma su sauƙin kuɗi. Kamar katifa, pillow da sanin gado leader carpet da labulaye sai sauran kayan aikin da ba'a rasa ba."

"Okay Hajiya Allah ya kai mu lafiya."

Da haka ya dauki hanyar da zai kai Ma'eesha ta yi siyayya.


_Nadrah_

Tafiya take yi kamar mai jin tsoron ƙasa, don tsakanin ya ba ta wuyar tafiya, bugu da kari ga kayan jikinta da ta kasa saukewa a cikinsa.

Abun ya hadu ma ta biyu ga kaya ga takalma, duk sun takura ma ta.

Hannayen ta biyu ta saka tana kare ƙirjinta wanda rigar aka yi shi da gidan breast. Karon farko kenan a rayuwarta da za ta fita babu hijabi ga shi kayan ba yadda take so ba.

Ta cikin mirror Fahad ya kalli yadda take kare ƙirjinta tana tafiya kamar za ta faɗi, gajeren tsuki ya ja yana mai jin takaicin yanayin yadda take yi don za ta iya kunyata shi a gaban jama'a, ga manyan baƙin da abokansa da suke masa kallon wayayye mutum mai ji da kai da aji.


*Mamman Ihsan ce*✍️

09065327995

Follow the TASKAR MAMAN IHSAN channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaiufWb3LdQYnzC2vH0z


*MAKAHO NE*


*NA*

Maman Ihsan ce ✍️


https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️


page0️⃣7️⃣

Ta cikin mirror Fahad ya kalli yadda take kare ƙirjinta tana tafiya kamar za ta faɗi, gajeren tsuki ya ja yana mai jin takaicin yanayin yadda take yi, don za ta iya kunyata yi don za ta iya kunyata shi a gaban jama'a, ga manyan baƙin da abokansa da suke masa kallon wayayye mutum mai ji da kai da aji.

Dauke idanunsa ya yi ransa ya na ɓaci, a hankali take tafiya har ta karaso wajen motar.

Da sauri Direban ya fito ya buɗe mata murfin bayan motar ganin za ta buɗe.

Kallonta ta yi ya gaishe ta da cewa.

"Ina wuni Madam?"

"Kai kawai ta jinjina ma sa ba tare da ta iya amsa wa ba."

Shiga bayan motar ta yi bakinta ɗauke da sallama.

"Assalamu alaikum."

Idanunsa na kan wayarsa bai kalle ta ba ya amsa sallamar ciki-ciki wanda ita kanta ba ta ji ya amsa ba shi kadai kawai ya ji kayansa.

Bayan ta zauna ne direban ya rufe murfin motar, ba abinda ke tashi a motar sai sanyin A.C da ƙamshin turarensa.

Duk da cewar tana cikin ɓacin rai da takaici amma haka.n bai hana ta ta gaishe shi ba."

"Ya Fahad ina wuni?"

Kamar ba zai amsa ba har ta fidda ran zai amsa sai ta ji ya amsa da.

"Kina lafiya?"

Ta amsa da Alhamdulillah kanta a sunkuye.

Direban ya ja motar suka bar gidan.

Sun ɗan fara tafiya ta kalle shi ta ce.

"Ya Fahad?"

Sai a lokacin ya ɗago kai ya kalle ta ba tare da ya amsa ba.

"Na ga kamar kana cikin damuwa ko?"

Bai ce ma ta komai ba sai dai ya ɗauka yadda ya saki ransa ba wanda zai gane yana cikin damuwa, tun da ita da yake ma ta kallon ba ta da wayau ta iya karantar yanayinsa ashe tana da wayau. Kuma kowa zai iya karantar yanayinsa. Kallon kayan dake jikinta ya yi wanda ya siya wa Sidra ne last week tare, hatta sarƙar gold ɗin da su warwaro da ɗan kunnen duka seti ne ya siya ma ta.

Bai ce ma ta komai ba kuma kamar bai ji tambayar da ta yi ma sa ba.

Sun yi nisa da tafiyar ne duk ta damu da kayan da za ta shiga cikin jama'a da shi, ta kalli jikinta ta fara maganar zuci wanda ya fito fili ɗin ba ta yi don ya ji ba.

'Mtswww, wannan wane irin iskanci ne ba in da zan fita da kayan nan na shiga cikin jama'a, don ni ba ƴar iska ba ce. Haba sai ka ce ba ƴar musulma ba Aunty Sidra ta zaɓo kayan nan a matsayin kayan da za ta shiga jama'a bayan an ɗaura aure tana matar aure? Kodayake ba laifn ta kaɗai ba ne har da laifin shi Mijin nata ta ya ya Yaya Fahad zai yarda ya siye wannan kayan matarsa ta saka sai ka ce wanda baya da kishin matarsa, zai so a kalli matarsa a haka cikin wanann shigar, kalli rigar ko hannun arziki babu ga ta an yi gaban rigar kamar na bra duk siffar kirjin mace a bayyane yake. Wallahi da na san har da wannan tsinannen Dinner party za'a ce wai na je a madadinta da islamiyya na wuce. Na samu lada da wannan bidi'ar da zan je. Ga Aunty Sidra har yanzu ba ta dawo daga gyaran jikin ba ta je da daɗe duk ita ta jawo Mani wannan abun. Idan Allah ya kai ni ranar aurena da Ya Sayyadina walima kawai za mu yi ayi lectures kan aure mallamai su yi wa'azi amma ba wannan bidi'ar. Ko ya Sayyadina idan ya ganni haka sai ransa ya ɓaci.'

Fahad idanunsa na kan wayarsa ne amma duk maganar da take yi a kunnensa, ita ba ta san a bayyane ta yi maganar ba. Kuma yanzu ne ya tabbatar da cewa iyayenta ba su faɗa ma ta cewa an ɗaura auren da ita ba, to amma ai da sun sanar da ita musamman da suka san akwai saurayin da take so wato Ya Sayyadi. Shi kansa Fahad ya san Ya Sayyadi kuma Ya Sayyadi ya san shi shi ma. Saboda sau tari idan ya zo wajen Sidra ya kan ga Ya Sayyadi tare da Nadra kullum cikin jallabiya yake da hula taɓa ni ka ji hadisi yana zuwa ne da tsohon babur nasa kullun. Har Sidra ta yi ta faɗa wai me na sama zai ci ballantana ya ba na ƙasa Nadra ta rasa wa za ta so sai wannan abar da ba lallai ya iya ɗaukar ɗawainiyar ta ba, in ban da kuɗin Laraba da ke kai wa islamiyya me yake da shi. Ta tsayar da mai kuɗi ta aura cikin ma su son ta sai wannan ya Sayyadin mai gemu kamar na bunsuru, har wata rana Fahad ya yi Sidra faɗar abun da take yi wa Ya Sayyidi.

Yana tsaka da tunanin baya wayar ta fara ringing, sai dai har ta katse bai ɗaga ba.
Aka sake kiran ɗayar wayar nan ma bai ɗaga ba. Ta na kallonsa ta gefen ido a zuciyarta ta ce.

"Sun haɗu sun dace, don ita ma Sidra haka za'a dinga kiran wayarta ba za ta ɗaga ba sai ta ga dama.

Tana ganin an kawo wajen gabanta ya tsananta faɗuwa. Ita ma za ta iya fita a haka ba. Musamman da ta hangi cikar da aka yi, don ma ba ta shiga ciki ba.

Kowa white and black ne maza da mata.

Motar na tsaya wa sai ga mutane sun nufo motar ma su ɗaukar photo da ma su ɗaukar video wasu da wayoyinsu wasu da Camera 📷. An tsaya ana jiran fitowar Amarya da ango.


_Ma'eesha_

Mai keke napep ɗin bai dire ta a ko ina ba sai gaban wasu shaguna dake bakin titi.

"Hajiya yanzu ba'a fito a kasuwa ba, don sai zuwa karfe tara ko goma idan kina son wasu kayan da kike so za ki iya samun su a nan, idan kin kai su gidan sai mu dawo na kai ki kasuwa."

"Okay."

Ta faɗa tana fitowa shi ma ya kashe keken ya zare key sannan ya bi bayanta.

"Shagon katifa ne da su pilows ake siyarwa, ta siye madaidaicin katifa ba mai girma ba, ta siye pillow guda biyu ta biya kuɗin, ma keke napep ɗin ya ɗaure katifar da pillow ya ɗaura a keke nape ɗin, sannan ta shiga shagon dake kusa da wanda ta siye katifa. Ta siye zanin gado kala biyu da labule guda biyu, sannan ta siye leader carpet, saboda ta san shi ne mai sauƙin kuɗi.

Za su wuce sai ta ga shagon dake kusa da in da ta yi siyayya.

Ana siyar da kayan kitchen.

"Ka ga bari na shiga can na duba abind da zan buƙata."

"To Hajiya."

Daga nan ta nufi cikin shagon don ta ga kayan da take buƙata.

Tukunya guda biyu ta cire gefe mai ɗan girma da karami, sai ta siye tukunyar suya sannan ta siye set ɗin food flask mai guda uku a kwali ta siye cokular cin abinci guda shida na cin taliya wato fork guda uku, ta siye plate na cin abinci ma su fadi guda huɗu ma su zurfi ƙanana guda hudu da service spoon, sai babban tire sai kofin shan ruwa huɗu na shan shayi ko kunu guda huɗu. Ta siye rariya da cikakin girki

Lissafi aka yi ma ta ta biya kuɗin sannan mai napep ɗin ya ɗauki kayan da ta siyo ya saka a bayan keken.

Sannan ta tuna da robar zuba ruwa wato duram ɗin roba ta siye da bokitin roba guda biyu da baho madaidaita biyu da robar ɗiban ruwa. Ta gama abinda za ta siya
ta yaya wannan bangaren.
Sannan ta shiga ganin keken ya ya cika da kaya yawa.

"Mallam mu je ka kai ni gidan idan na ajiye sauran kayan sai mu dawo ka kai ni in da zan siye kayan abinci sai ka mai da ni gida ."

"To Hajiya Allah ya kai mu lafiya."

Da Amin ta amsa , daƙyar da ita gane layin, don dama dai ta san sunan unguwar, amma layin ne ya ba ta wahalar gane wa sakamakon lungu ya yi yawa a unguwar.

A ƙofar gidan ya sauke ya tsaya sannan ya fito daga ciki yana fito da kayan.

Kasancewar ba kaya ma su nauyi ba ne, ya saka yana ajiye wa tana ɗauka tana kai wa cikin gidan.

Bakinta ɗauke da sallama ta shiga cikin gida.

Daga cikin ɗakin ta ji muryarsa ya amsa ma ta da

"Wa'alaiki Salam warahmatullah."

Ya fito rike da sandarsa ta jagora, sai dai ya canza kayan jikinsa ba wanda ta bar shi da shi ba ne, wannan farare ne su ma yadi ne ma su sauƙin kuɗi wanda aka cewa Yi shirunka maraya.

"Ma'eesha kin dawo ne?"

"Eh."

Ta fada tana ajiye katifar wanda aka ɗaure su da filo a hannunta a saman barandar.

Komawa ta yi ta ɗako sauran kayan, sau uku tana fita tana kwaso kayan kafin ta gama ta kalle shi ta ga ya yi tsaye yana rike da sandar jagoransa. Kansa a ƙasa kamar mai karantar wani abu.

"Ban gama siyayyar da zan yi ba, mai napep na jira na a waje, zan koma na karasa sai na dawo na nema ma na abun da za mu yi breakfast. Don yanzu karfe goma ake nema, ni dama ina kai karfe goma sha ɗaya ko sha biyu ban yi breakfast ba, don haka kai nake tunani."

Murmushi mai ciwo ya yi tare da cewa.

"Ma'eesha ke nake ji da sabuwar rayuwar da kika tsinci kanki a ciki, ni kada ka damu da ni, wata rana sau ɗaya nake cin abinci a rana. Ko ina jin yunwa ba na da mai bani abinci, sau ranar da Allah ya saka naje gidanku idan mahaifiyarki ta bani nake ci, duk da ta ce na dinga zuwa kullum ina cin abinci ba na iya wa, sai dai duk sati nake kai mata ziyarar juma'a wato duk ranar juma'a, ranar ne nake ci na ƙoshi , wata rana ai ke take saka wa ki zuba Mani wanda zan tafi gida da shi, Allah ya jiƙanta da rahama ya sa aljanna ce makomarta, halinta nagari ya bi ta."

Kuka ne ya suɓuce wa Ma'eesha tuna mahaifiyar ta da Fahad ya yi ma ta, ji take ina ma tana da dangin mahaifiya da can za ta tafi ko ta samu sassauci abinda yake ranta. Ita kanta ba ta san yaushe ne za ta daina kukan mijin marainiya ba, amma tana ji a ƙasan ranta wata rana za ta yi dariya.

Sallamar mai daidaita sahun dake jiranta ya sa ta goge hawayenta da sauri ta fice daga gidan ba tare da ta sake magana ba.

"Ka yi hakuri na bar ka kana jira na ko?"

"Ba matsala."

Ya fada yana yi wa keken burki suka bar kofar gidan.

Ganin tana ƙwalla ta cikin mirror yake kallonta ya ce.

"Hajiya lafiya?"

Sai sa lokacin ta lauba fuskarta ta ji hawaye ke bin fuskarsta

Da sauri ya goge.

"Ba komai Mallam."

"Anya kuwa ba komai?"

"Eh."

"To na ga kina kuka ne duk na damu."

Murmushin takaici ta yi tana cewa.

"Kawai na tuna da mahaifiyata ce."

"Allah sarki ki Allah ya jikanta da rahama."

"Amin na gode."

"Rayuwa kenan Allah ya ba mu guzurin cin ma su."

"Amin ya Allah."

Ta fada tana kau da kai gefe tana kallon titi.

Still hawaye ne dai ke yi ma ta zarya wanda duk yadda taso dakatar da hawayen ta kasa hakan .

"Yana kallonta ta madubi ya ce.

"Aunty na ki yi hakuri Allah ya jikanta."

Ai kamar ya ce ta ci gaba dai ji ta yi ta fashe da kuka mai tsuma zuciya wanda tun daga kasar zuciyarta take jin ƙuna da raɗaɗin rasa mahaifiyarta, ga wani sabuwar rayuwa da ta tsinci kanta a ciki mai cike da ƙalubale, haƙika mutuwar mahaifiyarta ya durƙusar da duk wani motsi nata, ya gurguntar da tunanin gobenta. Wannan sabuwar rayuwa da ta shiga tamkar hanya ne mai cike da kwazazzaba da ƙayoyi. Jin yadda take kuka kamar za ta shiɗe ne ya saka hankalinsa ya tashi ya yi parking gefen hanya .


*Mamman Ihsan ce*✍️


09065327995

Follow the TASKAR MAMAN IHSAN channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaiufWb3LdQYnzC2vH0z


*MAKAHO NE*


*NA*

Maman Ihsan ce ✍️


https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️


page0️⃣8️⃣

Ai kamar ya ce ta ci gaba sai ji ya yi ta fashe da kuka mai tsuma zuciya wanda tun daga kasar zuciyarta take jin ƙuna da raɗaɗin rasa mahaifiyarta. Ga wani sabuwar rayuwa da ta tsinci kanta a ciki mai cike da ƙalubale, haƙika mutuwar mahaifiyarta ya durƙusar da duk wani motsi nata, ya gurguntar da tunanin gobenta. Wannan sabuwar rayuwa da ta shiga tamkar hanya ne mai cike da kwazazzaba da ƙayoyi. Jin yadda take kuka Kamar za ta shiɗe ne ya saka hankalinsa ya tashi ya yi parking a gefen hanya.

Ya juya ya kalle ta sai ya ga ta jaɗa kanta guiwarta, wato ta ɗora ƙafarta tana cigaba da kuka.

"Hajiya ki yi hakuri don Allah addu'ar ki take buƙata ba kuka ba. Domin wannan kukan ba zai amfane ta ba."

Ɗago kanta ta yi ta goge idanunta sa suka yi jajir sannan ta ce.

"Mu tafi."

Kunna nape ɗin ya yi sannan ya fara tuƙi a hankali don shi ma jikinsa ya yi sanyi sosai, yana son ya tambaye ya amma yana tsoeon amsar da za ta ba shi. Musamman da ya ga wayar da ta siyar ya san wace irin waya ce. Sannan ga shi yanzu bayan ta siyar da wayar irin kayan da take siye, kuma yadda ya ga take yi kamar ita ce za ta yi amfani da kayan, ga gidan da ta kai kayan sam gidan bai dace da ita ba.

Har suka ƙarasa kasuwa ba wanda ta sake yin magana s cikinsu.

Bayan ya yi parking a In da ya dace ne ya zauna ciki. Ta kalle shi ta ce.

"Mallam ko za ku je ka taimaka ma ni ban taɓa shigowa kasuwar ba, don ban san ta ina zan bi da ake siyar da kayan abinci kamar su shinkafa da sauransu."

"Okay mu je na nuna ma ki na ha kamar ke baƙuwa ce a garin."

Ya yi maganar ne don ya tabbatar da abun da ke ransa, ita kuma ba ta ce ma sa komai ba. Har suka ƙarasa wani layi.

"Yauwa Hajiya ga wani shagon za ki iya samun komai a ciki."

"Toh na gode Allah ya saka da alkhairi."

Da Amin ya amsa sannan suka shiga cikin shagon da sallama a bakinsu.

"Assalamu alaikum "

Wa'alaiki Salam warahmatullah."

Cewar wani matashin saurayi dake kusa da su. Don shagon babban shago ne mutane biyar ke sigar da kaya a ciki har da Alhaji me shagon yana zaune kan kujera yana lissafa babban calculator.

Matashin saurayin ya ce .

"Me da me za'a kawo?"

Ya yi maganar yana ajiye ma ta plastic chairs ta zauna tana ma sa godiya.

Bayan ta zauna ta ƙare wa shagon kallo dake da masu siyen kaya a ƙalla za su kai mutane goma.

"Ka bani karamin buhun shinkafa, da katon ɗin taliya da makarani kowane guda ɗaya."

Ta yi maganar tana nuna ma sa kalar wanda take so.

Ya dauko shi kafar da taliyar da macaroni ya ajiye ma ta .

"Ka kawo ma Ni buhun semolina da kuma cus-cus."

Ta ce ya kawo ma ta wani madaidaicin galan manja da man gyaɗa, sai wake mudu biyar.

Sannan ta saka shi ya kawo ma ta ledar Maggi know da kuma star, sai gishiri da su kayan ƙamshi . Sannan ta ce a kawo kwalin indomie.

Total aka yi ma ta ta biya sannan mai napep ɗin ya ɗauki kayan tana bin sa a baya rike da wanda za wanda za ta iya ɗauka. Suka nufi wajen keke napep ɗin.

Bayan sun saka kayan a baya ne ya kalle ta ya ce

"Ki zauna a ciki bari na kwaso sauran kayan."

Ba musu ta shiga ta zauna ya koma ya kwaso sauran kayan , sau biyu yana ki komawa.

A na karshe sai ga shi ya dawo tare da Alhajin nan mai shagon, wanda da dukkan alamu shi ne mamallakin wannan shago.

Washe ba ki ya yi ma ta yana cewa.

"Ƴan mata ya za ki tafi bayan kin sace ma ni zuciya."

Kallo ɗaya ta yi ma sa ta dauke kai.

Murmushi ya yi tare da cewa.

"Da alama wannan ƴan matan akwai jin kai, to a jiƙaina ko lambar waya a bani ba "

Kallon mai napep ɗin ta yi ta ce.

"Mallam mu tafi ma na."

"Don girman Allah ki saurare ni."

"Matar aure ce ni."

Ta fada a takaice.

"Subhanallah don Allah ki yi hakuri ban sani ba."

Daidai lokacin mai napep ya ja suka bar wajen.

"Yauwa na mance ina buƙatar Gas ƙarami kamar 3kg."

"To Hajiya zan kai ki in da za ki samu, ko za ki hada da murhun gawayi saboda yau da gobe wata rana Gas zai kare ba za ki iya fita ba sai ki zuba gawayi ki cigaba."

Ita dai ba ta san yadda za ta yi amfani da shi ba, amma ta amsa mai da to.

Ya kai ta ta siye Gas, a wajen da ta siye aka cika ma ta shi da Gas.sannan ya kai ta inda ta siye murhun gawayi da kuma wani ɗan ƙaramin buhu da aka zuba gawayi, ta siye ya ɗauka ya saka ma ta suka bar wajen.

"Mallam ina zan samu kayan miya?"

Daga cikin keken ya nuna ma ta . Ya zauna yana jiranta.

Ba jimawa ta dawo da manyan ledoji guda biyu cike da kayan miya, sannan ta kalle shi ta ce.

"Bari na siye dankalin turawa a can ."

Ta juya ta siye dankalin turawa da ƙwai kiret daya sannan ta dawo, ya ja napep suka bar wajen."

"Yanzu ina za mu je?"

Gida Mallam za ka kai ni "


_Nadra_

Ganin yadda ka zagaye motar da take ciki sannan ga ma su ɗaukar photo da video sun zagaye su ne ya saka ta kasa yunƙurin fitowa .

Sai sake noƙewa take yi ba ta ma da niyyar fitowa.

Direbansa ne ya zagayo ya bude ma sa bayan motar, a hankali ya ziro ƙafarsa ɗaya waje, sai da ya ɗauki seconds kafin ya dake ziro da ɗaya kafar waje. Sannan ya fito cikin takunsa na ƙasaita fuskarsa ba yabo ba fallasa.

Daidai lokacin Aunty Rahama ta karaso wajen tana Murmushi.

Da ido ta ma sa alamar ya riko hannunta su karasa wajan a tare.

Zagayawa ya yi gefen da take ya yi ƙasa da kansa saitin fuskarta ya yi magana ta yadda ita kadai za ta ji.

"Ko sai an fito da ke ne, ka da ku kuskura ko da wasa ki yi mani gidadanci anan, na san ki kamar bagidajiya haka kike, ina mamakin yadda zama da Sidra bai saka kin waye ba. Nan cikin jama'a ne akwai manyan mutane nan da suka halarci wannan taron har daga ƙasar waje wasu suke, ka da ki kunyata ni, be careful."

"Ƙwalla ce ta cika ma ta idanu."

"Kada ki mani kuka anan."

Ya faɗa yana ciro hankaci cikin aljihun Suit ɗin sa ya goge ma ta ƙwallar.

Tafi wasu suka hau yi don an ɗauka kalaman soyayya yake yi ma ta musamman da fuskarsa ke daf da tata.

Tana fitowa daga cikin motar aka fara watsa ma su wani fure mai ƙamshi.

"Ma sha Allah."

Aunty Rahama ta fada lokacin da ta yi tozali za Nadra.

Kasa ɗaga ƙafa Nadra ta yi sakamakon hangen jama'a da suke a cike a wajen, ga wasu na ɗaukarta video da photo.

Ganin ta coge tana tunani ya saka ya sakala hannunsa cikin nata. A bazata ta ji lalluasan hannunsa cikin nata hannun.

"A'uzubillahi minash a
shaiɗani rajim."

Ta furta tana kallon sa a razane, shi kam bai kalle ta ba yana kallon tarin jama'ar da bai yi zaton gani ba.

Koƙarin kwace hannunta take yi ta kasa.

Saboda riƙon da ya yi ma ta ba na wasa ba. Ba yadda ta iya haka ta dinga binsa kamar Raƙumi da akala. Sai dai kamar za ta yi kuka cike da shagwaɓa take cewa.

"Yaa Fahad please ka sakar ma ni hannu ba kyau haramun ne namiji ya taɓa wacce ba maharramarsa ba, ba Aunty Sidra ba ce ni ce fa Nadra haramun ne."

Bai kalle ta ba ya yi kamar baya jin ta. Ana ta watsa ma su fure me ƙamshi ana ma su feshi.

Jin yadda idanun mutane ke yawo a likita ya saka ta fara kokare kare jikinka ta hanyar ɗan shigewa jikinsa ta yadda ba za'a ga ƙirjinta da take ɓoye wa ba, wanda bai tsaya kusa da su ba zai ɗauka ta haɗa jikinsa da nata ne, amma a zahiri sun dai yi kusanci amma jikinsu bai haɗu ba, sai dai har lokacin yana rike da hannunta cikin nasa.

Kuma yana tafiya a hankali ganin yadda take tafiya ita ka sai yake bin ta a haka.

MC na bayani yana sanar da idowar amarya da ango ga wani sanyayyen kiɗa na tashi a hankali.

Har suka ƙarasa wajen zamansu suka zauna , ana ya saukar su photo.

Kowa dake wajan kayan jikinsa White and black ne maza da ma ta.

Taro ya kai taro jama'a da ba'ayi zato ba sun zo.

Waƙar auren na tashi sai dai abin da ya ba Fahad mamaki ya san dai waƙar auren da sunan Sidra aka rera, amma yanzu sai ya ji sunan Nadra ne ba na Sidra ba, duk da wakar ɗaya ce sunan kawai aka canza, bayan shi ba abinda aka canza daga sunan iyaye da dangi duka suna nan. Fahad ya san wannan ba aikin kowa ba ne sai Aunty Rahama. Ita ce za ta saka ayi wannan a kankanin lokaci.

Kamar yadda ka tsara haka aka yi aka kira abokin ango ya zo ya bayar da tarihin rayuwar ango da halayyarsa.

Daga nan aka bukaci ƙawar Amarya ta fito ta ba da tarihin rayuwar Amarya. A nan ne Nadra ta daga kai saboda ta san saboda ta san ba wata ƙawar da take da ita da ya wuce A'isha Humaira kuma ba ta zo wajan nan ba. Dama Khadijah ƙawar Sidra ce za ta bayar da labarin Sidra. Yanzu kuma tun da an fasa auren da Nadra ai ba zai yiwu ƙawar Sidra ta zo ba.

Ga mamakinta sai ta ga Khadijah ƙawar Sidra ta fito ta zo ta tsaya. Haɗa idanu suka yi ta sakar ma ta murmushi. Sai dai Nadra ta kawar da mamaki ne lokacin da ta tuna cewa ai labarin Amarya za ta bayar amarya kuma Sidra ce, dole za ta bayar da labarin Sidra, dama duk cikin ƙawayen Sidra ba wacce hankalin ta ya kwanta kamar Khadijah. Don tana ba ta shawara na kwarai tare da fada ma ta gaskiya. Shi ya sa ba wuya sun yi faɗa ita da Sidra saboda fadar gaskiyarta.

Cike da mamaki Nadra take kallon Khadijah ƙawar Sidra, jin ta ta ambaci sunan ta ba sunan Aunty Sidra ba kila tarihin rayuwar Nadra take bayar wa .

Sai dai ba ta ce komai ba kuma ba ta kawo komai a ranta ba.

Aka buƙaci amarya da ango su fito, nan fa Nadra ta noƙe ta ƙi fitowa, ganin take-taken ta ya saka ya riƙo hannunta, don idan ba haka ya yi ma ta ba ya san ba tashi za ta yi ba.

Janyo ta ya yi ya rike hannunsa cikin nata har suka fito cikin tsakiyar taron.

Ana ma su liƙin kuɗi ita da ƙokarin kare ƙirjinta take yi da hannayenta guda biyu.

Don abinda ya sa ta kara tsanar kayan saboda ƙirjinta da aka yi kamar na bra a tsuke kuma ga baby hannun arziki a jiki.

Ganin za ta rungume hannaye kamar mai jin sanyi ya saka ya yi saurin rike hannun nata yana rawa ana watsa ma su kuɗaɗe ƴan dubu-dubu har da ɗari biyar-biyar. Mama da su Aunty Rahama da sauran danginsa sai liƙi ake yi ma sa. Farin ciki ya lulluɓe Mama sai liƙi kawai take yi wa surikar tata. Don Nadra ta ji ta shiga ranta haka ma Aunty Rahama sai ɓarin kuɗi take yi, da sauran dangin Fahad.

Bayan dangin ango sun koma wajen zamansu sai ga dangin Amarya sun fito su ma. Su Gwaggo Laraba da Gwaggo Maimuna da saran dangin Abba da ƙawayen Umma.

Bayan sun ma sun yi ma su nasu liƙin sai abokan ango suka fito.

Nan fa Sidra ta kasa nutsuwa ganin samari matasa ne irin Fahad Ke ta yi ma su liƙi.

Ga Fahad ya ki sakin hannuwanta yadda yake rawa da ita ne ya saka ita ma idan ka kalle ta za ka yi zaton rawar take yi .

Ga takalmin ta gaji da shi kasancewar ita ba ma'abociya saka dogon takalmi ba ne, baya ta yi kamar za ta fadi sai ya yi saurin riƙo ƙugunta ya dawo da ita ta fado jikinsa.

Ba ta san san da ta kwantar da kai a ƙirjinsa ba saboda tsoron faɗuwar da za ta yi da dogon takalmin da ke ƙafarta.

Ta yi lamo a ƙirjinsa ta rintse idanunta tana jin yadda gaban ta ke faduwa.

Dariya ta ba shi yadda take da tsoro haka har ya yi murmushi yana kallon fuskanrta nan aka dinga tafi ana ɗaukarsu photo wanda hakan ya sa ta dawo cikin cikin nutsuwarta, da sauri ta raba jikinta da nasa.

Daga nan kuma aka fara daukar photo amarya da ango da sauran jama'a, dangi da abokan arziki.

Baga gama ba gajiya ya saka Nadra barin wajen ta nufi wajen zamanta ta zauna.

Daga nan kowa ya dinga zuwa yana dibar kalar abinci da abun sha da yake so.


*Abuja*

Satin Muryar Sidra ke tashi a cikin madaidaicin falon tana tsaye rike da kugu cike da masifa take kallon ƙawar tata Sady baby.

"Amma wannan ma su raunin hankali ne, wasa da hankalinmu ya yi ko me?"

"Ki hanyar da hankalinki ƙawata ba..."

"Dalla rufe ma ni baki wani kwantar da hankali zan yi, bayan na ga alamar mafarkina ba zai zama gaskiya ba, sanin kanki ne cewa burina na samu ɗaukaka na yi suna fiye da yadda waccen sakaryar da ta wulakanta ni saboda ta yi samu suna. Burina na rama wanda a dalilin haka na gudu ranar aurena da masoyina na bar kowa nawa don na samu cikar burina."

"Wallahi ya ce wai ai tun shekaran jiya aka yi ba mu zo akan lokaci ba bar an gama ta tacewa sun zaɓi wata, ya kuma tabbatar ma ni da cewa da a ce kin zo da ke za'a zaɓa saboda duk kin fi su haɗuwa kuma ya san za ki iya, lokaci daya za ka ki yi suna don babban kamfanin ne fa suke ɗaukar ƴan tallan."

"Aikin baza da wofi wallahi ni kin cuce ni kin sa na bar aurena na zo nan, da yanzu an ɗaura Mani aure da Fahad, dole na koma Kaduna a yammacin nan na roki iyayena gafara gobe a daura Mani aure da masoyina ba zan yi biyu babu ba."

"Biyu babu kam ai kin yi shi, ba ki ga tsunsu ba ki ga tarko kin ɓarar da damarki."

"Akan uban me kike magana ke kuma?"

Ta jiy maganar a fusace.

Mika ma ta wayar ta yi tana cewa

"Ga shi ki kalli yadda wannan bikin da Khadijah ta tura Mani."

A wulaƙance Sidra ke kallonta kafin ta karbi wayar ta fara dubawa. Photon farko shi ne in da ta ga Nadra kwance a kirjin Fahad ta rungume shi, yana kallon fuskarsa yana murmushi.

Sannan ta kalli in da suke tafiya yana rike da hannunta tana shigewa jikinsa sai na ukun in da suke rawa Ga mahaifiyar Fahad da Aunty Rahama na ma su liƙi tana dariya.

Sakin wayar ta yi tana dafe kanta da ta ji yana sara ma ta ga wani duhu da take gani. Tana girgiza kai tana cewa.

"No no no ba impossible ta ya Abba da Umma za su aiki ta haka, ko Fahad ba zai yarda da wannan abun ba, kawai editing ne aka haɗa amma Fahad nawa ne ni kaɗai ba babu macen da ta isa ta raɓe shi ban ga bayanta ba."

Wata budurwa ta karaso ta ajiye masu faranti da Fruits da wuƙa.

"Magana ta gaskiya dole ki hakura ya zama mijin ƙanwarki."

Wuƙar dake hannunta ta dauka tana nuna wacce ta yi maganar tana cewa

"Idan kika sake fadar haka sai na kashe ki."

Ganin ba ta da hankali ya saka ta ce.

"Allah huci zuciyarki na bar ki lafiya."

Wuƙar dake hannunsa ta fara yankar hannunta tana ta surutai cikin ficewar hayyaci.

Yadda jini ke zuba ya sa hankalin Sady baby tashi ta ce .

"Meye haka Sidra za ki illata kanki fa, ba ki ganin yadda jini ke fita daga jikinki?"

"Wallahi ba zan iya rayuwa ba Fahad ba ba wacce za ta raba ni da shi ki ce karya ne bai auri ƙanwa..."

Jiri ne ta ji yana ɗibarta ta zube wajen akan kujera.


*Maman Ihsan ce*✍️

09065327995
Follow the TASKAR MAMAN IHSAN channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaiufWb3LdQYnzC2vH0z


*MAKAHO NE*


*NA*

Maman Ihsan ce ✍️


https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️


page0️⃣9️⃣

Jiri ta ji yana ɗibarta ta zube a wajen akan kujera.

Sady baby ta yo kanta tana kiran sunanta, sai a lokacin ta fahimci ashe suma ta yi.

Ganin ba kowa a falon ya duk sun watse ta nufa fridge da kanta. Ruwa ga ɗauko mai sanyi ta yayyafa ma ta.

Wani ajiyar zuciya ta ja kafin ta fashe da kuka. Idanunta a rufe take cewa.

"Sady ina fatan ba gaskiya ba ne ko? Na san yadda Fahad Majidaɗi ke so na ba zai iya auren wata ba, na taho nan da zumar idan ba na nan za su ɗaga bikin zuwa lokacin da zan dawo sai a ɗaura ma ni aure da shi ko?"

Cikin kwantar ma ta da hantdady ta ce.

"Ba komai wannan fa ƙsrya ne ba gaskiya ba ne, ki daina saka damuwa a ranki ke ma ki. San wannan zamani da muke ciki fuska kawai za'ayi amfani da shi aje a haɗa kamar a tare suka dauki photo. Ki cire s ranki ke fa da bakin ki kika ce Fahad na son ki zai hakura har sai kin dawo kafin ayi bikin auren naku."

Ba dai ta gamsu ba haka ta dai yi shiru don kanta na matsa wani irin ciwo ne mai tsanani.

"Bari na kira wata nurse dake kusa da mu, ta zo ta dubs wannan raunin da lima ji wa kanki da wuƙa.

Tana fadar haka ta fice daga falon zuwa kiran nurse.

Sidra ta dafe kanta dake ma ta ciwo sosai sannan ta kwantar da kai tana lumshe ido zuciyarta cike da tunanin Fahad, tana tuna ƙamshinsa mai saka ta nutsuwa da shauƙi.


_Nadra_

Tana zaune a mazauminta Fahad na gefenta yayin da mutane ke zagayowa su tsaya bayansu ana ɗaukarsu photo.

Yayin da mafi yawanci suna zuwa su ɗebi kalar abincin da suke son ci da kalar ruwan da suke so sha.


Ita dai Nadra ga ta nan ne kamar me jin sanyi .

Har aka gama ciye-xiye da lashe-lashe.

Sannan aka zo wajan yanka cake suka ta so don yanka xaket, a nan ne ya sake ganin aminiyar Sidra wato Khadijah. Ya yi mamakin yadda ta fito take fadar halayyar Nadra bayan ita kawa ce ga Sidra. To me ta zo yi? Wani makirin murmushi ya yi saboda ya san dole za ta tura wa Sidra abinda ke faruwa wajen wannan bikin, kuma yana da yakinin cewa yadda Sidra ke mahaukacin son sa dole za ta ji zafi a ranta idan ta ji ya aure ƙanwarta. Duk da ba ya da tabbacin zaman nasa da Nadra. Don haka ya kalli Khadijah dake ma su video tabbas Sidra za ta gani zai aikata abun da idan Sidra ta gani zata ɗanɗani ɓacin rai kwatankwacin yadda ta saka ya ji shi ma. Zai tabbatar ma ta kamar bai ji haushin abinda ta aikata ba

Hannunsa ya ɗaura saman na Nadra tana kokarin janye hannunsa bai ba ta damar hakan ba. Ya rike hannunta suka fara yanka cake.

Ƙasa-ƙasa da murya ta fara magana tana cewa .

"Yaya Fahad ka daina taɓa jikina ba na so ni ba Sidra ba ce, haramun ne Please ka daina."

Kamai bai ji ta ba bayan sun yanka cake ɗin aka dinga yi ma su tafi ana ɗaukarsu photo.

Sanin ba ba za ta yi abinda yake so a wajen ba, da kuma kokarin ɓata ran Sidra don ya san za ta gani..

Suna yankawa ya riƙo hannunta dake rike da cake, zuwa bakinsa ya kai ta ciyar da shi ana ma su photo, sauran na bakinsa sai ya tallabo gefen fuskarta da hannayensa biyu, sauran ba bakinsa ya haɗe bakinsa da nata wuri guda na cikin bakinsa ya tura ma ta a bakinta, take wajen ya ɗauki sowa da ihu ana tafi.

Nadra mutuwar tsaye ta yi saboda mamaki da al'ahabin Fahad Majidaɗi. Wai yau ita ce wani namiji da ba mijinta ba ya haɗe bakinsa da na ta waje ɗaya yana tura ma ta abinda ke cikin bakinsa a tsakiyar jama'a ko kunya baya ji a gaban kowa zai iya aikata hakan har iyayen sa na wajen. Lallai yau ta kara tabbatar Fahad mara kunya ne lamba ɗaya.

Barin wajen ta yi ta koma mazaunin ta. Kanta a sunkuye tana goge ƙwalla.


Ana kiran sallar magrib aka tashi daga taron, Amarya da ango suka nufi wajan motarsu.

Kunyar abinda Fahad ya ma ta ya saka ta kasa daga kai ta kalli kowa.

Direbansa ya yi saurin bude ma ta murfin motar ta shiga ta zauna.

Daga nan ne ta fashe da kuka shi kuma yana can yana sallama da abokansa.

Har ya dawo ya shiga motar tana kuka. Kallonta ya yi cike da takaici ya ce.

"Ke me aka yi ma ki za ki saka mutane gaba kina kuka?"

"Kan me za ka aikata ma ni haka?"

Ƙyasta yatsunsa biyu ya yi ya ba da wani sauti wanda hakan ya saka diraban ya fita da sauri ya ba su waje, don ya gane uban gidan nasa na bukatar sirri ne."

"Kin ɗauka abun da na yi ma ki da son raina na yi ma ki ne, in ban da ƙaddara da ba ta riga fata ke kin isa ma na rike hannunki ne? Ba ki da wannan ajin da zan iya taɓa jikinki. Dole ne ta saka na aikata hakanna farko saboda biyayyar iyaye, na biyu don na ƙuntata. Amma ba don haka ba ko kallo ma kin ishe ni ne, ma ta masu class da waye wa ma ban kalle su b ballantana ke da kike..."

Kuka ta fashe da shi tana cewa.

"Ya isa ya ishe ni haka, ba sai ka ci mun mutunci ba, na ji ban ai matsayin..."

Tsawar da ya daka ma ta ne ya saka ta haɗiye sauran maganar, ke har kin isa ki dakatar da ni ina magana, last warning da zan Maki shi ne kada ki sake daga Mani hannu idan kina mun magana idan ba haka ba sai na ɓalla hannunki, don ma kin samu na taɓa jikinki har kike ma ni wani zancen banza dole ce ni ma ki sani ba don ƙaddara ba ba ki kai matsayin ba kuma ba za ki kai ba, dama wancan shashashan ustaz ɗin ya dace da ke ba ni ba "

Ya yi maganar yana saukd Glass ɗin motar ya yi dirban alama ya zo.

Zuciyarsa cike da takaici me ya saka ma ya sa wa iyayen yarinyar nan ya amince ne, sai yanzu take jin haushin kansa, ya dai san baya son ta to ta ta zai zauna da ita.

Har suka ƙarasa gidan ba wanda ya yi magana a cikinsu.

"Get out in my car."

Ya daka ma ta tsawa, da sauri ta fice tana kuka. Gajeren tsuki ya ja yayin da suke barin gidan.


*Ma'eesha.*

Suna ƙarasa wa ƙofar gidan hangi makaho na fitowa daga cikin gidan hannunsa rike da kayan aikinsa na gyaran takalma.

Tun daga nesa ta hango shi yana tafiya hannunsa ɗaya yana rike da kayan aikin gyaran takalminsa daya hannun rike da sandarsa ta jagora.

Yana jin mai nape ya tsaya a ƙofar gidan ya tsaya.

Fitowa ta yi daga cikin nape ɗin tana kallonsa da kayan aikinsa dake hannunsa.

Kafin ta dauke idanunta lokacin da mai keke nape ɗin ke ma ta magana.

"Hajiya sai kin samu wanda zai taimaka ma ki ya shigar ma ki da kayan cikin gidan."

"Ba damuwa ka ajiye kawai ka yi tafiyar ka zan nemo wanda zai taimaka ma ni."

"Idan ba damuwa zan shigar ma ki da shi ciki."

"A'a ka bar shi kawai ka yi tafiyar ka zan shigar da kayan."

Wani kallo mai nape ɗin ya yi ma sa kafin ya ce.

"Kai kuma daga ina, kana makaho har da sandar jagora ne za ka iya ɗaukar kayan nan da wani ido za ka ga in..."

Ma'eesha ta dakatar da shi ta hanyar cewa.

"Ya isa Mallam don yana makaho ba shi ke nufin kasashshe ba ne, to shi ne maigidan ya ce ba sai ka shiga ba don haka maganarsa ta zauna."

Wani kallo ya yi wa Ma'eesha na mamaki da al'ajabi kafin ya kalli makaho ya ce.

"Dama da kika ce ke matar aure ce daga gaske ne, kuma wannan ne mijin naki?"

"Eh shi ne mijin nawa sai aka yi ya ya?"

"Amma Hajiya a yadda kiken nan a ce makaho kike aure faƙiri ko dai asiri ya yi ma ki ko kuma auren manufa kika yi ne?"

Ba ta tanka ma sa ba ta buɗe jakarta ta ga 100k ya rage ma ta, ta ciro 10k ta mika wa mai nape ɗin ta ce.

"Na gode za ka iya tafiya ."

Washe baki ya yi sannan ya shiga ciki yana ma ta godiya ya bar wajen.

Makaho ne ya dauki karamin buhun shinkafar a hannu ɗaya, ɗayan hannun ya ɗauki katon ɗin taliya da na macaroni da cus-cus.

Da mamaki take kallonsa har ya shiga gidan ta bi bayansa tana kallon ikon Allah.

Ba ta yi mamakin ɗaukar kayan ba, saboda yana da ƙira irin na zaratan jaruman maza, don jikinsa ma a murɗe yake kamar irin mazan da suke yawan motsa jiki suna daga ƙarfe. Amma yadda ya ke tafiya haka nan ne ya ba ta mamaki.

Sai da ya gama ta kalle shi ta ce.

"Ta ya ka iya tafiya haka nan ba tare da ka yi karo da komai ba?"

Murmushi ya yi ya ce.

"Na riga na karanci yanayin gidan bayan fitar ki sai da na auna ta hanyar tafiya na san taku nawa zan yi da idan na kawo saitin ƙofar dakin na sani."

"Ina za ka je yanzu?"

"Zan je ne ko Allah zai sa na samu wani abun, gyaran tsakani nake zuwa?"

"Ta ya kake gane kalar takalmin da za ka san irin foolish ɗin takalmi fari ko baƙi?"

"Idan aka kawo ni kan tambaye wani kala ne, kafin na san irin kayan aikin da zan yi amfani da shi, duk countener dada nake amfani da su daban-daban ne na san na fari da na baki da kowane kala, iska tsinke wa ne idan na laluba ina gane wa sai na ɗinke."

"Ka hakura da fita don ina son mu yi gyaran dakin nan, za ka dinga ko mika Mani wani abun ne idan na ba ka ka rike za ka iya ko?"

"Zan iya in sha Allah."

Daga nan ya fita ya shigo da kayan aikinsa.

Ita kuma ta shiga ciki ta fara fito da trolly ɗin kayanta.

Har ya ajiye a barandar. Sai ya koma gefe ya tsaya.

Shara ta fara yi ta kwashe sannan ta shimfida leader carpet da ta siyo ya cika ɗakin ya yi kyau sosai.

Sannan ta shiga da ƴar madaidaiciyar katifarta ajiye a inda ya dace.

Sannan ta shimfida zanin godon ta sanya rigar pilow a pillow biyu da ta siyo ta jera.

Duk da kasancewar tana da mai yi ma ta gyaran ɗaki da wankin toilet amma hakan bai sa mahaifiyar ta ta bar ta haka ba ta koya ma ta ba, don ita ke gyara wa Mahaifinta ɗaki.

Labule ta ɗauko guda biyu na koda da window, a jikin bangon ɗakin ta samu ƙusa ta buga labulen na kofa da na window.

Sannan ta kalle shi ta ce.

"Ko za ka iya shigo ma ni da kayan nan duka?"

Kai ya jinjina ta ɗaga labulen ta sakala a jikin kofar.

Haka ya dinga shigo da kayan tana nuna ma sa in da zai ajiye, da zaran ya kai wajen za ta ce ma sa ya yi ya ajiye.

Har aka gama shigo da komai.

Kitchen ɗin fale-fale dake tsakar gidan ne ta ce ma sa ya dauki karamin buhun gawayin ya ajiye a ciki tare da murhun gawayi.

A barandar ta ajiye ƙaramin Gas da ta siyo ta ce.

"Ka yi a hankali kar ka karaso ta nan gefen na ajiye Gas zan yi girki."

"To in sha Allah."

Shiga ciki ta yi ta buɗe kwalin tukwane da ta siyo, ta ciro ƙaramar ciki ta kunna gask ta zuba ruwa. Sannan ta ɗauko tabarma ta shimfida a gefe ta ce.

"Ka zauna ma na "

Sai da ya laluba ya ji inda tabarmar take sannan ya zauna a gefe.

Ita kuma ta dauko kujerar tsuguno na roba da ta siya ta zauna akai.


Sallama suka ji daga waje ana yi.

Makaho ya amsa sallamar yana mikewa tare da ɗaukar sandarsa.

"Wa'alaika salam warahmatullah."

Ya amsa yana nufar kofar gidan.

"Mallam Iro mijin Larai Dillaliya ne ya zo amsar kuɗin haya."

Jin haka ya saka Ma'eesha cewa.

"Ga kuɗinsa ka kai ma sa na san shi ya zo amsa."

Ta yi Maganar tana shiga ɗaki ta dauki handbag ɗin ta.

"Ana zuwa ."

Makaho ya yi maganar yana daga murya yadda Iro zai ji shi.

50k ta ƙirga ta ba shi yayin da kudin ya rage ma ta saura dubu arba'in.

Yana ganin makaho ya ce.

"Khalifa Barka da safiya."

"Barka dai Mallam Iro ya al'amura?"

"Alhamdulillah."

Kudin ya mika ma sa ya karɓa ya kirga ya ga sun cika.

"Ma sha Allah kudi sun cika, amma fa akwai dubu biyar da ya kamata Ku ba Ni da dillanci. Amma na yafe ma ku."

"To mun gode Allah ya saka da alkhairi ya sa la fi haka."

Da Amin ya amsa ya ma sa sallama ya bar gidan.


_Nadra_

Da kuka ta shiga ciki kai tsaye ta nufi ƙofar ɗakinsu ta shige, kan gado ta faɗa tana ci gaba da rusa kuka.

Gwaggo Laraba ta bi bayan ta da sauri.

Kan gadon ta nufa in da Nadra ke kwance ta kalle ta tana ɗaga ta .

"Nadra lafiya me ya faru?"

"Ba a gaban idanunku kuna kallonsa yana taɓa jikina duk da haka bai ma sa ba sai da ya tallabo fuskata ya haɗa bakinsa da nawa ya tura mun cake a cikin bakina, ba wanda ya yi ma sa magana ko ya hana sai sai tafa ma sa ake yi. Sannan kuma don na ma sa magana rashin dacewar abun da yake ma ni don na daga ma sa hannu wai idan na sake daga ma sa hannu sai ya karya hannun har yana zagin saurayi na wai wancan shashashan ustaz ɗin ne ya dace da ni, wallahi Ya Sayyadi ba shashasha ba ne mutum ne mai tsoron Allah da kiyaye dokokin Allah ba kamar shi da yake take dokokin Allah ba yana taɓa macen da ba matarsa ba. Wallahi Gwaggo ba namijin da ya taba rike ko da ƙumbata amma shi lokaci ɗaya ya zo ya..."

Dariyar da ta ji daga bakin kofar ne ya saka ta dakata tana kallonta fuska a murtuƙe.

Wata ƴar Gwaggo Laraba ce take dariya ta ce.

"Yanzu ma aka fara ba ki yi kuka ba tukuna."

Wani kukan ta saka saboda dariyar ya ƙular da ita, sai da Gwaggo Laraba ta Kore ta Sannan ta ce wa Nadra ta tashi ta yi wa wanka ta yi sallah.

Bayan kamar mintuna talatin ta shigo ta samu Nadra akan sallaya.

Wasu kaya ta ajiye ma ta wanda Nadra na ganin kayan ta mike tsaye tana cewa.

"Wannan ai kayan da Sunyi Sidra za ta saka ne idan za'a kai ta gidan mijinta, ko har ta dawo ne?"

"Ba na son yawan tambaya ki shirya cikin wannan kayan ki fito Falon Abbanki yana kiranki."

Haka kawai ta tsinci kanta da mummunan faduwar gaba wanda ba ta san dalili ba. Wayar Sidra ta gwada kira still switch off.

Zama ta yi bakin gadon taba kallon tsadadden leshin da kudinsa zai kai Naira dubu ɗari biyu. Da set na ɗan kunne da sarƙa siriri na Gold.


_Fahad_

Yana zaune a falo shi da iyayensa. Baba, Mama, Aunty Rahama sai mahaifiyar Baba wacce ake kira da Inna.

Mama ce take faɗa tana cewa

"Zancen banza waye za ka ajiye wa ita a nan? Wato saboda ba ka son ta ko? Ina ce a baya da muka ce a gyara ma ka part ɗin ka ka zauna da ita ka ce ba za ka zauna da matarka a family house ba. Saboda za'a saka ma ka idanu a takura ma ku. Wato saboda wacce kake so ta gudu ita wannan tun da ba son ta kake yi ba shi ne za ka ce wai kada a kai ta sabon gidan da ka yi niyyar zama da matarka ka fasa ko? Sannan za ka ce a kawo ta a ajiye a family house bayan a baya ka nuna ba ka so ko? To ba ka isa ba yadda ks hana gyara gidan aka kai ma ta kaya gidan iyayenta suka jera kaya tun shekaranjiya ba wanda zai je ya kwaso kayan nan, kuma dole ka zauna da ita a gidan, to uban waye za ka bar wa gidan ya zauna?"

Ina ta amsa da cewa .

"Kila har yanzu yana jiran ita waccen da ta gudu ta dawo ne ya saka ta a ciki, don alama ya nuna haka."

"
Baba ya yi saurin cewa.

"Haba sai ka ce ba Musulmai ba ta ya ya zai auri wa sannan ya auri ƙanwa kamar maguzawa? Ko maguzawa ai ba za su yi haka ba."

"Idan ma tana cikin zuvuyarka ka cire ta don ko saki Nadra saboda Sidra ba wanda zai yarda ka aure ta."

Cewar Aunty Rahama tana kallon Fahad da ta hade fuska kamar bai taɓa dariya ba.

Tashi ya yi ya bar ma su ɗakin suka bi shi da kallo, Mama ta raka shi da harara don har ga Allah tana ƙaunar Nadra.


*Maman Ihsan ce*✍️

09065327995

Follow the TASKAR MAMAN IHSAN channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaiufWb3LdQYnzC2vH0z


*MAKAHO NE*


*NA*

Maman Ihsan ce ✍️


https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️


page1️⃣0️⃣

Tashi ya bar ma su ɗakin suka bi shi da kallo, Mama ta raka shi da harara don har ga Allah tana ƙaunar Nadra.

Baba ya kalli Mama ya ce.

Matuƙar yau iyayen yarinyar nan suka kai ta gidan mijinta to ki tabbatar bai kwana a gidan nan ba."

Jinjina kai Mama ta yi tare da cewa.

"In sha Allah."


_Makaho_

Yana zaune a tabarmar da Ma'eesha ta shimfiɗa ma sa ya ji muryarta tana cewa.

"Ba ri na je na siyo bread a shagon dake nan kusa da mu."

Bai tanka ma ta ba ita ma ba ta jira cewarsa ba ta yi ficewar ta.

Ba ya jima ba ta dawo da bread a leda da gwanhwanin milo da na madara.

Ta ajiye har ga Allah ta ji dadin siyayyar da ta yi, ba don ta yi tunanin siyar da wayar ba su da ba ta san yadda za ta yi ba. Duk da cewar a yanzu ma hankalin nata bai kwanta suka ba, saboda ta san yau da gobe duk abinda ta siyo za su ƙare ya za ta yi ne ina za ta samu wasu kuɗaɗen har ta sake siyo ma su wani ba. Don ta tabbatar makaho ba iya ɗaukar nauyin gidan zai yi ba, don wannan gyaran takalmin da yake yi ba ta tunanin shi kansa zai iya ɗ sa ɗaukar nauyinsa da shi ballantana ya dauki nata nauyin.

"Ma',eesha."

Ta ji ya kira sunanta lokacin da ta kashe Gas ɗin.

"Na'am."

"Don Allah ki daina yawan fita ko wane lokaci yanzu yai kin fita sau nawa a gidan nan?"

Shiru ta yi tana kallon da kafin ta ce.

"Idan ina buƙata abu za ka aje ma ni yaron da zan aika ne?"

"Meye amfanina ina gidan da sai kin fita?"

"Na ding aikenk kenan?"

"Wa ya fi cancanta ya fito ya nemi abun da ake bukata tsakanin ni da ke?"

"Kai ka fi cancanta amma gani nake za ka wahala ga sanda ga kaya a hannun ka."

"Kin manta haka nake fita neman na abinci, hannu daya riƙe da sandar hannu daya riƙe da kayan gyara. "

"Shi kenan dama na mance ban siyo ruwa ba sai ka je ka siyo."

Ta ciro ɗari biyar ta bashi ya karba.

"Wannan nawa ce?"

"Ɗari biyar ce, yanzu tsarin zai canza kamar yadda rayuwa ta ta canza. A baya bottle water nake sha, amma yanzu ba na da halin da zan cigaba da shan sa, ko da na siya yanzu nan da kwana biyu zai gagare ni don haka yanzi zan koyi shan ruwan pure water. Wannan ɗari biyar ka siyo ma na bag ɗaya wato jaka dayatina tunanin bai wuce dari biyar ba."

Ya fita don siyo wa ta bi shi da kallo har sai da ya fice sannan ta ɗauko ƙwai guda huɗu ta ta ɗan jajjaga bayan ta wanke ƙaramin turmi ta daka magi ta yanka albasa, sannan ta ɗauko fry pan ta wanke sannan ta zuba mangyaɗa ta soya.

Da sallama ya shigo gidan ta amsa tana miƙe wa ta karbi jakar ruwan dake hannunsa, ya ƙaraso ciki sai da ya ji ya taɓa tabarmar da sandarsa sannan ya gane ya ƙaraso wajen.

Bayan ya hau tabarmar ne ya zauna tare da yin Bismillah.

Kofuna biyu ta dauko na shan shayi ta ajiye bayan ya wanke da cokula. Ruwan shayin ta zuba wa kanta da nasa ta zuba sugar da milo da madara, ta fifita dai da ya rage zafi ta ajiye ma sa a gabansa da plate ɗin da ta saka ma sa soyayyen kwai ciki ta ajiye ma sa bread.

"Ga breakfast ɗin ka nan a gabanka."

Sannan ta haɗa na ta ta koma kan tabarmar ta zauna a gefensa.

"Na gode Ma'eesha Allah ya biya ki fa gidan aljanna."

"Amin ya Allah."

Ta amsa tana cigaba da cin abincin ta.


_Nadra_

Tana zaune a falon zuciyar ta cike da mamaki da ɗan firgici. Duk abinda take gani a gidan yana gudana tana ɗaukarsa ne na yayarta Sidra ba ta taɓa tunanin ita ce Amaryar ba.

Abba dake zaune kusa da kujerar dake kusa da Nadra dake zaune saman Centre carpet, fuskarsa cike da tsananin tausayin ƴar tasa mai biyayya da bin Umarninsa akan komai.

Idanunsa sun kaɗa sun yi jajir ya ce.

"Nadra yau ce ranar da rayuwarki za ta sauya."

Nadra ta kalli fuskarshi idanunwanta cike da rashin fahimta tana kallon jama'ar falon ɗaya bayan ɗaya.

Idanunta suka sauka akan kakarta mahaifin Abba, sai Gwaggo Maimuna Yar Abba sai Gwaggo Laraba ƙanwar Abba. Sai Yayan Umma wato Alhaji Bashir. Kafin ta mai da dubanta kan Abba.

"Nadra yau aka ɗauara aurenki ba tare da na shawarce ki ko jin ra'ayin ki ba, saboda ina da yaƙinin cewa ba za ki taɓa watsa ma ni ƙasa idanun ba."

A firgice take kallon su ta ce.

"Me kuke nufi wace ce Amaryar?"

Abba ya dube ta cike da kulawa da nauyi ya ce.

"Sidra ta gudu Allah ya kare ta a duk in da take. Amma ki sani rayuwarki aka ɗaure yau."

Nadra ta ji shiru na ɗan lokaci zuciyarta ta yi ma ta nauyi kamar dutse. Ƙwalla ce cike a idanunta ba zato ba tsammani zuciyarta ta fara fahimtar cewa ita ce Amarya. Ta taɓa kafafuwan Abba cikin tsanani ruɗani da firgici. Zuciyarta na bugawa da karfi. Sai ta ɗaga kai ta yi addu'a a cikin zuvuyarta.

"Allah ka bani ƙarfin fuskantar wannan sabuwar rayuwa , ka sa na zama mai haƙuri da biyayya."

Kuka ta fashe da shi mai tsuma zuciyar mai sauraro. Cikin wannan yanayi Nadra ta san cewa babu koma baya, kuma dole ta rungumi a abun da ya zo ma ta. Shin ma waye mijin da aka ɗaura ma ta auren da shi? Tambayar dake kai komo a zuciyarta kenan. Sai ta ji muryar wan Mahaifiyarta Alhaji Bashir yana cewa.

"Dama kana naka ne Allah ya gana nasa. Dama can Allah bai ƙadarto cewa Sidra ce matar Fahad ba sai ke, don haka ki rungum..."

Kukan da ta fashe da shi ne ya saka kowa dakata wa yana kallonta. Kuka take yi wanda ke fitowa can a kasar ranta.

"Ki yi hakuri Nadra na san za ki ji abin a baibai, amma ki sani ba ni da wani zaɓi da ya wuce hakan. Na gayyaci jama'a na tara su an zo daga garuruwa mabanbanta gari ya waye ana jiran rana ta yi a daura aure amma sai Sidra ta nemi tozarta ni da kunyata ni ta nemi zubar ma ni da ƙima a idanun jama'a. Da wani idanu zan kalli jama'ar da na gayyata zuwa auren ƴa ta na ce ma su an fasa daurin auren ƴata ta gudu? Hakan ba zai zubar mani da ƙima ba? Ke kadai ce na san cewa za ki iya kwaso ma ni ƙima ta da ƴar ki ta nemi zubar wa. Tun da na haife ki daga ni har mahaifiyar ki muna alfahari da ke, ba ki taɓa saɓa ma na ba, don haka ba na sa ran wannan karon za ki aikata wani abun da ba daidai ba. Na roke ki da Allah ki..."

Cikin sauri ta ce .

"Abba ka daina roƙo na don Allah ba abinda za ku aikata akaina ku roke ni Ko da hakan na nufin mutuwa ta ce, Abba dan Allah ka daina roƙo na sai na ji kamar na gaza zama ƴa gagari ce a gare ku. Na amince akan duk hukuncin da kuka yanke akaina. Amma Yaa Fahad fa Sidra yake so kuma ita ma na san tana tsananin son sa idan ta dawo ta tarar da..."

Abba ya kira sunanta a kausashe.

"Nadra!"

Ɗagowa ta yi ta kalle shi da idanunsa da suka yi jajir saboda kuka ta ce.

"Na'am Abba."

"Daga yau ba na son sake jin sunan Sidra a bakin ki, a cikin gidan nan ma na hana a kira sunan ta, ba zan yi ma ta baki ba amma na cire ta daga cikin mu, ki ɗauka ba ki da wata ƴar uwa a raye Sidra ta mutu a wajen ki."

Kuka ta saka sosai tana rokon Abba ya yafe wa Sidra amma bai saurare ta ba. Sai ya tashi tsaye ya kalli Nadra ya ce .

"Allah ya yi ma ki albarka ya kare ki a duk in da kike, yadda kike wa iyayen ki biyayya Allah ya sa ƴaƴan da za ki haifa su yi ma ki fiye da yadda kika yi mana. Allah ya zaunar da ke lafiya da mijinki ki yi ma sa ladabi da biyayya kome ya daka ki to kiyi masa matuƙar bai saɓawa addinin Musulunci ba, aljannarki na kasan ƙafansa idan ya daga ki shiga kada ki mance da wannan."

Yana fadar haka ya fita daga falon kamar zai yi kuka, don ba zai iya jurar ganin Nadra n kuka tana rokonsa akan wani abu bai yi ma ta ba, amma wanann karon ba ya jin zai saurare ta akan zancen Sidra.

Sauran jama'ar dake falon kowa nasiha sosai suka ji ma ta akan zaman aure da hakuri da rayuwar aure.

"Dare na yi ya kamata a ɗauke ta a kai ta gidan mijinta."

Cewar Gwaggo Maimuna tana kallon Ammi.

Ammi ta ce .

"To me kuke jira ku tafi a raka ta ma na ga jama'a can a falo suna jiran ku fito, ga motaci jere a waje."

Gwaggo Laraba ce ta ja hannun Nadra da ta kudundune cikin babban mayafin da aka yafa mata.
Chapter 2 · 0% Book details