Gabatarwa
Makaho Ne Part 1 Complete Hausa Novel · about 83 min read
*MAKAHO NE*
*NA*
Maman Ihsan ce ✍️
*Alhamdulillah na gode Allah da ya bani ikon rubuta wannan labarin da na daɗe ina son rubuta shi. Allah ya bani ikon rubuta abun da zai amfani al'umma.*
*Ni ce ta ku dai marubuciyar nan da na saba faɗakar da ku da misaɗantar da ku, to yanzu ma na zo ma ku da sabon labari mai cike da sarƙakiya tuggu da makirci, wanda zai bar ku cikin shauƙi da zumuɗi. Ku dai ku biyo ni kun san dai ba taɓa ba ku kunya ba, wannan na daban ne mu je zuwa*
Ɗanɗano
Page0️⃣1️⃣
Tafiya yake yi cikin takunsa na natsuwa da kamala, Sandar dake da hannunsa yana dogarawa ne zai tabbatar ma ka da cewa makaho ne shi, kuma sandar ce jagoransa. Sai baƙin glass dake sanye a idanunsa wanda ya zauna a karan dogon hancinsa da ya dace da kyakkyawar fuskarsa. Fari ne dogo mai matsakaicin jiki, sai dai kallo ɗaya za ka yi wa kyakkyawar fuskarsa ka fahimci cewa shi ba mai yawan fara'a ba ne da sakin fuska. Yana da ƙirar jiki da cikar zati irin na cikakken ɗa namiji. Sanye yake da wani royal blue yadi mai sauƙin kuɗi wanda ake kira da yi shirunka maraya, daga ganin kayan jikinsa za ka san sun sha jiki sai dai da dukkan alamu saurayin mai tsafta ne don kayan fes suke babu datti duk da kasancewarsa makaho ne.
Tafiya yake yi a cikin layin unguwar da ta kasance unguwa ce ta ma su hannu da shuni, tun daga ganin shimfiɗaɗiyar kwaltar da ta shiga cikin unguwar ta ko ina har zuwa ƙerarrun gidajen dake cikin unguwar. Unguwar ta kasance shiru ne ba hayaniya.
Har ya iso daidai katafaren wani gida ya tsaya, shiru ya yi na tsawon mintuna biyu kafin ya yi knocking ɗin danƙareren gate ɗin dake gidan.
Daga ciki ya ji muryar Musa mai gadi yana cewa.
"Waye nan?"
Don tun da ya ji ba'ayi horn ba ya san ko ma waye ba da mota ya zo ba talaka ne.
Ƙarasawa ya yi don dama daga toilet ya fito yana surutu shi kaɗai.
"Ko ma waye dole za ku haƙura ku koma, don ita matar kirkir dake da tausayin talakawa kuke zuwa rana ba ku yanzu Allah ya karɓi rayuwarta ba ta raye, wacce ta rage a gidan ko mutuwa za ku yi ba za ta lalle ku da gashi ba ballantana ta taimaka ma ku."
Yana buɗe ƙofar ya ga wanda ke tsaye ya ce ya ce.
"Mallam makaho ne?"
Shiru ya ma sa bai yanka ma sa ba, sai ya sake cewa.
"To daga yau sai dai ka daina zuwa don wacce kake zuwa domin ta take ba ka Allah ya larɓi rayuwarta, tsawon kwanaki hamsin kenan yau, kuma na san ka zo ta'aziyya , kuma ka zo bayan wata ɗaya da rasuwar . Ina mai ba ka shawara ka bar nan kafin waccen marar mutuncin ta fito ta ganka uwar ɗakinka ta rasu ka sani ko?"
Gundura ya fara yi da maganar ta Mallam Musa sakamakon ba ya son magana ko hayaniya , ga shi Mallam Musa bai iya magana a hankali ba, cike da mishkilanci ya yamutse fuskarsa yana ƙokarin shiga cikin gidan.
Da kallo Mallam Musa ya bishi yana cewa.
"Sai shegen girman kai da mishkilanci, ga shi nakasashshe yanzu an koro ka ka fito."
Mamy ce ta fito tana kallon Makaho tana washe baki tana cewa.
"Ango ya iso daukar Amaryarsa kenan Alhamdulillah."
Bai ce komai ba sai sake tsuke fuska da ya yi, yayin da Mallam Musa ya cika da mamaki to waye angon ba dai makahon nan ba.
Tsuke bakinsa ya yi ya koma bakin aikinsa yayin da Mamy ke yi wa Makaho iso tana cewa.
"Shigo sirikina."
"Alhaji dake zaune a falo ya ɗago kai yana kallon Makaho dake shigowa tare da sallama. Yana mai amsa sallamar ta sa yana bashi izinin zama. Zama ya yi a kan lallaudan centre carpet dake tsakiyar falon
"Ina wuni Daddy."
"Lafiya lau Khalifa."
Kallo ɗaya ya yi wa Mamy ya kau da kai kamar an masa dole ya ce .
"Ina wuni Mamy?"
"Lafiya lau angon Ma'eesaha."
Ta amsa tana wani dariya na mugunta.
Shiru falon ya yi tana jiran Dady ya yi magana sai ta ji shiru, gabadaya baya cikin tunanisa.
"Alhaji"
Shiru bai amsa ba sai da ta sake kiransa a karo na uku Sannan ya dawo tunanisa yana cewa.
"Na'am."
"Ga shi ya zo ɗaukar Amaryarsa da aka ce ya zo ya ɗauka, ka bar shi zaune."
"To ai na kira ita Ma'eesha tana hanyar dawowa."
"Okay, ka jira amaryar ta karasa sai ku tafi ta je lalle da kitso ne."
Bai ce komai ba illa ya sunkuyar da kai ƙasa.
_Ma'eesha_
Fitowarta kenan daga cikin shagon saloon tana sanye da rigar Abaya green colour, tana gyara mayafin abyarta hannunta rike da handbag ɗin ta da wayarta I phone 16 pro max. Wayarta ce ta fara ruri tana dubawa ta ga Inno ce me masu aiki.
Ɗaga wa ta yi ta maƙala wayar a kunne tana maƙe kafaɗarta yadda wayar za ta zauna, ta zuge zip ɗin handbag ɗin ta ta ciro makullin motarta tana cewa.
"Hello Inno ya aka yi ne?"
Shiru Inno ta kasa magana don har ya nufi motarta ta bude Inno ba ta yi magana ba.
Zama ta yi a driving seat sannan ta ce.
"Inno lafiya kuwa."
Cikin kuka ta ji muryar Inno na cewa.
"Ma'eesha kada ku dawo gidan nan ki je wani wuri."
Cikin faɗuwar gaba ta ce.
"Me ya faru ne Inno?"
Ta ji ta sake cewa.
"Aure aka ɗaura ma ki yau da wannan makahon da ya taɓa ceton ran mahaifiyar ki har ta ke kyautata ma sa."
Wani dariya Ma'eesha ta yi tare da cewa
"No ba zai yiwu ba, kada ki dake Mani wannan wasar."
Ta katse kiran wayar tana cewa.
"Haba wane irin aure ba tare da an nemi amincewa ta ba, ko auren ne ma ai sai a ce na fito da wanda nake so amma ba za'a yi ma ni dole ba, ballantana s ce wani makaho wanda ko a mafarki bai isa ya zo mijina ba ballantana a zahiri?"
Tsuke ta ja tare da yi wa motarta key ta bar harabar Saloon ɗin.
Horn take dannawa har maigadi ya wangala ma ta gate ta shigar da motar tana mai yin yin parking a parking space.
A hankali ta sako da fararen ƙafafuwanta da suka sha zanen kalli ja ba baƙi.
Fitowarta yi hannunta rike da handbag ɗin ta da makullin motarta.
Da sallama ta shiga falon gabanta na faɗuwa.
Gabadaya suka amsa ma ya sallamar ta shiga ciki. Ganin makaho ya haifar ma ta da wata faɗuwar gabar da ba ta san dalili ba.
Bayan ta gaida Dady da Mamy ta miƙe za ta nufi ciki ta ji Mamy na cewa.
"Alhaji ka sanar da ita ta fito ta bi mijinta tun da ga shi nan zaune yana jira tun ɗazu.
Mummunar faɗuwar gaba ce ta ziyarce ta, wanda har sai da ta saki handbag ɗin ta a ƙasa.
"Ke Ma'eesha zo nan."
A hankali ta take taku kamar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki ta zo gaban Dady ta zube.
"An ɗaura auren ki da Khalifa makaho yau, ku tashi ki bi mijinki Allah ya ba ku zaman lafiya."
Kallon Dady take yi kamar wata sokuwa ta ma rasa me za ta ce ma sa, don ganin abin take yi kamar wani alamara.
"Da...Da...Da..."
Ta ma rasa me za ta ce wani kalma za ta kama da za ta yi amfani da shi wajen yi wa Dady magana. Kafin ta samu ƙarfin zuciyar furta.
"Dady wane laifi na aikata da ka hukunta ni ta wannan han?"
Tsawar da ya daka mata ne ya saka ta firgita.
"Tashi ki kwaso kayan sakawarki ki bi mijinki, idan kika sake yi Mani wata magana a nan sai na ba ki mamakin da ya fi wanda kike ciki?"
"Ba da ke mahaifinki ke magana ba kina zaune?"
Jiki ba ƙwari ta miƙe ta ɗauki handbag ɗin ta da makullin motarta ta nufi ɗakinta.
Nan ta samu Inno mai masu aiki, tana ganin Inno ta fada jikinta ta rungume ta tana fashewa da matsanancin kuka."
Ita ma Inno kuka take yi tana cewa.
"Allah ya yana tare da ke Ma'eesha, shi ya sa na kira ki a waya na ce kada ki dawo gidan nan. Wannan kishiya mahaifiyarki ba ta tsoron Allah, so take kawai ta ga rayuwarli ta tagayyara shi ya sa ta saka mahaifinki ya aura maki makaho musaki wanda ba ya da cin yau balle na gobe, ta ya ya mace irinki da kika taso cikin gata da jin ɗadin more rayuwa za ki auri fakiri nakasashshe? Ita me ya saka ba ta saka ya auri ƴarta Agola ba, sai ke da gidan uban ki ne za'a yi ma ki wannan cin kashin?"
Cikin kuka Ma'eesha ta ce.
"Mamy ba ta so na ta tsane ta saka mahaifina dake son farin cikina yanzu ya juya mani baya ya tsane ni, duk da haka bai ishe ta ba sai da ta saka ya aurar da ni a inda ta san zan wahala me na yi ma ta ne, Da zuciya daya mahaifiyata ta kawo su gidan nan ita da yaranta suna cin arziki, karshe ta ci amana ta auri mijin aminiyarta suka ci gaba da zama duk da haka Mahaifiyata ba ta nuna ta ji zafin abinda ta yi ma ta na aure ma ta miji ba, ta zauna da ita da zuciya ɗaya, sai bayan ran mahaifiyata ne za ta ma ni haka sakayyarta ga Mahaifiyata kenan?"
Kuka suke yi dukkansu, kamar daga sama suka ji an daka ma su tsawa. A firgice suke kallon ƙofar. Mamy ce tare da Autarta Laila.
"Sannu muna munafuka kina hure ma ta kunne ko?"
Cikin rawar jiki Inno take ba Mamy hakuri ta fita daga ɗakin.
Ma'eesha ta kalle su da idanunta da suka yi ja ta kawar da kai ta cigaba da haɗa kayanta a cikin babban trolly tana kuka.
"Hi Amaryar makaho ya kike?"
Cewar Laila tana dariya.
"Mamy idan ta tafi ɗakin nan zan dawo da zama don ya fi nawa girma, ko funiture ɗin ya fi nawa kyau."
Mamy ta kalli ƴarta ta ce .
"Kar ki damu Shalele sai yadda kike so za'ayi."
Kallon Ma'eesha dake hada kaya ta yi ta ce.
"Ba ke mai gidan uba ba? Har kina yi wa yarana gorin cewa su agololi ne ko? To yanzu ke da gidan uban ki ne na saka uban naki ya yi waje dake, su agolan da kike yi wa taƙama da gidan uba su ne za su yi iko da gidan, ke kuka sai ki je ki fara cin garin kwaki, don ko kayan Gara da kayan ɗaki na hana ayi ma ki su ki je can ku ƙarata. Kina hutawa anan sai dai masu aiki su gyara Maki ɗaki su wanke Maki toilet ayi maki wankin da guga, ki sa a girka Maki abinda ranki ke so yanzu duk ba wannan a gidan makaho."
Laila da Mamy suka sake saka wata dariyar har suna tafawa kamar wasu kewaye.
Wannan karon Ma'eesha kukanta ne ya ƙaru sosai kamar ranta zai fita, ita kadai ta san halin da take ciki a wannan yanayin.
Bayan ta cika babban trolly ne ta ɗauki madaidaici ta zuba underwears ɗinta a ciki.
Sannan ta dauki karamin cikinsu ta zuba kayan kwalliyarta da turarruka, sannan ta dauko set sarƙar zinarenta za ta saka Mamy ta ce ke dakata ba in da za ki je da wannan."
Wani kallo Ma'eesha ta yi ma ta ta ce .
"Na mahaifiyata ce ita ta bani kyautatarsa dole ne tafi da shi."
Daidai lokacin Dady ya shigo yana cewa.
"Me kike yi ne har yanzu?"
Mamy ta yi saurin cewa.
"Alhaji ka karbi sarƙar set ɗin Gold ɗin nan kafa ta tafi da shi a sace ka san dai darajarsa."
"Ke Ma'eesha kawo ɗan akwatin nan."
Ta mika masa kawai ta zuge zip ɗin, sannan ta bude wata drawer ta ɗauko 🏧 card ɗin ta na cire kuɗi.
"Alhaji ka karbi ATM ɗin nan, su ma, ta tafi haka nan daga ita sai kayanta."
Tana rufe baki ya karɓa Atm card ɗin kamar me jiran umarni.key ɗin motar dake saman handbag ɗin ta Mamy ta kalla ta ce.
"Har da makullin motarta ma ka karba, don gidan da za ta zauna ba ƙofa ballantana a samu gate na shigar da motar, idan aka ajiye waje za'a sace."
"Eh haka ne."
Ya fada yana mika hannu. Ba musu Ma'eesha ta miƙa ma sa ya karɓa ya fice daga ɗakin.
"Ai duk wani abu da na san zai Maki amfani ba zan bar ki da shi ba."
Ta fada tana jan hannun Laila suka fice.
Ɗayan trolly ɗin ta fara fitowa da shi ta ajiye falon ta koma ciki.
"Kai makaho tashi ka dauki babbar akwatin kayanta ku tafi za ta fito da kananan."
Tashi ya yi yana lalube har ya ji ya ci karo da akwati ya ja yana yi wa Dady godiya da sallama ya fita.
Tana fitowa rike da dayan madaidaicin akwatin sai karami dake da kayan turarrukannta ta nufi hanyar fita ba tare da ta kallon Dady ba ballantana Mamy."
Sakin baki Mamy ta yi tare da cewa.
"Amarya ba sallama?"
Ba ta yanka ma ta ba ta fice daga cikin falon.
"Ikon Allah, ko irin sallama da iyaye a nemi tafiyarsu ba za ki yi ba kin fice ko, za ki zo gidan za ki ga wulakanci.
Kasancewar tana bakin ƙofa ta ji komai ya saka ta ce.
"Idan kin ga na zo gidan nan Mamy duk wulaƙancin da kika dama ki yi ma ni."
Ta saka kai ta fice Mamy ta saki baki yayin da Dady ya sunkuyar da kai ya kasa kallon Ma'eesaha.
"Ungo Laila ga kudin sadakinta nan dubu uku ki ɗauka ki kai ma ta hakkinta ne."
Da sauri Laila ta ɗauki kudin ta fice tana dariyar mugunta.
A harabar gidan ta gan su Yana gaba da babban trolly tana bin sa da kananan a baya.
Daidai lokacin motar Jamil babban yaron Mamy Yayan Laila ya danno hancin motarsa cikin gidan.
Ko parking ɗin kirki bai yi ba sakamakon ganin Ma'eesha na kuka, ga makaho na gaba da wata babban trolly wanda ya fi na hannun Ma'eesha girma, ga Laila na miƙa wa Ma'eesha kuɗi.
"Subhanah Ma'eesha me ya same ki kuma ina zuwa da kaya?"
Ba ta tanka ma sa ba ta yi gaba. kallon ƙanwarsa ya yi yana cewa.
"Munafuka me kuka yi ma ta kuma yanzu?"
"Aure Mamy ta saka aka yi ma ta da wancan makahon, shi ne ya zo ɗaukarta za su wuce, ga kudin sadakinta dubu uku ta ki amsa."
"What?"
Ya yi tambayar a firgice.
Yana ƙarewa makaho kallo ganin yadin jikinsa ba ta wuce dubu ɗaya ba, kuka daga gani kayan ma sun ji jiki, ko takaman ƙafarsa ma na soso ne sai wata hular taɓa ni ka ji hadisi da ya saka.
"Aure da wannan nakasashen?"
Girgiza kai ya yi tare da cewa
"Da sake!."
Ya bi bayansu a guje yana kiran sunan Ma'eesha, har ya karasa inda suke tafiya ba ta kalle shi ba.
Haka ya dinga bin su yana rokon Ma'eesha amma ba ta saurare shi ba, haka ya hakura ya bar ta ya dawo.
Kamar zai tashi sama haka yake tafiya har ya isa gidan. Don yau ya kara jinjina makirci da rashin imani irin na mahaifiyarsa.
*KADUNA*
Da sanyin asuba ta fito daga cikin bathroom dake cikin ɗakinsu.
Harara ta watsawa ƙanwarta dake zaune saman sallaya tana karatun Alkur'ani mai girma.
Cije laɓɓanta ta yi cike da takaici ta yi tsuki.
Bayan ta kai karshen surar da take karantawa ta kalli yayat tata ta ce.
"Aunty Sidra lafiya kuwa?"
Harara ta watsa ma ta tare da cewa.
"Ban sani ba."
"Allah ya huci zuciyarki."
Ta faɗa tana mai ci gaba da karatunta, don in da sabo ta saba da halin yayar tata.
Komawa toilet ta yi sakamakon jin wayar dake hannunta tana vibration
Ɗagawa ta ji bayan ta rufe kofar toilet ɗin, sannan ta amsa kiran daga cikin wayar ta ji an ce.
"Haba Sidra ki yi ki fito ma na kin ce na zo na ɗauke ki karfe biyar da rabi ga shi ba ki fito ba, ko na wuce za ki zo da motarki ce?"
Cikin yin ƙasa da murya ta ce.
"Ba haka ba ne Sadiya kin san ƙanwata Nasara tana zaune idan ta ga na fito da trolly za ta gane zan tafi wani waje ne, kin san kuma za ta iya sauro ta faɗa a gidan namu idan aka kama ni fa? Yanzu ki bani mintuna kaɗan zan tura ta wani wajen idan ta fita zan fito ba tare da motata ba don asirina zai iya tonuwa."
Tana fadar haka ba ta jira jin me ƙawar za ta ce ma ta ba ta katse kiran wayar .
Fitowa ta yi tana kallon Nadra dake karatun Alkur'ani ta kira sunanta.
"Ke Nadra!"
Nadra ba ta dakata da karatun Alkur'anin ba sai da ta kai aya ta ce.
"Na'am Aunty Sidra."
"Ki tashi ku je garden ki duba mani zobe na ya faɗi ina ganin lokacin da muke fira da Fahad jiya daddare."
Shiru ta ɗan yi kafin ta ce.
"Aunty Sidra why not ki bari sai da safe, yanzu akwai sauran duhu gari bai gama wayewa ba, idan gari ya waye sai na fita na duba ma ki. Za'a fi gani ma idan ba duhu ai, amma yanzu ba lallai a gan..."
Idan ba za ki je ba ne ki fada ma ni, ai ga wayarki nan ki kunna torchlight ku je ki duba ma ni."
Ba tare da ta sake yin magana ba ta miƙe tsaye tana cewa.
"Bari na je na duba ma ki."
Fita ta yi daga ɗakin ba tare da ta cire dogon Hijabin dake jikinta ba, wmhannunta rike da wayarta tana cewa.
"Allah ya huci zuciyar Amarya a gidan Yaa Fahad, ai bai kamata a ce yau za'a ɗaura ma ki aure kina faɗa ba."
"Ke dai kika sani munafuka."
Sai da ta tabbatar ta nufi Garden ɗin sannan ta janyo trolly ɗin ta daga cikin wardrobe, kasancewar dogon Hijabi har ƙasa ta saka ba's ganin ko me take ɗauke da shi.
A hankali ta bude ƙofar ɗakin bayan ta rataya handbag ta saka wayarta ciki.
Akwai mutane a falon wasu na kwance wasu na zaune, kasancewar bikin auren Sidra ake yi ƴan uwa da abokan arziki na nesa duk sun zo garin, ɗakin ɓakin ya yi ma su kadan wasu suka kwana a falon.
Cikin sanɗa take tafiya wata ma ta dake zaune ta ce.
"Ke wace ce nan ke sanɗa?"
Sai da gaban Nadra ya faɗi sannan ta juyo ta ce.
"Ina kwanaku?"
"Oh Amaryar ce ashe, lafiya lau ya kike?"
Suka hada baki wajen amsa gaisuwar, wata dattijuwa ta ce ni fa ba na banbance wace ce Sidra wace ce Nadra."
Wata buduwar ta ce .
"Wacce ta fara fitowa ta karasa ta durƙusa ta gaishe ku ita ce Nadra, wannan ta yanzu kuma ita ce Sidra wacce za'a ɗaura wa auren yau, ai suna da banbanci ita Amaryar Sidra ai fara ce, ita kuma Nadra baƙa ce."
Ita dai ba ta bi ta kansu ba ta wucewarta waje.
Sai wata buduwar ta ce
"Ai wannan Amaryar ba ta da kirki wallahi, jiya da Nadra ta ce mu zo mu kwana a ɗakinsu tun da su biyu ne amma fir wanan Amaryar ta ce wai ga falo nan ai, Sidra ba ta da kirki."
Suna ta firarsu har Nadra ta dawo ta yi ma su sannu ta shiga ɗaki.
Sai dai ba ta ga Sidra ba a tunaninta tana toilet ne don haka ta koma ta zauna a saman sallayarta tana cewa.
"Aunty Sidra ban ga komai ba wallahi."
Ta cigaba da karatunta don hadda take yi ba da Alkur'ani take karatun ba.
_Sidra_
Tana zuwa harabar gidan ba kowa maigadi dawowarsa daga masallaci kenan ya ga tana kokarin fita ya ce.
"Amarya lafiya kuwa."
Kamar ba za ta yi magana ba ta ce.
"Zan ba kawata saƙo ne tana waje."
"A dawo lafiya."
Ya fada yana zama kan kujerarsa hannunsa rike da carbi.
Tana ƙarasawa ta buɗe bayan motar ta saka jakar kayanta sannan ta zagaya ta zaune wajen me zaman banza.
Ba tare da ɓata lokaci ba Sadiya ta yi wa motarta key suka bar layin.
"Na daɗe ina jiran ki fa."
"Wallahi Nadra ce nake ta so na ɗauke hankalinta kar ta ga fita ta da akwatin kaya ta tona ma ni asiri shirina ya lalace."
Shiru Sady baby ta yi tana rage gudun motar tana rage gudun motar bayan sun bar layin.
Kiran waya ne ya shigo wayar Sidra, ta ɗaga tana cewa.
"Hellow Khadijah ya aka yi ne?"
"Kina ina ne?"
"Ya kike tambaya ta kamar ba ki san komai ba, amma ai na fada ma ki komai kasancewar ki ƙawata."
"Sidra abun da kike ƙoƙarin aikatawa kuskure ne, za ki wulaƙanta iyayenki ne, bayan kin san sun tara jama'a ana shagalin biki yau za'a ɗaura auren ki a ce kin gudu ya kike so su yi da jama'ar da suka tara? Sannan ga shi Fahad ɗin da iyayesa su ma sun tara na su jama'ar sai su ji labarin matar da Ɗan su zai aura ta gudu zai ji shi Fahad ɗin."
"Ke ba gudawa fa zan yi ba, da zaran na samu abinda na je nema zan dawo ne sai a sake saka ma na ranar ɗaurin auren zuwa gaba, don na san Fahad na masifar so na dole ya jira sai na dawo, iyayena kuma za su hakura ne kawai ba yadda za su yi da ni bayan na dawo, kin ga idan na ba su haƙuri ai za su karbe ni ko da sun yi fushi kuwa. kuma ba wani daɗewa zan yi ba me yiwuwa nan da watanni uku na dawo."
Tana fadar haka ta katse wayar tare da kashe wayar gabɗaya.
"Khadijah ƙawata ce tun da na fada ma ta plan ɗina ta saka ni gaba wai kar na aikata."
"Da ma me zai kai ki faɗa wa wata idan b ke ba."
Daga nan ba wanda ya sake magana a cikinsu.
_Nadra_
Tana idar da karatun Alqur'ani ta yi knocking ƙofar toilet ta tabbatar ba kowa kafin ta tura ƙofar. Ganin ba Sidra ya sa ta dauka ko ta fita zuwa wajen su Umma ne, don haka ta fita zuwa falon mutanen ɗazu ne a ciki, tana sanye har lokacin da hijabi ta nufi part ɗakin Umma. Da sallama a bakinta ta tarar da Umma tare da ƙanwar Abba wacce suke kira da Goggo Laraba da suka kwana ɗakin Umma."
Ta durƙusa ta gaishe su cikin girmamawa, suka amsa ma ta cike da kulawa. Gwaggo Laraba ta ce.
"Ina Amaryar take ne ko tana can tare da ƙawayenta?"
"Ai ƙawayenta tun jiya ta Kore su wai ta sallame su ba ta son kowa ta kwana a gidan."
Da mamaki Umma ke kallon Nadra, Gwaggo Laraba ta ce.
"Sidra ba ta da mutunci wallahi."
"Kira ma ni ita."
Cewar Umma tana budar drawar da take zuba magungunanta a ciki.
"To Umma bari na je na duba duk da ba ta cikin ɗakin."
Tana fita ta nufi part ɗin Abba ta gaishe she shi shi da wani wan Umma suna zaune .
Gaishe su ta yi cikin girmamawa sannan ta fita ta koma ɗakinsu. Ta nemi Sidra ba ta ciki.
Don haka sai ta yi tunanin bari ta zagaya duka gidan ko tana wanni wajen a cikin gidan.
Umma kuwa ta buɗe drawar da take saka magungunanta a ciki dan ta ɗauko man maganinta na sha'awa a ƙafa. Sai ta ga wata farar takarda, tana fitowa ta warware ta fara karantawa kamar haka.
*Assalamu alaikum*
*Iyayena ku gafarce ni zan yi wata tafiya domin cikar burina. Na san za ku shiga tashin hankali a yayin da kuka ga wannan wannan ya wasiƙar ta wa. Ku ba wa Fahad da iyayensa haƙiri na san yana so na zai jira har lokacin da na dawo mu yi aure.*
_Sidra Abdallah Maitama_
Wani jiri ne ya ɗebi Umma ta yi luu za ta faɗi, cikin zafin nama Gwaggo Laraba ta tare ta tare da zaunar da ita bakin gadon.
Takardar Gwaggo Laraba ta ɗauka tana karantawa.
"Innalillahi wa 'inna ilahir raji'un."
Shine kalmar da Gwaggo Laraba take furtawa.
Kafin ta ɗauki wayarta ta kira lambar wayar Yayanta wato Mahaifin Sidra.
Bugu ɗaya ya ɗaga, ta sanar da shi ya zo ɗakin Umma yanzu.
Sannan ta fita zuwa ɗakin da Mahaifiyarsu ta sauka, ta tarar da ita ita kaɗai, don ba wanda ya je wajenta saboda masifarta.
Ita ma Gwaggo Laraba ba ta sanar da ita abun da ya faru ba, ta dai ce ta zo ana neman ta a ɗakin Umma.
Carko-carko suka yi a ɗakin Umma, Daga Abba har mahaifiyar su da suke kira Ammi da Gwaggo Laraba.
Umma na kuka kamar ranta zai fita yayin da kowa ya kasa magana. Abba ransa ya kai matukar tashi, idanunsa sun yi jajir, Ammi sai alawadai da Sidra take yi yayin da Gwaggo Laraba ta kasa magana.
Nadra ce ta shigo da sallama, ganin mahaifinsu kwance tana hawaye ya saka ta ruga gabanta ta rike hannunta tana hawaye ta ce.
"Umma me ya same ki ?"
Ta ji tambayar tana hawaye. Ganin haka ya saka Gwaggo Laraba janyo Nadra tana cewa.
"Ba abinda ya same ta tana kukan rabuwa da Sidra ce, kin san daga Anjima za'a ɗaura aurenta shi ke nan fa ta zama yar wani Family."
Haka kawai Nadra ta ji ba ta gamsu ba tana son yin magana ta ki Umma na cewa.
"Kada ki damu Nadra kewa ne kawai da zan yi na Yayarki."
Ya karasa maganar tana murmushin karfin hali.
"Umma na duba ko ina ban ga Sidra ba."
"Eh ta tafi wajen gyaran jiki ne Anjima za ta dawo. Ta shi ki tafi."
Haka kawai jikinta ya yi sanyi ta tashi ta tafi .
Cikin damuwa Ammi ta ce.
"Amma yarinyar nan ta gama tozarta mu, sai da ta bari mun tara jama'a gida ya cika da mutane sannan za ta ma na haka? Ga wasu mutane suna kan hanyar zuwa daga wasu garuruwa na nesa don halartar wannan ɗaurin auren ne za ta kunyata mu."
Sai da ta goge hawaye kafin ta ce.
"Abdullahi ka kira wadanda ke hanyar zuwa garin nan wajen daurin aure ka dakatar da su su juya su koma ba zancen auren kuma. Wadanda ke nan garin na dan dole su zo don Allah kaɗai ya san yawan su idan sun zo a basu hakuri su koma. Suma dangin angon a kira a ba su haƙuri su sallami baƙin da suka gayyata na nesa su koma garinsu na kusa kada su zo, wallahi Sidra ta gama kunyata mu ta tozarta mu."
"Ba za'a kira kowa ba ba wanda za mu dakatar daga zuwa kowa ya zo, kanta ta yi wa ba mu ba, wallahi ba ta isa ta tozarta mu ba. "
Da mamakin kowa ke kallonsa kafin ya ce.
"Za'a daura auren yau sai dai ba da Sidra ba tun da ta gudu, za'a ɗaura auren da ƙanwarta Nadra."
Da mamaki Gwaggo Laraba ke kallonsa kafin ta ce.
"Kar ka aikata abun da zai zo ya saka mu yi nadama, ka san irin soyayya da shaƙuwar da Fahad ya yi da Sidra, suna masifar son juna, ba wanda ya haɗa su sune suka ga juna suka hada kansu suke soyayya. Shin idan aka yi haka kana ganin Fahad zai yarda ya karbi ƙanwar Sidra a matsayin matarsa, ita ma Nadra za ta yarda ta zauna da saurayin Yayanta a matsayin mijin aurenta? Kuma shi Fahad irin mazan nan ne ƴan boko ma su son rayuwar wayewa, Shi ya sa ya nemi Sidra don ita ma haka rayuwarta take ba, amma ita Nadra da take da kunya da ustazanci ba ta damu da rayuwa ba shin ta ya ya zaman su zai yi daidaita tun da ra'ayinsu ba ɗaya ba?"
*To masoyana ga ni ɗauke da sabon labari, tafiya ne tsakanin duhu da haske, wata kila ya zo daidai da ra'ayinku🥰 watakila kuma akasin haka😒 Ni dai fatana a duk lokacin da kuka ci karo da abinda bai ma ku ba a cikin labrina to ku kasance ma su fahimtata da kuma yi ma ni uzuri. A cikin wannan labarin za mu fuskanci rayuwar waɗan nan jaruman guda biyar*
Khalifa (makaho)
Ma'eesha Ibrahim Khalil
Fahad Umar Majidaɗi
Sidra Abdullahi Maitama
Nadra Abdullahi Maitama
*Waɗan da suke da labari mabanbanta, ku dai ku kasance da ni a cikin wanan labarin don ganin wani dararasi ya zo da shi.*
*Maman Ihsan ce*✍️
Follow the TASKAR MAMAN IHSAN channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaiufWb3LdQYnzC2vH0z
*MAKAHO NE*
*NA*
Maman Ihsan ce ✍️
https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
page0️⃣2️⃣
"Kar ka aikata wani abin da zai zo ya saka mu yi nadama, ka san irin soyayya da shaƙuwar da Fahad ya yi da Sidra, suna masifar son juna, ba wanda ya haɗa su sune suka haɗa kansu suke soyayya. Shin idan aka haka kana ganin Fahad zai zai yarda ya karɓi kanwar Sidra a matsayin matarsa, ita ma Nadra za ta yarda ta zauna da saurayin Yar ta a matsayin mijin aurenta? Kuma shi Fahad ɗin irin mazan nan ne ƴan boko ma su son rayuwar wayewa, shi ya sa ya nemi Sidra don ita ma haka rayuwarta take . Amma ita Nadra da take da kunya da ustazanci ba ta damu da rayuwa ba shin ta ya ya zaman su zai daidaita tun da ra'ayinsu ba ɗaya ba?"
"Ka da ki damu Laraba in sha Allah babu nadamar da zai biyo baya in dai Nadra ya aura. Ni na haife su na san halin kowacce a cikinsu, sai ya fi jin daɗin zama da Nadra akan Sidra. Domin ita ce nake da yaƙinin zai iya sarrafa ta ta sarrafu ma sa yadda yake so, kuma ita ce zai iya daka ma ta tsawa ta saurare shi saɓanin Sidra. Da a ce tun farko Nadra ya gani yake kuma ta gudu, to ba zan taɓa cewa zan musanya ma sa ita da Sidra ba, don kada ya yi kuka da ni daga baya, amma Alhamdulillah tun da har Sidra ce ta gudu zan musanya ma sa madadinta da Nadra na tabbatar wata rana sai ya yi alfahari da wannan madadin, domin kuwa Nadra mace ɗaya ce har da ƙari."
Shiru dakin ya ɗauka ba wanda ya sake yin wata magana, domin kuwa sun san cewa Nadra ba ta da matsala.
"To yanzu ya kamata ka sanar da Fahad ɗin idan ya amince da Nadra."
Cewar Ammi tana kallonsa.
Wayarsa ya lalubo a cikin aljihun rigarsa yana dannawa lambar Fahad kira.
_Fahad_
Kwance yake a gadonsa ya lulluɓe da bargo yana barci.
Wayarsa dake saman side ta fara ruri.
Cikin barci ya ji kiran wayar, a tunaninsa Sidra ce, don da ita ya kwanta a ransa, bai same ta a waya ba. Kuma ya san ita ba ma'abiciyar kashe waya ba ne, kuma kullun asuba yakan kira wayarta ko ya turaa ta saƙon barka da safiya. Amma yau sai ya kira switch off.
A hankali ya bude idanunsa yana tashi zaune ya miƙa hannunsa ya ɗauki wayar.
Ganin sunan Mahaifin Sidra ne sai da gabansa ya faɗi.
Ya ɗauki wayar tana gab da tsinkewa.
"Assalamu alaikum."
Daga cikin wayar ya ji muryar Abba ya ce.
"Wa'alaika salam Fahad?"
"Na'am Abba."
"Idan ba damuwa ina son ganinka yanzu a gidana."
"To Abba."
Ya amsa sannan Abba ya kashe kiran wayar. Bargon da ya lulluɓe ya yaye ya sauko daga kan gadon. Farin wando ne Three-quarter ya sanya, babu riga a jikinsa ga wani zanen Tattoo a ƙirjinsa zuwa hannunsa.
Bathroom ya faɗa don yin wanka.
Tsawon mintuna talatin ya ɗauka yana wanka kafin ya fito ɗaure da towel a ƙugunsa da wani ƙarami yana goge dogon gashinsa. Jikinsa sai kamshin shower gel da turaren wanka yake yi.
Tsadadden man shafawarsa ya shafa a jikisa, sannan ya fesa body spray. Closet ɗin sa ya shiga ya cikin tsadadden ɗanyar shaddar sky blue, sannan ya fesa turarensa mai suna Creed Aventus turare mai ƙarfi da jan hankali. Sannan ya ɗauki agogonsa Rolex date just ya ɗaura a tsitsiyar hannunsa. Ya duba bangaren takalmominsa ya ɗauki takalminsa Jimmy choo ya saka a ƙafarsa tsakanin nevy blue don haka ya saka hularsa nevy blue.
Ya fito ina da ya dauki wayoyinsa tare da key ɗin motarsa ya fara takunsa cikin izza wanda kallo ɗaya za ka yi ma sa ka san yana kan cin ganiyar samartakansa, kyau da cikar haibarsa suka sake bayyana.
Ƙamshin turarensa ya tabbatar wa da jama'ar dake falon yana gab da saukowa.
Idanu suka zuba wa upstairs ɗin yayin idanunsu ya sauka akansa.
A ƙalla mutanen da suke falon za su kai su goma kuma duk baƙi ne da suka zo bikin.
Gaishe su ya yi suka amsa suna ma sa ƴar tsokanar da ake yi wa ango.
Bai saurare su ba ya nuf part ɗin Mama. A falo ya same ta ita da ƙanwarta ya gaishe su.
"Ina za ka je na gan ka da makullin motar ko breakfast ba ka yi ba."
"Ina sauri zan je na dawo kafin abokaina su iso don suna hanya."
"Ina za ka je ne wai?"
Cewar Aunty Nana ƙanwar mahaifiyarsa.
"Gidan surukaina ne suke nema na."
"Okay a dawo lafiya."
Daga nan ya fice, zuwa part ɗin Baba. Shi ma ya gaishe shi sannan ya sanar da shi fitar da zai yi.
Ta ƙofar falon Baba ya fita ba tare da ya koma main falon ba.
Wajen motar da zai fita da ita ya nufa, ya shiga motarsa ƙirar Mercedes Benz G63 AMG ya yi ma ta key, kafin ya horn har maigadi ya wangale ma sa gate ɗin gidan ya fice da motarsa. Wanda kallo ɗaya za ka yi wa motar ka san cewa an narka dukiya wajen siyen motar.
Kai tsaye ya dauki hanyar da za ta sada shi da unguwar su Sidra.
_Maeesha_
Tafiya kawai take yi tana hawaye hannunta rike da akwatina biyu, yayin da Makaho ke jan babbar akwatin da ɗaya hannunsa. Ɗayan hannu kuma yana rike da sandarsa yana dogarawa.
Bin bayansa kawai take yi ba tare da ta san in da za su tafi ba.
Tsawon lokaci suka ɗauka suna tafiya, kasancewar ba ta saba yin tafiyar kafa ba ga kaya duk ta bi ta gaji.
Don haka ta tsaya ba tare da ta yi magana ba, shi ma sai ya tsaya kamar ya san ta tsaya.
Sai dai bai yi magana ba ya yi shiru. Ganin ba ta da niyyar cigaba da tafiya ya saka ya ce.
"Ki yi hakuri mu tafi akwai sauran tafiya a gaban mu ga magrib ta kusa."
"Ba zan iya sake wani tafiya ba na gaji."
Kafin ya yi magana ta hangi mai keke nape ya fito layinsu tsaida shi ta yi ya tsaya a gabanta .
"Hajiya ina zuwa."
Kallon Makaho ta yi tare da cewa.
"Ka zo ka faɗa ma sa sunan unguwar."
Ya karasa yana lalube da sanda ya faɗa wa mai napep ɗin .
Mai nape ya saka akwatunan a baya ya ajiye daya a gefe, sannan ya ce su shiga .
Sai da ta shiga sannan ta ce wa makaho.
"Mallama ka shigo."
Kamar ba zai shiga ba sai kuma ya shiga baya bayan ya laluba ya zauna.
Shi ya sanar wa mai napep ɗin unguwar da zai kai su tare da ma sa kwatance.
Tun da suka shiga layin jikin Ma'eesha ya yi sanyi . Don kallo ɗaya za ka yi wa yankin ka san cewa unguwa ce ta talakawa. Don ba gini mai kyau a layin da zai tabbatar ma ka da akwai masu rufin asiri a layin.
Kamar yadda ya yi ma sa kwatance da masallacin kuwa haka aka yi, sai da ya kawo daidai masallacin da ya sanar da shi ya tsaya ya ce.
"Mun iso wajen."
"Mallam don Allah ka taya mu sauke kayan kasa."
"To Hajiya."
Ya fada yana saukowa bayan ya kashe keke nape ɗin nasa.
Sai dai ya sauke ma su kayan sannan ta tambaye shi kudinsa.
"Nawa ne mallam."
"Ki bada yadda kuke zuwa ."
"Mallam ka yi magana ban san ya ake biya ba, don ban taɓa hawa keke nape ba sai yau."
Wani kallo ya ma ta har zai yi wata magana sai ya lura da haƙorin Gold ɗin dake bakinta, hakan ya tabbatar ma sa da cewa Hajiya ce ita, kuma yanayin ta ma ya nuna ƴar hutu ce.
"Ki bayar da dubu ɗaya."
Ya fada yana shiga cikin napep ɗin nasa. Handbag ɗin ta ta zuge ta ciro 1k ta bashi.
Bayan ta sallame shi ne Makaho ya ja akwatin kayanta babba ya yi gaba, ita dai bisa ta yi a baya har suka ƙarasa ƙofar wani gida. Gidan ƙofarsa ta ɓalle tun daga waje ma ana hangen wa su matan dake tsakar gidan.
'Na shiga uku ni Ma'eesha wane irin gida ne nan na faɗo.'
Sallama Makaho ya fara yi sai da aka ba shi izinin shiga sannan ya shiga tana bin sa a baya.
Ɗakunan gidan za su kai Ashirin. Don tsakar gidan ma cike yake da mata ga yara barkatai ta ko ina. A tsakar gidan.
Wasu yaran suna wasa, yayin da wasu na faɗa sai wasu yaran zaune sun jeru suna kashi a ta ko ina suke zaune ba tsari .
Wata dattijuwa ta kalli Makaho ta ce.
"Mallam Khalifa ka dawo ?"
"Eh Baba na dawo."
"To ma sha Allah, wannan ita ce Amaryar taka?"
"Eh ita ce."
Wata uwar ashar suka ji an danna, wanda ya saka hatta Makaho da Ma'eesha sai da suka tsaya cak daga tafiyar da suke yi.
Larai Dillaliya ce ta yi zargin tana kallon takalmar dake ƙafar Ma'eesha wanda a ƙalla kuɗinsa za su kai dubu ɗari 100k haka handbag ɗinda ke hannunta ma zai kai dubu ɗari.
Kafin a gama mamakin ashariyar da ta ɗura aka ci muryar Larai ta sake cewa.
"Wannan ita ce matar Khalifa makaho kenan?"
"Makaho ya cigaba da tafiya Ma'eesha kamar za ta faɗi sakamakon idanun da ta ji suna yawo a jikinta, sai dai kanta a ƙasa ba ta ba da damar ganin fuskarta sakamakon mayafin abyarta da ta rufe rabin fuskarta da shi hawaye ne kawai ke bin fuskarsta ba tare da kowa ya sani ba.
Hakan ya saka kanta a sunkuye tana kallon ƙasa yake tafiya ba ta yarda ta gaishe da mutanen gidan ba saboda kuka zai iya ƙwace ma ta matukar ta ce za ta buɗe baki ta yi magana.
Ɗakin karshen gidan wanda ke da ƙofar langa-langa ya tura ya shiga da sallama.
Ita ma shiga ta yi idanunsa na sauka kan buhun siminti da aka shimfiɗa a ɗakin
Ƙafarta ya harɗe cikin buhun da ake shimfiɗa madadin carpet. Nan ta lura ashe ɗakin ko flour babu, ba'ayi simintin ƙasar ɗakin ba ƙasa ne kawai sai aka shimfiɗa buhu a ƙasan ɗakin wanda ya rufe ƙasar ɗake ƙasan ɗakin. Hatta bangon ɗakin ana iya ƙirga bulo ɗin don shi na bangon ba'a shafa ma sa siminti ba. Ga bangon duk ya yi gantsa kuka alamar ya sha ruwa kafin aka yi rufin ɗakin.
Kanta ta ɗaga sama tana kallon rufin ɗakin, nan take hangen haske daga sama, wato zink ɗin ɗakin ya hude a wasu wuraren aka hangen hasken waje, langa-langa ba sabo ba ne aka saka.
Kuma idan ana ruwan sama da alama ba ƙaranin yoyon ruwa zai yi ba, don ba makawa dai ruwa ya cika ɗakin idan har mai ƙarfi ne.
Toshe bakinta ta yi tana kuka don kada sautin kukan ya fita, kafin ta ji tsayuwar ya gagare ta ta zube akan ƙafarta tana kuka mai tsuma zuciya.
Kamar ya san kuka take yi sai ta ji ya kira sunanta cikin kamilalliyar muryarsa mai cike da nutsuwa.
"Ma'eesha."
Ba ta amsa masa ba sai hawaye dake bin fuskarta.
"Ki yi haƙuri na san wannan gidan bai dace da macen da ta taso cikin gata da hutu ba, kin taso cikin farin ciki na sani kina kwana a cikin A.c da katifa mai laushi ba'a dauke wuta ko an dauke ba iya sani saboda na'ura za ta fara aiki ki nan kuma ko fanka babu ballantana A.C ba na da halin da zan iya ciyar dake irin abincin da kike ci da ruwan da kike sha..."
Shiru ya yi sakamakon jin fitar ta daga ɗakin, tana fita ta yi tozali da fo da yarinya ta yi kashi ta tashi ba tare da an yi ma ya tsarki ba tana wasar ta. Wani na zaune kusa da fo ɗin yarinyar shi ma yana Kashin, Ma'eesha ta yamutse fuska, ta ji wata mata na cewa.
"Amarya hakuri za ki yi ɗakinki shi ne kuka da banɗaki dole ki dinga ganin haka.
"Ina ne banɗaki."
Ta tambaya tana kallon matar da idanunta da suka kumbura.
"Ga banɗaki nan jikin ɗakinki. Bari a kawo ma ki buta."
Kafin matar ta yi magana sai wata budurwa ta kawo wa Ma'eesha buta da ruwa a ciki.
Karɓa ta yi tana shiga ban dakin ta toshe hanci tare da fitowa a guje ta duƙa ƙofar ɗakinta tana kakarin amai, sakamakon wari da zaurin fitsari dake tashi a toilet ɗin.
Da kallo suka bi ta wasu na yi ma ta sannu. Bayan ta gama ne ta ga wannan buduwar da ta ba ta buta tana cewa .
"Tashi bari na gyara wajen."
Tana magana tana mika ma ta kasar pure water na ruwa, karba ta yi ta wanke baki sannan cikin kasalliyar murya ta ce.
"Thank you."
Cikin ɗakin ta koma ta ga makaho tsaye kamar yadda ta bar shi.
"Wallahi ba zan iya rayuwa a cikin wannan gidan ba."
Tana fadar haka ta janyo akwatin kayanta ta fito, shi ma ya janyo babban ya biyo ta suka fito suna tafiya."
Baba ta lalle su ta ce.
"Lafiya kuwa Khalifa?"
"Baba ina zuwa "
Abun da ya iya fada kenan saura. Matan kowa sai bin su yake da kallo. Suka ji muryar Larai Dillaliya tana cewa.
"Ni Ko da na kalli yarinyar nan na san ba kamar unguwar nan ba ne ballantana gidan nan, ko dai asiri Khalifa ya yi wa iyayen yarinyar nan ne da suka ɗauki ƴa suka ba shi aure?"
Ita dai Ma'eesaha ko kallo ba ta yi ma ta ba ballantana ta gane wa ke magana .
Tana zuwa ƙofar gidan ta ajiye akwatin hannunta, shi ma ya tsaya in da ya ji ta tsaya, ya ajiye akwatin amma sandarsa ta Manafi na hannunsa.
Handbag ɗin ta ta buɗe ta duba daga wayoyinta sai kuɗi 9k dama dubi goma ne ta ba mai napep dubu ɗaya ya rage dubu tara.
Ga shi matar Babanta ta amshe ATM card ɗin ta wanda a ƙalla tana da Naira sama da miliyan biyar a ciki. Pink lips din ta ta cije tana goge hawaye.
Kafin ta ce.
"Ina zan samu gidan haya kamar na zaman mutum ɗaya?"
"Gaskiya ban sani ba, amma dai idan aka tambaye Iro mijin Larai Dillaliya zai samo ma na, saboda dillancin gidajen haya yake yi a unguwar nan."
"Ina za'a same shi yanzu ?"
Kafin ya yi magana ne suka ji muryar wani mutum dake ƙoƙarin shiga cikin gidan yana cewa.
"Mallam Khalifa Amaryar ce nan?"
Yana tambayar amma idanunsa akan Ma'eesha wacce ta tsuke fuska, sakamakon kallon ƙurillar da yake yi ma ta.
"Yauwa Mallam Iro ka dawo?"
"Eh Allah ya yi."
"Dama yanzu muke maganar ka dai ga shi ka zo."
"Ikon Allah, ka san an ce ɗan halal ya ƙi ambato."
Kallon Ma'eesha ya yi yana cewa.
"Amarya ya garin ."
Ba ta amsa ma sa ba ta ce.
"Gidan haya za ka nema ma ni a yanzu nake buƙata iya na zaman mutum ɗaya."
Shiru ya yi yana tunani kafin ya ce.
"Eh akwai guda ɗaya a unguwar nan, shi kadai ne iya na zaman mutum ɗaya, sauran dole sai kin samu makota."
"Ina so sannan ina son ya kasance gidan mai tsafta ne."
"Ba matsala in dai tsafta ce, sai dai ƙarami ne sosai gidan. In taƙaice ma ki iya ɗaki ɗaya ne tal a ciki wato single room ne, ba falo ɗaki ɗayan nan ne sai banɗaki da kitchen madaidaita."
Ba haka ta so ba ta so ko da mai falo ɗaya da ɗakin barci a samu, amma tun da ya ce wannan kadai ne za ta amshe shi, ya fi ma ta wanann gidan da ta fito yanzu na ƙazamai."
"Ina ne gidan?"
"Farkon layin nan ne?"
"Okay nawa ne kuɗin?"
"Ba tsada dubu hamsin ne a shekara ɗaya."
Tunanin ta ina za ta samu dubu hamsin ne, ga shi dama ba ta iya yin transfer money from account ɗin ta har tana tunanin zuwa bank sa saboda matsalar ga shi dubu tara take da shi yanzu haka, ga shi ana maganar gidan dubu hamsin.
*KADUNA*
_Fahad_
A ƙofar gate ɗin gidan su Sidra ya yi horn.
Maigadi ya wangale ma sa gate ya shiga da motarsa ciki .
Bayan ya yi parking bai fito daga cikin motar ba ya ɗauki wayarsa ya kira Abba. Ya sanar da shi ya iso, nan Abba ya ce ya shigo yana part ɗin sa.
Da sallama ya shiga ƙofar part ɗin Abba.
Suka amsa ma sa gabaɗaya suna zaune a falon. Abba, Umma, sai mahaifiyar Abba wato Ammi, da ƙanwar Abba Gwaggo Laraba sai Aminin Abba Alhaji Abubakar
Kallo ɗaya Gwaggon Laraba ta yi wa Fahad a zuciyarta ta ce.
"Sidra kin yi wa kanki, domin wannan yaron miji ne na kece raini ne da da gudun wuce sa'a. Allah ya sa ya amince da zaɓin Nadra kada ya ki amince."
Ƙamshinsa ya cika falon ya karasa ya durƙusa ya gaishe su. Suka amsa ma sa gabaɗaya.
Shiru ne ya biyo baya, kafin Abba ya ce.
"Fahad."
"Na'am Abba."
"Ka yi waya da Sidra ce?"
"A'a Abba ba mu yi waya da ita ba."
"Tun yaushe kenan kuma wani magana kuka yi?"
"Wannan karon sai da gabansa ya faɗi sakamakon tambayar da aka yi ma sa."
"Lokacin ta ce mani za'ayi ma ta zanen lalle zuwa dare za mu yi waya, to a daren na yi ta kira ba ta ɗauka ba har yau na ji wayar a kashe ."
Cikin fargaba ya ce.
"Ina fatan dai tana lafiya ba wani abun ne ya same ta ba ko?"
"Tana lafiya."
Ɓoyayyar ajiyar zuciya ya sauke yana jiran dalilin kiransa.
Abba ya mika ma sa wasikar da ta bari ya karba ya fara karantawa.
Sai da ya mike tsaye tsabar dirgici da tashin hankali. Kafin ya kalli gabɗaya jama'ar dake falon ɗaya bayan daya, sai a lokacin ya lura da dukkansu a kwai rashin hankali a tattare da su.
"Innalillahi wa 'inna ilahir raji'un."
Kalmar da ya furta kenan idanunsa sun rikiɗe zuwa ja.
Cikin sanyin jiki ya zauna yana cewa .
"Sidra why why do this to me me ya sa kika amince tun farko? Ina kika je kika bar ahalinki cikin tashin hankali ba tare da yin tunanin halin da za su shiga ba."
Tashi ya yi yana kallon su idanunsa sun yi ja hatta farar fuskarsa sai da ta ji ja.
"Ku sanar da mutane kawai an fasa daurin auren , zan je ni ma na sanar da nawa dangin da abokan. Da ma su niyyar zuwa su dakata, ni ma zan dakatar da ma su niyyar zuwa. Duk da dai dama akwai wadan da za su zo daga ƙasar waje or ready suna hanya ba zancen juyawa tun da fly ne ba mota ba."
Ajiyar zuciya mai ƙarfi Abba ya sauke kafin ya ce.
"Ka bar su kawai su zo kar ka dakatar da kowa."
Da mamaki Fahad ke kallon Abba kafin ya yi magana Abba ya ce.
"Sidra ta gudu a ranar aurenka da ita, don haka zan maye ma ka gurbin ta da ƙanwarta Nadra idan har ka amince "
A matuƙar ruɗe Fahad ya kalli Abba ya na girgiza kai alamar a'a.
*Maman Ihsan ce*✍️
09065327995
Follow the TASKAR MAMAN IHSAN channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaiufWb3LdQYnzC2vH0z
*MAKAHO NE*
*NA*
Maman Ihsan ce ✍️
https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
page0️⃣3️⃣
"Sidra ta gudu a ranar aurenka da ita, don haka zan maye ma ka gurbin ta da ƙanwarta Nadra idan ka amince."
A matuƙar ruɗe Fahad ya kalli Abba ya na girgiza kai alamar a'a .
Sai a lokacin Ammi ta yi magana ta ce.
"Kai yaro Fahad kake ko, to bari na faɗa ma ka gaskiya auren Nadra da za mu aura ma ka gata muka yi ma ka, ka rubuta ka ajiye wata rana sai ka zo ka durƙusa kana yi ma na godiya, sannan za ka ce gara ma da waccen fitananniyar ta gudu ta bar ka ta gudu. Ka ga waccan da ta gudu masifar, girman kai, isa da gadara, sannan ga shegen taurin kai, ko ka aure ta da ƙyar za ta yi ma ka biyayya saboda ko anan gidan ba ta ganin kowa da gashi sam ba ta san darajar mutane ba. Amma yanzu Allah ya raba ka da ita za ka auri mai hakuri juriya da hangen nesa, uwa uba ilimin addini da tarbiyya."
Shi kam gabaɗaya Fahad ba ya ma gane me suke faɗa, don hankalinsa da tunaninsa na can wata duniyar ne daban. Ya kasa gane dalilin da zai saka Sidra ta aikata haka.
Muryar Abba ya dawo da shi daga duniyar tunanin da ya lula.
"Fahad ban yi ma ka tayin auren Nadra ba sai da na tabbatar da cewa na ma ka sakayya ne akan abin da Sidra ta yi ma ka, in dai har za ka iya zama da Sidra zaman aure to ina mai tabbatar ma ka sai ka fi jin daɗin zama da Nadra akan Sidra. Amma ba zan takura ma ka ba idan har ba ka son ka aure ta shi kenan mu bar maganar kawai Allah ya haɗa kowa da rabonsa na alkhairi."
Shiru ya yi yana nazari shi dai gaskiya ba ya jin son Nadra a Zuciyarsa. Kuma rayuwarta da ra'ayinsa ya sha banban da nata, shi ya fi son wayayyun mata masu aji kamar Sidra, ita kuma Nadra ga ta nan kamar wacce ba ta waye ba, shi tun da yake ma bai taba ganinta babu hijabi ba. Kullum cikin hijabi ko a cikin gida ma saka hijabi take yi kamar wata mai takaba, wani namiji ma zai ga surar jikinta har ta ja hankalinsa ya ce yana son ta, sannan ita baƙa ce shi kuma baƙar mace ba ta burge shi.
"Ba ka ce komai ba."
Sai a lokacin ya daga ya kalli Abba da Umma wacew ta kasa cewa komai, don tun da ya shigo bai ji muryar ta ba, ya san tashin hankali ya yi ma ta yawa. Sannan suna da karamci da mutunci, yanzu indai bai amince ba kamar ya kunyata su ne , domin tabbas da kunya sun tara jama'a a ce an watse ƴar su ta gudu ranar aurenta. Wanann ciwon zai dade bai bar zuciyarsu ba domin sun kunyata a idanun mutane, shi bai damu da kansa ba don an fasa aurensa iyayen ta ne abin dubawa .
Cikin sanyin murya ya ce.
"Na amince."
Gabɗaya suka saki ajiyar zuciya tare da saka ma sa albarka.
Tashi ya yi ya ma su sallama ya yi ficewarsa.
Abba ya kalli Ƙanwarsa ya ce.
"Kada a sanar da Nadra wannan zancen sai bayan ɗaura aure."
"Me ya saka haka to Yaya, tun da an ji ra'ayinta shi ma ya kamata a ki nata ra'ayin."
"Ba sai an ji ba, domin na san yarinya ce ita mai biyayya, ba ta taɓa tsallake magana ta ba, idan na ajiye kara na ce kada ta tsallaka ba za ta tsallaka shi ba. Ba ta da ra'ayi in da iyayenta muna so, don haka na hana a fada ma ta ne saboda tana da raunin zuciya, za ta shiga tashin hankali da damuwa wanda zai tona asirin abun da muka binne. A bar zancen akan cewa dama Nadra ce Amaryar ba Sidra ba, an yi mistake wajen saka sunan ne. Ko ita Nadra kada ta san cewa ba Sidra ta gudu ballantana hakan ya shafi walwalarta."
Jinjina kai Goggo Laraba ta yi ta fice daga part ɗin.
Kai tsaye ɗakin su Sidra da Nadra ta nufa, bakinta ɗauke da sallama.
Nadra tana waya da Ya Sayyadin ta, wato Mallamin su na islamiyya ke son ta suna son juna duk da cewar shi talaka ne, amma hakan bai dame ta ba.
Ganin Goggo Laraba ta ta ce.
"Zan kira ka Ya Sayyadi."
Daga haka ta katse kiran wayar tana kallon Goggon tasu.
_Ma'eesha_
Kallon Mallam Iro mijin Larai Dillaliya ta yi tana cewa.
"Mallam ina bukatar gidan hayan nan a yanzu ba sai Anjima ba. Amma gaskiya ina son na zaman mutum ɗaya ne kuma ya kasance akwai toilet da kitchen a ciki ."
"Hajiya idan na fahimce ki ginin zamani kike so ko? To gaskiya babu a unguwar nan. Gidan haya mai zaman mutum ɗaya da na sani akwai a ƙasa yaba can farkon layin kamar yadda na fada ma ki, sai dai ƙarami ne gidan, kuma ɗaki ɗaya ne tal ba barci bai da falo, sai kitchen a tsakar gida, toilet ma a tsakar gidan ba cikin ɗaki yake ba, kuma tsohon gida ne ba na zamani yadda kike so ba, idan dole sai ba zamani sai dai ki je ki nemi manyan dillalan gidan haya."
Cikin gajiya ta ce.
"Yanzu shi wanann da kake magana akwai a ƙasa nake so yanzu nan, amma ba na da kudin yanzu a ƙasa."
Kallon ta ya yi ya tabbata ba ta yi kama da wacce za'a ce miliyan ma ya fi karfin ta ba ballantana dubu hamsin.
"Hajiya ai wanan ba matsala ba ne za ki iya transfer."
"Account ɗina ya samu matsala sai dai na cire kuɗi da ATM card amma ba na iya transfer, sai na je banki akan matsalar."
"Yanzu yanzu ya kike so ayi dubu hamsin ne za ki iya zama ?"
"Idan ba za ka damu ba, ina son ka ka bani gidan yanzu, in sha Allah zuwa gobe da rana ka zo ka karbi kuɗin hayar gidan. Don ba kuɗi ba kuɗi hannuna 4k ne kawai."
"Ba damuwa mu je na kai ku gidan ga shi can farkon layin ba nisa gida uku ne ya shiga tsakanin da wanann gidan da aka ba makaho ɗaki kyauta kin ce ba kya iya zama."
Yana gaba suna bin sa a baya har suka wuce gidan uku, a na huɗun ne ta ga ya tsaya a ƙofar wani karamin gida dake da kofar fale-fale.
Sakata kawai ya cire ya tura kofar suna bin sa a baya .
Ƙaranin gida ne sosai ba wani wadancan tsakar gida. Kuka tsakar gidan ma ƙasa ne ba'a shafa siminti ba, hatta ƙofar ɗakin ma na fale-fale ne sai karamin window shi na ƙofar fale-fale ne.
Barandar ƙofar ɗakin dai siminti ne sai cikin ɗakin siminti ne sai dai an shafa siminti a bango.
Daga tsakar gidan ga toilet nan karami shi ma siminti ne a ƙasa, sai kitchen wanda ba wai gina shi aka yi ba, fale-fale aka buga aka killace wurin ya zama kitchen, aka masa ƙofa.
Godiya ta yi ma sa ya fice yana ma su sallama.
Akwatunan kayanta ta kalla ta kalli ko ina na gidan, kasancewar lokacin sanyi muke ciki gidan duk ya yi ƙura.
Ga shi ita ba wani aikin kirki yake yi ba a gidansu .
Masu aiki ke gyara ma ta daki da gado su wanke ma ta toilet, ayi ma ta wanki da guga, girki kawai take yi shi ka Mahaifiyar ta ce ta ce sai ta koya, gidan mijinta wata rana za ta tafi ba kowane namiji ke cin abincin masu aiki ba.
Ta ina za ta iya rayuwa ba wanda zai yi ma ta waɗan nan ayyukan?
"Dole na je banki gobe na samu na yi transfer ɗin kuɗaɗen dake cikin account ɗin na, za su iya kai miliyan goma. Zan nemi gida kamar na miliyan uku na siya mai kyau da zan iya rayuwa a cikinsa. Sannan zan ja jari na fara sana'a ko da Naira miliyan biyar ne, saura miliyan biyu da zai rage ma sai na siya kayan daki da kayan kitchen da abinci ma su sauƙin kuɗi."
Tana cikin wannan maganar ta ji karar shigowar sako a wayarta, sai da gabanta ya faɗi. Tana dubawa ta ga messages ne daga banki, jikinta na ruwa ta duba in da ta ga miliyan goma da ke account ɗin ta an kwashe su duka.
Salati ta saka tare da sakin wayar ta faɗi ƙasa, dubawa ta yi akan guiwar ya tana riskar kuka.
Tabbas ta san cewa mahaifinta kawai ya san Pin ɗin ta na cire kuɗi, kuma Mamy ce ta karbi ATM card ɗin lokacin da ta shigo ta ga tana tattara kaya. Kenan Mamy ta tambayi Mahaifinta Pin ɗin ya fada ma ta kenan, sun kwashe kudin don sun san za ta iya transfer suka riga ta.
Cikin kuka ta ce .
"Innalillahi wa 'inna ilahir raji'un, Allah humma ajirni fi musibati wa'a khalifni khalifan min ha."
"Shi ke nan Mamy kin ruguza Mani rayuwa Allah ba zai bar ki ba. Allah ga ni gare ka ka da kai na dogara ya zuljalalu wal ikhram."
Kuka take yi sosai ana kiran sallar magrib ta ga ya fita da sandarsa yana dogarawa ya fice daga gidan ba tare da ya ce ma ta koma ba.
Ta dade tana kuka kafin ta mike tsaye tana goge hawayenta ta ce.
"Daina kuka Ma'eesha ki daina ɓata hawayenki anan zaluncin da aka yi ma ki, ki rungume ƙaddarar da ta zo ma ki Allah yana tare da ke. Kuka ba bali ba ne ki shirya fuskantar sabuwar rayuwar da kika tsinci kanki a ciki."
Ita kadai take magana kamar wata zararriya.
Fitilar wayarta ta kunna kasancewar akwai duhu kuma ba wutar nepa.
Waige-waige take yi nan ta lura ashe akwai rijiya a gidan can karshen gidan
Handbag ɗin ta ta duba ta ciro karamin bottle of water wanda ta shiga shagon saloon da shi ba ta sha ba.
Alwala ta yi sannan ta duba cikin akwatin kayanta ta dauki Ɗankwali ta shimfida ta gabatar da sallar magrib.
Tana cikin addu'a aka kira isha'i ta tashi ta gabatar.
Tashi ta yi bayan ta yi addu'a ta nufi kofar fita gidan hannun ta rike da handbag.
Wani shago dake kusa da gidan ta tambaye shi in da ake fitar da tsintsiya da faka ya ce wata bayarabiya ce kuma tun karfe shida take rufe shago ta wuce gidan.
"Cikin damuwa ta ce .
"Ba wani wajen kuma?"
"Gaskiya sai dai ki bari da safe ."
"Yanzu nake bukata wallahi."
" Daren nan kuma?"
Ya tambaya yana mamakin yadda ta dage.
"Eh yau muka tare a wancan gidan, ya yi ƙura dole sai na share kafin mu kwana a ciki."
"Allah Sarki, bari na ara Maki na shagona zuwa da safe sai ki dawo Mani da shi ko?"
"To na gode."
Ya mika ma ta tsitsiyar da faka ta amsa ta tafi.
Har ta fara tafiya ta dawo ta fiye ruwar roba gida biyu ta wuce.
Ko da ta koma ta samu makaho tsaye a tsakar gidan hannunsa rike da sandarsa.
Ba ta kalli in da yake ba ta shiga cikin ɗakin.
Yanar gizo-gizo ta fara cire wa a silin da bango, sai da ta kakkaɓe sannan ta share ɗakin ta kwashe dattin cikin faka tana kai wa waje can karshen bangon gidan.
Sannan ta fito ta share simintin barandar ƙofar.
Tsakar gidan ta fara share wa, sai dai kasancewar kasa ce ba siminti ba ƙura ya addababe ta ta fara atishawa da tari sakamakon kuran.
Gefen mayafin abayar dake jikinta ta sa tana toshe hanci da daya hannun daya hannunta tana shafa har ta gama.
Fita ta sake yi tana tari da atishawa ta koma wajen me shagon.
Ganin akwai mutane ta tsaya gefe tana jiran a rage, bayan an rage ta samu ta karasa bakin kofar shagon.
"Hajiya kin dawo?"
"Eh dama ina son ne ka bar mun tsintsiyar nan da zuwa gobe sai na siya maka wata, saboda zan wanke toilet da shi ne kuma bai dace na dawo maka da ita ba bayan na wanke toilet."
"Ba damuwa ki rike duka na bar ma ki."
"To na gode sosai."
"Ina son ka ba ni detergent da hypo ne."
Daidai lokacin da wani mai siyar da robobi yake dawowa daga talla.
"Dakata mallam."
Sai ya tsaya ta karasa wajensa ta siya madaidaicin bokintin roba na 1k ta detergent da hypo dama ta siye ruwa Roba biyu ta kashe 1k ta zuba su a roba ta koma cikin gidan.
Handbag ɗin ta ta duba tana tafiya ta ga 2k ya rage ma ta cikin 5k da ga bar gidan da shi
Cire kayan ta yi daga cikin bokitin sannan sai ta karasa wajan rijiyar duk da ba ta da tabbacin cewa akwai guga.
Ta haska torchlight na karamar wayarta ya ga an daure guga jikin karfe dake jikin murfin rijiyar.
Abinda ba ta taɓa yi ba a rayuwar ta jan ruwa daga rijiya .
Kamilalliyar muryarsa mai cike da kamala ta s ji ya ce.
"Me kike ta yi a daren nan ne?"
Kamar ba za ta amsa ma sa sai ta ce .
"Ruwan zan ka a rijiya zan wanke ɗakin ne da kuma toilet, don ba zan iya amfani da su a haka ba."
"Bari na taya ki jar ruwan, ki je dakin sai na kawo ma ka."
Kallon mamaki ta masa ta ce.
"Da wake idanun za ka gani ruwan kuka har ka kawo mani?"
Ganin bai yanka ta ba kuma kamar ransa ya ɓaci ta wuce ta ba shi wuri."
Laluben rijiyar ya yi har hannunsa ya sauka akan gugar ya janyo ta ya ji nauyi, don dama igiyar na ɗaure a jikin karfe guga na cikin ruwa .
Sau uku ya janyo ya cika bokitin.
Ya kai tana mamaki ya karba ta wanke dakin bayan ta zuba hypo da detergent.
Sau biyar yana ciki bokitin yana kawo wa tana wanke wa tana sharo ruwan a waje, tana kashewada faka har ta gama ta wanke barandar.
Daga nan kuma ta nufi toilet ɗin, nan ma siminti ne irin toilet na tsuguno na gargajiya.
Sai dai ya kawo ma ta ruwa bokati uku ta ɗauraye toilet ɗin bayan ta wanke.
Tana kallon ikon Allah makaho da ɗibar ruwa a rijiya, yana rike da bokitin a daya hannu yayin da daya hannun kuma yake dogara sandarsa ta makafi.
*KADUNA*
Bayan Nadra ta katse kiran wayar da take yi da Ya Sayyadinta.
Cikin ƴar damuwa ta ce .
"Goggo har yanzu ban san in da Aunty Sidra ta shiga ba, tun dazu nake zagaye gidan nan, ko dai ta fita ne?"
"Eh kada ki damu ta je gyaran jiki ne kuma a'ba za ta dawo da wuri ba."
"Allah ya dawo ma na da ita lafiya."
"Amin ya Allah. Yauwa ki tashi yanzu nan direba zai kai mu wajen gyaran jiki da kitso."
"Waye za'a yi wa?"
"Da ni da ke."
"Goggo ke ma kin san ba na son kitso, saboda gashin kaina yana da yawa sosai, tsayin kitson ma yana damuna."
"Sai da an yi shi don haka ba baƙi mintuna Talatin ki yi breakfast ki fito."
"Toh."
Ta fada duk da ba ta son kitso sai dai ta dunƙule kanta kanta ta cusa cikin hula ko Ɗankwali. Amma kasancewar ta ba mai musu ko gardama ba ne ya saka ta tashi ta nufi bathroom don yin wanka.
Bayan ta fito ne ta shafa man ta mai sanyin ƙamshi ta shafa, wanda yake karɓar baƙaar fatarta mai sheƙi. Ta shirya cikin kayan doguwar rigar material ta saka. Sannan ta sanya dogon Hijabinta ta dauki handbag da wayarta ta fice bayan ta saka flat shoe.
Wayar Sidra take sake kira har lokacin switch off.
Part ɗin mahaifiyar ta ta nufa saboda tana son sake duba jikinta. Sai dai an fada mata Umma na part ɗin Abba. Kamar sa ta bi ta can sai ta fasa
Tana fitowa ta ga jama'a kowa na kallonta jama'ar dake falon dangin Abban ta ne.
Wata ma daga cikin su ta ce.
"Allah Sarki Nadra rabon dai ke za ki riga yar taki aure.?"
"Ni kuma ?"
Ta tambaya cikin mamaki. Matar za ta sake magana kenan sai Goggo Laraba ta dakatar da ita ta hanyar girgiza ma ta kai."
Hakan ya saka matar ta fahimci Nadra ba ta san da ita za'ayi auren ba.
Shagwaɓe fuska ta yi ta ce
"Goggo lalle kawai nake so jiya fa na je saloon aka gyara mun kai na "
Murmushi Gwaggo Halima ta yi ta ja hannun ta suka nufi ƙofar fita suka fice .
Direba ne ya kai su har shagon da Gwaggo Laraba ta sanar da shi
Bayan sun fita ya tsaya jiran su yayin da suka shiga.
Nadra ta zauna yayin da Goggo Laraba ta yi wa mai saloon maganar uzuri suna sauri kuma amarya ce za su je reception ne, take ta kira ɗaya daga cikin yaran aiki ta ta karasa yi wa wata lalle, ita kuma ta fara tsantsara wa Nadra lafiyyarnb zanen lalle mai dauker hankali.
*Maman Ihsan ce.*✍️
09065327995
Follow the TASKAR MAMAN IHSAN channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaiufWb3LdQYnzC2vH0z
*MAKAHO NE*
*NA*
Maman Ihsan ce ✍️
https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
page0️⃣4️⃣
Nadra ta zauna yayin da Goggo Laraba ta yi wa mai saloon maganar uzuri suna sauri kuma amarya ce za su je reception ne. Take ta kira ɗaya daga cikin yaran aikinta ta karasa yi wa wata lalle, ita kuma ta fara yi wa Nadra lafiyyarn zanen lalle mai ɗaukar hankali.
Kamar yadda ta nuna ba ta son kitson haka aka yi ba'ayi ma ta ba, sai sai gashin na ta ya sha gyara sai sheƙi da wani ni'imtacen ƙamshi take yi.
Abun da ya sake ba ta mamaki bayan na gama ma ta sai ta ga Mama Laraba ta ce su je ta shiga ciki za'ayi ma ta gyaran jiki.
"Mama wani gyaran jiki kamar wata Amarya?"
"Ai ke ƙanwar Amarya ce ya kamata duk abin za'a yi ma ta a yi ma ki?"
"Amma Mama ban taɓa jin in da aka yi haka ba."
Ganin za ta ba ta ma su lokacin kuma tana son su koma gida akan lokaci ya sa ka ta ce.
"Nadra ki shiga don Allah ana jiran mu."
"To Goggo Dinner da za'a yi ai sai bayan an ɗaura aure ne, karfe biyar aka..."
Ganin yadda Goggon nata ta tsuki fuska ya saka ta ja bakinta ta yi shiru, kasancewar tana da gudun ɓacin ran mutum.
Shiga ciki ta yi aka ce ta cire kayan jikinta. Aka ba ta wasu ƙananun kaya ta saka aka shigar da ita wani ruwa mai kumafa da ƙamshi.
Matar sai lallaɓa ta take yi tana cewa ban san har da gyaran jikin nan za'a yi ma ki ba da shi muka fara yi kafin muka yi lalle.
Ita dai ba ta ce komai ba sai faɗuwar gaba da take tsintar kanta a ciki.
_Makaho_
Sai da ya gama dibar ruwar yana daukar hannu daya da bokitin ruwa hannu daya da sandar dogarawa har ya gama.
Don sai da Nasara ta wanke banɗakin nan tas da detergent da hypo. Duk da cewar ba tile ba ne a toilet ba ne siminti ne.
Bayan ta gama ne ruwan karshe da ya kawo ta ajiye a banɗakin ta fito.
Duk abinda take yi hawaye bai tsaya daga tsiyayar da take a idanunta ba.
Kiran sallar isha'i ake yi don haka ya ce ma ta .
"Zan je masallaci."
Ba ta ce ma sa komai ba, shi ma bai jira cewar ta ba ya fice.
Tsayawa ta yi tana kallon ɗakin da take haskawa da wayarta, tana tunanin dakin zai dauki lokaci kafin ya bushe.
Kawatin kayanta ta buɗe ta ɗauki wani rigar sanyinta da yake da kauri ta san zai kashe ruwa, ta dauka ta dinga goge ɗakin har ya tsane ba ruwa a kasan simintin dakin.
Ɗankwalinta ta shimfida sannan ta fita ta ɗauro alwala ta fito ta gabatar da sallar isha'i.
Bayan ta idar ta tsaya ta yi addu'o'i tana kai kukanta ga Allah ya ba ta karfin zuciyar cinye wannan jarabawar.
Tana zaune ta ji ya yi sallama.
"Assalamu alaikum."
"Wa'alaiki Salam."
Ya dinga lalube har ya ji ɗakin sannan ya shiga bayan ya cire takalminsa a waje.
Shiru ne ya biyo baya har tsawon mintuna biyar ba wanda ya yi magana a cikinsu.
Maganar zuci da take yi ya fito fili ba tare da ta sani ba.
"Mamy ba zan yafe ma ki ba, kin aurar da ni in da kike ganin zan tagayyara, kin san cewa rayuwata za ta iya inganta ta hanyar amfani da kuɗaɗena. Kin amshe ATM card kin je kin kwashe kudint.
Makaho ya gyara tsayuwar sa tare da jingine sandarsa a jikin bango ya ce.
"Ba lallai sai ta ATM card kawai ba, ta yi multiple withdrawal (cire kuɗin sau da yawa a ATM daban-daban. Ko ta yi transfer ta amfani da USSD (*737# *901# da sai sauran su saboda ta san Pin ta samu damar yin hakan. Ba zai yiwu ta fitar da miliyan goma a ATM lokaci guda ba amma a cikin awa biyu za ta iya gama komai . Don idan har lissafi na ya yi daidai lokacin da kika fahimci ba kudin a cikin asusun ki an yi awa biyu da barin mu gidanku. Ta kwashe kudin ne ta hanyoyi daban-daban (ATM + Transfer kasancewar ta san Pin da bayanan asusun. Saƙonnin bankin sun nuna cewa kuɗin sun fita ne ta hanyoyi daban-daban a cikin awa biyu duk da sahihin Pin?"
Da mamaki take kallonsa kafin ta ce.
"Saƙonnin bankin sun nuna mani cewa ba ciro kudin aka yi ba, an kwashe kudin ne ta USSD da canja wuri (transfer) a cikin awa biyu duka da sahihin Pin."
Mamaki ya kama Ma'eesaha ta ce.
"Ya aka yi ka san irin waɗan nan tsarukan na banki?"
"Ba abin mamaki ba ne, don ni ma wasu na ji suna fira ina kwance a masallaci ina jin su."
"Su waye?"
" Da wani idanun zan gane su? Wata rana bayan an sallame sallah ɗaya yake faɗa wa wani an kwashe ma sa miliyan goma ta hanyar amfani da ATM card na shi to wannan da aka fada wa ya fadi bayanin nan da na maki."
Shiru ta yi dai tana kau da idsnun ta daga kallonsa, ita babban damuwar ta yadda idan Mallam Iro ya zo karɓar kudin haya wani bayani za ta ma sa kan dubu hamsin, bayan ya ma ta taimako a daren nan ba ba su gida. Su zauna.
Ganin ga lokacin na tafiya kuma tauna ya addababe ta ne ga karfe tara da ta yi ne ya saka ta mike tsaye ta ɗauki handbag ɗin ta sauran 2k ɗin da ya rage ta dauka ta rasa me za ta siyo da za su ci a daren.
Ita kanta ta san 2k ya yi kadan ya siya ma ta irin abincin da za ta ci ballantana ga makahon mijinta. Kuma idan ta kashe kudin duka da me za su yi breakfast da safe?
Don haka ta ɗauki ɗauki 1k ta fita da shi sannan ta bar 1k a cikin handbag ɗin ta.
Wajen me shagon dake kusa da gidan ta nufa, yanzu ma yana da jama'a. Don haka sai ta jira daga gefe har aka rage.
"Mallam nawa ne coke na roba?"
"Hajiya ɗari huɗu da hamsin ne."
Shiru ta yi idan ta siye guda biyu kudin ba zai isa ba, don haka sai ta ce.
"Ka bani guda ɗaya nawa kake siyar da bread. Biredin nan akwai na dubi daya da ɗari biyar, akwai na dubu daya da ɗari uku akwai na dubu daya, akwai na ɗari biyar dai kuma karamin nan na ɗari uku."
"Ka bani na ɗari biyar ɗin."
Ta amsa bayan ya saka ma ya a leda ya ba ta canjin Naira hamsin.
Tana tafiya tana hawaye, da a baya ne kafin yau canji ko nawa ne idan ta siye abu ba ta karɓar canji sai dai ta bar wa mai kayan. Amma yau ita ce da karbar canjin Naira hamsin.
Murmushi ta yi tana goge hawayenta ta ce.
"Alhamdulillah ala kulli halin."
Ta shiga gidan, sannan ta mai da ƙofar langa-langan ta rufe tare da saka sakata.
Shiga gidan ta yi kasancewar ta fita da hasken fitilar wayarta, sai ta bar shi cikin duhu shi kadai a ɗakin. Ita a tunaninta tun da ba gani yake yi ba ai ba amfanin bar ma sa haske da za ta yi.
Ta shafa ta same shi tsaye tana mamakin yanda ba ya gajiya da tsayuwa.
Tana kallon ɗakin yanzu ina za su kwanta ne, ba tabarma ba katifa.
Zaninta ta ɗauko guda biyu ta shimfiɗa ɗaya a in da take zaune, sannan ta ciro daya ta shimfiɗa ma sa a inda yake tsaye ta ce.
"Ka zauna a nan."
Kamar bai ji ta kuma ya ji ta ya san me take cewa .
Coke din ta ciro tare da bread ɗin, ta ɗebi Biredin kaɗan sannan ta ɗebi rabin cike ɗin cikin robar ruwa da ta yi alwala da shi.
Ta ajiye wanda ta ɗiba a gabanta sannan ta ajiye sauran da kuma ladar bread ɗin.
Coke dake cikin goran ta ajiye ma sa da robar coke din da ta ɗiba ta bar ma sa sauran.
"Ga bread nan da abun sha na ajiye ma ka."
Shiru bai ce da ita komai ba, sake kallonta ta yi tana maimaita abun da ta faɗa, nan ma shiru bai amsa ba, don haka ta yi shiru tana kallon da da mamaki, har shi zai dinga ji da kansa waye shi?
Murmushin takaici ta yi ta zauna a saman zanen da ta shimfiɗa.
Da kyar take cin bread ɗin don ba ta taɓa cin irinsa ba, daure wa kawai take yi ba wai don dadi ba sai don yunwa.
Haka ta cinye wanda ta ɗeba tare da coke ɗin, sannan ta janyo bottle wataer da ta siya guda biyu ta buɗe daya ta sha, sannan ta rufe ta ajiye .
"Za ki iya kwana a nan ɗakin kuwa?"
Wani kallo ta ma sa kafin ta ce.
"To ya zan yi kana da gidan da ya fi wannan ne da za ka kai ni na kwana?"
"Babu ni ma a masallaci nake kwana."
Ba ta ce komai ba ta daga kai tana kallon rufin ɗakin.
"Na kwanta a nan ne ko kuma na tafi masallaci da na saba kwana a ciki ne na kwanta?"
"Wannan kuma ra'ayin ka ne."
Shiru ya yi kafin ya ce .
"Bai dace na bar ki ki kwana a nan ke kaɗai a cikin wannan gidan."
"To idan ka kwana akwai abun da za ka yi mani ne? Ko za ka iya kare ni ne daga cutarwar wani abun?"
"Saboda ina makaho ba na gani ko?"
Da alama maganar ta soke sa a zuciya, bisa la'akari da yanayin amsar da ya ba ta ransa a ɓaci ko bai fada ba.
Sandarsa ya ɗauka ya fice daga cikin ɗakin ya nufi hanyar fita ba ta ce komai ba.
Tana ji ya fice daga cikin gidan.
Sai anan take ta ji babu dad'i, ga wani tsoro da ta ji ya dirar ma ta lokaci guda. Ko ba komai idan tana jin motsin mutum kusa da ita ai ya fi da ta zauna ita kaɗai.
Tsoron gidan ya kama ta ta mike zumbur ta fita daga cikin gidan ita ma tana cewa.
"Wallahi ba zan iya kwana ni kaɗai ba."
_Sidra_
Suna zaune a katafaren falon gidan, wanda kallo ɗaya za ka yi ma su ka gane wayayyun ƴan mata ne ma su ji da kansu.
Wata daga cikin su ta kalli Sidra ta ce .
"Yanzu ba za ki haƙura da wanann burin naki ki koma gida tun lokaci bai ƙure ma ki ba?"
"Khadijah kenan, ai ba zan koma gida ba har sai burina ya cika."
"Matsalarki kenan ki ce ke ba wanda zai fi ki sai dai ki fi kowa? Idan Allah bai yi za ki samu wanan ɗaukakar ba fa?"
Murmushi Sidra ta yi kafin ta ce
"Khadija duk abinda nake nema zan same shi , ban taɓa neman abu na rasa ba, Hakazalika wanann abun da na saka a gaba zan same shi in sha Allah."
"Eh watakila ki samu wancan abu amma za ki iya rasa Fahad da kika ƙwallafa rai sai shi, kodayake yanzu ba ki son sa tun da kuka gudu a ranar aurenku."
"Fahad nawa ne ni kaɗai ba wata mace da ta isa ta raɓe shi ban ga bayanta ba. Kuma ba wai don ba na son sa ba ne, sanin cewa yana masifar so na kuma na san zai jira ni na dawo ya sa na tafi ba tare da tunanin wata matsala ba, kuma iyaye na na san da zaran na dawo za su yafe mani don farin cikin gani na za su yi. Ke dai kawai Allah ya kai mu gobe mu bar garin nan na samu burina ya cika na samu ɗaukaka na dawo gida cike a alfahari."
Ta yi maganar tana Murmushi.
"Sady baby kin san na kashe wayata, ki ara mun taki wayar na kalli hoton masoyina Fahad."
Mika ma ta wayar ta yi tana karba ta kunna Data ta shiga Instagram, shafin Fahad ta shiga in da ta dinga kallon kyawawan photonsa a shafinsa nasa na Instagram.
Hoton da ya dora ta zuba wa idanu taba kallonsa. Sanye yake cikin tsadadden Suit baƙi a jikinsa, ya daura kafa ɗaya kan ɗaya, bakin hannunsa ɗaure tsadadden agogo.
Ya yi kyau sosai, ba ta san lokacin da ta sumbaci wayar ba
tana furta furta kalmar
"I love you Fahad."
Kafin ta rufe datar ta miƙa wa Sady wayarta.
"Dole ki haukace akan son Fahad domin ya hadu iya haɗuwa ga kyau ga kuɗi ga gayu ai kowace mace za ta so shi."
Wata ce ta faɗa a cikinsu
Nam dai suka cigaba da firar su akan Fahad, ita kuma tana jin dadi yadda ake cewa saurayin ta ya haɗu.
_Fahad_
Bayan ya yi parking motarsa ya fito daga cikin motar fuskarsa ta yi jajir.
Gabɗaya jama'ar dake falon kasancewar duka dangi ne bare ba su fara shigowa ba.
Muryar mahaifiyarsa ya ji tana cewa.
"Fahad."
Sai da ya ɗan tsaya kafin ya juyo duk suka kalle shi.
Cikin tashin hankali Mama ta mike tsaye ta karasa inda yake tsaye ta dafa kafaɗunsa da hannayen ta biyu ta ce.
"Daga gidan surukan naka kake?"
Kai kawai ya jinjina ba tare da ya yi magana ba.
"Me yake faruwa to?"
"Sidra ta gudu yau ba wanda ya san in da ta je."
"What! Ta gudu?"
Gabadaya falon shiru ya ɗauka yayin Mama ke salati.
Kalarsa ce ta ce
"Dama ba ta son sa ne?"
Ma ta ba ta amsa da cewa.
"Wallahi tana masifar son sa, maybe ma son da take yi ma sa ya fi nasa yawa. Ban san dalilin haka ba.
Ɓoyayyar ajiyar zuciya Farida ta sauke tana mai farin cikin jin amarya ta gudu. Ko ba komai yanzu dole ya aure ta.
Mahaifiyar Faridan ce ta ce.
"Ga irin ta nan ya je ya nemi aure gidan ƙananun mutane, ga dangi ana ta yi ma sa tallar ƴan uwansa ya nemi daya ya ce baya so. Ga Farida nan sabida son da take ma sa ta bar kowa nata ta zo ta tare a gidan nan sabida shi amma yake wulaƙanta ta.
"Kalarsa ta ce ai kuwa dole ya aure ta."
Daidai lokacin Baba ya fito daga part ɗin sa yana tambayar me ke faruwa.
Mama ta ma sa bayani shi ma salati ya yi yana cewa.
"Allah ya sa hakan shi ne mafi alkhairi."
Sai a je a kwaso kayan lefen da aka kai ma su ya ke ya siye uban kaya kamar wanda zai bude shago ko bai san zafin kudi ba.
"Aunty kar ku je Please."
Ya fada yana kallon ƙanwar mahaifiyarsa.
"Saboda me?"
"Sun bani hakuri sun ce na amince a maye mani gurbin ta da ƙanwarta Nadra."
Wani kuka Farida ta saka wanda kowa sai da ya kalle ta, ta haura sama tana kuka.
Baba ya ce.
"Kai kana son ƙanwarta ɗin ne?"
"Wallahi ni ma ban sani ba."
Ƙanwarsa ta yi caraf ta ce.
"Wallahi in dai Nadra ce ba ta da matsala, wallahi wacce kake so ita ce mai matsalar. Sai girman kai da izza ni dama wallahi ba da ɗin raina za ka yi auren..."
Mugun kallon da ya yi mata ya saka ta ja baki ta yi shiru, ita kanta Mama ta ji dadin hakan, don ta san su sau uku suna zuwa gidan kuma ta fi yabawa da hankali da nutsuwar Sidra."
"Yanzu aka amsa masu cewa za ka auri ƙanwarta?"
Jinjina kai ya yi ba tare da ya yi magana ba, Baba ya ce
"Allah ya sa hakan ya fi zama alkhairi, a cigaba da shirye-shiryen da ake yi.
Daidai lokacin da kiranta shigo wayar Fahad, ganin abokinsa ne ya saka ya fita zuwa harabar gidan, motoci guda biyu ne suka shigo.
Matasan samari ne ma su ji da kansu kimanin su takwas suka zo gidan.
Jagora ya yi ma su zuwa part ɗin sa, ta kofar baya ba tare da sun shiga part falon ba aika shiga part ɗin nasa.
Suna shiga ciki suka Zazzauna a falon yayin da shi ya shiga cikin bedroom ɗin sa.
Ganin yanayinsa ya sa suka san cewa a kai matsala, ba wanda ya yi magana har ya fito fuska ba walwala yake yi ma su barka da zuwa.
Musamman waɗanda ba a kasar nan suke ba daga wata ƙasar suka zo halartar bikin aurensa.
"Man lafiya kuwa?"
A jiyar zuciya ya sauke don ya san ba ɓoye ma su komai zai yi ba.
"Sidra ta gudu yau da safe."
Mamaki da kasuwa suka shiga, suna tambayar sa dalili.
Nan ya ba su labarin komai da ya faru har ƙanwarta da iyayen suka ba shi a madadin ta.
Nan aka shiga jajanta lamarin tare da kara ma sa ƙarfin guiwa akan auren Nadra, sannan suka bashi shawara ya cire damuwa ko saboda jama'a da za su zo daurin auren kada a fahimci wata matsala.
Haka suka dinga ba shi kwarin gwiwa har ya ɗan saki ransa suka fara shirye-shiryen zuwa ɗaurin aure.
_Nadra_
Lokacin da aka fito da ita daga ɗakin da aka shiga da ita sai da Gwaggo Laraba ta saki. baki tana kallonta.
Ba karamin kyau ta yi ba baƙar fatarta ta kara sheƙi da ɗaukar idanu.
Kudin aikinsu Goggo Laraba ta bayar suka wuce don har lokacin dire ba na jiran su.
Suna bayan motar Nadra ta sake gwada kiran wayar Sidra.
Har lokacin wayar a kashe.
"Gwaggo har yanzu fa wayar Aunty Sidra ba ta shiga, wani irin wurin gyaran jiki ta tafi da za ta kashe waya?"
Gwaggo Laraba dai ba ta ce ma ta komai ba, sai ta sake cewa.
"Maybe ma tana gida ta dawo ko?"
"Ba na tunanin ta dawo don wajan da nisa kuma ana dadewa kafin a gama. Yanzu mutane sun taru ba mu son a san cewa Amarya ba ta nan, don haka ke ce za ki saka kayanta a matsayin kece Amarya kafin ta dawo, kin ga ba kowa ke banbance sunan ku ba ko?"
Cikin rashin fahimta ta ce .
"Ni na kasa gane wannan al'amari ta ya zan shirya a matsayin ta bayan ba ni ba ce Amarya."
"Eh saboda mutane za'a iya ayi ta tambayar amarya ba dadi a ce ba ta nan, kuma Ummanki da Abba su ne suka ce a yi haka ko ba za ki bi maganar su ba ne?"
"Shi ke nan zan yi Allah ya dawo da ita lafiya."
"Amin yarinyar kirki ."
Daga haka suka ƙarasa gidan dake cike da jama'a, don rana ta yi gidan ya fara cika.
Ta part ɗin Umma suka bi suka shiga bedroom ɗin ta.
Duk da ta yi kwalliya amma akwai damuwa a tattare da ita.
Nadra ta rike hanjun Umma ta ce
"Umma ba ki da lafiya ko?"
Shafar gefen fuskar Nadra ta yi tana Murmushi ta ce
"Lafiya ta lau ki yi sauri ga mau kwalliya can tana jiran ki tun ɗazu ta zo."
Za ta sake wata magana Umma ta rufe ma ta baki ta ce.
"Sarkin magana je ki kar ki ɓata ma su lokaci."
Haka ta fita cikin sanyin jiki Umma ta bi ta da kallo tana goge ƙwalla.
_Makaho_
Yana zaune a barandar masallacin ya jingina da bangon masallacin ya daga kai sama.
Kamar daga sama ya ji ƙamshin turarenta, lalubar sandarsa ya yi ya na cewa.
"Ma'eesha ke ce?"
"Eh ka taso mu tafi gida."
Tausayinta ta kama shi amma duk da haka bai hana shi cewa ba.
"To ni da nake Makaho ba na gani wani amfani zan yi ma ki, tun da ba zan iya kare ki daga cutarwar wani abun ba."
Shiru ta yi don ita ma ta san dole ya ji ba dad'i. Tashi ya yi ya na rike da sandarsa ya yi gaba ba tare da ya ce komai ba, ita ma tana bisa a baya har suka shiga gidan ta mayar da kofar ta saka sakata ta rufe.
*Mamman Ihsan ce*✍️
09065357995
Follow the TASKAR MAMAN IHSAN channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaiufWb3LdQYnzC2vH0z
*MAKAHO NE*
*NA*
Maman Ihsan ce ✍️
https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
page0️⃣5️⃣
Shiru ta yi don ita ma ta sa dole ya ji ba daɗi .Tashi ya yi yana rike da sandarsa ya yi gaba ba tare da ya ce komai ba, ita ma tana bin shi a baya har suka shiga gidan ta mayar da ƙofar ta saka sakata.
Da lalube ya shiga cikin ɗakin, in da yake tsaye ɗazu can ya je ya kara tsaya wa.
Ta shiga tana rike da ƙaramar wayarta ta kunna torchlight.
Wanka take so ta yi sai dai ba ta iya wanka da ruwan sanyi, ga shi ba ruwan zafi.
Kayan jikinta ta cire ba ta damu da yana wajen ba saboda ta san makaho ne, towel ta daura ta nufi ƙofar fita.
"Ina kuma za ki ke dare ne yanzu fa."
Ba ta iya amsa ma sa ba sakamakon kukan da take yi na rayuwar da ta tsinci kanta a ciki. Sai dai kuka mara sauti take yi, idan ba wanda ya kalli idanunta ba to ba zai je tana kuka ba.
Banɗakin ta nufa kasancewar akwai ruwa da makaho ya cika bokitin na karshe ta ajiye.
Sai da ta rintse idanunta tana sakin ajiyar zuciya sannan ta iya yin wankan.
Tana fitowa ta same shi tsaya a kusa da ƙofar banɗakin, ba ta yi ma sa magana ba shi ma bai yi ma ta magama ya fito rike da bokitin ya nufi bakin Rijiya zai ɗebo ruwa.
Man shafar ta ta dauka bayan ta goge jikinta sannan ya shafa mai. Bayan ya shafa mai ta fesa turare na jiki wato body spray. Kayan barci ta saka riga da wando da wata hula mara nauyi ta saka.
Tana kallon ɗakin ta rasa ta ina za ta kwanta, ga ba gado ba katifa ballantana tabarma.
Tana tsaka da wannan tunanin sai ya shigo cikin ɗakin da sallama a bakinsa.
Ta amsa ma sa ba tare da ta lalle shi ba.
Yana shigowa daidai yana kawowa wajen shimfidar ta ta yi ma sa ta ce.
"Ga zanin da na shimfida ma ka nan ka zauna akai ."
Ba musu kuwa ya zauna ya tanƙware ƙafarsa, shiru dakin ya ɗauka ba wanda ya yi magana.
Bayan ta gama tunani sai ta koma ta rufe kofar dakin ta saka sakata.
Daidai lokacin nepa suka kawo wuta haske ya gauraye ɗakin gabaɗaya.
Kallon bread da coke ɗin da ta ajiye ma sa ta yi ta ga bai taɓa ba.
Taɓe baki ta yi sannan ta dauki karamin akwatin ta yi pilow da shi bayan ta kwanta.
Sai ta ji ya yi ma ta girma da yawa wuyanta zai iya ciwo.
Cire shi ta yi sannan ta yi pilow da hannunta ta kwanta.
Lokacin karfe goma sha daya na dare ne. Wayarta ta soma ruri ta ga lambar ba ta ƙasar nan ba ne, kuma ta san waye, katse kiran wayar ta yi tare da gyara kwanciyarta da sam ba ta ji fadinsa ba."
Sake kira aka yi har ya katse ba ta ɗaga ba, a karo na uku ne ta ambaci sunansa.
"Oh Allah Abdul ban san me zan ce ma ka ba."
Ta yi maganar tana goge ƙwallar tausayin kanta da take ji, take wani sabon kuka ya zo ma ta sai ta toshe bakinta tana yin sa a hankali.
Messages ne ya shigo wayarta ta duba still shi ne.
*Ina fatan jina cikin aminci farin cikina, na ga kina katse ma ni kira fatan ba wani laifin na aikata ba, Please ki amsa wayata ko hankalina zai kwanta.*
Tana gama karantawa ta katse kiran wayar, gabaɗaya ta kashe wayar ta koma ta kwanta tana hawaye.
Kamar sauro na jiran ta kwanta suka fara kai ma ta hari.
Abinda bai taɓa faruwa da ita ba kenan, sauro su addababe ta haka.
Ga cizon sauro ga kuma kukan sauro da suke yi ma ta a kunne.
Tashi zaune ta yi ta saka kuka tana kara sakin kuka kamar karamar yarinya.
"Ma'eesha lafiya."
"Wallahi sauro suke damuna ba zan iya barci a haka ba."
"Ayyah sorry, ba ni ɗankwalin kayan ki."
Ba musu ta zuge zip ta ɗako ta mika ma sa, ya matso kusa da ita ya karɓa.
"Ki manta to."
Kwanciya ta yi kamar yadda ya ce, ya dinga kore ma ta sauro da ɗankwalin. Tana jin kamar yana ma ta fifita har ɓaci ya ɗan fara daukarta kuma ya hadu ma ta da gajiya.
Haka makaho ya dinga yi wa Ma'eesha fifita har ta yi barci .
Tun karfe sha daya har biyu na dare yana zaune yake kore ma ta sauro.
A lokacin ta farka ta ga yadda ta bar shi haka yake yi ma ta fifita. Awa uku kenan yana abu ɗaya.
Tausayinsa ya kama shi cikin tashin murya ta ce .
"Ka kwanta ka yi barci na gode."
"Ba za ki iya barci ba idan na daina ku yi barci kawai, dama ni ban saba yin barcin dare ba."
Barcin ta cigaba da yi har aka yi kira sallar asuba.
Sai a lokacin ya ajiye ɗankwalin ya mike tsaye daidai tana buɗe idanunta.
"Da ido ta bishi ya fice daga dakin bayan ta dauki Sandarsa."
Bayan kamar mintuna goma ya shiga da alama alwala ya yi, sai ya ce .
"Zan tafi masallaci sai an yi sallah zan shigo."
Kai kawai ta jingina kamar yana ganin ta, ita ma tashi ta yi ta nufi banɗaki don ɗauro alwala.
_Nadra_
Tana shiga cikin ɗakin ta samu mai kwalliya na jiranta. Da sallama dauke a bakinta ta shiga in da ta samu ɗaiyar Gwaggo Laraba tare da mai kwalliya.
Duk da kasancewar ita ba mai son kwalliya ba ce kamar Sidra. Amma yanzu kam ba ta isa ta ce ba ta son kwalliya ba.
Hijabinta ta cire wani ni'imtacen ƙamshi na tashi daga jikinta.
"Bari na yi sallah lokacin sallah ta yi ."
Ba ta jira cewar kowa ba ta nufi bathroom don sauro alwala
Sai da ta gabatar da sallar sannan ta dawo kan su.
Zama ta yi dadai lokacin da wayarta ke ringing, ta duba ta ga Ya Sayyadinta ne ke kiran wayarta.
Murmushi ta yi za ta ɗaga sai Gwaggo Laraba ta karbi wayar ta kashe ta gabaɗaya ta ce.
"Ki tsaya a gama da sauri ba lokaci, kina gani gidan ya fara cika da jama'a ko?"
Mai kwalliyar ta buɗe akwatin kayan kwalliyar ta dubi Nadra ta ga ba ita ba ce ta kira ta, hasalima wacce ta kira ta fara ce ita kuma wanann baƙa ce. Kallon Gwaggo Laraba ta yi ta ce .
"Ko dai ba gidan ba ne?"
"Nan ne kar ki damu wannan ce za'ayi wa wacce ta kira ki Sidra ce ita ce ƴar wannan."
"Okay."
Ta faɗa a takaice ta fara yin aikin da ta kawo ta yi.
Nan ta tsantsara wa Sidra kwalliya wanda ya yiasifar yi ma ta kyau kamar ba ita ba.
Sannan aka ɗauko ma ta kayan Sidra wanda dama shi za ta saka a lokacin. Sai dai an ɗan sake ba tela ya sake buɗa ma ta faɗin kayan kasancewar Nadra ta fi Sidra diri da cikar halitta.
Karba ta yi ta shiru tare da taimakon mai kwalliyar ta shirya ta, ta yi ma ta ɗaurin Ɗankwali.
Nan ƴan uwa suka dinga ɗaukarta photo, ita dai har lokacin ba ta saki jiki ta ba, ta rasa dalilin dai zai saka a ce saboda Sidra ba ta nan ta maye gurbin ta. Ga shi an ce ba yanzu za ta dawo ba, ita dai addu'ar ta Allah yasa kafin karfe huɗu ta dawo, don idan ba ta dawo ba to ita kam ba za ta iya maye gurbin ta a wajen Dinner party ba. Ta ya ya za ta fito ta tsaya tare da Fahad kai ba zai yiwu ba ma.
Ita kadai take saƙa da warwara har ta ji ana cewa karfe biyu ya yi yanzu za'a daura aure. Tsintar kanta ta yi cikin faɗuwar gaba da tsoro.
_Fahad_
Kwance yake a bayan motar ya jingine bayansa da jikin motar, sanyi A.C da ƙamshin turarensa ke tashi a cikin motar.
Mukhatar da Aluyi sun saka shi a tsakiya, Kabir na zaune a gefen direba wajen me zaman banza
Suna ba shi baki tare da kwantar ma sa da hankali, don sun san yana cikin damuwa.
Har aka karasa kofar gidan surukan nasa bai buɗe idanunsa ba. Kowa ya fito ya bar sa a cikin motar.
"Ko sai mun fito da kai ne?"
Cewar Mukhtar yana kallonsa yana Murmushi.
"Hana Majidaɗi ka saki ranka ma na sai ka ce wanda aka yi wa auren dole?"
Harararaa Fahad ya yi tare da cewa .
"To idan ba auren dole aka yi ma ni ba na soyayya ne?"
Ya faɗa yana ziro fararen ƙafarsa wanda ke cikin takal ki ƙirar kamfanin Prada, takalmar baƙi ne.
Yana sanye da farar shadda gezna wanda aka yi ma sa aiki da baƙin zare riga da wando har da babbar riga. Ya fito yana gyara zaman babban rigarsa. Kansa sanye da bakin hula, hannunsa ɗaure da tsadadden agogonsa na Rolex Day-Date 40 (president watch) wanda ya zauna a hannunsa kamar don shi aka yi .
Duk wanda ya kalle shi zai gane shi ne angon domin ya sha banban da kowa a wajen.
Zuwan su ba jimawa aka fara shirye-shiryen ɗaurin auren.
Ɗaurin aure ne da ya tara manyan mutane na gida da waje. Manyan kusoshin gwamnati da da saraki da ma su mulki, har da shahararrun ƴan kasuwa .
Mutane suna ta yi wa Fahad fatan alkhairi ana taya shi murna, sai dai ya yi kokarin ganin damuwar da yake ciki bai shafi walwalarsa ba.
Yana nan zaune ba abinda yake yi sai tunanin Sidra sam ya kasa dalilin da ya sa ta aikata ma sa haka, duk ikirarin da take yi na tana son sa har za ta iya yin haka?
Bai ankare sa an ɗaura ma sa auren ba sai da ya ji an dafa sa ana taya shi murna.
Bayan an gama an tashi ana ta ma sa fatan alkhairi ana ɗaukar hotuna.
Daga nan Baba ya ce wa Fahad su shiga shi da abokansa su su gaida surukansa
Haka kuwa aka yi da shi da Mukhtar, Khabir da Aliyu suka shiga cikin gidan.
Falon Abba wanda shigowar su kenan shi da ƴan uwansa da abokansa.
Suka durƙusa suka gaishe su tare da yi ma su godiya da ba su ƴa da aka yi .
Daga nan kuma suka nufi main falon gidan, suka ga jama'a mafi yawansu ƴan uwa ne.
Tun da suka shiga gidan kansa a ƙasa yake har suka durƙusa suka gai da dangin Amaryar.
Kasancewar ba kowa ya san angon ba, kuma duk wani abin rabo da za'a raba wanda yake da photon Sidra da Fahad ba'a raba ba don kada jama'a su gan shi tare da Sidra a photo a fahimci wani abu.
"Ina angon yake?"
Wata Dattijuwa ta tambaya, Haidar ya nuna ma sa Fahad da ya sunkuyar da kai tun da suka shigo.
"Ma sha Allah kyakkyawan saurayi kuwa ta samu, Allah ya ba ku zaman lafiya mai ɗore wa da zuri'a ma su albarka. Yadda muka zo taron biki Allah ya sa nan da watanni tara mu zo taron suna."
Amin aka amsa ana sake rangaɗa guɗa wanda Fahad yake jin samuwar har cikin kansa.
Nan suka yi ma sa nasiha sosai sannan ya mike su ma abokan nasa suka mike, in da suka nufi part ɗin Umma.
Har lokacin tana cikin bedroom ɗin ta ita da wasu ƙawayenta.
Gwaggo Laraba dake falon ita da jama'a ce ta shigo don kiran Umma ta zo ga ango ba abokansa
Gabadaya suka fito ita da ƙawayenta, angwayen suka gaishe su suka sa ita dai Ummar karfin hali take yi, hade ɗaya damuwar halin da Nadra z ga shiga ciki take yi. Sanin irin son da Sidra ke yi wa Fahad, da yadda Fahad ke son ta. Ita Nadra da ba ce yana son ta ba ya za ta yi musamman da ta san halin Halin Nadra da dabi'arta ya sha banban da na Fahad.
Har suka gama gaisuwar suka tafi ta kasa magana tausayin Nadra kawai take yi .
Sallama suka yi ma su suka tafi .
A hanya ma kasa magana da juna su Fahad ya yi, domin su kadai suke ta firar su.
Suna isa gidan tun a harabar gidan ana ganinsa aka fara rangaɗa guɗa.
Abokan wasan sa na tsokanarsa bai bi ta kansu ba ya yi wucewarsa part ɗin sa.
Bai tsaya falo ba ya shiga bedroom ya mirza key ya rufe ya cire takalminsa da hularsa, sannan ya cire babban rigarsa ya cire rigar ciki.
Ya saura sai farin singileti a jikinsa. Agogon hannunsa ya kwance ya kwanta a saman tangamemen gadonsa.
.
Yana jin ana knocking amma ya share bai bude ba har suka gaji suka bar shi.
Abinci da aka ajiye masu da abun sha kowa ya fara ɗibar abinda ke ransa yana ci.
Suna nan sai ga wasu abokan na Fahad sun shigo cikin falon.
_Nadra_
Ta sha kyau iya kyau kamar ba ita ba, baƙar fatarta mai matukar kyau da ƙyalki sai shinning take yi.
Ga kayan ɗinkin riga da siket na less ta saka a jikinta, cikin kayan da Fahad ya siye wa Sidra ne wanda kudinsa zai kai kimanin dubu ɗari biyu. Sai arkar gold da ta saka kunne da wuya, har da warwaro da zobe.
Kasancewar ta ba mai son nuna jiki ba kuma less ɗin sun kama ma ta jiki ya saka ta saka babban gyale, duk da Hijabi ta so sakawa sai da Gwaggo Maimuna Yar Abba ta hana ta.
Shi ne fa ta saka babban Hijabin kasancewar ba kowa ya san cewa Sidra ba ta nan ba ya saka wasu da suka san ba Nadra ke aure ba ya saka suka tambayar ina Sidra take, ita kam sai sai ta ce ma su tana nan dawowa ta fita ne, wasu kuma sai ta sanar da su cewa ta tafi gyaran jiki ne.
Mamaki wasu ke yi ace yau ɗairin auren amma a ce ta je gyaran jiki, me ya saka ba ta yi da wuri ba
Ƙawar Nadra ɗaya ce wato A'isha Humaira, ta zo tana sanye da hijabi da niƙab a fuskarta.
Tana zaune kusa da Nadra suna firar yadda Sidra ya tafi wani wajen ta dade ba ta dawo ba.
Har lokacin sallah la'asar ta yi suka tashi Nadra ta shiga ta ɗauro alwala, sannan A'isha ta shiga.
Suna zaune suna azkar din yamma sai ga ƴar Gwaggo Laraba, wacce ba za ta wuce sa'ar Nadra ba ta shigo ta ce.
"Dama Mama ce ta ce na duba ko kin yi sallah mai kwalliya za ta zo ta yi ma ki kwalliyar zuwa Dinner party kafin ango ya ƙaraso tare za ku tafi da shi."
Zumbur ta mike tsaye tare da cewa.
"What?"
Wani kallo ta yi wa Salma kafin ta ce .
"Waye zai je Dinner party? Allah ya kiyaye, ni duk ire-iren waɗan nan wurare ban taɓa zuwa ba, duk wani taro in dai ba walima ba ce to ba zan tafi ba ballantana q ce na je a madadin Aunty Sidra, a jira idan ta dawo su je ta yi amma ba zan iya ba, I try my best but ba zan iya zuwa Dinner party ba."
Ta fada kamar za ta yi kuka.
Salma ta fit don ta sanar wa Mahaifiyar ta abinda ya faru.
_Fahad_
Har karfe uku da rabi bai fito ba, da ya ga lokacin sallah ta yi na ya shiga bathroom ya ɗauro alwala ya fito
Nan suka cigaba da firarsu .Ganin karfe uku da da rabi ta yi ne ya saka suka je suna knocking.
Daidai lokacin shi ma zai fito don zuwa masallaci.
Shi ma sai a lokacin ya lura da abokinsa Sadik daje ƙasar Canada ya iso.
Rungume juna suka yi sanan suka fita tare don duk sun yi alwala a bathroom dake falon.
Gabɗaya suka je masallaci, suka bi jam'i aka yi sallah.
Bayan an idar a tare suka fito suka koma ciki.
Daidai lokacin ne Yar Fahad Aunty Rahama ta shigo.
Dukkanin su suka gaishe da ita don duk sun san ta don Fahad na zuwa da su gidanta .
"Se Aunty Babba."
Cewar Sadik yana dariya .
Kallon su ta yi tana cewa.
"Lokacin Dinner party ya kusa ku je ku saka shi ya shirya bana son Afrikan time."
"Wai ya ce b zai je Dinner party din nan ba an fasa yi ."
"Akan me wanna ai zandan banza ne, dole a yi shi kamar yadda ka tsara tun farko, idan zai cire wa kansa damuwa ya rungumi ƙaddararsa."
Tana fadar haka ta shiga bedroom, yana zaune a bakin gado ya yi shiru cikin tunani
Dafa kafaɗarsa t yi ya ɗago kai ya kalle ta.
"Tashi ka shirya ku je ka ɗauki Amaryarka ku je wajen Dinner party."
Kwaɓe fuska ya yi kamar zai yi kuka, kafin ya buɗe baki zai yi magana ta ce.
"Ba na son jin komai, kuma na fahimci matsalarka, ka yi abinda na ce maka kawai."
Dole ya tashi ba tare da ransa ya so ba ya nufi bathroom, sai da ta ji saukar ruwa alamar ya fara wanka sannan ta fice.
Don dama su matan sun shirya zuwa reception ɗin .
_Ma'eesha_
Tana zaune a ɗakin tun da ta idar da Sallah ta yi azkar ba ta tashi ba, tana tunanin hanyar da za ta samu dubu hamsin ta biya kudin hayar gidan nan.
Ga shi ta yi ma sa alkawarin yau za ta bashi kudin.
Sallamar makaho ta ji ya shigo, ta amsa ba tare da ta kalle shi ba.
Shigowa ya yi ya zauna kafin ya ce .
"Ina kwana?"
Sai a lokacin ita ma ta ce ma sa .
"Ina kwana?"
"Kin tashi lafiya?"
"Alhamdulillah."
"Ya zaman hakuri da rashin barci."
"Ai Ni na yi barci kai ne dai ka kwana a zaune kana ma ni fifita ."
"Ke ma ba barcin kika yi ba, na ji kina ta motsawa."
Tunani take yi 1k ya rage ma ta idan ta siyo abin da za su ci shi kenan ba ta da komai.
Wani tunani ta yi kafin ta ce.
"Zan fita na je na siyar da wayata ko zan samu na biya kudin hayar gidan nan, kuma sauran canjin mu samu na cin abinci da dan abun buƙata da ya dace.
Shiru ya yi kafin ya ce .
"Idan kika siyar haka za ki zauna ba waya?"
"Ai wayoyina biyu ne da ni, zan siyar da babbar na rike ƙaramar ina amfani da shi. Na san kudin zai yi yawa . Don wayar miliyan daya da dubu ɗari biyar aka siya mun, ko miliyan ɗaya idan na siyar zan samu abubuwa da yawa da zan siya ma su sauƙin kuɗi, kamar karamar katifa labule kayan aiki da kuma kayan abinci."
Shiru ya yi kafin ya ce .
"Allah ya tsare ya dawo dake lafiya ya sa ki samu abin da kike nema."
"Amin ya Allah, bari na je kafin mai karɓar kudin hayar ya zo ya yi Mani sallama."
Tana fadar haka ta tashi dama rigar Abaya ne a mijinta baƙa. Rolling kanta ta yi da mayafin abayar sannan ta dauki handbag ɗin ta da wayoyin ke ciki ta fice.
*Maman Ihsan ce.*
090 5327995
Follow the TASKAR MAMAN IHSAN channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaiufWb3LdQYnzC2vH0z
*MAKAHO NE*
*NA*
Maman Ihsan ce ✍️
https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
page0️⃣6️⃣
Tana fadar haka ta tashi dama rigar Abaya ne a jikinta baƙa. Rolling kanta ta yi da mayafin abayar sannan ta dauki handbag ɗin ta da wayoyin ta ke ciki ta fice ba tare da ta san in da ta dosa ba.
_Aunty Rahama_
Tana fita daga part ɗin Fahad ta nufi part ɗin Mama.
Tun kafin ta karasa jikin kofar bedroom ɗin take ta jin muryar kanwar mahaifiyar su wato Hajiya Jummai mahaifiyar Farida.
"Ai shi kenan ku shirya ku tafi wajen Dinner ni dai ba in da zan je a yanzu haka. Don Yaya na gama gane cewa ba ki ƙaunata ba ki ƙaunar ƴata. Saboda Fahad Farida ta bar garin ta ta bar iyayen ta da kowa na ta ta dawo nan gidan da zama, ba don komai ba sai don ta samu kusanci da Fahad. Amma yaron nan ya yi kamar bai gane tana son sa ba. Da ta gaji da bayyana ma sa irin son da take ma sa ya wulakanta ta, kuma kina cikin gidan nan kun san me ke faruwa. Yanzu yarinyar da ya ƙwallafa rai a kanta an ce ta gudu ta bar gidan iyayen ta. Madadin ya zo a bashi ƙanwarsa ya aura shi ne ya je aka ba shi kanwar yarinyar ya aura ko? Sanadin Haka ga Farida can kwance na kasa gane kanta, ba sunan da take kira sai na Yaya Fahad."
Murmushi Mama ta yi tare da cewa .
"In ban da abin ki Jummai ai ni abun farin ciki ne a wajena a ce ga ɗana zai auri ƴar ƙanwata. Amma ya ce baya son ta to ya za mu yi? Ba dole a bar shi ya auri wacce take so."
Hajiya Jummai za ta sake wata magana ta ga Mama ya tsuke ma ta fuska tana dauke kai alamar ba ta son zancen, ga hankulan mutane ya dawo kansu.
Mama fita ta yi daga cikin dakin tana tarbar baƙin da ke zuwa a lokacin.
Kasancewar Yamma ta yi lokacin da za'a je Dinner party ya yi mutane suka fara shirye-shiryen zuwa Dinner party. Ankon fari da baƙi suka yi . White an black.
Mata suka sanya ankon nasu material fari da baƙi ne sun yi kyau sosai.
Bangaren Fahad ma zuwa lokacin samari ne cike da falon nasa, su na sun yi ankon yadi na fari mai ratsin baƙi a jiki.
Gabɗaya kalar yadin suka sanya ba abinda ke tashi daga cikin falon sai waƙar bikin Fahad da aka yi da sunan Sidra.
_Aunty Rahama_
Ita ma ta shirya cikin ankon nata ɗinkin doguwar riga, tana rike da hannun ƙaramar ƴar ta mai suna Zahrah yar shekaru uku a duniya.
*NA*
Maman Ihsan ce ✍️
*Alhamdulillah na gode Allah da ya bani ikon rubuta wannan labarin da na daɗe ina son rubuta shi. Allah ya bani ikon rubuta abun da zai amfani al'umma.*
*Ni ce ta ku dai marubuciyar nan da na saba faɗakar da ku da misaɗantar da ku, to yanzu ma na zo ma ku da sabon labari mai cike da sarƙakiya tuggu da makirci, wanda zai bar ku cikin shauƙi da zumuɗi. Ku dai ku biyo ni kun san dai ba taɓa ba ku kunya ba, wannan na daban ne mu je zuwa*
Ɗanɗano
Page0️⃣1️⃣
Tafiya yake yi cikin takunsa na natsuwa da kamala, Sandar dake da hannunsa yana dogarawa ne zai tabbatar ma ka da cewa makaho ne shi, kuma sandar ce jagoransa. Sai baƙin glass dake sanye a idanunsa wanda ya zauna a karan dogon hancinsa da ya dace da kyakkyawar fuskarsa. Fari ne dogo mai matsakaicin jiki, sai dai kallo ɗaya za ka yi wa kyakkyawar fuskarsa ka fahimci cewa shi ba mai yawan fara'a ba ne da sakin fuska. Yana da ƙirar jiki da cikar zati irin na cikakken ɗa namiji. Sanye yake da wani royal blue yadi mai sauƙin kuɗi wanda ake kira da yi shirunka maraya, daga ganin kayan jikinsa za ka san sun sha jiki sai dai da dukkan alamu saurayin mai tsafta ne don kayan fes suke babu datti duk da kasancewarsa makaho ne.
Tafiya yake yi a cikin layin unguwar da ta kasance unguwa ce ta ma su hannu da shuni, tun daga ganin shimfiɗaɗiyar kwaltar da ta shiga cikin unguwar ta ko ina har zuwa ƙerarrun gidajen dake cikin unguwar. Unguwar ta kasance shiru ne ba hayaniya.
Har ya iso daidai katafaren wani gida ya tsaya, shiru ya yi na tsawon mintuna biyu kafin ya yi knocking ɗin danƙareren gate ɗin dake gidan.
Daga ciki ya ji muryar Musa mai gadi yana cewa.
"Waye nan?"
Don tun da ya ji ba'ayi horn ba ya san ko ma waye ba da mota ya zo ba talaka ne.
Ƙarasawa ya yi don dama daga toilet ya fito yana surutu shi kaɗai.
"Ko ma waye dole za ku haƙura ku koma, don ita matar kirkir dake da tausayin talakawa kuke zuwa rana ba ku yanzu Allah ya karɓi rayuwarta ba ta raye, wacce ta rage a gidan ko mutuwa za ku yi ba za ta lalle ku da gashi ba ballantana ta taimaka ma ku."
Yana buɗe ƙofar ya ga wanda ke tsaye ya ce ya ce.
"Mallam makaho ne?"
Shiru ya ma sa bai yanka ma sa ba, sai ya sake cewa.
"To daga yau sai dai ka daina zuwa don wacce kake zuwa domin ta take ba ka Allah ya larɓi rayuwarta, tsawon kwanaki hamsin kenan yau, kuma na san ka zo ta'aziyya , kuma ka zo bayan wata ɗaya da rasuwar . Ina mai ba ka shawara ka bar nan kafin waccen marar mutuncin ta fito ta ganka uwar ɗakinka ta rasu ka sani ko?"
Gundura ya fara yi da maganar ta Mallam Musa sakamakon ba ya son magana ko hayaniya , ga shi Mallam Musa bai iya magana a hankali ba, cike da mishkilanci ya yamutse fuskarsa yana ƙokarin shiga cikin gidan.
Da kallo Mallam Musa ya bishi yana cewa.
"Sai shegen girman kai da mishkilanci, ga shi nakasashshe yanzu an koro ka ka fito."
Mamy ce ta fito tana kallon Makaho tana washe baki tana cewa.
"Ango ya iso daukar Amaryarsa kenan Alhamdulillah."
Bai ce komai ba sai sake tsuke fuska da ya yi, yayin da Mallam Musa ya cika da mamaki to waye angon ba dai makahon nan ba.
Tsuke bakinsa ya yi ya koma bakin aikinsa yayin da Mamy ke yi wa Makaho iso tana cewa.
"Shigo sirikina."
"Alhaji dake zaune a falo ya ɗago kai yana kallon Makaho dake shigowa tare da sallama. Yana mai amsa sallamar ta sa yana bashi izinin zama. Zama ya yi a kan lallaudan centre carpet dake tsakiyar falon
"Ina wuni Daddy."
"Lafiya lau Khalifa."
Kallo ɗaya ya yi wa Mamy ya kau da kai kamar an masa dole ya ce .
"Ina wuni Mamy?"
"Lafiya lau angon Ma'eesaha."
Ta amsa tana wani dariya na mugunta.
Shiru falon ya yi tana jiran Dady ya yi magana sai ta ji shiru, gabadaya baya cikin tunanisa.
"Alhaji"
Shiru bai amsa ba sai da ta sake kiransa a karo na uku Sannan ya dawo tunanisa yana cewa.
"Na'am."
"Ga shi ya zo ɗaukar Amaryarsa da aka ce ya zo ya ɗauka, ka bar shi zaune."
"To ai na kira ita Ma'eesha tana hanyar dawowa."
"Okay, ka jira amaryar ta karasa sai ku tafi ta je lalle da kitso ne."
Bai ce komai ba illa ya sunkuyar da kai ƙasa.
_Ma'eesha_
Fitowarta kenan daga cikin shagon saloon tana sanye da rigar Abaya green colour, tana gyara mayafin abyarta hannunta rike da handbag ɗin ta da wayarta I phone 16 pro max. Wayarta ce ta fara ruri tana dubawa ta ga Inno ce me masu aiki.
Ɗaga wa ta yi ta maƙala wayar a kunne tana maƙe kafaɗarta yadda wayar za ta zauna, ta zuge zip ɗin handbag ɗin ta ta ciro makullin motarta tana cewa.
"Hello Inno ya aka yi ne?"
Shiru Inno ta kasa magana don har ya nufi motarta ta bude Inno ba ta yi magana ba.
Zama ta yi a driving seat sannan ta ce.
"Inno lafiya kuwa."
Cikin kuka ta ji muryar Inno na cewa.
"Ma'eesha kada ku dawo gidan nan ki je wani wuri."
Cikin faɗuwar gaba ta ce.
"Me ya faru ne Inno?"
Ta ji ta sake cewa.
"Aure aka ɗaura ma ki yau da wannan makahon da ya taɓa ceton ran mahaifiyar ki har ta ke kyautata ma sa."
Wani dariya Ma'eesha ta yi tare da cewa
"No ba zai yiwu ba, kada ki dake Mani wannan wasar."
Ta katse kiran wayar tana cewa.
"Haba wane irin aure ba tare da an nemi amincewa ta ba, ko auren ne ma ai sai a ce na fito da wanda nake so amma ba za'a yi ma ni dole ba, ballantana s ce wani makaho wanda ko a mafarki bai isa ya zo mijina ba ballantana a zahiri?"
Tsuke ta ja tare da yi wa motarta key ta bar harabar Saloon ɗin.
Horn take dannawa har maigadi ya wangala ma ta gate ta shigar da motar tana mai yin yin parking a parking space.
A hankali ta sako da fararen ƙafafuwanta da suka sha zanen kalli ja ba baƙi.
Fitowarta yi hannunta rike da handbag ɗin ta da makullin motarta.
Da sallama ta shiga falon gabanta na faɗuwa.
Gabadaya suka amsa ma ya sallamar ta shiga ciki. Ganin makaho ya haifar ma ta da wata faɗuwar gabar da ba ta san dalili ba.
Bayan ta gaida Dady da Mamy ta miƙe za ta nufi ciki ta ji Mamy na cewa.
"Alhaji ka sanar da ita ta fito ta bi mijinta tun da ga shi nan zaune yana jira tun ɗazu.
Mummunar faɗuwar gaba ce ta ziyarce ta, wanda har sai da ta saki handbag ɗin ta a ƙasa.
"Ke Ma'eesha zo nan."
A hankali ta take taku kamar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki ta zo gaban Dady ta zube.
"An ɗaura auren ki da Khalifa makaho yau, ku tashi ki bi mijinki Allah ya ba ku zaman lafiya."
Kallon Dady take yi kamar wata sokuwa ta ma rasa me za ta ce ma sa, don ganin abin take yi kamar wani alamara.
"Da...Da...Da..."
Ta ma rasa me za ta ce wani kalma za ta kama da za ta yi amfani da shi wajen yi wa Dady magana. Kafin ta samu ƙarfin zuciyar furta.
"Dady wane laifi na aikata da ka hukunta ni ta wannan han?"
Tsawar da ya daka mata ne ya saka ta firgita.
"Tashi ki kwaso kayan sakawarki ki bi mijinki, idan kika sake yi Mani wata magana a nan sai na ba ki mamakin da ya fi wanda kike ciki?"
"Ba da ke mahaifinki ke magana ba kina zaune?"
Jiki ba ƙwari ta miƙe ta ɗauki handbag ɗin ta da makullin motarta ta nufi ɗakinta.
Nan ta samu Inno mai masu aiki, tana ganin Inno ta fada jikinta ta rungume ta tana fashewa da matsanancin kuka."
Ita ma Inno kuka take yi tana cewa.
"Allah ya yana tare da ke Ma'eesha, shi ya sa na kira ki a waya na ce kada ki dawo gidan nan. Wannan kishiya mahaifiyarki ba ta tsoron Allah, so take kawai ta ga rayuwarli ta tagayyara shi ya sa ta saka mahaifinki ya aura maki makaho musaki wanda ba ya da cin yau balle na gobe, ta ya ya mace irinki da kika taso cikin gata da jin ɗadin more rayuwa za ki auri fakiri nakasashshe? Ita me ya saka ba ta saka ya auri ƴarta Agola ba, sai ke da gidan uban ki ne za'a yi ma ki wannan cin kashin?"
Cikin kuka Ma'eesha ta ce.
"Mamy ba ta so na ta tsane ta saka mahaifina dake son farin cikina yanzu ya juya mani baya ya tsane ni, duk da haka bai ishe ta ba sai da ta saka ya aurar da ni a inda ta san zan wahala me na yi ma ta ne, Da zuciya daya mahaifiyata ta kawo su gidan nan ita da yaranta suna cin arziki, karshe ta ci amana ta auri mijin aminiyarta suka ci gaba da zama duk da haka Mahaifiyata ba ta nuna ta ji zafin abinda ta yi ma ta na aure ma ta miji ba, ta zauna da ita da zuciya ɗaya, sai bayan ran mahaifiyata ne za ta ma ni haka sakayyarta ga Mahaifiyata kenan?"
Kuka suke yi dukkansu, kamar daga sama suka ji an daka ma su tsawa. A firgice suke kallon ƙofar. Mamy ce tare da Autarta Laila.
"Sannu muna munafuka kina hure ma ta kunne ko?"
Cikin rawar jiki Inno take ba Mamy hakuri ta fita daga ɗakin.
Ma'eesha ta kalle su da idanunta da suka yi ja ta kawar da kai ta cigaba da haɗa kayanta a cikin babban trolly tana kuka.
"Hi Amaryar makaho ya kike?"
Cewar Laila tana dariya.
"Mamy idan ta tafi ɗakin nan zan dawo da zama don ya fi nawa girma, ko funiture ɗin ya fi nawa kyau."
Mamy ta kalli ƴarta ta ce .
"Kar ki damu Shalele sai yadda kike so za'ayi."
Kallon Ma'eesha dake hada kaya ta yi ta ce.
"Ba ke mai gidan uba ba? Har kina yi wa yarana gorin cewa su agololi ne ko? To yanzu ke da gidan uban ki ne na saka uban naki ya yi waje dake, su agolan da kike yi wa taƙama da gidan uba su ne za su yi iko da gidan, ke kuka sai ki je ki fara cin garin kwaki, don ko kayan Gara da kayan ɗaki na hana ayi ma ki su ki je can ku ƙarata. Kina hutawa anan sai dai masu aiki su gyara Maki ɗaki su wanke Maki toilet ayi maki wankin da guga, ki sa a girka Maki abinda ranki ke so yanzu duk ba wannan a gidan makaho."
Laila da Mamy suka sake saka wata dariyar har suna tafawa kamar wasu kewaye.
Wannan karon Ma'eesha kukanta ne ya ƙaru sosai kamar ranta zai fita, ita kadai ta san halin da take ciki a wannan yanayin.
Bayan ta cika babban trolly ne ta ɗauki madaidaici ta zuba underwears ɗinta a ciki.
Sannan ta dauki karamin cikinsu ta zuba kayan kwalliyarta da turarruka, sannan ta dauko set sarƙar zinarenta za ta saka Mamy ta ce ke dakata ba in da za ki je da wannan."
Wani kallo Ma'eesha ta yi ma ta ta ce .
"Na mahaifiyata ce ita ta bani kyautatarsa dole ne tafi da shi."
Daidai lokacin Dady ya shigo yana cewa.
"Me kike yi ne har yanzu?"
Mamy ta yi saurin cewa.
"Alhaji ka karbi sarƙar set ɗin Gold ɗin nan kafa ta tafi da shi a sace ka san dai darajarsa."
"Ke Ma'eesha kawo ɗan akwatin nan."
Ta mika masa kawai ta zuge zip ɗin, sannan ta bude wata drawer ta ɗauko 🏧 card ɗin ta na cire kuɗi.
"Alhaji ka karbi ATM ɗin nan, su ma, ta tafi haka nan daga ita sai kayanta."
Tana rufe baki ya karɓa Atm card ɗin kamar me jiran umarni.key ɗin motar dake saman handbag ɗin ta Mamy ta kalla ta ce.
"Har da makullin motarta ma ka karba, don gidan da za ta zauna ba ƙofa ballantana a samu gate na shigar da motar, idan aka ajiye waje za'a sace."
"Eh haka ne."
Ya fada yana mika hannu. Ba musu Ma'eesha ta miƙa ma sa ya karɓa ya fice daga ɗakin.
"Ai duk wani abu da na san zai Maki amfani ba zan bar ki da shi ba."
Ta fada tana jan hannun Laila suka fice.
Ɗayan trolly ɗin ta fara fitowa da shi ta ajiye falon ta koma ciki.
"Kai makaho tashi ka dauki babbar akwatin kayanta ku tafi za ta fito da kananan."
Tashi ya yi yana lalube har ya ji ya ci karo da akwati ya ja yana yi wa Dady godiya da sallama ya fita.
Tana fitowa rike da dayan madaidaicin akwatin sai karami dake da kayan turarrukannta ta nufi hanyar fita ba tare da ta kallon Dady ba ballantana Mamy."
Sakin baki Mamy ta yi tare da cewa.
"Amarya ba sallama?"
Ba ta yanka ma ta ba ta fice daga cikin falon.
"Ikon Allah, ko irin sallama da iyaye a nemi tafiyarsu ba za ki yi ba kin fice ko, za ki zo gidan za ki ga wulakanci.
Kasancewar tana bakin ƙofa ta ji komai ya saka ta ce.
"Idan kin ga na zo gidan nan Mamy duk wulaƙancin da kika dama ki yi ma ni."
Ta saka kai ta fice Mamy ta saki baki yayin da Dady ya sunkuyar da kai ya kasa kallon Ma'eesaha.
"Ungo Laila ga kudin sadakinta nan dubu uku ki ɗauka ki kai ma ta hakkinta ne."
Da sauri Laila ta ɗauki kudin ta fice tana dariyar mugunta.
A harabar gidan ta gan su Yana gaba da babban trolly tana bin sa da kananan a baya.
Daidai lokacin motar Jamil babban yaron Mamy Yayan Laila ya danno hancin motarsa cikin gidan.
Ko parking ɗin kirki bai yi ba sakamakon ganin Ma'eesha na kuka, ga makaho na gaba da wata babban trolly wanda ya fi na hannun Ma'eesha girma, ga Laila na miƙa wa Ma'eesha kuɗi.
"Subhanah Ma'eesha me ya same ki kuma ina zuwa da kaya?"
Ba ta tanka ma sa ba ta yi gaba. kallon ƙanwarsa ya yi yana cewa.
"Munafuka me kuka yi ma ta kuma yanzu?"
"Aure Mamy ta saka aka yi ma ta da wancan makahon, shi ne ya zo ɗaukarta za su wuce, ga kudin sadakinta dubu uku ta ki amsa."
"What?"
Ya yi tambayar a firgice.
Yana ƙarewa makaho kallo ganin yadin jikinsa ba ta wuce dubu ɗaya ba, kuka daga gani kayan ma sun ji jiki, ko takaman ƙafarsa ma na soso ne sai wata hular taɓa ni ka ji hadisi da ya saka.
"Aure da wannan nakasashen?"
Girgiza kai ya yi tare da cewa
"Da sake!."
Ya bi bayansu a guje yana kiran sunan Ma'eesha, har ya karasa inda suke tafiya ba ta kalle shi ba.
Haka ya dinga bin su yana rokon Ma'eesha amma ba ta saurare shi ba, haka ya hakura ya bar ta ya dawo.
Kamar zai tashi sama haka yake tafiya har ya isa gidan. Don yau ya kara jinjina makirci da rashin imani irin na mahaifiyarsa.
*KADUNA*
Da sanyin asuba ta fito daga cikin bathroom dake cikin ɗakinsu.
Harara ta watsawa ƙanwarta dake zaune saman sallaya tana karatun Alkur'ani mai girma.
Cije laɓɓanta ta yi cike da takaici ta yi tsuki.
Bayan ta kai karshen surar da take karantawa ta kalli yayat tata ta ce.
"Aunty Sidra lafiya kuwa?"
Harara ta watsa ma ta tare da cewa.
"Ban sani ba."
"Allah ya huci zuciyarki."
Ta faɗa tana mai ci gaba da karatunta, don in da sabo ta saba da halin yayar tata.
Komawa toilet ta yi sakamakon jin wayar dake hannunta tana vibration
Ɗagawa ta ji bayan ta rufe kofar toilet ɗin, sannan ta amsa kiran daga cikin wayar ta ji an ce.
"Haba Sidra ki yi ki fito ma na kin ce na zo na ɗauke ki karfe biyar da rabi ga shi ba ki fito ba, ko na wuce za ki zo da motarki ce?"
Cikin yin ƙasa da murya ta ce.
"Ba haka ba ne Sadiya kin san ƙanwata Nasara tana zaune idan ta ga na fito da trolly za ta gane zan tafi wani waje ne, kin san kuma za ta iya sauro ta faɗa a gidan namu idan aka kama ni fa? Yanzu ki bani mintuna kaɗan zan tura ta wani wajen idan ta fita zan fito ba tare da motata ba don asirina zai iya tonuwa."
Tana fadar haka ba ta jira jin me ƙawar za ta ce ma ta ba ta katse kiran wayar .
Fitowa ta yi tana kallon Nadra dake karatun Alkur'ani ta kira sunanta.
"Ke Nadra!"
Nadra ba ta dakata da karatun Alkur'anin ba sai da ta kai aya ta ce.
"Na'am Aunty Sidra."
"Ki tashi ku je garden ki duba mani zobe na ya faɗi ina ganin lokacin da muke fira da Fahad jiya daddare."
Shiru ta ɗan yi kafin ta ce.
"Aunty Sidra why not ki bari sai da safe, yanzu akwai sauran duhu gari bai gama wayewa ba, idan gari ya waye sai na fita na duba ma ki. Za'a fi gani ma idan ba duhu ai, amma yanzu ba lallai a gan..."
Idan ba za ki je ba ne ki fada ma ni, ai ga wayarki nan ki kunna torchlight ku je ki duba ma ni."
Ba tare da ta sake yin magana ba ta miƙe tsaye tana cewa.
"Bari na je na duba ma ki."
Fita ta yi daga ɗakin ba tare da ta cire dogon Hijabin dake jikinta ba, wmhannunta rike da wayarta tana cewa.
"Allah ya huci zuciyar Amarya a gidan Yaa Fahad, ai bai kamata a ce yau za'a ɗaura ma ki aure kina faɗa ba."
"Ke dai kika sani munafuka."
Sai da ta tabbatar ta nufi Garden ɗin sannan ta janyo trolly ɗin ta daga cikin wardrobe, kasancewar dogon Hijabi har ƙasa ta saka ba's ganin ko me take ɗauke da shi.
A hankali ta bude ƙofar ɗakin bayan ta rataya handbag ta saka wayarta ciki.
Akwai mutane a falon wasu na kwance wasu na zaune, kasancewar bikin auren Sidra ake yi ƴan uwa da abokan arziki na nesa duk sun zo garin, ɗakin ɓakin ya yi ma su kadan wasu suka kwana a falon.
Cikin sanɗa take tafiya wata ma ta dake zaune ta ce.
"Ke wace ce nan ke sanɗa?"
Sai da gaban Nadra ya faɗi sannan ta juyo ta ce.
"Ina kwanaku?"
"Oh Amaryar ce ashe, lafiya lau ya kike?"
Suka hada baki wajen amsa gaisuwar, wata dattijuwa ta ce ni fa ba na banbance wace ce Sidra wace ce Nadra."
Wata buduwar ta ce .
"Wacce ta fara fitowa ta karasa ta durƙusa ta gaishe ku ita ce Nadra, wannan ta yanzu kuma ita ce Sidra wacce za'a ɗaura wa auren yau, ai suna da banbanci ita Amaryar Sidra ai fara ce, ita kuma Nadra baƙa ce."
Ita dai ba ta bi ta kansu ba ta wucewarta waje.
Sai wata buduwar ta ce
"Ai wannan Amaryar ba ta da kirki wallahi, jiya da Nadra ta ce mu zo mu kwana a ɗakinsu tun da su biyu ne amma fir wanan Amaryar ta ce wai ga falo nan ai, Sidra ba ta da kirki."
Suna ta firarsu har Nadra ta dawo ta yi ma su sannu ta shiga ɗaki.
Sai dai ba ta ga Sidra ba a tunaninta tana toilet ne don haka ta koma ta zauna a saman sallayarta tana cewa.
"Aunty Sidra ban ga komai ba wallahi."
Ta cigaba da karatunta don hadda take yi ba da Alkur'ani take karatun ba.
_Sidra_
Tana zuwa harabar gidan ba kowa maigadi dawowarsa daga masallaci kenan ya ga tana kokarin fita ya ce.
"Amarya lafiya kuwa."
Kamar ba za ta yi magana ba ta ce.
"Zan ba kawata saƙo ne tana waje."
"A dawo lafiya."
Ya fada yana zama kan kujerarsa hannunsa rike da carbi.
Tana ƙarasawa ta buɗe bayan motar ta saka jakar kayanta sannan ta zagaya ta zaune wajen me zaman banza.
Ba tare da ɓata lokaci ba Sadiya ta yi wa motarta key suka bar layin.
"Na daɗe ina jiran ki fa."
"Wallahi Nadra ce nake ta so na ɗauke hankalinta kar ta ga fita ta da akwatin kaya ta tona ma ni asiri shirina ya lalace."
Shiru Sady baby ta yi tana rage gudun motar tana rage gudun motar bayan sun bar layin.
Kiran waya ne ya shigo wayar Sidra, ta ɗaga tana cewa.
"Hellow Khadijah ya aka yi ne?"
"Kina ina ne?"
"Ya kike tambaya ta kamar ba ki san komai ba, amma ai na fada ma ki komai kasancewar ki ƙawata."
"Sidra abun da kike ƙoƙarin aikatawa kuskure ne, za ki wulaƙanta iyayenki ne, bayan kin san sun tara jama'a ana shagalin biki yau za'a ɗaura auren ki a ce kin gudu ya kike so su yi da jama'ar da suka tara? Sannan ga shi Fahad ɗin da iyayesa su ma sun tara na su jama'ar sai su ji labarin matar da Ɗan su zai aura ta gudu zai ji shi Fahad ɗin."
"Ke ba gudawa fa zan yi ba, da zaran na samu abinda na je nema zan dawo ne sai a sake saka ma na ranar ɗaurin auren zuwa gaba, don na san Fahad na masifar so na dole ya jira sai na dawo, iyayena kuma za su hakura ne kawai ba yadda za su yi da ni bayan na dawo, kin ga idan na ba su haƙuri ai za su karbe ni ko da sun yi fushi kuwa. kuma ba wani daɗewa zan yi ba me yiwuwa nan da watanni uku na dawo."
Tana fadar haka ta katse wayar tare da kashe wayar gabɗaya.
"Khadijah ƙawata ce tun da na fada ma ta plan ɗina ta saka ni gaba wai kar na aikata."
"Da ma me zai kai ki faɗa wa wata idan b ke ba."
Daga nan ba wanda ya sake magana a cikinsu.
_Nadra_
Tana idar da karatun Alqur'ani ta yi knocking ƙofar toilet ta tabbatar ba kowa kafin ta tura ƙofar. Ganin ba Sidra ya sa ta dauka ko ta fita zuwa wajen su Umma ne, don haka ta fita zuwa falon mutanen ɗazu ne a ciki, tana sanye har lokacin da hijabi ta nufi part ɗakin Umma. Da sallama a bakinta ta tarar da Umma tare da ƙanwar Abba wacce suke kira da Goggo Laraba da suka kwana ɗakin Umma."
Ta durƙusa ta gaishe su cikin girmamawa, suka amsa ma ta cike da kulawa. Gwaggo Laraba ta ce.
"Ina Amaryar take ne ko tana can tare da ƙawayenta?"
"Ai ƙawayenta tun jiya ta Kore su wai ta sallame su ba ta son kowa ta kwana a gidan."
Da mamaki Umma ke kallon Nadra, Gwaggo Laraba ta ce.
"Sidra ba ta da mutunci wallahi."
"Kira ma ni ita."
Cewar Umma tana budar drawar da take zuba magungunanta a ciki.
"To Umma bari na je na duba duk da ba ta cikin ɗakin."
Tana fita ta nufi part ɗin Abba ta gaishe she shi shi da wani wan Umma suna zaune .
Gaishe su ta yi cikin girmamawa sannan ta fita ta koma ɗakinsu. Ta nemi Sidra ba ta ciki.
Don haka sai ta yi tunanin bari ta zagaya duka gidan ko tana wanni wajen a cikin gidan.
Umma kuwa ta buɗe drawar da take saka magungunanta a ciki dan ta ɗauko man maganinta na sha'awa a ƙafa. Sai ta ga wata farar takarda, tana fitowa ta warware ta fara karantawa kamar haka.
*Assalamu alaikum*
*Iyayena ku gafarce ni zan yi wata tafiya domin cikar burina. Na san za ku shiga tashin hankali a yayin da kuka ga wannan wannan ya wasiƙar ta wa. Ku ba wa Fahad da iyayensa haƙiri na san yana so na zai jira har lokacin da na dawo mu yi aure.*
_Sidra Abdallah Maitama_
Wani jiri ne ya ɗebi Umma ta yi luu za ta faɗi, cikin zafin nama Gwaggo Laraba ta tare ta tare da zaunar da ita bakin gadon.
Takardar Gwaggo Laraba ta ɗauka tana karantawa.
"Innalillahi wa 'inna ilahir raji'un."
Shine kalmar da Gwaggo Laraba take furtawa.
Kafin ta ɗauki wayarta ta kira lambar wayar Yayanta wato Mahaifin Sidra.
Bugu ɗaya ya ɗaga, ta sanar da shi ya zo ɗakin Umma yanzu.
Sannan ta fita zuwa ɗakin da Mahaifiyarsu ta sauka, ta tarar da ita ita kaɗai, don ba wanda ya je wajenta saboda masifarta.
Ita ma Gwaggo Laraba ba ta sanar da ita abun da ya faru ba, ta dai ce ta zo ana neman ta a ɗakin Umma.
Carko-carko suka yi a ɗakin Umma, Daga Abba har mahaifiyar su da suke kira Ammi da Gwaggo Laraba.
Umma na kuka kamar ranta zai fita yayin da kowa ya kasa magana. Abba ransa ya kai matukar tashi, idanunsa sun yi jajir, Ammi sai alawadai da Sidra take yi yayin da Gwaggo Laraba ta kasa magana.
Nadra ce ta shigo da sallama, ganin mahaifinsu kwance tana hawaye ya saka ta ruga gabanta ta rike hannunta tana hawaye ta ce.
"Umma me ya same ki ?"
Ta ji tambayar tana hawaye. Ganin haka ya saka Gwaggo Laraba janyo Nadra tana cewa.
"Ba abinda ya same ta tana kukan rabuwa da Sidra ce, kin san daga Anjima za'a ɗaura aurenta shi ke nan fa ta zama yar wani Family."
Haka kawai Nadra ta ji ba ta gamsu ba tana son yin magana ta ki Umma na cewa.
"Kada ki damu Nadra kewa ne kawai da zan yi na Yayarki."
Ya karasa maganar tana murmushin karfin hali.
"Umma na duba ko ina ban ga Sidra ba."
"Eh ta tafi wajen gyaran jiki ne Anjima za ta dawo. Ta shi ki tafi."
Haka kawai jikinta ya yi sanyi ta tashi ta tafi .
Cikin damuwa Ammi ta ce.
"Amma yarinyar nan ta gama tozarta mu, sai da ta bari mun tara jama'a gida ya cika da mutane sannan za ta ma na haka? Ga wasu mutane suna kan hanyar zuwa daga wasu garuruwa na nesa don halartar wannan ɗaurin auren ne za ta kunyata mu."
Sai da ta goge hawaye kafin ta ce.
"Abdullahi ka kira wadanda ke hanyar zuwa garin nan wajen daurin aure ka dakatar da su su juya su koma ba zancen auren kuma. Wadanda ke nan garin na dan dole su zo don Allah kaɗai ya san yawan su idan sun zo a basu hakuri su koma. Suma dangin angon a kira a ba su haƙuri su sallami baƙin da suka gayyata na nesa su koma garinsu na kusa kada su zo, wallahi Sidra ta gama kunyata mu ta tozarta mu."
"Ba za'a kira kowa ba ba wanda za mu dakatar daga zuwa kowa ya zo, kanta ta yi wa ba mu ba, wallahi ba ta isa ta tozarta mu ba. "
Da mamakin kowa ke kallonsa kafin ya ce.
"Za'a daura auren yau sai dai ba da Sidra ba tun da ta gudu, za'a ɗaura auren da ƙanwarta Nadra."
Da mamaki Gwaggo Laraba ke kallonsa kafin ta ce.
"Kar ka aikata abun da zai zo ya saka mu yi nadama, ka san irin soyayya da shaƙuwar da Fahad ya yi da Sidra, suna masifar son juna, ba wanda ya haɗa su sune suka ga juna suka hada kansu suke soyayya. Shin idan aka yi haka kana ganin Fahad zai yarda ya karbi ƙanwar Sidra a matsayin matarsa, ita ma Nadra za ta yarda ta zauna da saurayin Yayanta a matsayin mijin aurenta? Kuma shi Fahad irin mazan nan ne ƴan boko ma su son rayuwar wayewa, Shi ya sa ya nemi Sidra don ita ma haka rayuwarta take ba, amma ita Nadra da take da kunya da ustazanci ba ta damu da rayuwa ba shin ta ya ya zaman su zai yi daidaita tun da ra'ayinsu ba ɗaya ba?"
*To masoyana ga ni ɗauke da sabon labari, tafiya ne tsakanin duhu da haske, wata kila ya zo daidai da ra'ayinku🥰 watakila kuma akasin haka😒 Ni dai fatana a duk lokacin da kuka ci karo da abinda bai ma ku ba a cikin labrina to ku kasance ma su fahimtata da kuma yi ma ni uzuri. A cikin wannan labarin za mu fuskanci rayuwar waɗan nan jaruman guda biyar*
Khalifa (makaho)
Ma'eesha Ibrahim Khalil
Fahad Umar Majidaɗi
Sidra Abdullahi Maitama
Nadra Abdullahi Maitama
*Waɗan da suke da labari mabanbanta, ku dai ku kasance da ni a cikin wanan labarin don ganin wani dararasi ya zo da shi.*
*Maman Ihsan ce*✍️
Follow the TASKAR MAMAN IHSAN channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaiufWb3LdQYnzC2vH0z
*MAKAHO NE*
*NA*
Maman Ihsan ce ✍️
https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
page0️⃣2️⃣
"Kar ka aikata wani abin da zai zo ya saka mu yi nadama, ka san irin soyayya da shaƙuwar da Fahad ya yi da Sidra, suna masifar son juna, ba wanda ya haɗa su sune suka haɗa kansu suke soyayya. Shin idan aka haka kana ganin Fahad zai zai yarda ya karɓi kanwar Sidra a matsayin matarsa, ita ma Nadra za ta yarda ta zauna da saurayin Yar ta a matsayin mijin aurenta? Kuma shi Fahad ɗin irin mazan nan ne ƴan boko ma su son rayuwar wayewa, shi ya sa ya nemi Sidra don ita ma haka rayuwarta take . Amma ita Nadra da take da kunya da ustazanci ba ta damu da rayuwa ba shin ta ya ya zaman su zai daidaita tun da ra'ayinsu ba ɗaya ba?"
"Ka da ki damu Laraba in sha Allah babu nadamar da zai biyo baya in dai Nadra ya aura. Ni na haife su na san halin kowacce a cikinsu, sai ya fi jin daɗin zama da Nadra akan Sidra. Domin ita ce nake da yaƙinin zai iya sarrafa ta ta sarrafu ma sa yadda yake so, kuma ita ce zai iya daka ma ta tsawa ta saurare shi saɓanin Sidra. Da a ce tun farko Nadra ya gani yake kuma ta gudu, to ba zan taɓa cewa zan musanya ma sa ita da Sidra ba, don kada ya yi kuka da ni daga baya, amma Alhamdulillah tun da har Sidra ce ta gudu zan musanya ma sa madadinta da Nadra na tabbatar wata rana sai ya yi alfahari da wannan madadin, domin kuwa Nadra mace ɗaya ce har da ƙari."
Shiru dakin ya ɗauka ba wanda ya sake yin wata magana, domin kuwa sun san cewa Nadra ba ta da matsala.
"To yanzu ya kamata ka sanar da Fahad ɗin idan ya amince da Nadra."
Cewar Ammi tana kallonsa.
Wayarsa ya lalubo a cikin aljihun rigarsa yana dannawa lambar Fahad kira.
_Fahad_
Kwance yake a gadonsa ya lulluɓe da bargo yana barci.
Wayarsa dake saman side ta fara ruri.
Cikin barci ya ji kiran wayar, a tunaninsa Sidra ce, don da ita ya kwanta a ransa, bai same ta a waya ba. Kuma ya san ita ba ma'abiciyar kashe waya ba ne, kuma kullun asuba yakan kira wayarta ko ya turaa ta saƙon barka da safiya. Amma yau sai ya kira switch off.
A hankali ya bude idanunsa yana tashi zaune ya miƙa hannunsa ya ɗauki wayar.
Ganin sunan Mahaifin Sidra ne sai da gabansa ya faɗi.
Ya ɗauki wayar tana gab da tsinkewa.
"Assalamu alaikum."
Daga cikin wayar ya ji muryar Abba ya ce.
"Wa'alaika salam Fahad?"
"Na'am Abba."
"Idan ba damuwa ina son ganinka yanzu a gidana."
"To Abba."
Ya amsa sannan Abba ya kashe kiran wayar. Bargon da ya lulluɓe ya yaye ya sauko daga kan gadon. Farin wando ne Three-quarter ya sanya, babu riga a jikinsa ga wani zanen Tattoo a ƙirjinsa zuwa hannunsa.
Bathroom ya faɗa don yin wanka.
Tsawon mintuna talatin ya ɗauka yana wanka kafin ya fito ɗaure da towel a ƙugunsa da wani ƙarami yana goge dogon gashinsa. Jikinsa sai kamshin shower gel da turaren wanka yake yi.
Tsadadden man shafawarsa ya shafa a jikisa, sannan ya fesa body spray. Closet ɗin sa ya shiga ya cikin tsadadden ɗanyar shaddar sky blue, sannan ya fesa turarensa mai suna Creed Aventus turare mai ƙarfi da jan hankali. Sannan ya ɗauki agogonsa Rolex date just ya ɗaura a tsitsiyar hannunsa. Ya duba bangaren takalmominsa ya ɗauki takalminsa Jimmy choo ya saka a ƙafarsa tsakanin nevy blue don haka ya saka hularsa nevy blue.
Ya fito ina da ya dauki wayoyinsa tare da key ɗin motarsa ya fara takunsa cikin izza wanda kallo ɗaya za ka yi ma sa ka san yana kan cin ganiyar samartakansa, kyau da cikar haibarsa suka sake bayyana.
Ƙamshin turarensa ya tabbatar wa da jama'ar dake falon yana gab da saukowa.
Idanu suka zuba wa upstairs ɗin yayin idanunsu ya sauka akansa.
A ƙalla mutanen da suke falon za su kai su goma kuma duk baƙi ne da suka zo bikin.
Gaishe su ya yi suka amsa suna ma sa ƴar tsokanar da ake yi wa ango.
Bai saurare su ba ya nuf part ɗin Mama. A falo ya same ta ita da ƙanwarta ya gaishe su.
"Ina za ka je na gan ka da makullin motar ko breakfast ba ka yi ba."
"Ina sauri zan je na dawo kafin abokaina su iso don suna hanya."
"Ina za ka je ne wai?"
Cewar Aunty Nana ƙanwar mahaifiyarsa.
"Gidan surukaina ne suke nema na."
"Okay a dawo lafiya."
Daga nan ya fice, zuwa part ɗin Baba. Shi ma ya gaishe shi sannan ya sanar da shi fitar da zai yi.
Ta ƙofar falon Baba ya fita ba tare da ya koma main falon ba.
Wajen motar da zai fita da ita ya nufa, ya shiga motarsa ƙirar Mercedes Benz G63 AMG ya yi ma ta key, kafin ya horn har maigadi ya wangale ma sa gate ɗin gidan ya fice da motarsa. Wanda kallo ɗaya za ka yi wa motar ka san cewa an narka dukiya wajen siyen motar.
Kai tsaye ya dauki hanyar da za ta sada shi da unguwar su Sidra.
_Maeesha_
Tafiya kawai take yi tana hawaye hannunta rike da akwatina biyu, yayin da Makaho ke jan babbar akwatin da ɗaya hannunsa. Ɗayan hannu kuma yana rike da sandarsa yana dogarawa.
Bin bayansa kawai take yi ba tare da ta san in da za su tafi ba.
Tsawon lokaci suka ɗauka suna tafiya, kasancewar ba ta saba yin tafiyar kafa ba ga kaya duk ta bi ta gaji.
Don haka ta tsaya ba tare da ta yi magana ba, shi ma sai ya tsaya kamar ya san ta tsaya.
Sai dai bai yi magana ba ya yi shiru. Ganin ba ta da niyyar cigaba da tafiya ya saka ya ce.
"Ki yi hakuri mu tafi akwai sauran tafiya a gaban mu ga magrib ta kusa."
"Ba zan iya sake wani tafiya ba na gaji."
Kafin ya yi magana ta hangi mai keke nape ya fito layinsu tsaida shi ta yi ya tsaya a gabanta .
"Hajiya ina zuwa."
Kallon Makaho ta yi tare da cewa.
"Ka zo ka faɗa ma sa sunan unguwar."
Ya karasa yana lalube da sanda ya faɗa wa mai napep ɗin .
Mai nape ya saka akwatunan a baya ya ajiye daya a gefe, sannan ya ce su shiga .
Sai da ta shiga sannan ta ce wa makaho.
"Mallama ka shigo."
Kamar ba zai shiga ba sai kuma ya shiga baya bayan ya laluba ya zauna.
Shi ya sanar wa mai napep ɗin unguwar da zai kai su tare da ma sa kwatance.
Tun da suka shiga layin jikin Ma'eesha ya yi sanyi . Don kallo ɗaya za ka yi wa yankin ka san cewa unguwa ce ta talakawa. Don ba gini mai kyau a layin da zai tabbatar ma ka da akwai masu rufin asiri a layin.
Kamar yadda ya yi ma sa kwatance da masallacin kuwa haka aka yi, sai da ya kawo daidai masallacin da ya sanar da shi ya tsaya ya ce.
"Mun iso wajen."
"Mallam don Allah ka taya mu sauke kayan kasa."
"To Hajiya."
Ya fada yana saukowa bayan ya kashe keke nape ɗin nasa.
Sai dai ya sauke ma su kayan sannan ta tambaye shi kudinsa.
"Nawa ne mallam."
"Ki bada yadda kuke zuwa ."
"Mallam ka yi magana ban san ya ake biya ba, don ban taɓa hawa keke nape ba sai yau."
Wani kallo ya ma ta har zai yi wata magana sai ya lura da haƙorin Gold ɗin dake bakinta, hakan ya tabbatar ma sa da cewa Hajiya ce ita, kuma yanayin ta ma ya nuna ƴar hutu ce.
"Ki bayar da dubu ɗaya."
Ya fada yana shiga cikin napep ɗin nasa. Handbag ɗin ta ta zuge ta ciro 1k ta bashi.
Bayan ta sallame shi ne Makaho ya ja akwatin kayanta babba ya yi gaba, ita dai bisa ta yi a baya har suka ƙarasa ƙofar wani gida. Gidan ƙofarsa ta ɓalle tun daga waje ma ana hangen wa su matan dake tsakar gidan.
'Na shiga uku ni Ma'eesha wane irin gida ne nan na faɗo.'
Sallama Makaho ya fara yi sai da aka ba shi izinin shiga sannan ya shiga tana bin sa a baya.
Ɗakunan gidan za su kai Ashirin. Don tsakar gidan ma cike yake da mata ga yara barkatai ta ko ina. A tsakar gidan.
Wasu yaran suna wasa, yayin da wasu na faɗa sai wasu yaran zaune sun jeru suna kashi a ta ko ina suke zaune ba tsari .
Wata dattijuwa ta kalli Makaho ta ce.
"Mallam Khalifa ka dawo ?"
"Eh Baba na dawo."
"To ma sha Allah, wannan ita ce Amaryar taka?"
"Eh ita ce."
Wata uwar ashar suka ji an danna, wanda ya saka hatta Makaho da Ma'eesha sai da suka tsaya cak daga tafiyar da suke yi.
Larai Dillaliya ce ta yi zargin tana kallon takalmar dake ƙafar Ma'eesha wanda a ƙalla kuɗinsa za su kai dubu ɗari 100k haka handbag ɗinda ke hannunta ma zai kai dubu ɗari.
Kafin a gama mamakin ashariyar da ta ɗura aka ci muryar Larai ta sake cewa.
"Wannan ita ce matar Khalifa makaho kenan?"
"Makaho ya cigaba da tafiya Ma'eesha kamar za ta faɗi sakamakon idanun da ta ji suna yawo a jikinta, sai dai kanta a ƙasa ba ta ba da damar ganin fuskarta sakamakon mayafin abyarta da ta rufe rabin fuskarta da shi hawaye ne kawai ke bin fuskarsta ba tare da kowa ya sani ba.
Hakan ya saka kanta a sunkuye tana kallon ƙasa yake tafiya ba ta yarda ta gaishe da mutanen gidan ba saboda kuka zai iya ƙwace ma ta matukar ta ce za ta buɗe baki ta yi magana.
Ɗakin karshen gidan wanda ke da ƙofar langa-langa ya tura ya shiga da sallama.
Ita ma shiga ta yi idanunsa na sauka kan buhun siminti da aka shimfiɗa a ɗakin
Ƙafarta ya harɗe cikin buhun da ake shimfiɗa madadin carpet. Nan ta lura ashe ɗakin ko flour babu, ba'ayi simintin ƙasar ɗakin ba ƙasa ne kawai sai aka shimfiɗa buhu a ƙasan ɗakin wanda ya rufe ƙasar ɗake ƙasan ɗakin. Hatta bangon ɗakin ana iya ƙirga bulo ɗin don shi na bangon ba'a shafa ma sa siminti ba. Ga bangon duk ya yi gantsa kuka alamar ya sha ruwa kafin aka yi rufin ɗakin.
Kanta ta ɗaga sama tana kallon rufin ɗakin, nan take hangen haske daga sama, wato zink ɗin ɗakin ya hude a wasu wuraren aka hangen hasken waje, langa-langa ba sabo ba ne aka saka.
Kuma idan ana ruwan sama da alama ba ƙaranin yoyon ruwa zai yi ba, don ba makawa dai ruwa ya cika ɗakin idan har mai ƙarfi ne.
Toshe bakinta ta yi tana kuka don kada sautin kukan ya fita, kafin ta ji tsayuwar ya gagare ta ta zube akan ƙafarta tana kuka mai tsuma zuciya.
Kamar ya san kuka take yi sai ta ji ya kira sunanta cikin kamilalliyar muryarsa mai cike da nutsuwa.
"Ma'eesha."
Ba ta amsa masa ba sai hawaye dake bin fuskarta.
"Ki yi haƙuri na san wannan gidan bai dace da macen da ta taso cikin gata da hutu ba, kin taso cikin farin ciki na sani kina kwana a cikin A.c da katifa mai laushi ba'a dauke wuta ko an dauke ba iya sani saboda na'ura za ta fara aiki ki nan kuma ko fanka babu ballantana A.C ba na da halin da zan iya ciyar dake irin abincin da kike ci da ruwan da kike sha..."
Shiru ya yi sakamakon jin fitar ta daga ɗakin, tana fita ta yi tozali da fo da yarinya ta yi kashi ta tashi ba tare da an yi ma ya tsarki ba tana wasar ta. Wani na zaune kusa da fo ɗin yarinyar shi ma yana Kashin, Ma'eesha ta yamutse fuska, ta ji wata mata na cewa.
"Amarya hakuri za ki yi ɗakinki shi ne kuka da banɗaki dole ki dinga ganin haka.
"Ina ne banɗaki."
Ta tambaya tana kallon matar da idanunta da suka kumbura.
"Ga banɗaki nan jikin ɗakinki. Bari a kawo ma ki buta."
Kafin matar ta yi magana sai wata budurwa ta kawo wa Ma'eesha buta da ruwa a ciki.
Karɓa ta yi tana shiga ban dakin ta toshe hanci tare da fitowa a guje ta duƙa ƙofar ɗakinta tana kakarin amai, sakamakon wari da zaurin fitsari dake tashi a toilet ɗin.
Da kallo suka bi ta wasu na yi ma ta sannu. Bayan ta gama ne ta ga wannan buduwar da ta ba ta buta tana cewa .
"Tashi bari na gyara wajen."
Tana magana tana mika ma ta kasar pure water na ruwa, karba ta yi ta wanke baki sannan cikin kasalliyar murya ta ce.
"Thank you."
Cikin ɗakin ta koma ta ga makaho tsaye kamar yadda ta bar shi.
"Wallahi ba zan iya rayuwa a cikin wannan gidan ba."
Tana fadar haka ta janyo akwatin kayanta ta fito, shi ma ya janyo babban ya biyo ta suka fito suna tafiya."
Baba ta lalle su ta ce.
"Lafiya kuwa Khalifa?"
"Baba ina zuwa "
Abun da ya iya fada kenan saura. Matan kowa sai bin su yake da kallo. Suka ji muryar Larai Dillaliya tana cewa.
"Ni Ko da na kalli yarinyar nan na san ba kamar unguwar nan ba ne ballantana gidan nan, ko dai asiri Khalifa ya yi wa iyayen yarinyar nan ne da suka ɗauki ƴa suka ba shi aure?"
Ita dai Ma'eesaha ko kallo ba ta yi ma ta ba ballantana ta gane wa ke magana .
Tana zuwa ƙofar gidan ta ajiye akwatin hannunta, shi ma ya tsaya in da ya ji ta tsaya, ya ajiye akwatin amma sandarsa ta Manafi na hannunsa.
Handbag ɗin ta ta buɗe ta duba daga wayoyinta sai kuɗi 9k dama dubi goma ne ta ba mai napep dubu ɗaya ya rage dubu tara.
Ga shi matar Babanta ta amshe ATM card ɗin ta wanda a ƙalla tana da Naira sama da miliyan biyar a ciki. Pink lips din ta ta cije tana goge hawaye.
Kafin ta ce.
"Ina zan samu gidan haya kamar na zaman mutum ɗaya?"
"Gaskiya ban sani ba, amma dai idan aka tambaye Iro mijin Larai Dillaliya zai samo ma na, saboda dillancin gidajen haya yake yi a unguwar nan."
"Ina za'a same shi yanzu ?"
Kafin ya yi magana ne suka ji muryar wani mutum dake ƙoƙarin shiga cikin gidan yana cewa.
"Mallam Khalifa Amaryar ce nan?"
Yana tambayar amma idanunsa akan Ma'eesha wacce ta tsuke fuska, sakamakon kallon ƙurillar da yake yi ma ta.
"Yauwa Mallam Iro ka dawo?"
"Eh Allah ya yi."
"Dama yanzu muke maganar ka dai ga shi ka zo."
"Ikon Allah, ka san an ce ɗan halal ya ƙi ambato."
Kallon Ma'eesha ya yi yana cewa.
"Amarya ya garin ."
Ba ta amsa ma sa ba ta ce.
"Gidan haya za ka nema ma ni a yanzu nake buƙata iya na zaman mutum ɗaya."
Shiru ya yi yana tunani kafin ya ce.
"Eh akwai guda ɗaya a unguwar nan, shi kadai ne iya na zaman mutum ɗaya, sauran dole sai kin samu makota."
"Ina so sannan ina son ya kasance gidan mai tsafta ne."
"Ba matsala in dai tsafta ce, sai dai ƙarami ne sosai gidan. In taƙaice ma ki iya ɗaki ɗaya ne tal a ciki wato single room ne, ba falo ɗaki ɗayan nan ne sai banɗaki da kitchen madaidaita."
Ba haka ta so ba ta so ko da mai falo ɗaya da ɗakin barci a samu, amma tun da ya ce wannan kadai ne za ta amshe shi, ya fi ma ta wanann gidan da ta fito yanzu na ƙazamai."
"Ina ne gidan?"
"Farkon layin nan ne?"
"Okay nawa ne kuɗin?"
"Ba tsada dubu hamsin ne a shekara ɗaya."
Tunanin ta ina za ta samu dubu hamsin ne, ga shi dama ba ta iya yin transfer money from account ɗin ta har tana tunanin zuwa bank sa saboda matsalar ga shi dubu tara take da shi yanzu haka, ga shi ana maganar gidan dubu hamsin.
*KADUNA*
_Fahad_
A ƙofar gate ɗin gidan su Sidra ya yi horn.
Maigadi ya wangale ma sa gate ya shiga da motarsa ciki .
Bayan ya yi parking bai fito daga cikin motar ba ya ɗauki wayarsa ya kira Abba. Ya sanar da shi ya iso, nan Abba ya ce ya shigo yana part ɗin sa.
Da sallama ya shiga ƙofar part ɗin Abba.
Suka amsa ma sa gabaɗaya suna zaune a falon. Abba, Umma, sai mahaifiyar Abba wato Ammi, da ƙanwar Abba Gwaggo Laraba sai Aminin Abba Alhaji Abubakar
Kallo ɗaya Gwaggon Laraba ta yi wa Fahad a zuciyarta ta ce.
"Sidra kin yi wa kanki, domin wannan yaron miji ne na kece raini ne da da gudun wuce sa'a. Allah ya sa ya amince da zaɓin Nadra kada ya ki amince."
Ƙamshinsa ya cika falon ya karasa ya durƙusa ya gaishe su. Suka amsa ma sa gabaɗaya.
Shiru ne ya biyo baya, kafin Abba ya ce.
"Fahad."
"Na'am Abba."
"Ka yi waya da Sidra ce?"
"A'a Abba ba mu yi waya da ita ba."
"Tun yaushe kenan kuma wani magana kuka yi?"
"Wannan karon sai da gabansa ya faɗi sakamakon tambayar da aka yi ma sa."
"Lokacin ta ce mani za'ayi ma ta zanen lalle zuwa dare za mu yi waya, to a daren na yi ta kira ba ta ɗauka ba har yau na ji wayar a kashe ."
Cikin fargaba ya ce.
"Ina fatan dai tana lafiya ba wani abun ne ya same ta ba ko?"
"Tana lafiya."
Ɓoyayyar ajiyar zuciya ya sauke yana jiran dalilin kiransa.
Abba ya mika ma sa wasikar da ta bari ya karba ya fara karantawa.
Sai da ya mike tsaye tsabar dirgici da tashin hankali. Kafin ya kalli gabɗaya jama'ar dake falon ɗaya bayan daya, sai a lokacin ya lura da dukkansu a kwai rashin hankali a tattare da su.
"Innalillahi wa 'inna ilahir raji'un."
Kalmar da ya furta kenan idanunsa sun rikiɗe zuwa ja.
Cikin sanyin jiki ya zauna yana cewa .
"Sidra why why do this to me me ya sa kika amince tun farko? Ina kika je kika bar ahalinki cikin tashin hankali ba tare da yin tunanin halin da za su shiga ba."
Tashi ya yi yana kallon su idanunsa sun yi ja hatta farar fuskarsa sai da ta ji ja.
"Ku sanar da mutane kawai an fasa daurin auren , zan je ni ma na sanar da nawa dangin da abokan. Da ma su niyyar zuwa su dakata, ni ma zan dakatar da ma su niyyar zuwa. Duk da dai dama akwai wadan da za su zo daga ƙasar waje or ready suna hanya ba zancen juyawa tun da fly ne ba mota ba."
Ajiyar zuciya mai ƙarfi Abba ya sauke kafin ya ce.
"Ka bar su kawai su zo kar ka dakatar da kowa."
Da mamaki Fahad ke kallon Abba kafin ya yi magana Abba ya ce.
"Sidra ta gudu a ranar aurenka da ita, don haka zan maye ma ka gurbin ta da ƙanwarta Nadra idan har ka amince "
A matuƙar ruɗe Fahad ya kalli Abba ya na girgiza kai alamar a'a.
*Maman Ihsan ce*✍️
09065327995
Follow the TASKAR MAMAN IHSAN channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaiufWb3LdQYnzC2vH0z
*MAKAHO NE*
*NA*
Maman Ihsan ce ✍️
https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
page0️⃣3️⃣
"Sidra ta gudu a ranar aurenka da ita, don haka zan maye ma ka gurbin ta da ƙanwarta Nadra idan ka amince."
A matuƙar ruɗe Fahad ya kalli Abba ya na girgiza kai alamar a'a .
Sai a lokacin Ammi ta yi magana ta ce.
"Kai yaro Fahad kake ko, to bari na faɗa ma ka gaskiya auren Nadra da za mu aura ma ka gata muka yi ma ka, ka rubuta ka ajiye wata rana sai ka zo ka durƙusa kana yi ma na godiya, sannan za ka ce gara ma da waccen fitananniyar ta gudu ta bar ka ta gudu. Ka ga waccan da ta gudu masifar, girman kai, isa da gadara, sannan ga shegen taurin kai, ko ka aure ta da ƙyar za ta yi ma ka biyayya saboda ko anan gidan ba ta ganin kowa da gashi sam ba ta san darajar mutane ba. Amma yanzu Allah ya raba ka da ita za ka auri mai hakuri juriya da hangen nesa, uwa uba ilimin addini da tarbiyya."
Shi kam gabaɗaya Fahad ba ya ma gane me suke faɗa, don hankalinsa da tunaninsa na can wata duniyar ne daban. Ya kasa gane dalilin da zai saka Sidra ta aikata haka.
Muryar Abba ya dawo da shi daga duniyar tunanin da ya lula.
"Fahad ban yi ma ka tayin auren Nadra ba sai da na tabbatar da cewa na ma ka sakayya ne akan abin da Sidra ta yi ma ka, in dai har za ka iya zama da Sidra zaman aure to ina mai tabbatar ma ka sai ka fi jin daɗin zama da Nadra akan Sidra. Amma ba zan takura ma ka ba idan har ba ka son ka aure ta shi kenan mu bar maganar kawai Allah ya haɗa kowa da rabonsa na alkhairi."
Shiru ya yi yana nazari shi dai gaskiya ba ya jin son Nadra a Zuciyarsa. Kuma rayuwarta da ra'ayinsa ya sha banban da nata, shi ya fi son wayayyun mata masu aji kamar Sidra, ita kuma Nadra ga ta nan kamar wacce ba ta waye ba, shi tun da yake ma bai taba ganinta babu hijabi ba. Kullum cikin hijabi ko a cikin gida ma saka hijabi take yi kamar wata mai takaba, wani namiji ma zai ga surar jikinta har ta ja hankalinsa ya ce yana son ta, sannan ita baƙa ce shi kuma baƙar mace ba ta burge shi.
"Ba ka ce komai ba."
Sai a lokacin ya daga ya kalli Abba da Umma wacew ta kasa cewa komai, don tun da ya shigo bai ji muryar ta ba, ya san tashin hankali ya yi ma ta yawa. Sannan suna da karamci da mutunci, yanzu indai bai amince ba kamar ya kunyata su ne , domin tabbas da kunya sun tara jama'a a ce an watse ƴar su ta gudu ranar aurenta. Wanann ciwon zai dade bai bar zuciyarsu ba domin sun kunyata a idanun mutane, shi bai damu da kansa ba don an fasa aurensa iyayen ta ne abin dubawa .
Cikin sanyin murya ya ce.
"Na amince."
Gabɗaya suka saki ajiyar zuciya tare da saka ma sa albarka.
Tashi ya yi ya ma su sallama ya yi ficewarsa.
Abba ya kalli Ƙanwarsa ya ce.
"Kada a sanar da Nadra wannan zancen sai bayan ɗaura aure."
"Me ya saka haka to Yaya, tun da an ji ra'ayinta shi ma ya kamata a ki nata ra'ayin."
"Ba sai an ji ba, domin na san yarinya ce ita mai biyayya, ba ta taɓa tsallake magana ta ba, idan na ajiye kara na ce kada ta tsallaka ba za ta tsallaka shi ba. Ba ta da ra'ayi in da iyayenta muna so, don haka na hana a fada ma ta ne saboda tana da raunin zuciya, za ta shiga tashin hankali da damuwa wanda zai tona asirin abun da muka binne. A bar zancen akan cewa dama Nadra ce Amaryar ba Sidra ba, an yi mistake wajen saka sunan ne. Ko ita Nadra kada ta san cewa ba Sidra ta gudu ballantana hakan ya shafi walwalarta."
Jinjina kai Goggo Laraba ta yi ta fice daga part ɗin.
Kai tsaye ɗakin su Sidra da Nadra ta nufa, bakinta ɗauke da sallama.
Nadra tana waya da Ya Sayyadin ta, wato Mallamin su na islamiyya ke son ta suna son juna duk da cewar shi talaka ne, amma hakan bai dame ta ba.
Ganin Goggo Laraba ta ta ce.
"Zan kira ka Ya Sayyadi."
Daga haka ta katse kiran wayar tana kallon Goggon tasu.
_Ma'eesha_
Kallon Mallam Iro mijin Larai Dillaliya ta yi tana cewa.
"Mallam ina bukatar gidan hayan nan a yanzu ba sai Anjima ba. Amma gaskiya ina son na zaman mutum ɗaya ne kuma ya kasance akwai toilet da kitchen a ciki ."
"Hajiya idan na fahimce ki ginin zamani kike so ko? To gaskiya babu a unguwar nan. Gidan haya mai zaman mutum ɗaya da na sani akwai a ƙasa yaba can farkon layin kamar yadda na fada ma ki, sai dai ƙarami ne gidan, kuma ɗaki ɗaya ne tal ba barci bai da falo, sai kitchen a tsakar gida, toilet ma a tsakar gidan ba cikin ɗaki yake ba, kuma tsohon gida ne ba na zamani yadda kike so ba, idan dole sai ba zamani sai dai ki je ki nemi manyan dillalan gidan haya."
Cikin gajiya ta ce.
"Yanzu shi wanann da kake magana akwai a ƙasa nake so yanzu nan, amma ba na da kudin yanzu a ƙasa."
Kallon ta ya yi ya tabbata ba ta yi kama da wacce za'a ce miliyan ma ya fi karfin ta ba ballantana dubu hamsin.
"Hajiya ai wanan ba matsala ba ne za ki iya transfer."
"Account ɗina ya samu matsala sai dai na cire kuɗi da ATM card amma ba na iya transfer, sai na je banki akan matsalar."
"Yanzu yanzu ya kike so ayi dubu hamsin ne za ki iya zama ?"
"Idan ba za ka damu ba, ina son ka ka bani gidan yanzu, in sha Allah zuwa gobe da rana ka zo ka karbi kuɗin hayar gidan. Don ba kuɗi ba kuɗi hannuna 4k ne kawai."
"Ba damuwa mu je na kai ku gidan ga shi can farkon layin ba nisa gida uku ne ya shiga tsakanin da wanann gidan da aka ba makaho ɗaki kyauta kin ce ba kya iya zama."
Yana gaba suna bin sa a baya har suka wuce gidan uku, a na huɗun ne ta ga ya tsaya a ƙofar wani karamin gida dake da kofar fale-fale.
Sakata kawai ya cire ya tura kofar suna bin sa a baya .
Ƙaranin gida ne sosai ba wani wadancan tsakar gida. Kuka tsakar gidan ma ƙasa ne ba'a shafa siminti ba, hatta ƙofar ɗakin ma na fale-fale ne sai karamin window shi na ƙofar fale-fale ne.
Barandar ƙofar ɗakin dai siminti ne sai cikin ɗakin siminti ne sai dai an shafa siminti a bango.
Daga tsakar gidan ga toilet nan karami shi ma siminti ne a ƙasa, sai kitchen wanda ba wai gina shi aka yi ba, fale-fale aka buga aka killace wurin ya zama kitchen, aka masa ƙofa.
Godiya ta yi ma sa ya fice yana ma su sallama.
Akwatunan kayanta ta kalla ta kalli ko ina na gidan, kasancewar lokacin sanyi muke ciki gidan duk ya yi ƙura.
Ga shi ita ba wani aikin kirki yake yi ba a gidansu .
Masu aiki ke gyara ma ta daki da gado su wanke ma ta toilet, ayi ma ta wanki da guga, girki kawai take yi shi ka Mahaifiyar ta ce ta ce sai ta koya, gidan mijinta wata rana za ta tafi ba kowane namiji ke cin abincin masu aiki ba.
Ta ina za ta iya rayuwa ba wanda zai yi ma ta waɗan nan ayyukan?
"Dole na je banki gobe na samu na yi transfer ɗin kuɗaɗen dake cikin account ɗin na, za su iya kai miliyan goma. Zan nemi gida kamar na miliyan uku na siya mai kyau da zan iya rayuwa a cikinsa. Sannan zan ja jari na fara sana'a ko da Naira miliyan biyar ne, saura miliyan biyu da zai rage ma sai na siya kayan daki da kayan kitchen da abinci ma su sauƙin kuɗi."
Tana cikin wannan maganar ta ji karar shigowar sako a wayarta, sai da gabanta ya faɗi. Tana dubawa ta ga messages ne daga banki, jikinta na ruwa ta duba in da ta ga miliyan goma da ke account ɗin ta an kwashe su duka.
Salati ta saka tare da sakin wayar ta faɗi ƙasa, dubawa ta yi akan guiwar ya tana riskar kuka.
Tabbas ta san cewa mahaifinta kawai ya san Pin ɗin ta na cire kuɗi, kuma Mamy ce ta karbi ATM card ɗin lokacin da ta shigo ta ga tana tattara kaya. Kenan Mamy ta tambayi Mahaifinta Pin ɗin ya fada ma ta kenan, sun kwashe kudin don sun san za ta iya transfer suka riga ta.
Cikin kuka ta ce .
"Innalillahi wa 'inna ilahir raji'un, Allah humma ajirni fi musibati wa'a khalifni khalifan min ha."
"Shi ke nan Mamy kin ruguza Mani rayuwa Allah ba zai bar ki ba. Allah ga ni gare ka ka da kai na dogara ya zuljalalu wal ikhram."
Kuka take yi sosai ana kiran sallar magrib ta ga ya fita da sandarsa yana dogarawa ya fice daga gidan ba tare da ya ce ma ta koma ba.
Ta dade tana kuka kafin ta mike tsaye tana goge hawayenta ta ce.
"Daina kuka Ma'eesha ki daina ɓata hawayenki anan zaluncin da aka yi ma ki, ki rungume ƙaddarar da ta zo ma ki Allah yana tare da ke. Kuka ba bali ba ne ki shirya fuskantar sabuwar rayuwar da kika tsinci kanki a ciki."
Ita kadai take magana kamar wata zararriya.
Fitilar wayarta ta kunna kasancewar akwai duhu kuma ba wutar nepa.
Waige-waige take yi nan ta lura ashe akwai rijiya a gidan can karshen gidan
Handbag ɗin ta ta duba ta ciro karamin bottle of water wanda ta shiga shagon saloon da shi ba ta sha ba.
Alwala ta yi sannan ta duba cikin akwatin kayanta ta dauki Ɗankwali ta shimfida ta gabatar da sallar magrib.
Tana cikin addu'a aka kira isha'i ta tashi ta gabatar.
Tashi ta yi bayan ta yi addu'a ta nufi kofar fita gidan hannun ta rike da handbag.
Wani shago dake kusa da gidan ta tambaye shi in da ake fitar da tsintsiya da faka ya ce wata bayarabiya ce kuma tun karfe shida take rufe shago ta wuce gidan.
"Cikin damuwa ta ce .
"Ba wani wajen kuma?"
"Gaskiya sai dai ki bari da safe ."
"Yanzu nake bukata wallahi."
" Daren nan kuma?"
Ya tambaya yana mamakin yadda ta dage.
"Eh yau muka tare a wancan gidan, ya yi ƙura dole sai na share kafin mu kwana a ciki."
"Allah Sarki, bari na ara Maki na shagona zuwa da safe sai ki dawo Mani da shi ko?"
"To na gode."
Ya mika ma ta tsitsiyar da faka ta amsa ta tafi.
Har ta fara tafiya ta dawo ta fiye ruwar roba gida biyu ta wuce.
Ko da ta koma ta samu makaho tsaye a tsakar gidan hannunsa rike da sandarsa.
Ba ta kalli in da yake ba ta shiga cikin ɗakin.
Yanar gizo-gizo ta fara cire wa a silin da bango, sai da ta kakkaɓe sannan ta share ɗakin ta kwashe dattin cikin faka tana kai wa waje can karshen bangon gidan.
Sannan ta fito ta share simintin barandar ƙofar.
Tsakar gidan ta fara share wa, sai dai kasancewar kasa ce ba siminti ba ƙura ya addababe ta ta fara atishawa da tari sakamakon kuran.
Gefen mayafin abayar dake jikinta ta sa tana toshe hanci da daya hannun daya hannunta tana shafa har ta gama.
Fita ta sake yi tana tari da atishawa ta koma wajen me shagon.
Ganin akwai mutane ta tsaya gefe tana jiran a rage, bayan an rage ta samu ta karasa bakin kofar shagon.
"Hajiya kin dawo?"
"Eh dama ina son ne ka bar mun tsintsiyar nan da zuwa gobe sai na siya maka wata, saboda zan wanke toilet da shi ne kuma bai dace na dawo maka da ita ba bayan na wanke toilet."
"Ba damuwa ki rike duka na bar ma ki."
"To na gode sosai."
"Ina son ka ba ni detergent da hypo ne."
Daidai lokacin da wani mai siyar da robobi yake dawowa daga talla.
"Dakata mallam."
Sai ya tsaya ta karasa wajensa ta siya madaidaicin bokintin roba na 1k ta detergent da hypo dama ta siye ruwa Roba biyu ta kashe 1k ta zuba su a roba ta koma cikin gidan.
Handbag ɗin ta ta duba tana tafiya ta ga 2k ya rage ma ta cikin 5k da ga bar gidan da shi
Cire kayan ta yi daga cikin bokitin sannan sai ta karasa wajan rijiyar duk da ba ta da tabbacin cewa akwai guga.
Ta haska torchlight na karamar wayarta ya ga an daure guga jikin karfe dake jikin murfin rijiyar.
Abinda ba ta taɓa yi ba a rayuwar ta jan ruwa daga rijiya .
Kamilalliyar muryarsa mai cike da kamala ta s ji ya ce.
"Me kike ta yi a daren nan ne?"
Kamar ba za ta amsa ma sa sai ta ce .
"Ruwan zan ka a rijiya zan wanke ɗakin ne da kuma toilet, don ba zan iya amfani da su a haka ba."
"Bari na taya ki jar ruwan, ki je dakin sai na kawo ma ka."
Kallon mamaki ta masa ta ce.
"Da wake idanun za ka gani ruwan kuka har ka kawo mani?"
Ganin bai yanka ta ba kuma kamar ransa ya ɓaci ta wuce ta ba shi wuri."
Laluben rijiyar ya yi har hannunsa ya sauka akan gugar ya janyo ta ya ji nauyi, don dama igiyar na ɗaure a jikin karfe guga na cikin ruwa .
Sau uku ya janyo ya cika bokitin.
Ya kai tana mamaki ya karba ta wanke dakin bayan ta zuba hypo da detergent.
Sau biyar yana ciki bokitin yana kawo wa tana wanke wa tana sharo ruwan a waje, tana kashewada faka har ta gama ta wanke barandar.
Daga nan kuma ta nufi toilet ɗin, nan ma siminti ne irin toilet na tsuguno na gargajiya.
Sai dai ya kawo ma ta ruwa bokati uku ta ɗauraye toilet ɗin bayan ta wanke.
Tana kallon ikon Allah makaho da ɗibar ruwa a rijiya, yana rike da bokitin a daya hannu yayin da daya hannun kuma yake dogara sandarsa ta makafi.
*KADUNA*
Bayan Nadra ta katse kiran wayar da take yi da Ya Sayyadinta.
Cikin ƴar damuwa ta ce .
"Goggo har yanzu ban san in da Aunty Sidra ta shiga ba, tun dazu nake zagaye gidan nan, ko dai ta fita ne?"
"Eh kada ki damu ta je gyaran jiki ne kuma a'ba za ta dawo da wuri ba."
"Allah ya dawo ma na da ita lafiya."
"Amin ya Allah. Yauwa ki tashi yanzu nan direba zai kai mu wajen gyaran jiki da kitso."
"Waye za'a yi wa?"
"Da ni da ke."
"Goggo ke ma kin san ba na son kitso, saboda gashin kaina yana da yawa sosai, tsayin kitson ma yana damuna."
"Sai da an yi shi don haka ba baƙi mintuna Talatin ki yi breakfast ki fito."
"Toh."
Ta fada duk da ba ta son kitso sai dai ta dunƙule kanta kanta ta cusa cikin hula ko Ɗankwali. Amma kasancewar ta ba mai musu ko gardama ba ne ya saka ta tashi ta nufi bathroom don yin wanka.
Bayan ta fito ne ta shafa man ta mai sanyin ƙamshi ta shafa, wanda yake karɓar baƙaar fatarta mai sheƙi. Ta shirya cikin kayan doguwar rigar material ta saka. Sannan ta sanya dogon Hijabinta ta dauki handbag da wayarta ta fice bayan ta saka flat shoe.
Wayar Sidra take sake kira har lokacin switch off.
Part ɗin mahaifiyar ta ta nufa saboda tana son sake duba jikinta. Sai dai an fada mata Umma na part ɗin Abba. Kamar sa ta bi ta can sai ta fasa
Tana fitowa ta ga jama'a kowa na kallonta jama'ar dake falon dangin Abban ta ne.
Wata ma daga cikin su ta ce.
"Allah Sarki Nadra rabon dai ke za ki riga yar taki aure.?"
"Ni kuma ?"
Ta tambaya cikin mamaki. Matar za ta sake magana kenan sai Goggo Laraba ta dakatar da ita ta hanyar girgiza ma ta kai."
Hakan ya saka matar ta fahimci Nadra ba ta san da ita za'ayi auren ba.
Shagwaɓe fuska ta yi ta ce
"Goggo lalle kawai nake so jiya fa na je saloon aka gyara mun kai na "
Murmushi Gwaggo Halima ta yi ta ja hannun ta suka nufi ƙofar fita suka fice .
Direba ne ya kai su har shagon da Gwaggo Laraba ta sanar da shi
Bayan sun fita ya tsaya jiran su yayin da suka shiga.
Nadra ta zauna yayin da Goggo Laraba ta yi wa mai saloon maganar uzuri suna sauri kuma amarya ce za su je reception ne, take ta kira ɗaya daga cikin yaran aiki ta ta karasa yi wa wata lalle, ita kuma ta fara tsantsara wa Nadra lafiyyarnb zanen lalle mai dauker hankali.
*Maman Ihsan ce.*✍️
09065327995
Follow the TASKAR MAMAN IHSAN channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaiufWb3LdQYnzC2vH0z
*MAKAHO NE*
*NA*
Maman Ihsan ce ✍️
https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
page0️⃣4️⃣
Nadra ta zauna yayin da Goggo Laraba ta yi wa mai saloon maganar uzuri suna sauri kuma amarya ce za su je reception ne. Take ta kira ɗaya daga cikin yaran aikinta ta karasa yi wa wata lalle, ita kuma ta fara yi wa Nadra lafiyyarn zanen lalle mai ɗaukar hankali.
Kamar yadda ta nuna ba ta son kitson haka aka yi ba'ayi ma ta ba, sai sai gashin na ta ya sha gyara sai sheƙi da wani ni'imtacen ƙamshi take yi.
Abun da ya sake ba ta mamaki bayan na gama ma ta sai ta ga Mama Laraba ta ce su je ta shiga ciki za'ayi ma ta gyaran jiki.
"Mama wani gyaran jiki kamar wata Amarya?"
"Ai ke ƙanwar Amarya ce ya kamata duk abin za'a yi ma ta a yi ma ki?"
"Amma Mama ban taɓa jin in da aka yi haka ba."
Ganin za ta ba ta ma su lokacin kuma tana son su koma gida akan lokaci ya sa ka ta ce.
"Nadra ki shiga don Allah ana jiran mu."
"To Goggo Dinner da za'a yi ai sai bayan an ɗaura aure ne, karfe biyar aka..."
Ganin yadda Goggon nata ta tsuki fuska ya saka ta ja bakinta ta yi shiru, kasancewar tana da gudun ɓacin ran mutum.
Shiga ciki ta yi aka ce ta cire kayan jikinta. Aka ba ta wasu ƙananun kaya ta saka aka shigar da ita wani ruwa mai kumafa da ƙamshi.
Matar sai lallaɓa ta take yi tana cewa ban san har da gyaran jikin nan za'a yi ma ki ba da shi muka fara yi kafin muka yi lalle.
Ita dai ba ta ce komai ba sai faɗuwar gaba da take tsintar kanta a ciki.
_Makaho_
Sai da ya gama dibar ruwar yana daukar hannu daya da bokitin ruwa hannu daya da sandar dogarawa har ya gama.
Don sai da Nasara ta wanke banɗakin nan tas da detergent da hypo. Duk da cewar ba tile ba ne a toilet ba ne siminti ne.
Bayan ta gama ne ruwan karshe da ya kawo ta ajiye a banɗakin ta fito.
Duk abinda take yi hawaye bai tsaya daga tsiyayar da take a idanunta ba.
Kiran sallar isha'i ake yi don haka ya ce ma ta .
"Zan je masallaci."
Ba ta ce ma sa komai ba, shi ma bai jira cewar ta ba ya fice.
Tsayawa ta yi tana kallon ɗakin da take haskawa da wayarta, tana tunanin dakin zai dauki lokaci kafin ya bushe.
Kawatin kayanta ta buɗe ta ɗauki wani rigar sanyinta da yake da kauri ta san zai kashe ruwa, ta dauka ta dinga goge ɗakin har ya tsane ba ruwa a kasan simintin dakin.
Ɗankwalinta ta shimfida sannan ta fita ta ɗauro alwala ta fito ta gabatar da sallar isha'i.
Bayan ta idar ta tsaya ta yi addu'o'i tana kai kukanta ga Allah ya ba ta karfin zuciyar cinye wannan jarabawar.
Tana zaune ta ji ya yi sallama.
"Assalamu alaikum."
"Wa'alaiki Salam."
Ya dinga lalube har ya ji ɗakin sannan ya shiga bayan ya cire takalminsa a waje.
Shiru ne ya biyo baya har tsawon mintuna biyar ba wanda ya yi magana a cikinsu.
Maganar zuci da take yi ya fito fili ba tare da ta sani ba.
"Mamy ba zan yafe ma ki ba, kin aurar da ni in da kike ganin zan tagayyara, kin san cewa rayuwata za ta iya inganta ta hanyar amfani da kuɗaɗena. Kin amshe ATM card kin je kin kwashe kudint.
Makaho ya gyara tsayuwar sa tare da jingine sandarsa a jikin bango ya ce.
"Ba lallai sai ta ATM card kawai ba, ta yi multiple withdrawal (cire kuɗin sau da yawa a ATM daban-daban. Ko ta yi transfer ta amfani da USSD (*737# *901# da sai sauran su saboda ta san Pin ta samu damar yin hakan. Ba zai yiwu ta fitar da miliyan goma a ATM lokaci guda ba amma a cikin awa biyu za ta iya gama komai . Don idan har lissafi na ya yi daidai lokacin da kika fahimci ba kudin a cikin asusun ki an yi awa biyu da barin mu gidanku. Ta kwashe kudin ne ta hanyoyi daban-daban (ATM + Transfer kasancewar ta san Pin da bayanan asusun. Saƙonnin bankin sun nuna cewa kuɗin sun fita ne ta hanyoyi daban-daban a cikin awa biyu duk da sahihin Pin?"
Da mamaki take kallonsa kafin ta ce.
"Saƙonnin bankin sun nuna mani cewa ba ciro kudin aka yi ba, an kwashe kudin ne ta USSD da canja wuri (transfer) a cikin awa biyu duka da sahihin Pin."
Mamaki ya kama Ma'eesaha ta ce.
"Ya aka yi ka san irin waɗan nan tsarukan na banki?"
"Ba abin mamaki ba ne, don ni ma wasu na ji suna fira ina kwance a masallaci ina jin su."
"Su waye?"
" Da wani idanun zan gane su? Wata rana bayan an sallame sallah ɗaya yake faɗa wa wani an kwashe ma sa miliyan goma ta hanyar amfani da ATM card na shi to wannan da aka fada wa ya fadi bayanin nan da na maki."
Shiru ta yi dai tana kau da idsnun ta daga kallonsa, ita babban damuwar ta yadda idan Mallam Iro ya zo karɓar kudin haya wani bayani za ta ma sa kan dubu hamsin, bayan ya ma ta taimako a daren nan ba ba su gida. Su zauna.
Ganin ga lokacin na tafiya kuma tauna ya addababe ta ne ga karfe tara da ta yi ne ya saka ta mike tsaye ta ɗauki handbag ɗin ta sauran 2k ɗin da ya rage ta dauka ta rasa me za ta siyo da za su ci a daren.
Ita kanta ta san 2k ya yi kadan ya siya ma ta irin abincin da za ta ci ballantana ga makahon mijinta. Kuma idan ta kashe kudin duka da me za su yi breakfast da safe?
Don haka ta ɗauki ɗauki 1k ta fita da shi sannan ta bar 1k a cikin handbag ɗin ta.
Wajen me shagon dake kusa da gidan ta nufa, yanzu ma yana da jama'a. Don haka sai ta jira daga gefe har aka rage.
"Mallam nawa ne coke na roba?"
"Hajiya ɗari huɗu da hamsin ne."
Shiru ta yi idan ta siye guda biyu kudin ba zai isa ba, don haka sai ta ce.
"Ka bani guda ɗaya nawa kake siyar da bread. Biredin nan akwai na dubi daya da ɗari biyar, akwai na dubu daya da ɗari uku akwai na dubu daya, akwai na ɗari biyar dai kuma karamin nan na ɗari uku."
"Ka bani na ɗari biyar ɗin."
Ta amsa bayan ya saka ma ya a leda ya ba ta canjin Naira hamsin.
Tana tafiya tana hawaye, da a baya ne kafin yau canji ko nawa ne idan ta siye abu ba ta karɓar canji sai dai ta bar wa mai kayan. Amma yau ita ce da karbar canjin Naira hamsin.
Murmushi ta yi tana goge hawayenta ta ce.
"Alhamdulillah ala kulli halin."
Ta shiga gidan, sannan ta mai da ƙofar langa-langan ta rufe tare da saka sakata.
Shiga gidan ta yi kasancewar ta fita da hasken fitilar wayarta, sai ta bar shi cikin duhu shi kadai a ɗakin. Ita a tunaninta tun da ba gani yake yi ba ai ba amfanin bar ma sa haske da za ta yi.
Ta shafa ta same shi tsaye tana mamakin yanda ba ya gajiya da tsayuwa.
Tana kallon ɗakin yanzu ina za su kwanta ne, ba tabarma ba katifa.
Zaninta ta ɗauko guda biyu ta shimfiɗa ɗaya a in da take zaune, sannan ta ciro daya ta shimfiɗa ma sa a inda yake tsaye ta ce.
"Ka zauna a nan."
Kamar bai ji ta kuma ya ji ta ya san me take cewa .
Coke din ta ciro tare da bread ɗin, ta ɗebi Biredin kaɗan sannan ta ɗebi rabin cike ɗin cikin robar ruwa da ta yi alwala da shi.
Ta ajiye wanda ta ɗiba a gabanta sannan ta ajiye sauran da kuma ladar bread ɗin.
Coke dake cikin goran ta ajiye ma sa da robar coke din da ta ɗiba ta bar ma sa sauran.
"Ga bread nan da abun sha na ajiye ma ka."
Shiru bai ce da ita komai ba, sake kallonta ta yi tana maimaita abun da ta faɗa, nan ma shiru bai amsa ba, don haka ta yi shiru tana kallon da da mamaki, har shi zai dinga ji da kansa waye shi?
Murmushin takaici ta yi ta zauna a saman zanen da ta shimfiɗa.
Da kyar take cin bread ɗin don ba ta taɓa cin irinsa ba, daure wa kawai take yi ba wai don dadi ba sai don yunwa.
Haka ta cinye wanda ta ɗeba tare da coke ɗin, sannan ta janyo bottle wataer da ta siya guda biyu ta buɗe daya ta sha, sannan ta rufe ta ajiye .
"Za ki iya kwana a nan ɗakin kuwa?"
Wani kallo ta ma sa kafin ta ce.
"To ya zan yi kana da gidan da ya fi wannan ne da za ka kai ni na kwana?"
"Babu ni ma a masallaci nake kwana."
Ba ta ce komai ba ta daga kai tana kallon rufin ɗakin.
"Na kwanta a nan ne ko kuma na tafi masallaci da na saba kwana a ciki ne na kwanta?"
"Wannan kuma ra'ayin ka ne."
Shiru ya yi kafin ya ce .
"Bai dace na bar ki ki kwana a nan ke kaɗai a cikin wannan gidan."
"To idan ka kwana akwai abun da za ka yi mani ne? Ko za ka iya kare ni ne daga cutarwar wani abun?"
"Saboda ina makaho ba na gani ko?"
Da alama maganar ta soke sa a zuciya, bisa la'akari da yanayin amsar da ya ba ta ransa a ɓaci ko bai fada ba.
Sandarsa ya ɗauka ya fice daga cikin ɗakin ya nufi hanyar fita ba ta ce komai ba.
Tana ji ya fice daga cikin gidan.
Sai anan take ta ji babu dad'i, ga wani tsoro da ta ji ya dirar ma ta lokaci guda. Ko ba komai idan tana jin motsin mutum kusa da ita ai ya fi da ta zauna ita kaɗai.
Tsoron gidan ya kama ta ta mike zumbur ta fita daga cikin gidan ita ma tana cewa.
"Wallahi ba zan iya kwana ni kaɗai ba."
_Sidra_
Suna zaune a katafaren falon gidan, wanda kallo ɗaya za ka yi ma su ka gane wayayyun ƴan mata ne ma su ji da kansu.
Wata daga cikin su ta kalli Sidra ta ce .
"Yanzu ba za ki haƙura da wanann burin naki ki koma gida tun lokaci bai ƙure ma ki ba?"
"Khadijah kenan, ai ba zan koma gida ba har sai burina ya cika."
"Matsalarki kenan ki ce ke ba wanda zai fi ki sai dai ki fi kowa? Idan Allah bai yi za ki samu wanan ɗaukakar ba fa?"
Murmushi Sidra ta yi kafin ta ce
"Khadija duk abinda nake nema zan same shi , ban taɓa neman abu na rasa ba, Hakazalika wanann abun da na saka a gaba zan same shi in sha Allah."
"Eh watakila ki samu wancan abu amma za ki iya rasa Fahad da kika ƙwallafa rai sai shi, kodayake yanzu ba ki son sa tun da kuka gudu a ranar aurenku."
"Fahad nawa ne ni kaɗai ba wata mace da ta isa ta raɓe shi ban ga bayanta ba. Kuma ba wai don ba na son sa ba ne, sanin cewa yana masifar so na kuma na san zai jira ni na dawo ya sa na tafi ba tare da tunanin wata matsala ba, kuma iyaye na na san da zaran na dawo za su yafe mani don farin cikin gani na za su yi. Ke dai kawai Allah ya kai mu gobe mu bar garin nan na samu burina ya cika na samu ɗaukaka na dawo gida cike a alfahari."
Ta yi maganar tana Murmushi.
"Sady baby kin san na kashe wayata, ki ara mun taki wayar na kalli hoton masoyina Fahad."
Mika ma ta wayar ta yi tana karba ta kunna Data ta shiga Instagram, shafin Fahad ta shiga in da ta dinga kallon kyawawan photonsa a shafinsa nasa na Instagram.
Hoton da ya dora ta zuba wa idanu taba kallonsa. Sanye yake cikin tsadadden Suit baƙi a jikinsa, ya daura kafa ɗaya kan ɗaya, bakin hannunsa ɗaure tsadadden agogo.
Ya yi kyau sosai, ba ta san lokacin da ta sumbaci wayar ba
tana furta furta kalmar
"I love you Fahad."
Kafin ta rufe datar ta miƙa wa Sady wayarta.
"Dole ki haukace akan son Fahad domin ya hadu iya haɗuwa ga kyau ga kuɗi ga gayu ai kowace mace za ta so shi."
Wata ce ta faɗa a cikinsu
Nam dai suka cigaba da firar su akan Fahad, ita kuma tana jin dadi yadda ake cewa saurayin ta ya haɗu.
_Fahad_
Bayan ya yi parking motarsa ya fito daga cikin motar fuskarsa ta yi jajir.
Gabɗaya jama'ar dake falon kasancewar duka dangi ne bare ba su fara shigowa ba.
Muryar mahaifiyarsa ya ji tana cewa.
"Fahad."
Sai da ya ɗan tsaya kafin ya juyo duk suka kalle shi.
Cikin tashin hankali Mama ta mike tsaye ta karasa inda yake tsaye ta dafa kafaɗunsa da hannayen ta biyu ta ce.
"Daga gidan surukan naka kake?"
Kai kawai ya jinjina ba tare da ya yi magana ba.
"Me yake faruwa to?"
"Sidra ta gudu yau ba wanda ya san in da ta je."
"What! Ta gudu?"
Gabadaya falon shiru ya ɗauka yayin Mama ke salati.
Kalarsa ce ta ce
"Dama ba ta son sa ne?"
Ma ta ba ta amsa da cewa.
"Wallahi tana masifar son sa, maybe ma son da take yi ma sa ya fi nasa yawa. Ban san dalilin haka ba.
Ɓoyayyar ajiyar zuciya Farida ta sauke tana mai farin cikin jin amarya ta gudu. Ko ba komai yanzu dole ya aure ta.
Mahaifiyar Faridan ce ta ce.
"Ga irin ta nan ya je ya nemi aure gidan ƙananun mutane, ga dangi ana ta yi ma sa tallar ƴan uwansa ya nemi daya ya ce baya so. Ga Farida nan sabida son da take ma sa ta bar kowa nata ta zo ta tare a gidan nan sabida shi amma yake wulaƙanta ta.
"Kalarsa ta ce ai kuwa dole ya aure ta."
Daidai lokacin Baba ya fito daga part ɗin sa yana tambayar me ke faruwa.
Mama ta ma sa bayani shi ma salati ya yi yana cewa.
"Allah ya sa hakan shi ne mafi alkhairi."
Sai a je a kwaso kayan lefen da aka kai ma su ya ke ya siye uban kaya kamar wanda zai bude shago ko bai san zafin kudi ba.
"Aunty kar ku je Please."
Ya fada yana kallon ƙanwar mahaifiyarsa.
"Saboda me?"
"Sun bani hakuri sun ce na amince a maye mani gurbin ta da ƙanwarta Nadra."
Wani kuka Farida ta saka wanda kowa sai da ya kalle ta, ta haura sama tana kuka.
Baba ya ce.
"Kai kana son ƙanwarta ɗin ne?"
"Wallahi ni ma ban sani ba."
Ƙanwarsa ta yi caraf ta ce.
"Wallahi in dai Nadra ce ba ta da matsala, wallahi wacce kake so ita ce mai matsalar. Sai girman kai da izza ni dama wallahi ba da ɗin raina za ka yi auren..."
Mugun kallon da ya yi mata ya saka ta ja baki ta yi shiru, ita kanta Mama ta ji dadin hakan, don ta san su sau uku suna zuwa gidan kuma ta fi yabawa da hankali da nutsuwar Sidra."
"Yanzu aka amsa masu cewa za ka auri ƙanwarta?"
Jinjina kai ya yi ba tare da ya yi magana ba, Baba ya ce
"Allah ya sa hakan ya fi zama alkhairi, a cigaba da shirye-shiryen da ake yi.
Daidai lokacin da kiranta shigo wayar Fahad, ganin abokinsa ne ya saka ya fita zuwa harabar gidan, motoci guda biyu ne suka shigo.
Matasan samari ne ma su ji da kansu kimanin su takwas suka zo gidan.
Jagora ya yi ma su zuwa part ɗin sa, ta kofar baya ba tare da sun shiga part falon ba aika shiga part ɗin nasa.
Suna shiga ciki suka Zazzauna a falon yayin da shi ya shiga cikin bedroom ɗin sa.
Ganin yanayinsa ya sa suka san cewa a kai matsala, ba wanda ya yi magana har ya fito fuska ba walwala yake yi ma su barka da zuwa.
Musamman waɗanda ba a kasar nan suke ba daga wata ƙasar suka zo halartar bikin aurensa.
"Man lafiya kuwa?"
A jiyar zuciya ya sauke don ya san ba ɓoye ma su komai zai yi ba.
"Sidra ta gudu yau da safe."
Mamaki da kasuwa suka shiga, suna tambayar sa dalili.
Nan ya ba su labarin komai da ya faru har ƙanwarta da iyayen suka ba shi a madadin ta.
Nan aka shiga jajanta lamarin tare da kara ma sa ƙarfin guiwa akan auren Nadra, sannan suka bashi shawara ya cire damuwa ko saboda jama'a da za su zo daurin auren kada a fahimci wata matsala.
Haka suka dinga ba shi kwarin gwiwa har ya ɗan saki ransa suka fara shirye-shiryen zuwa ɗaurin aure.
_Nadra_
Lokacin da aka fito da ita daga ɗakin da aka shiga da ita sai da Gwaggo Laraba ta saki. baki tana kallonta.
Ba karamin kyau ta yi ba baƙar fatarta ta kara sheƙi da ɗaukar idanu.
Kudin aikinsu Goggo Laraba ta bayar suka wuce don har lokacin dire ba na jiran su.
Suna bayan motar Nadra ta sake gwada kiran wayar Sidra.
Har lokacin wayar a kashe.
"Gwaggo har yanzu fa wayar Aunty Sidra ba ta shiga, wani irin wurin gyaran jiki ta tafi da za ta kashe waya?"
Gwaggo Laraba dai ba ta ce ma ta komai ba, sai ta sake cewa.
"Maybe ma tana gida ta dawo ko?"
"Ba na tunanin ta dawo don wajan da nisa kuma ana dadewa kafin a gama. Yanzu mutane sun taru ba mu son a san cewa Amarya ba ta nan, don haka ke ce za ki saka kayanta a matsayin kece Amarya kafin ta dawo, kin ga ba kowa ke banbance sunan ku ba ko?"
Cikin rashin fahimta ta ce .
"Ni na kasa gane wannan al'amari ta ya zan shirya a matsayin ta bayan ba ni ba ce Amarya."
"Eh saboda mutane za'a iya ayi ta tambayar amarya ba dadi a ce ba ta nan, kuma Ummanki da Abba su ne suka ce a yi haka ko ba za ki bi maganar su ba ne?"
"Shi ke nan zan yi Allah ya dawo da ita lafiya."
"Amin yarinyar kirki ."
Daga haka suka ƙarasa gidan dake cike da jama'a, don rana ta yi gidan ya fara cika.
Ta part ɗin Umma suka bi suka shiga bedroom ɗin ta.
Duk da ta yi kwalliya amma akwai damuwa a tattare da ita.
Nadra ta rike hanjun Umma ta ce
"Umma ba ki da lafiya ko?"
Shafar gefen fuskar Nadra ta yi tana Murmushi ta ce
"Lafiya ta lau ki yi sauri ga mau kwalliya can tana jiran ki tun ɗazu ta zo."
Za ta sake wata magana Umma ta rufe ma ta baki ta ce.
"Sarkin magana je ki kar ki ɓata ma su lokaci."
Haka ta fita cikin sanyin jiki Umma ta bi ta da kallo tana goge ƙwalla.
_Makaho_
Yana zaune a barandar masallacin ya jingina da bangon masallacin ya daga kai sama.
Kamar daga sama ya ji ƙamshin turarenta, lalubar sandarsa ya yi ya na cewa.
"Ma'eesha ke ce?"
"Eh ka taso mu tafi gida."
Tausayinta ta kama shi amma duk da haka bai hana shi cewa ba.
"To ni da nake Makaho ba na gani wani amfani zan yi ma ki, tun da ba zan iya kare ki daga cutarwar wani abun ba."
Shiru ta yi don ita ma ta san dole ya ji ba dad'i. Tashi ya yi ya na rike da sandarsa ya yi gaba ba tare da ya ce komai ba, ita ma tana bisa a baya har suka shiga gidan ta mayar da kofar ta saka sakata ta rufe.
*Mamman Ihsan ce*✍️
09065357995
Follow the TASKAR MAMAN IHSAN channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaiufWb3LdQYnzC2vH0z
*MAKAHO NE*
*NA*
Maman Ihsan ce ✍️
https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
page0️⃣5️⃣
Shiru ta yi don ita ma ta sa dole ya ji ba daɗi .Tashi ya yi yana rike da sandarsa ya yi gaba ba tare da ya ce komai ba, ita ma tana bin shi a baya har suka shiga gidan ta mayar da ƙofar ta saka sakata.
Da lalube ya shiga cikin ɗakin, in da yake tsaye ɗazu can ya je ya kara tsaya wa.
Ta shiga tana rike da ƙaramar wayarta ta kunna torchlight.
Wanka take so ta yi sai dai ba ta iya wanka da ruwan sanyi, ga shi ba ruwan zafi.
Kayan jikinta ta cire ba ta damu da yana wajen ba saboda ta san makaho ne, towel ta daura ta nufi ƙofar fita.
"Ina kuma za ki ke dare ne yanzu fa."
Ba ta iya amsa ma sa ba sakamakon kukan da take yi na rayuwar da ta tsinci kanta a ciki. Sai dai kuka mara sauti take yi, idan ba wanda ya kalli idanunta ba to ba zai je tana kuka ba.
Banɗakin ta nufa kasancewar akwai ruwa da makaho ya cika bokitin na karshe ta ajiye.
Sai da ta rintse idanunta tana sakin ajiyar zuciya sannan ta iya yin wankan.
Tana fitowa ta same shi tsaya a kusa da ƙofar banɗakin, ba ta yi ma sa magana ba shi ma bai yi ma ta magama ya fito rike da bokitin ya nufi bakin Rijiya zai ɗebo ruwa.
Man shafar ta ta dauka bayan ta goge jikinta sannan ya shafa mai. Bayan ya shafa mai ta fesa turare na jiki wato body spray. Kayan barci ta saka riga da wando da wata hula mara nauyi ta saka.
Tana kallon ɗakin ta rasa ta ina za ta kwanta, ga ba gado ba katifa ballantana tabarma.
Tana tsaka da wannan tunanin sai ya shigo cikin ɗakin da sallama a bakinsa.
Ta amsa ma sa ba tare da ta lalle shi ba.
Yana shigowa daidai yana kawowa wajen shimfidar ta ta yi ma sa ta ce.
"Ga zanin da na shimfida ma ka nan ka zauna akai ."
Ba musu kuwa ya zauna ya tanƙware ƙafarsa, shiru dakin ya ɗauka ba wanda ya yi magana.
Bayan ta gama tunani sai ta koma ta rufe kofar dakin ta saka sakata.
Daidai lokacin nepa suka kawo wuta haske ya gauraye ɗakin gabaɗaya.
Kallon bread da coke ɗin da ta ajiye ma sa ta yi ta ga bai taɓa ba.
Taɓe baki ta yi sannan ta dauki karamin akwatin ta yi pilow da shi bayan ta kwanta.
Sai ta ji ya yi ma ta girma da yawa wuyanta zai iya ciwo.
Cire shi ta yi sannan ta yi pilow da hannunta ta kwanta.
Lokacin karfe goma sha daya na dare ne. Wayarta ta soma ruri ta ga lambar ba ta ƙasar nan ba ne, kuma ta san waye, katse kiran wayar ta yi tare da gyara kwanciyarta da sam ba ta ji fadinsa ba."
Sake kira aka yi har ya katse ba ta ɗaga ba, a karo na uku ne ta ambaci sunansa.
"Oh Allah Abdul ban san me zan ce ma ka ba."
Ta yi maganar tana goge ƙwallar tausayin kanta da take ji, take wani sabon kuka ya zo ma ta sai ta toshe bakinta tana yin sa a hankali.
Messages ne ya shigo wayarta ta duba still shi ne.
*Ina fatan jina cikin aminci farin cikina, na ga kina katse ma ni kira fatan ba wani laifin na aikata ba, Please ki amsa wayata ko hankalina zai kwanta.*
Tana gama karantawa ta katse kiran wayar, gabaɗaya ta kashe wayar ta koma ta kwanta tana hawaye.
Kamar sauro na jiran ta kwanta suka fara kai ma ta hari.
Abinda bai taɓa faruwa da ita ba kenan, sauro su addababe ta haka.
Ga cizon sauro ga kuma kukan sauro da suke yi ma ta a kunne.
Tashi zaune ta yi ta saka kuka tana kara sakin kuka kamar karamar yarinya.
"Ma'eesha lafiya."
"Wallahi sauro suke damuna ba zan iya barci a haka ba."
"Ayyah sorry, ba ni ɗankwalin kayan ki."
Ba musu ta zuge zip ta ɗako ta mika ma sa, ya matso kusa da ita ya karɓa.
"Ki manta to."
Kwanciya ta yi kamar yadda ya ce, ya dinga kore ma ta sauro da ɗankwalin. Tana jin kamar yana ma ta fifita har ɓaci ya ɗan fara daukarta kuma ya hadu ma ta da gajiya.
Haka makaho ya dinga yi wa Ma'eesha fifita har ta yi barci .
Tun karfe sha daya har biyu na dare yana zaune yake kore ma ta sauro.
A lokacin ta farka ta ga yadda ta bar shi haka yake yi ma ta fifita. Awa uku kenan yana abu ɗaya.
Tausayinsa ya kama shi cikin tashin murya ta ce .
"Ka kwanta ka yi barci na gode."
"Ba za ki iya barci ba idan na daina ku yi barci kawai, dama ni ban saba yin barcin dare ba."
Barcin ta cigaba da yi har aka yi kira sallar asuba.
Sai a lokacin ya ajiye ɗankwalin ya mike tsaye daidai tana buɗe idanunta.
"Da ido ta bishi ya fice daga dakin bayan ta dauki Sandarsa."
Bayan kamar mintuna goma ya shiga da alama alwala ya yi, sai ya ce .
"Zan tafi masallaci sai an yi sallah zan shigo."
Kai kawai ta jingina kamar yana ganin ta, ita ma tashi ta yi ta nufi banɗaki don ɗauro alwala.
_Nadra_
Tana shiga cikin ɗakin ta samu mai kwalliya na jiranta. Da sallama dauke a bakinta ta shiga in da ta samu ɗaiyar Gwaggo Laraba tare da mai kwalliya.
Duk da kasancewar ita ba mai son kwalliya ba ce kamar Sidra. Amma yanzu kam ba ta isa ta ce ba ta son kwalliya ba.
Hijabinta ta cire wani ni'imtacen ƙamshi na tashi daga jikinta.
"Bari na yi sallah lokacin sallah ta yi ."
Ba ta jira cewar kowa ba ta nufi bathroom don sauro alwala
Sai da ta gabatar da sallar sannan ta dawo kan su.
Zama ta yi dadai lokacin da wayarta ke ringing, ta duba ta ga Ya Sayyadinta ne ke kiran wayarta.
Murmushi ta yi za ta ɗaga sai Gwaggo Laraba ta karbi wayar ta kashe ta gabaɗaya ta ce.
"Ki tsaya a gama da sauri ba lokaci, kina gani gidan ya fara cika da jama'a ko?"
Mai kwalliyar ta buɗe akwatin kayan kwalliyar ta dubi Nadra ta ga ba ita ba ce ta kira ta, hasalima wacce ta kira ta fara ce ita kuma wanann baƙa ce. Kallon Gwaggo Laraba ta yi ta ce .
"Ko dai ba gidan ba ne?"
"Nan ne kar ki damu wannan ce za'ayi wa wacce ta kira ki Sidra ce ita ce ƴar wannan."
"Okay."
Ta faɗa a takaice ta fara yin aikin da ta kawo ta yi.
Nan ta tsantsara wa Sidra kwalliya wanda ya yiasifar yi ma ta kyau kamar ba ita ba.
Sannan aka ɗauko ma ta kayan Sidra wanda dama shi za ta saka a lokacin. Sai dai an ɗan sake ba tela ya sake buɗa ma ta faɗin kayan kasancewar Nadra ta fi Sidra diri da cikar halitta.
Karba ta yi ta shiru tare da taimakon mai kwalliyar ta shirya ta, ta yi ma ta ɗaurin Ɗankwali.
Nan ƴan uwa suka dinga ɗaukarta photo, ita dai har lokacin ba ta saki jiki ta ba, ta rasa dalilin dai zai saka a ce saboda Sidra ba ta nan ta maye gurbin ta. Ga shi an ce ba yanzu za ta dawo ba, ita dai addu'ar ta Allah yasa kafin karfe huɗu ta dawo, don idan ba ta dawo ba to ita kam ba za ta iya maye gurbin ta a wajen Dinner party ba. Ta ya ya za ta fito ta tsaya tare da Fahad kai ba zai yiwu ba ma.
Ita kadai take saƙa da warwara har ta ji ana cewa karfe biyu ya yi yanzu za'a daura aure. Tsintar kanta ta yi cikin faɗuwar gaba da tsoro.
_Fahad_
Kwance yake a bayan motar ya jingine bayansa da jikin motar, sanyi A.C da ƙamshin turarensa ke tashi a cikin motar.
Mukhatar da Aluyi sun saka shi a tsakiya, Kabir na zaune a gefen direba wajen me zaman banza
Suna ba shi baki tare da kwantar ma sa da hankali, don sun san yana cikin damuwa.
Har aka karasa kofar gidan surukan nasa bai buɗe idanunsa ba. Kowa ya fito ya bar sa a cikin motar.
"Ko sai mun fito da kai ne?"
Cewar Mukhtar yana kallonsa yana Murmushi.
"Hana Majidaɗi ka saki ranka ma na sai ka ce wanda aka yi wa auren dole?"
Harararaa Fahad ya yi tare da cewa .
"To idan ba auren dole aka yi ma ni ba na soyayya ne?"
Ya faɗa yana ziro fararen ƙafarsa wanda ke cikin takal ki ƙirar kamfanin Prada, takalmar baƙi ne.
Yana sanye da farar shadda gezna wanda aka yi ma sa aiki da baƙin zare riga da wando har da babbar riga. Ya fito yana gyara zaman babban rigarsa. Kansa sanye da bakin hula, hannunsa ɗaure da tsadadden agogonsa na Rolex Day-Date 40 (president watch) wanda ya zauna a hannunsa kamar don shi aka yi .
Duk wanda ya kalle shi zai gane shi ne angon domin ya sha banban da kowa a wajen.
Zuwan su ba jimawa aka fara shirye-shiryen ɗaurin auren.
Ɗaurin aure ne da ya tara manyan mutane na gida da waje. Manyan kusoshin gwamnati da da saraki da ma su mulki, har da shahararrun ƴan kasuwa .
Mutane suna ta yi wa Fahad fatan alkhairi ana taya shi murna, sai dai ya yi kokarin ganin damuwar da yake ciki bai shafi walwalarsa ba.
Yana nan zaune ba abinda yake yi sai tunanin Sidra sam ya kasa dalilin da ya sa ta aikata ma sa haka, duk ikirarin da take yi na tana son sa har za ta iya yin haka?
Bai ankare sa an ɗaura ma sa auren ba sai da ya ji an dafa sa ana taya shi murna.
Bayan an gama an tashi ana ta ma sa fatan alkhairi ana ɗaukar hotuna.
Daga nan Baba ya ce wa Fahad su shiga shi da abokansa su su gaida surukansa
Haka kuwa aka yi da shi da Mukhtar, Khabir da Aliyu suka shiga cikin gidan.
Falon Abba wanda shigowar su kenan shi da ƴan uwansa da abokansa.
Suka durƙusa suka gaishe su tare da yi ma su godiya da ba su ƴa da aka yi .
Daga nan kuma suka nufi main falon gidan, suka ga jama'a mafi yawansu ƴan uwa ne.
Tun da suka shiga gidan kansa a ƙasa yake har suka durƙusa suka gai da dangin Amaryar.
Kasancewar ba kowa ya san angon ba, kuma duk wani abin rabo da za'a raba wanda yake da photon Sidra da Fahad ba'a raba ba don kada jama'a su gan shi tare da Sidra a photo a fahimci wani abu.
"Ina angon yake?"
Wata Dattijuwa ta tambaya, Haidar ya nuna ma sa Fahad da ya sunkuyar da kai tun da suka shigo.
"Ma sha Allah kyakkyawan saurayi kuwa ta samu, Allah ya ba ku zaman lafiya mai ɗore wa da zuri'a ma su albarka. Yadda muka zo taron biki Allah ya sa nan da watanni tara mu zo taron suna."
Amin aka amsa ana sake rangaɗa guɗa wanda Fahad yake jin samuwar har cikin kansa.
Nan suka yi ma sa nasiha sosai sannan ya mike su ma abokan nasa suka mike, in da suka nufi part ɗin Umma.
Har lokacin tana cikin bedroom ɗin ta ita da wasu ƙawayenta.
Gwaggo Laraba dake falon ita da jama'a ce ta shigo don kiran Umma ta zo ga ango ba abokansa
Gabadaya suka fito ita da ƙawayenta, angwayen suka gaishe su suka sa ita dai Ummar karfin hali take yi, hade ɗaya damuwar halin da Nadra z ga shiga ciki take yi. Sanin irin son da Sidra ke yi wa Fahad, da yadda Fahad ke son ta. Ita Nadra da ba ce yana son ta ba ya za ta yi musamman da ta san halin Halin Nadra da dabi'arta ya sha banban da na Fahad.
Har suka gama gaisuwar suka tafi ta kasa magana tausayin Nadra kawai take yi .
Sallama suka yi ma su suka tafi .
A hanya ma kasa magana da juna su Fahad ya yi, domin su kadai suke ta firar su.
Suna isa gidan tun a harabar gidan ana ganinsa aka fara rangaɗa guɗa.
Abokan wasan sa na tsokanarsa bai bi ta kansu ba ya yi wucewarsa part ɗin sa.
Bai tsaya falo ba ya shiga bedroom ya mirza key ya rufe ya cire takalminsa da hularsa, sannan ya cire babban rigarsa ya cire rigar ciki.
Ya saura sai farin singileti a jikinsa. Agogon hannunsa ya kwance ya kwanta a saman tangamemen gadonsa.
.
Yana jin ana knocking amma ya share bai bude ba har suka gaji suka bar shi.
Abinci da aka ajiye masu da abun sha kowa ya fara ɗibar abinda ke ransa yana ci.
Suna nan sai ga wasu abokan na Fahad sun shigo cikin falon.
_Nadra_
Ta sha kyau iya kyau kamar ba ita ba, baƙar fatarta mai matukar kyau da ƙyalki sai shinning take yi.
Ga kayan ɗinkin riga da siket na less ta saka a jikinta, cikin kayan da Fahad ya siye wa Sidra ne wanda kudinsa zai kai kimanin dubu ɗari biyu. Sai arkar gold da ta saka kunne da wuya, har da warwaro da zobe.
Kasancewar ta ba mai son nuna jiki ba kuma less ɗin sun kama ma ta jiki ya saka ta saka babban gyale, duk da Hijabi ta so sakawa sai da Gwaggo Maimuna Yar Abba ta hana ta.
Shi ne fa ta saka babban Hijabin kasancewar ba kowa ya san cewa Sidra ba ta nan ba ya saka wasu da suka san ba Nadra ke aure ba ya saka suka tambayar ina Sidra take, ita kam sai sai ta ce ma su tana nan dawowa ta fita ne, wasu kuma sai ta sanar da su cewa ta tafi gyaran jiki ne.
Mamaki wasu ke yi ace yau ɗairin auren amma a ce ta je gyaran jiki, me ya saka ba ta yi da wuri ba
Ƙawar Nadra ɗaya ce wato A'isha Humaira, ta zo tana sanye da hijabi da niƙab a fuskarta.
Tana zaune kusa da Nadra suna firar yadda Sidra ya tafi wani wajen ta dade ba ta dawo ba.
Har lokacin sallah la'asar ta yi suka tashi Nadra ta shiga ta ɗauro alwala, sannan A'isha ta shiga.
Suna zaune suna azkar din yamma sai ga ƴar Gwaggo Laraba, wacce ba za ta wuce sa'ar Nadra ba ta shigo ta ce.
"Dama Mama ce ta ce na duba ko kin yi sallah mai kwalliya za ta zo ta yi ma ki kwalliyar zuwa Dinner party kafin ango ya ƙaraso tare za ku tafi da shi."
Zumbur ta mike tsaye tare da cewa.
"What?"
Wani kallo ta yi wa Salma kafin ta ce .
"Waye zai je Dinner party? Allah ya kiyaye, ni duk ire-iren waɗan nan wurare ban taɓa zuwa ba, duk wani taro in dai ba walima ba ce to ba zan tafi ba ballantana q ce na je a madadin Aunty Sidra, a jira idan ta dawo su je ta yi amma ba zan iya ba, I try my best but ba zan iya zuwa Dinner party ba."
Ta fada kamar za ta yi kuka.
Salma ta fit don ta sanar wa Mahaifiyar ta abinda ya faru.
_Fahad_
Har karfe uku da rabi bai fito ba, da ya ga lokacin sallah ta yi na ya shiga bathroom ya ɗauro alwala ya fito
Nan suka cigaba da firarsu .Ganin karfe uku da da rabi ta yi ne ya saka suka je suna knocking.
Daidai lokacin shi ma zai fito don zuwa masallaci.
Shi ma sai a lokacin ya lura da abokinsa Sadik daje ƙasar Canada ya iso.
Rungume juna suka yi sanan suka fita tare don duk sun yi alwala a bathroom dake falon.
Gabɗaya suka je masallaci, suka bi jam'i aka yi sallah.
Bayan an idar a tare suka fito suka koma ciki.
Daidai lokacin ne Yar Fahad Aunty Rahama ta shigo.
Dukkanin su suka gaishe da ita don duk sun san ta don Fahad na zuwa da su gidanta .
"Se Aunty Babba."
Cewar Sadik yana dariya .
Kallon su ta yi tana cewa.
"Lokacin Dinner party ya kusa ku je ku saka shi ya shirya bana son Afrikan time."
"Wai ya ce b zai je Dinner party din nan ba an fasa yi ."
"Akan me wanna ai zandan banza ne, dole a yi shi kamar yadda ka tsara tun farko, idan zai cire wa kansa damuwa ya rungumi ƙaddararsa."
Tana fadar haka ta shiga bedroom, yana zaune a bakin gado ya yi shiru cikin tunani
Dafa kafaɗarsa t yi ya ɗago kai ya kalle ta.
"Tashi ka shirya ku je ka ɗauki Amaryarka ku je wajen Dinner party."
Kwaɓe fuska ya yi kamar zai yi kuka, kafin ya buɗe baki zai yi magana ta ce.
"Ba na son jin komai, kuma na fahimci matsalarka, ka yi abinda na ce maka kawai."
Dole ya tashi ba tare da ransa ya so ba ya nufi bathroom, sai da ta ji saukar ruwa alamar ya fara wanka sannan ta fice.
Don dama su matan sun shirya zuwa reception ɗin .
_Ma'eesha_
Tana zaune a ɗakin tun da ta idar da Sallah ta yi azkar ba ta tashi ba, tana tunanin hanyar da za ta samu dubu hamsin ta biya kudin hayar gidan nan.
Ga shi ta yi ma sa alkawarin yau za ta bashi kudin.
Sallamar makaho ta ji ya shigo, ta amsa ba tare da ta kalle shi ba.
Shigowa ya yi ya zauna kafin ya ce .
"Ina kwana?"
Sai a lokacin ita ma ta ce ma sa .
"Ina kwana?"
"Kin tashi lafiya?"
"Alhamdulillah."
"Ya zaman hakuri da rashin barci."
"Ai Ni na yi barci kai ne dai ka kwana a zaune kana ma ni fifita ."
"Ke ma ba barcin kika yi ba, na ji kina ta motsawa."
Tunani take yi 1k ya rage ma ta idan ta siyo abin da za su ci shi kenan ba ta da komai.
Wani tunani ta yi kafin ta ce.
"Zan fita na je na siyar da wayata ko zan samu na biya kudin hayar gidan nan, kuma sauran canjin mu samu na cin abinci da dan abun buƙata da ya dace.
Shiru ya yi kafin ya ce .
"Idan kika siyar haka za ki zauna ba waya?"
"Ai wayoyina biyu ne da ni, zan siyar da babbar na rike ƙaramar ina amfani da shi. Na san kudin zai yi yawa . Don wayar miliyan daya da dubu ɗari biyar aka siya mun, ko miliyan ɗaya idan na siyar zan samu abubuwa da yawa da zan siya ma su sauƙin kuɗi, kamar karamar katifa labule kayan aiki da kuma kayan abinci."
Shiru ya yi kafin ya ce .
"Allah ya tsare ya dawo dake lafiya ya sa ki samu abin da kike nema."
"Amin ya Allah, bari na je kafin mai karɓar kudin hayar ya zo ya yi Mani sallama."
Tana fadar haka ta tashi dama rigar Abaya ne a mijinta baƙa. Rolling kanta ta yi da mayafin abayar sannan ta dauki handbag ɗin ta da wayoyin ke ciki ta fice.
*Maman Ihsan ce.*
090 5327995
Follow the TASKAR MAMAN IHSAN channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaiufWb3LdQYnzC2vH0z
*MAKAHO NE*
*NA*
Maman Ihsan ce ✍️
https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
page0️⃣6️⃣
Tana fadar haka ta tashi dama rigar Abaya ne a jikinta baƙa. Rolling kanta ta yi da mayafin abayar sannan ta dauki handbag ɗin ta da wayoyin ta ke ciki ta fice ba tare da ta san in da ta dosa ba.
_Aunty Rahama_
Tana fita daga part ɗin Fahad ta nufi part ɗin Mama.
Tun kafin ta karasa jikin kofar bedroom ɗin take ta jin muryar kanwar mahaifiyar su wato Hajiya Jummai mahaifiyar Farida.
"Ai shi kenan ku shirya ku tafi wajen Dinner ni dai ba in da zan je a yanzu haka. Don Yaya na gama gane cewa ba ki ƙaunata ba ki ƙaunar ƴata. Saboda Fahad Farida ta bar garin ta ta bar iyayen ta da kowa na ta ta dawo nan gidan da zama, ba don komai ba sai don ta samu kusanci da Fahad. Amma yaron nan ya yi kamar bai gane tana son sa ba. Da ta gaji da bayyana ma sa irin son da take ma sa ya wulakanta ta, kuma kina cikin gidan nan kun san me ke faruwa. Yanzu yarinyar da ya ƙwallafa rai a kanta an ce ta gudu ta bar gidan iyayen ta. Madadin ya zo a bashi ƙanwarsa ya aura shi ne ya je aka ba shi kanwar yarinyar ya aura ko? Sanadin Haka ga Farida can kwance na kasa gane kanta, ba sunan da take kira sai na Yaya Fahad."
Murmushi Mama ta yi tare da cewa .
"In ban da abin ki Jummai ai ni abun farin ciki ne a wajena a ce ga ɗana zai auri ƴar ƙanwata. Amma ya ce baya son ta to ya za mu yi? Ba dole a bar shi ya auri wacce take so."
Hajiya Jummai za ta sake wata magana ta ga Mama ya tsuke ma ta fuska tana dauke kai alamar ba ta son zancen, ga hankulan mutane ya dawo kansu.
Mama fita ta yi daga cikin dakin tana tarbar baƙin da ke zuwa a lokacin.
Kasancewar Yamma ta yi lokacin da za'a je Dinner party ya yi mutane suka fara shirye-shiryen zuwa Dinner party. Ankon fari da baƙi suka yi . White an black.
Mata suka sanya ankon nasu material fari da baƙi ne sun yi kyau sosai.
Bangaren Fahad ma zuwa lokacin samari ne cike da falon nasa, su na sun yi ankon yadi na fari mai ratsin baƙi a jiki.
Gabɗaya kalar yadin suka sanya ba abinda ke tashi daga cikin falon sai waƙar bikin Fahad da aka yi da sunan Sidra.
_Aunty Rahama_
Ita ma ta shirya cikin ankon nata ɗinkin doguwar riga, tana rike da hannun ƙaramar ƴar ta mai suna Zahrah yar shekaru uku a duniya.