← Book details Kuncin Zuci Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
CHAPTER 13 OF 32

Chapter 13

Kuncin Zuci Part 1 Complete Hausa Novel · about 10 min read

Rufe cab din motan Ahmad yayi bayan ya fito, ya jingina jikin motan hannuwansa cikin aljihun kayan jiikinsa yana kallonta, kauda kai na'ima tayi daga kallonsa Jin zuciyar ta tafara bugawa kamar yanda takeyi aduk lokacin da suka hadu, dan sunkuyar da kansa yayi yana dan murmushi sannan ya dago ya cigaba da kallonta baya ko kifta ido, sunanan tsaye babu me magana ya dan gyara tsayuwa zai fara takawa gurinta Laila ta fito daga gidan, Ahmad ya dauke kai daga kallon Na'ima ya kalli lailan, tuni ya dinke fuskanshi kamar bashi yake murmushi yanzu ba, tunkarosa Laila tayi, tadanyi wani irin kallo a na'ima sannan ta qarasa wajensa tana murmushi kamar bakin ta zai yanke tace "yaya..Ashe kazo, Ina wuni" babu yabo babu fallasa yace "Lafiya" Laila tace "ko inzo mu koma gidan tare" Ahmad yadan kalleta yace "tare mukazo ne?" Laila batasan lokacin da ta juya ta kalli Na'ima data juya kanta ba, ta sake juyawa tana kallon Ahmad tanajin kunyan tsinka ta dayayi a gaban na'iman, ta sake cewa "kaiii yaya" coldly Ahmad yace "su anty Amnah nazo dauka" kafin ta amsa sai ga anty Amnah ta fito daga gidan itada wasu wata guda biyu, qarasowa sukayi gurin motan daya daga cikin matan tace "Laila kema dake zamu koma kenan" Anty Amnah ta riga Laila amsawa da "a'a haba dai, ai salma bazata ji dadi ba, bayan ga 'yan uwanta can suma suna jiran ango da abokansa" matar tace "Gaskiya dai, ki jira abokan angon suzo su maidaku tukun" Shidai Ahmad tuni ya bude motan ya shiga, Laila ta matsa zasu bude kofan motan, anty Amnah ta juya ta kalli Na'ima dake Shirin shiga back seat tace "zo na'ima ki shiga gaba, mu saimu shiga bayan" Na'ima ba don ranta yaso ba ta bude gaban motan tashiga, Laila sai hararanta na'ima jin kamar ta maketa.
Shigan na'ima cikin motan qamshin turaren Ahmad mai sanyi wanda ya rikide dana motan ya bugeta, Jin proximity dinsu yayi kusa yasa ta Jin kamar ta fice daga motan amma haka ta dake idanunta na kallon gabanta, Ahmad yatada motan suka wuce aka bar Laila nan tsaye kaman ta fashe....
Na'ima tayi shiru kamar bata cikin motan, su anty Amnah sai hiransu suke, sunyi nisa anty Amnah tace "Habibtin mami yaushe hutun naku zai qare" cikin nutsuwa da sanyinta daya zame mata jiki na'ima ta amsa da "next week in Sha Allah anty" Anty Amnah tace "mu zuwa Monday zamu koma gaskiya" daya daga cikin matan tace "itama a England din take ne?"
Anty Amnah ta amsa da "Eh suna makaranta acan tareda nafisa, yarinyar Mami ce itama" matan suka amsa da "ma Sha Allah...Allah ya taimaka" ciki ciki na'ima ta amsa da Amin, Ahmad yadan juyo ya kalleta.

Isarsu gidan Mamin sun fito dukansu Anty Amnah ke tambayan na'ima "Anan zaki kwana ne kema" Na'ima ta dan jijjaga kai tace "yaya faruk zaizo mu wuce, zan dauki jakan mu a dakin husna ne" Anty tace "toh"
Wuce su tayi tabarsu nan suna magana da Ahmad din daya fito shima ya tsaya.
Shigarta falon ta tadda mamma ta fito daga kitchen din dake nan downstairs hannunta riqe da wasu ledoji, na'ima ta qarasa zata tayata riqe wasu, mamma tace "No, kibarshi daughter i can manage" duk da haka saida ta karba suka fara tafiya zasu wuce upstairs su anty Amnah suka shigo, mamma tace "kun dawo" a gajiye su anty Amnah suka zube akan kujera nan falon tace "mun dawo mamma, Ahmad ne yakawomu, kinganshi can waje wai bazai shigo ba da mutane gidan" murmushi mamma tayi tace "nima sai asuba yake shigomin tunda aka fara hidiman bikin nan" ta qarasa magana ta na maida hankali kan Na'ima dake tsaye tana jiran su gama magana tace "muje daughter", Sai da na'ima ta taya mamma ajiye ledojin inda yakamata sannan ta wuce dakin husna dauko jakarsu, wasu 'yammata tasamu a dakin kwance kan gadon kowacce na danna waya, dagowa sukayi suna kallonta
Na'ima ta wuce gurin wardrobe din husna ta dauko kayan nasu ko kallon gefen 'yammatan batayi ba, daya daga cikinsu tace "kema a garin nan kike ne?" Na'ima tace "Eh" suka sake tambayanta "ke yar'uwar su nafisa ce?" wannan karon gyada kai kawai na'ima tayi ta fice daga dakin aranta tana mitan "kamar ita kadai ce aka gani baquwar fuska a taron bikin, sai tambaya ake mata kaman wadda taje gidan jarida"
Tana sauqa stairs kiran faruk ya shigo wayanta ta dauka, daga dayan bangaren yace "Na'ima kinanan gidan Baban ne?" tace "Eh yaya" yace "to ki fito compound ki jirani ganinan na kusa qarasowa" ta amsa da "toh" sannan ta qarasa sauka tayi sallama da su anty Amnah dake nan falon basu tashi ba..
Fitanta wajen taganshi tsaye jikin motan hannunsa daya cikin aljihu dayan kuma yana danna wayanshi, Jin takun mutum yasashi dagowa ya kalleta
Na'ima tadanyi stiff a tsaye ganin Ahmad aranta tana tunanin "daman bai tafi ba"
Gyara tsayuwa yayi yana kallonta yace "Let me drop you" Na'ima bata bashi amsa ba ta tsaya kallonsa, sai da taga ya bude front seat sannan tace "daman yaya faruk yace...uh..uh..munyi waya.." Zuba mata idanu Ahmad yayi batasan lokacin da tafara tako wa gurinsa ba, miqa hannu yayi ya karbi jakan ta sake masa, ya zagaya ya saka a booth sannan ya dawo wajenta ya jira ta shiga motan ya rufe mata kofan sannan ya shiga driver seat.
Sun fito daga street din gidan Baban na'ima ta hango motan faruk zai shiga street din shikuma, juyawa tayi ta kalli Ahmad da hankalinsa na ga tuqinsa, dan juyowa yayi, tayi saurin kauda kanta..Saida sukayi nisa na'ima taji yace "Did i got something on my face?" Na'ima tadan juyo batareda ta kalli fuskansa tace "Na'am?" parking motan yayi a gefen street, na'ima batason lokacin da tadan ware idanu ta juya ta kalleshin ba, hada idanu sukayi yadan duqo kanshi kusada ita yana kallonta, na'ima jitayi isakan motan ya mata kadan kamar ta bude motan ta fice.. Ahmad yayi qasa da murya yace "meyasa bakyason kallona?" Na'ima ta kauda kanta tana kallon titi bata amsa ba, ji take muryanshi na karya duk wasu gabobi na jikinta, ya sake yin qasa da murya yace "Look at me Na'eemah" tadan juyo bata kalleshin ba cikin sanyin murya tace "meyasa zan kalleka" still yana kallonta shima cikin sanyin murya yace "because i want to see your eyes" batasan lokacin da ta juya kanta tana kallon window ba tana dan murmushi, shima murmushin yayi yace "Na'eemah kin maida ni sirikinki ko" ta jijjaga kanta tana cigaba da murmushin, shidai Ahmad duk ya lalace wajen kallonta, baisan meyasa yarinyar nan takeda effect me karfi akansa ba, ganin ba kallonsan zatayi ba yasa ya tada motan yace "shikenan, I'll have to try harder"

Babu wanda ya sake cewa komai a cikin su,Ahmad yana driving din jefi jefi zai juya ya kalli Na'ima da har yanzu kallon window take, amma zuciyoyinsu are aware of each other, wani irin yanayi suke shiga dukansu biyun aduk lokacin da sukayi gamo da juna and it seems like zuciyarsu kowannensu is reaching out to one another.

Bayan Ahmad yayi parking a kofar gidan Daddyn, na'ima ta bude qofan zata fita taji muryasa cikin sanyi yace "Gidan anty Amnah kuke zama a England din?" Na'ima ta dan juyo tace "a Oxford muke" ya sake cewa "when are you going back?" Na'ima tadan dago ta kalleshi kadan tace "sai next week thursday" bata jira Jin abunda zaice ba ta bude kofan ta fice, fita Ahmad yayi ya zagaya booth yaciro mata jakan sannan ya qaraso gabanta ya miqa mata, karba na'ima tayi cikin sanyinta tace "thanks for the lift" ya dan gyada kai yace "Take of yourself Okay" Na'ima ta gyada kai alaman toh sannan ta juya ta shige gate din gidan yana binta da kallo
Shigan ta falon ta samu Mami da samarin gidan suna hira, Mami tace "Sannu habibti, kun dawo?" Na'ima ta qarasa ta zauna kujeran kusada Mami tace "Eh Mami" Mami tace "Faruk dinne ya dawo daku?, don daga nan ya fita zaije daukoku " Na'ima tace "A'a..yaya Ahmad ne" Mami tace "ya kyauta kuwa, shine bai shigo" Na'ima batace komai ba, Abubakar yace "Ina anty nafisan" Na'ima tace "Su zasu jira abokan ango" dan dariya sukayi Al'ameen yace "ai abokan angon ma sun shigo uku a hannun su anty nafisa" Mami tadan kada kai tana dan dariyan itama tace "ai baby sai godiyan Allah" Abubakar yace "anty nafisa ba sauqi, sai sunjira sunyi cash out tukunna, suyi draining abokan angon tas" suka sake kwashewa da dariya shida Al'ameen, na'ima na kallonsu tana murmushi ta jijjaga kai tace "wannan maganan kamar a kunnenta" Abubakar yadan ware idanu yace "haba anty" Al'ameen bai fasa dariyan ba, Mami tace "rabu dasu, kije ki dan watsa ruwa ki huta tukunna" amsawa na'ima tayi da "toh" sannan ta miqe tana daukan jakarsu ta nufi upstairs

Shiganta dakin ta jefa jakan akan gado tacire veil dinta sannan ta danyi qaramin tsalle ta kife akan gadon tana sauke numfashin gajiya, tunanin moment dinta da Ahmad tafara, his eyes..his voice... Ta tambayi kanta, why is she luring herself into another trap? as if her past didn't teach her enough to stay way from any man, gamuwanta dashi baifi 'yan satittika ba, amma why is her heart reaching out to him aduk lokacin da suka gamu...yakamata ta farka daga wannan mafarkin da ta fara, ya kamata ta gina katanga tsakaninta da Ahmad don this is not the right time for it.
Tananan kwance taji anfara knocking door din dakin nata, miqewa tayi ta bude, Ido hudu sukayi da Faruk dake kallonta yace "Na'ima naje daukoki anty Amnah tace kin fita kina jirana kuma banganki ba" Na'ima ta dan kauda idonta daga kallonsa tace "Eh nafito...uhm..shine yaya ya dawo dani" yana kallonta yace "wani yayan?" tace "yaya Ahmad" kallonta yayi baice komai ba, Jin shiru yasa Na'ima dagowa ta kalleshi, ya kauda idonsa yace "Okay, saida safe" ta amsa da "toh" ta mayar da qofan ga rufe

Wanka tayi ta saka doguwan riga na cutton mara nauyi ta fice downstairs don neman abunda zataci, su Mamin still tasamu a falon suna hira Mami tace "Habibti ga abinci can na ajiye muku a kitchen" Na'ima ta amsa da "toh" ta wuce kitchen ta debo abinci tadawo tazauna nan aka cigaba da hiran da ita, sunanan zaune faruk ya sake shigowa shima ya samu wuri ya zauna, tambayansa na'ima tayi ko zata kawo masa abincin yace "Eh" ta miqe ta je ta debo masa shima, Abba ne yashigo falon yace "yau kunyiwa falona yaji kenan" sukayi dariya gabadaya, yasamu guri ya zauna aka cigaba da hiran dashi.
Sai qarfe tara nafisa suka shigo gidan itada husna, duk mutan falon suka dago kai suna kallonsu, qarasowa sukayi a gajiye nafisa ta zube kusada Mami, Al'ameen yace "sannu uwar bikin gaba daya" sukayi dariya, Abba yace "'yar'uwarku tadawo tundazu shine bazaku biyota ku dawo baki daya ba, me kuka tsayayi can gidan salman daren nan?" Nafisa ta marairaice tace "Abba itafa na'ima cewa tayi bazata jira rakiyan abokan angon ba" Abba yace "menene shidin?" Abubakar yace "charges dinsu suka tsaya karba Abba" Al'ameen ya buge masa kafada suna dan dariya, nafisa ta juya tana hararansu, na'ima dai jijjaga kai tayi tana murmushi, Husa tace "Abba daman ana jiran abokan ango suzo sai su maida kawayen amaryan gida" Abba ya sake cewa "to from henceforth, banason ku sake yin dare haka a ko'ina" suka amsa da "Toh Abba" Husna ta miqe tace "Mami akwai abinci" Mami tace "kije gashican a kitchen din" Nan suka zauna cin abincin nafisan da husna sukayi ta fayyacen yanda suka wanki abokan angon millions, Na'ima na mamakin yanda wasu basa jin nauyin cire kudi a familyn su nafisan.
A daren na'ima tazo kwanciya su nafisan suka shigo dakinta, hayewa kan gadonta sukayi nafisa nacewa "Bobo wani abu ya sake hadoki da Laila ne" Naima ta miqe zaune ta jingina jikin fuskan gadon tace "nafee me ya taba hadoni da ita nikuma" Husna tace "ke madai nafisa kinsan wannan
yarinya mara setin ko ba'a mata abu ba haka take" na'ima tace "wani abu ya faru ne?" Nafisa tace "babu komai"

Bintu Musa ce ✍️📚

ArewaPen
https://arewapen.com/book?id=690bd06dec64f173aa42354c

✨ KUNCIN ZUCI✨
Na Bintu Musa

WhatsApp group 👇
https://chat.whatsapp.com/JcjTYhJtKFh92V5nqhBk3z
Chapter 13 · 0% Book details