Chapter 11
Kuncin Zuci Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Suna cikin hira husna ta tambayi nafisa "Sis meya faru jiya nakiraki zan miki gulma naji wayanki a kashe?" Nafisa tace "na kashe ne dan nasan Umar zai kirani" husna ta jijjaga kai tace "Kai..keda guy dinnan dai bansan yanda zanyi defining kalan taku matsalar ba wallahi" Na'ima batasan lokacin da tafara yar dariya ba suka juya suna kallonta husna na dariya tace "Allah kuwa, yanda kikasan numfashinsu ne ajikin na juna, su basu rabu ba,Kuma matsalar taqi qarewa, Na'ima ta girgiza kai tace "karma ace sai sun rabun,dan banason su rabu but it's high time su fahimci a Ina matsalarsu take" Nafisa tace bazaku gane bane" Husna tace "toh fahimtar damu yanda zamu gane din, guy dinnan kunason juna amma kullum matsalar yau daban ta gobe daban, Bobo get a break please" Nafisa bata amsa ba ta cigaba da shan yogurt dinta, Salma ce ta shigo dakin Na'ima tadan kalleta ganin bazata wuce mate dinsu ba,ta qaraso bakin gadon ta tsaya tace "sannunku" suka amsa nafisa nacewa "amarsu kinsha qamshi" Salma tayi yar dariya sannan tacewa husna "dazu yaya Adam ya shigo yana neman ki bakyanan" husna tace "Eh munyi waya dashi ai" Salma ta juya tana kallon Na'ima tace "wannan da,daga Ina?" tsuka mai karfi husna tayi tace "kefa matsalata dake kenan, meye hakan kuma" nafisa ma ta juyo tana hararan Salma
Salma tace "Ha'a daga tambaya" cikin fusata husna tace "dalla to haka ake tambayan? Ji rainin wayo wai 'daga ina' " ta qarasa tana quoting maganar Salman
Nafisa tace "banida lokacinki Salma". Na'ima tayi tsuru tsuru ganin fada zai kaure akanta, tadan kamo skirt din jikin nafisa alamun su bari.
Sanin masifa da rashin hakurin husna da nafisan yasa Salma juyawa ta fice tana cewa "kwaji dashi" Husna ta dan daga murya tace "zamu hade ne, yar rainin hankali" tamaida hankalinta wajen nafisa tace "wallahi duk Laila ce take koya musu salon magana mai dauke da rainin nan,balle yanzu da tunda watan bikin yakama suke sintirin yawo tare, idiots" Nafisa tayi tsuka tace "can gidansun zamuje daga nan, Mami harda min gargadin batason fada" husna ta kyabe baki tace "Lailan ce sai kana mata zafi zafi" nafisa tace "ita tasa Salma ta fitar da wannan ankon mai kama dana 'yan iska ko?" Husna tace"Eh mana, ba don mamma tace sai nayi ba su sun isa su sa nayi wannan kayan ne" nafisa ta sake tsuka jin ranta yana neman baci tace "wace gulman kika kirani zakimin din jiya?" Husna tace "ke jiya Farha tasake hotunan wanda ta auran a insta" nafee tace "haba? Kice anata rugumtsumi babu ni kadai" husna tace "kedai bari..5k comments a jiyan fa".
Cikin zumudi suka fara maganganunsu da ya shafi Instagram wanda na'ima ba ganewa takeyi ba dan duk ta qosa su tafi kuma, jitayi duk ta taquru.
Bayan sunyi sallama dasu mamma akan zasu tafi ta basu humra da turaren kabbasa sukayi godiya suka je wajen anty itama,sama sama ta amsa musu, husna ta rakasu suka fice, sun fito compound din gida suka hango Ahmad sunkuye cikin boot din motarsa yana neman abu , husna tace "tab ga yaya can" nafisa tace "bari muje mugaisa" riqo hannun nafisa husna tayi tace "mamma takai qarata jiya, kuzo mu wuce tun bai ganmu ba" nafisa tace "to inya juyo fa,Kinga na'ima zo muje" ta qarasa tana riqo hannun Na'ima itama, Na'ima jitayi kamar tacewa nafisan "bazai juyo bama" amma ganin husna yasa bata fada ba, haka dai ranta babu dadi suka qarasa wajensa da har a lokacin yana duqe
Nafisa ce tafara magana tace "sannu yaya" ya dago ya rufe boot sannan ya juyo, idonsa bai sauqa kan komai ba sai Na'ima, suka sake hada Ido na'ima tayi saurin kauda kanta ganin yauma kallon ta yakeyi, jitayi kafafunta na neman gagara daukanta gashi saita ganta qarama a kasansa don Allah ya masa tsayi da qaqqarfan jiki,dauke idonsa yayi daga kallonta ya maida hankalinsa wajen qannen nasa yana amsawa cikin muryarsa dake hana na'ima nutsuwa yace "yauwa sannu nafisa,ya gida" nafisa ta amsa, cikin low voice na'ima tace "Ina wuni" tana kallon everywhere but not his face, dan motsa lips dinsa yayi wanda inba lura kayi ba bazaka kace murmushi yayi ba, yana nazarin yadda take escaping kallon fuskansa,ya amsa mata da "lafiya" Husa tace "'yar'uwarsu nafisa ce yaya, sunanta na'ima" ya sake kallon na'iman yana nanata sunan a zuciyarsa, a Fili yace "I know" Na'ima tadan juya ta kallesa ganin ya maida kallonsa wajen qannensa, within sakanni Sha biyar ta gama kallon fuskansa a sace sannan tayi saurin kauda kanta kar ya juyo, nafisa ta tambayi Ahmad "yaya Adam yana nan kuwa yaya?" Ya dan gyada kansa yace "yana falo" hanyar bangarensu Ahmad din suka nufa, yadan bi bayan na'ima da kallon gefen Ido kafin ya shiga motarsa ya tayar.
Sun tadda Adam yana Shirin fitan shima yana maqala link jikin hannun rigarsa, suka gaisa yace musu fita zasuyi shida Ahmad shima, tare suka fito ya musu sallama ya wuce gurin motan da Ahmad yake ciki suka fice, Suma tasu motar suka shiga suka bar gidan husna na nan tsaye ta daga musu hannu.
Isarsu gidan Daddy basu samu kowa a falo ba, basuyi azarbabin bin mummy part dinta ba nafisa tasa sukayi zamansu nan falon, basu jima da zama ba mummy ta sauqo cikin shiga ta alfarma cike da qasaita ta qaraso ta zauna tace "sannunku" suka gaisheta kan Na'ima na qasa dan tunda mummy ta shigo taji kwata kwata Aura din matar bai mata ba sam, suna gama gaisawa mummy ta dan kwala kira wata mai aiki ta shigo mummy ta umarceta ta kawo musu refreshments, sunanan zaune shiru babu me magana mummy ta kalli Na'ima sannan tace da nafisa"Ina kika samo wannan fa? Kawarkice?" Nafisa ta amsa da "A'a yar uwar muce" mummy ta qarewa Na'ima kallo tace "to sannu"
Laila ce ta fito daga wani qofa alamun kitchen ne a gurin, ta qaraso cikin falon ta zauna gefen mummy tana kallonsu sama sama tace "sannu fa" nafisa tadan juyo itama sama sama tace "sannu" Na'ima ta dago ta kalli Laila zata gaisheta atake ta rasa me zata fada ganin attachment da nails din da suke jikin Lailan yayi triggering wasu memories acikin brain dinta, tayi saurin sauqe idonta , Laila da kyawun na'ima took her by surprise ta kalli nafisa tace "wannan fa,daga Ina?" Nafisa najinta kuma bata kulata ba tacigaba da kallon tv kamar bada ita Lailan ke magana ba,mummy ce ta amsawa Lailan tace "nima yanzu nake tambayanta,wai 'yar'uwarsu ce,Inaga sai dai ta fannin Mamin tasu daga nijar"
Laila tasake tambayan nafisan tace "daga gidan baba kuke ne?, Salma tananan?" Sai lokacin nafisa ta juyo ta amsa coldly da "Eh" Laila tace "yaya Ahmad fa?" Nafisa tace "bansani ba nima" tasake juyawa tana kallon tv, na'ima dai kamar ta arce daga falon haka takeji, the atmosphere become toxic to her, daga mummyn har Lailan tuna mata suke da wasu mutane a rayuwan ta da batason tunasu kwata kwata yanzu. Jin Laila na tambayan Ahmad yasa mummy tace "ba kince zaki kirasa ba" cikin rashin da'a Lailan ta amsawa mummy da "toh nakirasa bai dauka ba yazanyi mummy, ni zuwa kawai zanyi dakaina in kaimasa cakes din,tunda bai dauki kiran ba" ta miqe tana turo baki ta sake suka ga wuce stairs su nafisa na bin ta da kallo, mummy tace "ke kika sani ai" ta sake kwala kiran me aiki tace mata "ki dan debo musu snacks dinda Lailan tayi" ta amsa da toh ta koma kitchen din tadawo dauke da different shape of small pieces of cakes ta ajiye gabansu, basu ko taba plate din ba nafisa ta fara miqewa tareda cewa mummy zamu wuce gida" na'ima ta miqe tana mata sallama mummy tace "toh aigaida gida" suka fice, isarsu wajen motansu nafisa tace "shegiya" juyowa na'ima tayi zagin yayi tooking dinta by surprise tace "haba nafee" adan fusace nafisa tace "ke bakiga yanda shegiyar ke mana magana bane, wallah badan Mami ta gargadeni akan fada da Laila ba da watarana sai na zubar mata da haqora tas" na'ima tadan ware Ido tace "toh ba gashi har mun gaisa mun fito ba, komai dan haquri ne ai, keda ba wani haduwa kukeyi bama" nafisa tayi tsuka suka shiga motan suka bar gidan tana mitan sai sun koyawa Laila hankali itada husna, itadai na'ima Allah Allah take su qarasa gida ta huta da wannan tunanin da suka zo ranta tun safiyar yau har zuwa barinsu gidansu Laila.
Bintu Musa ce ✍️ 📚
ArewaPen @Bintu Musa
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JcjTYhJtKFh92V5nqhBk3z
✨KUNCIN ZUCI✨
Na Bintu Musa
ArewaPen::https://arewapen.com/book?id=690bd06dec64f173aa42354c
Salma tace "Ha'a daga tambaya" cikin fusata husna tace "dalla to haka ake tambayan? Ji rainin wayo wai 'daga ina' " ta qarasa tana quoting maganar Salman
Nafisa tace "banida lokacinki Salma". Na'ima tayi tsuru tsuru ganin fada zai kaure akanta, tadan kamo skirt din jikin nafisa alamun su bari.
Sanin masifa da rashin hakurin husna da nafisan yasa Salma juyawa ta fice tana cewa "kwaji dashi" Husna ta dan daga murya tace "zamu hade ne, yar rainin hankali" tamaida hankalinta wajen nafisa tace "wallahi duk Laila ce take koya musu salon magana mai dauke da rainin nan,balle yanzu da tunda watan bikin yakama suke sintirin yawo tare, idiots" Nafisa tayi tsuka tace "can gidansun zamuje daga nan, Mami harda min gargadin batason fada" husna ta kyabe baki tace "Lailan ce sai kana mata zafi zafi" nafisa tace "ita tasa Salma ta fitar da wannan ankon mai kama dana 'yan iska ko?" Husna tace"Eh mana, ba don mamma tace sai nayi ba su sun isa su sa nayi wannan kayan ne" nafisa ta sake tsuka jin ranta yana neman baci tace "wace gulman kika kirani zakimin din jiya?" Husna tace "ke jiya Farha tasake hotunan wanda ta auran a insta" nafee tace "haba? Kice anata rugumtsumi babu ni kadai" husna tace "kedai bari..5k comments a jiyan fa".
Cikin zumudi suka fara maganganunsu da ya shafi Instagram wanda na'ima ba ganewa takeyi ba dan duk ta qosa su tafi kuma, jitayi duk ta taquru.
Bayan sunyi sallama dasu mamma akan zasu tafi ta basu humra da turaren kabbasa sukayi godiya suka je wajen anty itama,sama sama ta amsa musu, husna ta rakasu suka fice, sun fito compound din gida suka hango Ahmad sunkuye cikin boot din motarsa yana neman abu , husna tace "tab ga yaya can" nafisa tace "bari muje mugaisa" riqo hannun nafisa husna tayi tace "mamma takai qarata jiya, kuzo mu wuce tun bai ganmu ba" nafisa tace "to inya juyo fa,Kinga na'ima zo muje" ta qarasa tana riqo hannun Na'ima itama, Na'ima jitayi kamar tacewa nafisan "bazai juyo bama" amma ganin husna yasa bata fada ba, haka dai ranta babu dadi suka qarasa wajensa da har a lokacin yana duqe
Nafisa ce tafara magana tace "sannu yaya" ya dago ya rufe boot sannan ya juyo, idonsa bai sauqa kan komai ba sai Na'ima, suka sake hada Ido na'ima tayi saurin kauda kanta ganin yauma kallon ta yakeyi, jitayi kafafunta na neman gagara daukanta gashi saita ganta qarama a kasansa don Allah ya masa tsayi da qaqqarfan jiki,dauke idonsa yayi daga kallonta ya maida hankalinsa wajen qannen nasa yana amsawa cikin muryarsa dake hana na'ima nutsuwa yace "yauwa sannu nafisa,ya gida" nafisa ta amsa, cikin low voice na'ima tace "Ina wuni" tana kallon everywhere but not his face, dan motsa lips dinsa yayi wanda inba lura kayi ba bazaka kace murmushi yayi ba, yana nazarin yadda take escaping kallon fuskansa,ya amsa mata da "lafiya" Husa tace "'yar'uwarsu nafisa ce yaya, sunanta na'ima" ya sake kallon na'iman yana nanata sunan a zuciyarsa, a Fili yace "I know" Na'ima tadan juya ta kallesa ganin ya maida kallonsa wajen qannensa, within sakanni Sha biyar ta gama kallon fuskansa a sace sannan tayi saurin kauda kanta kar ya juyo, nafisa ta tambayi Ahmad "yaya Adam yana nan kuwa yaya?" Ya dan gyada kansa yace "yana falo" hanyar bangarensu Ahmad din suka nufa, yadan bi bayan na'ima da kallon gefen Ido kafin ya shiga motarsa ya tayar.
Sun tadda Adam yana Shirin fitan shima yana maqala link jikin hannun rigarsa, suka gaisa yace musu fita zasuyi shida Ahmad shima, tare suka fito ya musu sallama ya wuce gurin motan da Ahmad yake ciki suka fice, Suma tasu motar suka shiga suka bar gidan husna na nan tsaye ta daga musu hannu.
Isarsu gidan Daddy basu samu kowa a falo ba, basuyi azarbabin bin mummy part dinta ba nafisa tasa sukayi zamansu nan falon, basu jima da zama ba mummy ta sauqo cikin shiga ta alfarma cike da qasaita ta qaraso ta zauna tace "sannunku" suka gaisheta kan Na'ima na qasa dan tunda mummy ta shigo taji kwata kwata Aura din matar bai mata ba sam, suna gama gaisawa mummy ta dan kwala kira wata mai aiki ta shigo mummy ta umarceta ta kawo musu refreshments, sunanan zaune shiru babu me magana mummy ta kalli Na'ima sannan tace da nafisa"Ina kika samo wannan fa? Kawarkice?" Nafisa ta amsa da "A'a yar uwar muce" mummy ta qarewa Na'ima kallo tace "to sannu"
Laila ce ta fito daga wani qofa alamun kitchen ne a gurin, ta qaraso cikin falon ta zauna gefen mummy tana kallonsu sama sama tace "sannu fa" nafisa tadan juyo itama sama sama tace "sannu" Na'ima ta dago ta kalli Laila zata gaisheta atake ta rasa me zata fada ganin attachment da nails din da suke jikin Lailan yayi triggering wasu memories acikin brain dinta, tayi saurin sauqe idonta , Laila da kyawun na'ima took her by surprise ta kalli nafisa tace "wannan fa,daga Ina?" Nafisa najinta kuma bata kulata ba tacigaba da kallon tv kamar bada ita Lailan ke magana ba,mummy ce ta amsawa Lailan tace "nima yanzu nake tambayanta,wai 'yar'uwarsu ce,Inaga sai dai ta fannin Mamin tasu daga nijar"
Laila tasake tambayan nafisan tace "daga gidan baba kuke ne?, Salma tananan?" Sai lokacin nafisa ta juyo ta amsa coldly da "Eh" Laila tace "yaya Ahmad fa?" Nafisa tace "bansani ba nima" tasake juyawa tana kallon tv, na'ima dai kamar ta arce daga falon haka takeji, the atmosphere become toxic to her, daga mummyn har Lailan tuna mata suke da wasu mutane a rayuwan ta da batason tunasu kwata kwata yanzu. Jin Laila na tambayan Ahmad yasa mummy tace "ba kince zaki kirasa ba" cikin rashin da'a Lailan ta amsawa mummy da "toh nakirasa bai dauka ba yazanyi mummy, ni zuwa kawai zanyi dakaina in kaimasa cakes din,tunda bai dauki kiran ba" ta miqe tana turo baki ta sake suka ga wuce stairs su nafisa na bin ta da kallo, mummy tace "ke kika sani ai" ta sake kwala kiran me aiki tace mata "ki dan debo musu snacks dinda Lailan tayi" ta amsa da toh ta koma kitchen din tadawo dauke da different shape of small pieces of cakes ta ajiye gabansu, basu ko taba plate din ba nafisa ta fara miqewa tareda cewa mummy zamu wuce gida" na'ima ta miqe tana mata sallama mummy tace "toh aigaida gida" suka fice, isarsu wajen motansu nafisa tace "shegiya" juyowa na'ima tayi zagin yayi tooking dinta by surprise tace "haba nafee" adan fusace nafisa tace "ke bakiga yanda shegiyar ke mana magana bane, wallah badan Mami ta gargadeni akan fada da Laila ba da watarana sai na zubar mata da haqora tas" na'ima tadan ware Ido tace "toh ba gashi har mun gaisa mun fito ba, komai dan haquri ne ai, keda ba wani haduwa kukeyi bama" nafisa tayi tsuka suka shiga motan suka bar gidan tana mitan sai sun koyawa Laila hankali itada husna, itadai na'ima Allah Allah take su qarasa gida ta huta da wannan tunanin da suka zo ranta tun safiyar yau har zuwa barinsu gidansu Laila.
Bintu Musa ce ✍️ 📚
ArewaPen @Bintu Musa
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JcjTYhJtKFh92V5nqhBk3z
✨KUNCIN ZUCI✨
Na Bintu Musa
ArewaPen::https://arewapen.com/book?id=690bd06dec64f173aa42354c