Chapter 10
Kuncin Zuci Part 1 Complete Hausa Novel · about 9 min read
Daren ranan after maghrib suna zaune falon Mami itada nafisa, ipad ne a hannun Na'ima tana game don tunda suka dawo gidan bata bude wayanta dake ajiye cikin box dinta ba
Hira sukeyi jefi jefi da Mami dake zaune itama tana kallon hiran da akeyi cikin tv a tashar BBC, Mami tace da nafisa "baby kina jira sai nace kije ku gaisa da iyalan uncles dinki ko?" Nafisa ta dago daga danna wayan datakeyi kwance a kujera tace "Mami I thought tunda za'ayi bikin nan basai naje bafa" Mami na kallonta tace "ke tunaninki bazai baki kije ku gaisa kafin ku hadu a gurin bikin ba ko, for a week now na zuba miki Ido ai" nafisa tayi shiru batace komai ba Mami ta cigaba "gobe ki shirya kuje tareda Na'ima ku gaishe su and that's final" Nafisa ta amsa da "Yes Mami"
Mami ta maida hankalinta kan Na'ima data ajiye ipad din nata jin mamin na magana tace "Habibti, gobe kuje gidansu baba ku gaishesu" cikin sanyi na'ima ta amsa da "toh Mami in Sha Allah" bayan sunyi sallahn ishansu nan falon tareda mami,sauqa sukayi downstairs suka bar Mamin
Zama sukayi anan falon nafisa na turo baki ita a dole abunda Mami ta sa suyi bai mata dadi ba, Na'ima ta kasa shiru tana murmushi dan yanayin nafisan dariya ma yabata tace "Nafee it's just ziyara fa, what's the harm in that? Beside, ba kince yayun Abba bane sudin" Nafisa ta bata rai tace "Eh..amma Mami ce take taqurawa sai munje alhalin su ba wani zuwa gidan nan suke ba,
tunda muka dawo kinga yaran gidan sunzo gaisheta ne?.." Na'ima batace komai, Nafisa ta cigaba " har gwara ma su yaya Adam da anty Fatima sai dan dama dama husna, Amma 'ya'yan anty da mummy fa bawanda yake zuwa gaishe da Mami" Na'ima da bawai saninsu tayi ba, tanadai jin labarin su wani lokaci a bakin nafisan, tace "yaran anty sune twins da Salman da za'ayi bikin nata ko?"
Ganin na'ima ba wani saninsu tayi ba yasa nafisan cewa "Kinga yaya Ahmad,wanda sukazo rannan to shine babba a gidan baba, forget it bari na miki dalla dalla, su Abba su hudu iyayensu suka haifa that is Babba sai Abba sannan Daddy and last dinsu Anty Amnah, to gidan baba yanada mata biyu da mamma sannan anty, yaran mamma sune yaya Ahmad,Anty Fatima,Husna sannan hafsa saikuma yaran anty wanda Salma itace fari sannan twins safiyya da sumayya" Na'ima ta gyada kai alamun fahimta at the same time idanun Ahmad neh suka fado mata arai tayi stiff tana tuna yanda yake kallonta dazu.
Nafisa ta cigaba "sai gidan Daddy kuma, kinga yaya Adam shine babba wanda shi mahaifiyarsa ta rasu so practically he was raised by mamma tareda yaya Ahmad, Mummy ce Matar Daddyn ita kadai, ita kuma yaranta akwai anty murja,anty ummi sannan Laila ce autarsu, to anty Amnah kam kinsanta ai" Na'ima ta gyada kai tace "Nagane" nafisa tace "Mami itadai kayi ta zuwa gaishesu kamar wa'enda akayiwa mutuwa" Na'ima tayi murmushi tace "to ai 'yan'uwankune nafisa, yazama dole" Nafisa tace "ni ba gidan Baba bane banason zuwa, gidan Daddy ne, mummyn ce ba sauqi a lamarinta" yar dariya Na'ima tayi tace "kijiki sai kace wata sa'arki" Dariya itama nafisan tayi tace "bazaki gane bane"
Abba ne ya shigo tareda samarin gidan dawowansu daga masallaci kenan su na'ima suka gaishesu, nan kowa ya nufi dinning don yin dinner Mami ta sauqo itama, Na'ima ce tayi serving dinsu, don tun farkon zuwanta gidan Mami kan sata itama tayi serving a table din so that she could feel at home, hakan yazame musu al'ada ko ita ko nafisa sune servers in an zauna cin abinci, Abubakar ne ya bubbude flask din ganin babu tuwo yace "anty yau ba'ayi mutuminki tuwo ba" Na'ima data koma ta zauna tayi murmushi tace "Abu tsokala ko" Abba yana fara'a yace "tuwo abunso ne ai Abu" Abubakar yace "inaaa, Abba munfi gane yaren shinkafah" akayi dariya gaba daya.
Bayan sun gama cin abinci aka koma main falon ana hira, su na'ima suka tattare kwanikan suka wankesu a kitchen sannan suka koma falon aka cigaba da hiran dasu, Al'adan gidan ne yawanci dare ana zama ayi hira in ba dai ranan da Abba ya gaji ba ko kuma yanada wani muhimmin uzuri ba, Morning ne dai ba'a cika haduwa ba dan kowa yanada lokacin tashinsa, so breakfast ma kowa da lokacin yin nasa.
Washegari...
Na'ima ta fito daga wanka ta zauna kan stool nan gaban madubi, cire hulan wankan nata tayi tafara taje gashinta da ya kasance mai santsi da laushi, har wani curls yakeyi gashin nata tsabar laushi. Taje gashin take while tana kallon kanta cikin madubin, idonta ne yakai kan bakin wani tabo a gefen kafadanta gashinta ya dan rufeshi, ta qurawa gurin ido acikin mirror takai hannu tana tattare gashinta daya sauqa kafadunta har zuwa bayanta, wani babban tabo ne ya bayyana sosai a gurin mai kama da yanka anyi dinki, takai hannu ta shafa kanshi tana tuna dalilin Jin ciwon,komai yana dawo mata cikin brain dinta kamar yanzu glass din da aka jefon ya yanketa a wajen, idanunta ne suka ciko da hawaye takai hannu ta sharesu still wasu ma suka sake gangarowa,
Tana cikin share idonta Mami ta shigo dakin, Na'ima tayi saurin kauda kanta gefe tana goge idanun nata, qarasowa Mami tayi ta dafata tace "Na'ima" juyowa na'iman tayi tacigaba da share hawayenta , Mami tayi shiru tana kallonta sai kuma ta kama hannunta ta jata suka zauna bakin gado, cikin kwantar da murya Mami tace "Na'ima fadamin meke damunki?" Muryan na'ima na dan rawa tace "babu komai Mami" shiru Mamin tayi tana kallonta sai kuma ta sake cewa "Kinason komawa wajensu ne?" da sauri na'ima ta jijjaga kai tace "A'a Mami" sai kuma ga wasu hawayen, Mami ta dan rungumota tana shafa dogon gashinta tace "it's okay dear, it's alright..... everything is going to be fine kinji" na'ima dake jikin Mamin ta gyada kanta, mami tacigaba "I won't let things be repeated again in sha Allah, we will do anything to protect you,ki kwantar da hankalinki kiyi karatun ki kinji, this is your home too..talk to me duk lokacin da kike buqatan someone to talk to" na'ima ta dago daga jikin Mami tana gyada kanta mami tace "Now wipe those tears, you had so much ahead to live for in sha Allah, stop wasting your tears kinji" na'ima ta sake gyada kanta tace "toh mami" Mami tace "in bakyason fitan ma kiyi zamanki ki huta" tayi murmushi tace "A'a Mami zanje"
Mami ta shafa kanta tace "toh tashi ki shirya" miqewa na'ima tayi ta nufi wardrobe dinta Mami ta bita da kallo zuciyanta na karyewa ta miqe ta fita daga dakin
Na'ima na cikin saka kayanta nafisa ta shigo all set tace "har yanzu wai baki shirya ba?" Na'ima ta kalleta tace "gashi fa inayi" nafee ta zauna kan gadon tana kunna wayanta, bayan na'ima ta gama saka kayan ta fara neman veil din da zata yafa jikin light blue doguwar rigan jikinta na atamfa dayasha beadwork, ta bincika bata samu wanda ya dace ba acikin jerin veils dinta na cikin wardrobe din sai kawai ta jawo babban box dinta data dawo dashi daga England tafara bincikawa aciki, idon nafisa ne yakai kan wayar na'iman dake cikin kayan, ta miqa hannu ta dauka tace "Bobo ni lafiyanki kuwa da bazakiyi amfani da wayarki ba" na'ima dake abun gabanta tace "nafee to wa zan kira?" Shiru nafisan tayi saikuma tace "to aiba kira kadai akeyi da wayaba akwai abubuwa da dama" Na'ima na rufe box din tace "duk inayinsu da ipad plus laptop dina ai" bayan ta mayar da box din ma'ajiyansa ta qaraso ta karbi wayar nata dake hannun nafisan ta jawo bedside drawer ta jefa nafisa na binta da kallo.
Sun fito zasu tafi nafisa ta jefawa na'iman key tace "kiyi driving dinmu yau kema" na'ima tayi dariya tace "kinfa sani hannuna bai gama fadawa ba" nafisa data bude side din mai zaman banza tace "ai sai kinayin a hankali zaki qware din" Na'ima ta bude driver seat ta shige itama, haka tayi driving din nafisa na qara nuna mata yanda zatayi,Kuma balaifi ta iya din.
Isarsu gidan Baba bayan maigadin ya bude musu gate din babban mansion din na'ima tayi parking, ta fito tana dan bin gidan da kallo ganin yafi nasu mami girma, shigansu babban falon gidan suka samu babu kowa sai Mai aiki dake faman goge goge suka gaisa nafisa ta tambayeta ko su mamma na nan, ta amsa da Eh tana sashinta.
A falonta suka samu mamman, na'ima ta dan tsurawa kamilan Matar Ido ganin kamarta daya da Ahmad, bayan sun gaisheta ta amsa da "lafiya nafisa, yakuka baro Mamin ?" Nafisa ta amsa da "lafiya,tace agaisheki" Mamma ta amsa tana kallon Na'ima tace "yarinyar wajen Mamin naku ce wannan ko" nafisa tace "Eh mamma itace, sunanta na'ima" mamma tace "ma Sha Allah sannu na'ima,ya zaman qasar tamu, ba kamar nijar ba ko?" Na'ima ta dan sunkuyar da kanta tana jin yanayin ta wani iri aduk lokacin da aka dangantata da nijar,gurin da bata ma taba sanin inda yake ba balle taje, murmushi tayi tace "Alhamdulillah" bayan Mami tasa an kawo musu drinks da snacks suka dan taba hira gameda karatunsu sannan suka miqe nafisa tace "mamma zamu je gurin anty" mamma tace "toh nafisa" nafisa ta sake cewa "Husna tananan kuwa?" Mamma tace "bansani ba ku duba dakinta , dan dazu tacemin zataje gidansu course mate dinta" Nafisa ta amsa da to sannan tayi gaba na'ima ta bita suka fice daga falon mamma. Bayan sun fito da part din anty wacce suka gaisa da ita sama sama dan mace ce wadda nukurci ya cinye mata zuciya bata cika fara'a ba, batasan na'ima ba kuma bata damu da tambaya ba har suka fice, dakin husna suka shiga suka sameta kwance kan babban gadonta,tana ganinsu ta miqe tadanyi ihun murna ta riqo hannun nafisa
Nafisa ta fusge hannunta tace "dalla sakeni bayan kinsan nadawo amma ko kizo"
Husna tace "Bobo Dan Allah kiyi hakuri school ce ta riqeni amma kina raina wallahi" Na'ima ta kalli husna jin kalman "Bobo" a bakinta,dama nafisa ta fada mata sunan dasuke kiran juna ne itada Salma
Nafisa ta kyabe baki tace "bawaninan" dariya husna tayi ta juya tana kallon Na'ima tace "sannunki da zuwa" na'ima tace "yauwa sannu" ta qarasa zata zauna kan resting sofa data gani a dakin husna ta riqo ta tace "mu qarasa gadon yafi dadin zama" na'ima ta girgiza kai zata zauna husna ta riqe hannunta ta jata kan gadon da nafisa ta hakimce aka ta miqe kafafu harda cire gyale. Bayan sun gaisa husna ta kawo musu yogurt me sanyi ba cups haka ta miqawa kowannensu a hannu ta hau gadon itama riqeda daya, tana kallon Na'ima ganin itadai bata Santa ba ta juya tadan taba nafisa tana mata sign da Ido alamun "wacece wannan" a fili nafisa tace "Na'ima ce fa wadda nabaki labarin muna tare a Oxford" husna tace "ohhh cousin dinki dinnan?" Na'ima ta hada Ido da nafisa, waskewa nafisan tayi tace "Eh ita" Husa tace "Ma Sha Allah, she's so beautiful" ta juya ya kalli Na'ima ta sake cewa "sis, you're beautiful" Na'ima ta sauke idonta tana murmushin kunya batace komai ba, nafee ta dan daki kafadan husna tace "dalla kina sata kunya" husna tayi dariya tace "Aiiii...sorry"
Bintu Musa ce ✍🏻
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JcjTYhJtKFh92V5nqhBk3z
✨KUNCIN ZUCI✨
Na Bintu Musa
ArewaPen::https://arewapen.com/book?id=690bd06dec64f173aa42354c
Hira sukeyi jefi jefi da Mami dake zaune itama tana kallon hiran da akeyi cikin tv a tashar BBC, Mami tace da nafisa "baby kina jira sai nace kije ku gaisa da iyalan uncles dinki ko?" Nafisa ta dago daga danna wayan datakeyi kwance a kujera tace "Mami I thought tunda za'ayi bikin nan basai naje bafa" Mami na kallonta tace "ke tunaninki bazai baki kije ku gaisa kafin ku hadu a gurin bikin ba ko, for a week now na zuba miki Ido ai" nafisa tayi shiru batace komai ba Mami ta cigaba "gobe ki shirya kuje tareda Na'ima ku gaishe su and that's final" Nafisa ta amsa da "Yes Mami"
Mami ta maida hankalinta kan Na'ima data ajiye ipad din nata jin mamin na magana tace "Habibti, gobe kuje gidansu baba ku gaishesu" cikin sanyi na'ima ta amsa da "toh Mami in Sha Allah" bayan sunyi sallahn ishansu nan falon tareda mami,sauqa sukayi downstairs suka bar Mamin
Zama sukayi anan falon nafisa na turo baki ita a dole abunda Mami ta sa suyi bai mata dadi ba, Na'ima ta kasa shiru tana murmushi dan yanayin nafisan dariya ma yabata tace "Nafee it's just ziyara fa, what's the harm in that? Beside, ba kince yayun Abba bane sudin" Nafisa ta bata rai tace "Eh..amma Mami ce take taqurawa sai munje alhalin su ba wani zuwa gidan nan suke ba,
tunda muka dawo kinga yaran gidan sunzo gaisheta ne?.." Na'ima batace komai, Nafisa ta cigaba " har gwara ma su yaya Adam da anty Fatima sai dan dama dama husna, Amma 'ya'yan anty da mummy fa bawanda yake zuwa gaishe da Mami" Na'ima da bawai saninsu tayi ba, tanadai jin labarin su wani lokaci a bakin nafisan, tace "yaran anty sune twins da Salman da za'ayi bikin nata ko?"
Ganin na'ima ba wani saninsu tayi ba yasa nafisan cewa "Kinga yaya Ahmad,wanda sukazo rannan to shine babba a gidan baba, forget it bari na miki dalla dalla, su Abba su hudu iyayensu suka haifa that is Babba sai Abba sannan Daddy and last dinsu Anty Amnah, to gidan baba yanada mata biyu da mamma sannan anty, yaran mamma sune yaya Ahmad,Anty Fatima,Husna sannan hafsa saikuma yaran anty wanda Salma itace fari sannan twins safiyya da sumayya" Na'ima ta gyada kai alamun fahimta at the same time idanun Ahmad neh suka fado mata arai tayi stiff tana tuna yanda yake kallonta dazu.
Nafisa ta cigaba "sai gidan Daddy kuma, kinga yaya Adam shine babba wanda shi mahaifiyarsa ta rasu so practically he was raised by mamma tareda yaya Ahmad, Mummy ce Matar Daddyn ita kadai, ita kuma yaranta akwai anty murja,anty ummi sannan Laila ce autarsu, to anty Amnah kam kinsanta ai" Na'ima ta gyada kai tace "Nagane" nafisa tace "Mami itadai kayi ta zuwa gaishesu kamar wa'enda akayiwa mutuwa" Na'ima tayi murmushi tace "to ai 'yan'uwankune nafisa, yazama dole" Nafisa tace "ni ba gidan Baba bane banason zuwa, gidan Daddy ne, mummyn ce ba sauqi a lamarinta" yar dariya Na'ima tayi tace "kijiki sai kace wata sa'arki" Dariya itama nafisan tayi tace "bazaki gane bane"
Abba ne ya shigo tareda samarin gidan dawowansu daga masallaci kenan su na'ima suka gaishesu, nan kowa ya nufi dinning don yin dinner Mami ta sauqo itama, Na'ima ce tayi serving dinsu, don tun farkon zuwanta gidan Mami kan sata itama tayi serving a table din so that she could feel at home, hakan yazame musu al'ada ko ita ko nafisa sune servers in an zauna cin abinci, Abubakar ne ya bubbude flask din ganin babu tuwo yace "anty yau ba'ayi mutuminki tuwo ba" Na'ima data koma ta zauna tayi murmushi tace "Abu tsokala ko" Abba yana fara'a yace "tuwo abunso ne ai Abu" Abubakar yace "inaaa, Abba munfi gane yaren shinkafah" akayi dariya gaba daya.
Bayan sun gama cin abinci aka koma main falon ana hira, su na'ima suka tattare kwanikan suka wankesu a kitchen sannan suka koma falon aka cigaba da hiran dasu, Al'adan gidan ne yawanci dare ana zama ayi hira in ba dai ranan da Abba ya gaji ba ko kuma yanada wani muhimmin uzuri ba, Morning ne dai ba'a cika haduwa ba dan kowa yanada lokacin tashinsa, so breakfast ma kowa da lokacin yin nasa.
Washegari...
Na'ima ta fito daga wanka ta zauna kan stool nan gaban madubi, cire hulan wankan nata tayi tafara taje gashinta da ya kasance mai santsi da laushi, har wani curls yakeyi gashin nata tsabar laushi. Taje gashin take while tana kallon kanta cikin madubin, idonta ne yakai kan bakin wani tabo a gefen kafadanta gashinta ya dan rufeshi, ta qurawa gurin ido acikin mirror takai hannu tana tattare gashinta daya sauqa kafadunta har zuwa bayanta, wani babban tabo ne ya bayyana sosai a gurin mai kama da yanka anyi dinki, takai hannu ta shafa kanshi tana tuna dalilin Jin ciwon,komai yana dawo mata cikin brain dinta kamar yanzu glass din da aka jefon ya yanketa a wajen, idanunta ne suka ciko da hawaye takai hannu ta sharesu still wasu ma suka sake gangarowa,
Tana cikin share idonta Mami ta shigo dakin, Na'ima tayi saurin kauda kanta gefe tana goge idanun nata, qarasowa Mami tayi ta dafata tace "Na'ima" juyowa na'iman tayi tacigaba da share hawayenta , Mami tayi shiru tana kallonta sai kuma ta kama hannunta ta jata suka zauna bakin gado, cikin kwantar da murya Mami tace "Na'ima fadamin meke damunki?" Muryan na'ima na dan rawa tace "babu komai Mami" shiru Mamin tayi tana kallonta sai kuma ta sake cewa "Kinason komawa wajensu ne?" da sauri na'ima ta jijjaga kai tace "A'a Mami" sai kuma ga wasu hawayen, Mami ta dan rungumota tana shafa dogon gashinta tace "it's okay dear, it's alright..... everything is going to be fine kinji" na'ima dake jikin Mamin ta gyada kanta, mami tacigaba "I won't let things be repeated again in sha Allah, we will do anything to protect you,ki kwantar da hankalinki kiyi karatun ki kinji, this is your home too..talk to me duk lokacin da kike buqatan someone to talk to" na'ima ta dago daga jikin Mami tana gyada kanta mami tace "Now wipe those tears, you had so much ahead to live for in sha Allah, stop wasting your tears kinji" na'ima ta sake gyada kanta tace "toh mami" Mami tace "in bakyason fitan ma kiyi zamanki ki huta" tayi murmushi tace "A'a Mami zanje"
Mami ta shafa kanta tace "toh tashi ki shirya" miqewa na'ima tayi ta nufi wardrobe dinta Mami ta bita da kallo zuciyanta na karyewa ta miqe ta fita daga dakin
Na'ima na cikin saka kayanta nafisa ta shigo all set tace "har yanzu wai baki shirya ba?" Na'ima ta kalleta tace "gashi fa inayi" nafee ta zauna kan gadon tana kunna wayanta, bayan na'ima ta gama saka kayan ta fara neman veil din da zata yafa jikin light blue doguwar rigan jikinta na atamfa dayasha beadwork, ta bincika bata samu wanda ya dace ba acikin jerin veils dinta na cikin wardrobe din sai kawai ta jawo babban box dinta data dawo dashi daga England tafara bincikawa aciki, idon nafisa ne yakai kan wayar na'iman dake cikin kayan, ta miqa hannu ta dauka tace "Bobo ni lafiyanki kuwa da bazakiyi amfani da wayarki ba" na'ima dake abun gabanta tace "nafee to wa zan kira?" Shiru nafisan tayi saikuma tace "to aiba kira kadai akeyi da wayaba akwai abubuwa da dama" Na'ima na rufe box din tace "duk inayinsu da ipad plus laptop dina ai" bayan ta mayar da box din ma'ajiyansa ta qaraso ta karbi wayar nata dake hannun nafisan ta jawo bedside drawer ta jefa nafisa na binta da kallo.
Sun fito zasu tafi nafisa ta jefawa na'iman key tace "kiyi driving dinmu yau kema" na'ima tayi dariya tace "kinfa sani hannuna bai gama fadawa ba" nafisa data bude side din mai zaman banza tace "ai sai kinayin a hankali zaki qware din" Na'ima ta bude driver seat ta shige itama, haka tayi driving din nafisa na qara nuna mata yanda zatayi,Kuma balaifi ta iya din.
Isarsu gidan Baba bayan maigadin ya bude musu gate din babban mansion din na'ima tayi parking, ta fito tana dan bin gidan da kallo ganin yafi nasu mami girma, shigansu babban falon gidan suka samu babu kowa sai Mai aiki dake faman goge goge suka gaisa nafisa ta tambayeta ko su mamma na nan, ta amsa da Eh tana sashinta.
A falonta suka samu mamman, na'ima ta dan tsurawa kamilan Matar Ido ganin kamarta daya da Ahmad, bayan sun gaisheta ta amsa da "lafiya nafisa, yakuka baro Mamin ?" Nafisa ta amsa da "lafiya,tace agaisheki" Mamma ta amsa tana kallon Na'ima tace "yarinyar wajen Mamin naku ce wannan ko" nafisa tace "Eh mamma itace, sunanta na'ima" mamma tace "ma Sha Allah sannu na'ima,ya zaman qasar tamu, ba kamar nijar ba ko?" Na'ima ta dan sunkuyar da kanta tana jin yanayin ta wani iri aduk lokacin da aka dangantata da nijar,gurin da bata ma taba sanin inda yake ba balle taje, murmushi tayi tace "Alhamdulillah" bayan Mami tasa an kawo musu drinks da snacks suka dan taba hira gameda karatunsu sannan suka miqe nafisa tace "mamma zamu je gurin anty" mamma tace "toh nafisa" nafisa ta sake cewa "Husna tananan kuwa?" Mamma tace "bansani ba ku duba dakinta , dan dazu tacemin zataje gidansu course mate dinta" Nafisa ta amsa da to sannan tayi gaba na'ima ta bita suka fice daga falon mamma. Bayan sun fito da part din anty wacce suka gaisa da ita sama sama dan mace ce wadda nukurci ya cinye mata zuciya bata cika fara'a ba, batasan na'ima ba kuma bata damu da tambaya ba har suka fice, dakin husna suka shiga suka sameta kwance kan babban gadonta,tana ganinsu ta miqe tadanyi ihun murna ta riqo hannun nafisa
Nafisa ta fusge hannunta tace "dalla sakeni bayan kinsan nadawo amma ko kizo"
Husna tace "Bobo Dan Allah kiyi hakuri school ce ta riqeni amma kina raina wallahi" Na'ima ta kalli husna jin kalman "Bobo" a bakinta,dama nafisa ta fada mata sunan dasuke kiran juna ne itada Salma
Nafisa ta kyabe baki tace "bawaninan" dariya husna tayi ta juya tana kallon Na'ima tace "sannunki da zuwa" na'ima tace "yauwa sannu" ta qarasa zata zauna kan resting sofa data gani a dakin husna ta riqo ta tace "mu qarasa gadon yafi dadin zama" na'ima ta girgiza kai zata zauna husna ta riqe hannunta ta jata kan gadon da nafisa ta hakimce aka ta miqe kafafu harda cire gyale. Bayan sun gaisa husna ta kawo musu yogurt me sanyi ba cups haka ta miqawa kowannensu a hannu ta hau gadon itama riqeda daya, tana kallon Na'ima ganin itadai bata Santa ba ta juya tadan taba nafisa tana mata sign da Ido alamun "wacece wannan" a fili nafisa tace "Na'ima ce fa wadda nabaki labarin muna tare a Oxford" husna tace "ohhh cousin dinki dinnan?" Na'ima ta hada Ido da nafisa, waskewa nafisan tayi tace "Eh ita" Husa tace "Ma Sha Allah, she's so beautiful" ta juya ya kalli Na'ima ta sake cewa "sis, you're beautiful" Na'ima ta sauke idonta tana murmushin kunya batace komai ba, nafee ta dan daki kafadan husna tace "dalla kina sata kunya" husna tayi dariya tace "Aiiii...sorry"
Bintu Musa ce ✍🏻
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JcjTYhJtKFh92V5nqhBk3z
✨KUNCIN ZUCI✨
Na Bintu Musa
ArewaPen::https://arewapen.com/book?id=690bd06dec64f173aa42354c