← Book details Jinah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
CHAPTER 27 OF 27

CHAPTER 27

Jinah Part 1 Complete Hausa Novel · about 36 min read

~*Wilaya Writers association of Nigeria*~
(Home of peace & hospitality).💦we are here to educate and entertain the heart of readers,we are the best among the rest💦

Visit to like our page:https://www.facebook.com/Al-wilaya-writers-association-of-Nigeria-113198586763490/?referrer=whatsappwhatsapp

Ganin Jinah da kuma yanayin da suka shiga a yanzu, yasa Fally ɗorawa kan sa wasu tambayoyi da ya kasa samun amsar su : "Me yasa nake jin damuwa akan wata halitta da ko sanin ta ban yi ba? Me yasa nake jin ina bukatar ta a kusa da ni? Me yasa zuciya ta ke jin zafi domin na cutar da wadda kasheta nazo zan yi? Me yasa bana jin sheɗancin dake jiki na domin ina kusa da ita? Me yasa lokacin da jikin mu ya haɗu, nake jin zuciya ta kamar zata fashe? Me yasa ganin hawayen ta, nake jin tamkar ana zuba min ruwan zafi a jiki?"

Zafin da Jinah take ji ne ya dawo da ita hayyacin ta, iya karfin ta tasa ta ture Fally, sannan ta jawo lullubi ta rufe jikin ta, zuciyar ta na wani irin bugu. Kallon kallo suka shiga yi, nan Jinah ta gasgatawa kan ta da ba mafarki take ba.

-Fally?
Cewar ita cike da mamaki. Shi kuwa bai bata amsa ba.

-Wai mafarki nake ne?
Ta sake maimaitawa.

-Ke wacece a gare ni?
Ya bata amsa da wata tambayar.

-F..Fa..
Wannan karon rawan tsoro take, domin ta gasgata Fally ne da kan shi, sai dai ya manta ko wacece ita. Nan kalaman Infa suka dawo mata : "Zai iya tashi a sheɗani." Tsoron ta kara daɗuwa yayi.

Fally rage dan nisan dake tsakanin su yayi, ita ta ƙwalla kara sosai, wadda ta janyo hankalin Sarah, ƴaƴan mijin ta da kuma Dauda. Ba tare da wani tunani ba, suka kwasa zuwa dakin Jinah, nan suka ganewa idanun su, wani ƙato na kokarin cutar da Jinah. Kafin suyi wani ƙwaƙwaran motsi, ya ɓace da Jinah akan idanun su, Sarah da Nafisa zubewa suka yi sumammu. Jinah da wannan mutumin da basu san ko waye sun bace a gaban idanun su. Shi kuwa Abdul kasa motsawa daga inda yake yayi. Dauda ne kawai, ya karasa daidai wurin, hankalin sa a tashe. Nan ya shiga dukan bangon, da sa ƙafa yana kutufo da duk abinda ke kusa da shi. Yau ne yake bakin cikin rashin karfin kwato Jinah, baida wata dabara ta sanin inda zai ga Jinah, babu wanda zai iya taimakon sa a yanzu. A take ya tuna da ƴan biyu su zasu iya taimakon sa, sai dai daga baya jikin sa yayi sanyi, domin yasan da ƴan biyu na cikin gidan da su zasu fara kawowa mahaifiyar su ɗauki, ko kuma Infa yana ina? Rashin ganin su, bai nuna masa alamu mai kyau.

Fita yayi daga ɗakin ya bar sauran cikin yanayin rudu. A bakin ƙofar gida, Dauda ya shiga dukan kan sa da hannayen sa. Idan ka gani zaka ɗauka mahaukaci ne sai dai shi yasan me yake yi, domin yanzu wannan hanyar ce kaɗai zata sa ya samu wata solution; yana son ya fitar da Jinah daga kan sa, domin aljanin dake jikin sa ya dawo aiki. Yasan akwai haɗari yin hakan amma wannan ita kaɗai ce damar sa. Sai dai hakan ba sauki gare shi ba domin ya kasa fitar da hoton aljanin da ya gudu da Jinah daga cikin kan sa.

Daga karshe cuisine (kitchen) ya nufa, ya ɗauki wata ƴar ƙaramar wuƙa, ya saita daidai hannun sa, ya rufe idanu tare da cije hakoran sa, sannan ya cakawa hannun sa wuƙar. Wani ihun wahala ya saki, sai dai ya ci nasarar abinda yake son yi, zafin da yaji na dan lokaci yasa ya manta da Jinah, a take aljanin jikin sa ya ɗau aiki. A nan yaji babu alamar aljani cikin gidan. Babu Infa, babu ƴan biyu a cikin yankin gaba ɗaya. Tunanin sa na farko ya kai kan Hindu, ba ɓata lokaci, sai gashi ya bayyana a maɓoyar ta. Bai yi mamakin ganin ƴan biyu kwance a wurin, ba a hayyacin su ba. Ƙoƙarin zuwa yayi inda suke, Hindu ta daka masa wata tsawa :

-Me kake yi a nan?

-Ba ni nayi miki alƙawarin zan kawo miki su ba?!

-Na samu wata hanyar da tafi take. Wai ya ma aka yi bai kawar min da kai ba?

Waro idanu Dauda yayi, da mamaki.

-Wa kenan? Wani kika tura ya kashe ni?!

-A'a ya kashe ku dai! Domin baka da wani sauran amfani gare ni.

-Kenan shi ne ya ɗauke Jinah? Waye wannan?

-Hahah, sheɗani na, Fally!

-M..me? Bai mutu ba?

-Eh, amma kai yanzu zaka mutu.

Wani irin bugu zuciyar Dauda tayi. Tunani ya fara : A'a ba zan bari ta kashe ni ba, wa zai ceci Jinah da yaran ta? Hindu zata haɗa musibu da dama idan har tayi nasarar mallakar karfin ƴan biyu. Hannu yasa ya danna ciwon da ya jiwa kan shi dazu, take zafi yasa ya manta da Jinah, aljanin ya sake dawowa, Dauda ya ɓace daga wurin, sai dai cikin rashin sa'a yana dira inda yake tunanin ya gujewa Hindu, sai gata itama ta dira a wurin.

-Na roƙe ki kar ki kashe ni!

-Na ƙyale ka, kaje ka aikata wani abun a bayan ido na ko, ai nasan yanda ka damu da Jinah da ƴaƴanta.

-Zan fitar da su daga tunani na, sai aljanin dake jiki na ya dawo aiki, kuma kinsan irin biyayyar da yake miki.

-Bari nayi tunani...
Jim tayi kaɗan kafin tace "A'a!". Yatsu kawai ta ƙyasta sai gasu sun dawo maɓoyar ta. Tattaɓa jikin sa Dauda ya shiga yi, domin ya ɗauka ko har ta gama dashi ne.

-Kar ka damu, zaka jira na dan lokaci, zan ji da kai daga baya, yanzu zan ji da waɗancen ƴan biyun, domin gubar da na basu ba mai daɗewa bace.

Cewar Hindu. Kokarin motsawa Dauda yayi, amma yaji kamar an riƙe masa ƙafafuwa, nan ya fahimci tayi hakan dan kar ya sake wani yunkuri.

Wani jan ƙyalle Hindu ta shimfiɗa a kasa, sannan ta zuba wasu ruwa dake cikin wata kwalba da ta bayyana a hannun ta. Matsawa tayi kusan ƴan biyun, sannan ta dauko Ayu. Roƙon ta Dauda ya shiga yi da kar tayi, amma kamar ma yana zuga ta. Kwantar da Ayu tayi kan jan ƙyallen. Sannan ta shiga karanto wasu kalaman tsafi, wanda dakyar na iya gano kalmar : "Uwar gijiyar sammai da kassai!"

-Ki dakata Hindu, ki daina na roƙe ki! Dauda bai yi kasa a gwiwa ba, yana cigaba da roƙon ta, yana kuka kamar jinjiri sabon haihuwa dake jin yunwa. Duk da namiji ne shi, amma bai damu da irin kukan da yake ba, domin zafin biyu ya zamar masa, na farko saboda shi, yana ganin za'a kashe masa ɗa, sai kuma Jinah, wayyo Allah, idan aka fada mata ɗanta ya mutu, ba lallai bane ta iya jurewa ba.

Da taga ya fara isarta da raki. Wani surkulle Hindu tayi bakin Dauda ya rufe, ta mayar dashi kurma, babu abinda ya iya yi yanzu face hawaye. Wata ƙar karamar sanda ta ɗauko, wadda take da tsini kamar mashi. Hannun ta ta kai kan tsinin, nan take ya soketa sai ga jini. Wata mahaukaciyar dariya tayi. Da wannan karamar sandar ta zana croix (cross) bisa kirjin Ayu, kafin ƙyaftawar ido ta cakata a tsakiyar cross din dake kirjin Ayu. Ba ɓata lokaci sai ga wani bakin hayaki na fitowa daga ƙirjin Ayu zuwa jikin Hindu da ta ɗaga hannuwa sama cike da jin dadi.

*****

-Ka taimake ni, ni kuma zan amsa maka duk wasu tambayoyin ka.

Cewar Jinah. Mamaki ne ya kama Fally, tambayar kan sa yayi, ko dai karanta tunanin sa tayi. Sai dai ba haka bane, Jinah ta yiwa Fally farin sani, tasan idan har Fally yana da tambayoyin da ya kasa samun amsar su, ya kan yawaita motsa yatsun sa kamar mai jan carbi. Duk da yanzu alaƙar dake tsakanin su ta rushe, amma akwai wata alakar da tun kafin su je suyi aure akwai ta. Sun so junan su kafin aure, ya kula da ita tun kafin ta iya rarrafe, shi ya taimaka mata ta iya rarrafe, ya taimaka mata ta iya tafiya, ya kula da ita, ya saka kan sa a haɗari domin ta, ya sadaukar domin ta, ba sau ɗaya ba. Yanzu ya manta da ita, amma kuma zuciyar sa da ruhin sa sun san ita ko wacece. Akwai alaƙa mai girma tsakanin Jinah da Fally kuma babu abinda zai canja hakan.

-Ta yaya kike son na taimake ki?

-ƴaƴana, kafin ka shiga ɗaki na, nayi mafarkin suna cikin haɗari. Gashi yanzu ina tunani, kuma ina jin tsoron abi..abinda zai same su.

-ƴaƴan ki?

-ƴaƴan mu, ƴan biyu, Aya da Ayu!

-Su..suna tare da shugaba ta, Hindu.

-Mene? A'a! Ka cece su, nayi maka alƙawarin, zaka samu amsoshin tambayoyin ka. Hindu tana amfani da kai ne, kada ka yarda da wannan sheɗaniyar.

-Ke ma ba zan yarda da ke ba.

-Kalle ni cikin ido Fally, ka yarda da ni, dan Allah.

Dan jim Fally yayi kafin yace :

-Shikenan!

Da falar haka, ba'a dau wani lokaci ba, sai gasu sun bayyana a maɓoyar Hindu. Da isar su wurin, kasa ta fara girgiza, sama tayi jawur. Duk da wannan bai tayar da hankalin Jinah ba, dalilin tsinkayo ɗanta da tayi a kwance, jini na zuba, ga kuma wani mashi soke a daidai zuciyar shi. Numfashi ne ya fara gagarar Jinah, yin ƙarar ma ta kasa, lokaci guda ta koma tamkar marar baki. Ɗanta ya mutu, bata gasgata hakan ba, sai da taga ya koma normal yaro, da ba zai wuce shekaru uku ba. Idan jin zafi yana kashe mutum a take, toh da tuni Jinah ta jima da mutuwa domin zafin da take ji, ya wuce na misali.

Dauda yana nan a wurin, yana kallon ta, ba tare da ya iya matsowa kusa da ita ba, bare ya rungume ta, ya tayata bakin ciki, domin kafafuwan sa tamkar an saka siminti. Ba kuma zai iya faɗa mata : Kada kiyi kuka Jinah, kwantar da hankalin ki, kiyi juriya, Allah yana tare da ke, komai zai wuce, ke jaruma ce... saboda babu murya.

Shi kuwa Fally, ba tare da sanin dalili ba, wata shawara ta zo masa a kai, ya kashe wannan Hindun, abinda bai sani ba, shi ne : Karfin ta ya karu, ta yanda lokacin da yayi ƙoƙarin kai mata farmaki, naushi ɗaya tayi masa, sai gashi ya bugu da bango, bai yi ƙasa a gwiwa ba, ya sake kai mata wani farmakin. Wannan karon, a daidai ƙafafuwan Jinah ta jefo shi.

-Ki bar nan! Ni zan ji da ita! Ki gudu!

Cewar Fally, kafin ya sake miƙewa; Aya! Jinah ta shiga kiran sunan ƴarta, idanu ta shiga rarrabawa, cen ta hango ƴar tata a kwance. Wani karfi ne yazo mata, ta ɗauka a guje ta nufi wajen ƴarta, ɗaukan ta tayi ta rungume.

Gudu Jinah take iya karfin ta, ba tare da tasan inda take nufa ba, hawayen kuwa sun kasa daina zubo mata. Wata iriyar faɗuwa tayi, lokacin da Hindu ta dira gaban ta.

-Ita! Babu inda zata je!

A yanayin yanda Hindu tayi maganar, zai iya fasa kunnen mutum tsabar rashin dadi da tsoratarwa. Ita kan ta Jinah sai da taji zuciyar ta, ta canja bugu tamkar ana buga ganga. Fally ne ya bayyana a gurin tare da kaiwa Hindu wani mahaukacin naushi, a nan take su biyun suka bace, ita kuwa Jinah ta cigaba da gudun ta. Hakan ce tayi ta faruwa, kuma a ko da yaushe sai Jinah tayi tunanin tasu ta ƙare.

Fally ya gaji, kawai ya riƙe wuta ne, kuma kare kai kawai yake yi, domin ba zai iya hada ƙarfin sa da na Hindu ba, sake taso shi daga mutuwa, shi ya kara masa ƙarfi, sai dai ita Hindu nata ninkin ba ninkin nasa ne, domin cen dama ita mai ƙarfi ce, gashi kuma ta ƙara da na ɗaya daga cikin ƴan biyu, duk da ba duka ƙarfin Ayu ba ta kwashe, domin sai an ɗau lokaci kafin ta same shi baki ɗaya. Fally kam yayi ƙoƙari tunda har ya iya kai wannan lokaci yana gwabzawa da ita.

Amma yanzu, Karfin sa ya ƙare, ganin tsayuwa na shirin gagarar sa, ya shammaci Hindu, ya ɓace da Jinah, ya kaita gida. Sannan ya haɗa wata katangar tsafi a bakin kofar da ta hana Hindu shigowa.

-Gata nan zuwa! Gata nan tafe! Sheɗaniya!

Yo kan Jinah su Sarah suka yi, cike da ruɗu da farin cikin ganin ta, tuni suka dawo hayyacin su, sai dai yanzu kuma wani sabon tsoron ne ya shige su, jin abinda Jinah ta faɗa.

-Ku mu gudu daga nan, za.. Sauran kalaman nata suka tsaya a baki, ganin Fally ya faɗo daga sama a kan idon su. Kafin suyi wani yunƙuri tuni Surayya ta dira gaban su, cikin wata mummunar shiga. Jinah kara ƙanƙame ƴarta tayi cikin ƙirjin ta, Nafisa ta ɓoye bayan Sarah da Abdul.

Ita kuwa dan ta ƙara tsorata su, sai ta ɓacewa ganin su. Jinah ji tayi ana ƙoƙarin ƙwace mata ƴa ba tare da tana ganin ko waye ba, faɗa ta shiga yi iya ƙarfin ta domin ganin ƴarta tata bata bar jikin ta ba. Sake bayyana Hindu tayi rai a ɓace.

-Ya..ya aka yi na kasa raba ku?!
Hindu ta faɗa cike da ƙaraji da jin haushi.

-Ki bani ita, ni kuma zan rabu da ku!
Hindu ta sake faɗa, ita kuwa Jinah taƙi sakin ɗiyar. Hindu kallon Sarah kawai tayi, ita kuwa ta shiga kokowar ƙwatar numfashi kamar an shaƙe ta.

-Ki rabuta da ita, dan Allah!
Jinah ta shiga roƙon Hindu. Abdul ne ya taƙarƙare, ƙawadawa Hindu wani benci dake kusa da shi. Hakan da yayi kuwa, yayi nasar dawo da numfashin Sarah. Sai dai kuma hakan ya ƙara fusata Hindu, nuna hannu kawai tayi sai ga Abdul yayi sama, kanshi ya gauru da bango, ya faƙi sumamme.

-Abdul! Dukan su, suka kira sunan sa a tare. Da gudu yar uwar shi tayi kan sa tana jijjiga shi, tana kuka.

-Kin raba ni da ɗana, ki ƙyale min ƴata, ki bar min ita! Ki bar min ita!

-Ta kashe min dan uwa, mama!
Aya ta faɗa da wata ƙaramar murya, ta faɗi hakan ne ba tare da bakin ta ya buɗe ba. Da alama gubar ta fara raguwa.

-Ayu ya mutu mama, na sani, kuma naji a jiki na. Aya ta sake faɗa, har wa yau tana kwance jikin maman ta.

Hakan yasa Jinah ƙara shiga cikin ƙunci, kalamn ƴarta sun taɓa ta.

-Bani da lokaci! Ki bani ita yanzu kafin ta wartsake daga gubar, ko kuma na kashe su duka.

Hindu ta fada a fusace tana nuna su Sarah, Jinah kuka take iya ƙarfin ta, zaɓi tsakanin ƴarta ko Sarah, wadda ta zame mata kamar uwa, ƴar uwa, babbar aminiya... a taiƙace ita komai ce gareta. Sai kuma Abdul da Nafisa, mutanen nan biyu da take matuƙar so, waɗanda take jin kamar akwai wata alaƙa mai ƙarfi tsakanin su... Ta yaya zata iya wannan zaɓi.

-Ni ki ɗauke ni, ki rabu da su. Cewar Sarah. Wata mahaukaciyar dariya Hindu tayi.

-Babu wani amfani da zaki min!

-Mama, ki barta ta ɗauke ni. Cewar Aya, wadda maman ta ce kadai taji hakan, jin maman tata na shakku tace :

-Ki yarda da ni mama, komai zai tafi daidai.

-Ki ɗauke ta, amma kafin nan ki barsu su tafi, ki barsu su kai Abdul asibiti.

Cewar Jinah cike da dauriyar zuciya,tana mai miƙawa Hindu Aya. Ita kuwa Hindu tsabar murna, kamar ƙyaftawar ido, ta kai su Abdul asibiti, sannan ta dawo ba ɓata lokaci, ta ɗauki ƴar yarinya Aya, sai dai farin cikin nata bai wani ɗauki lokaci ba, domin Aya tuni ta ɓacewa ganin ta, daga kan hannayen ta.

-A'A! AHHHH!!! Hindu rai a ɓace, tayi wata kururuwa, ƙasa ta shiga girgiza, tuni guba aikin ta ya ƙare a jikin Aya, Hindu bata yi tsamanin abun ba zai mata sauki ba kamar yanda tayi fata. Ƙoƙarin kama Jinah take domin tayi garkuwa da ita, kafin Aya tayi wani yunƙuri, bata kai ga kudirin ta ba, taji wani abu na mata tafiya cikin jiki, kafin tayi ƙoƙarin kakkaɓe wannan abun, tuni har ya kai ga zuciyar ta. Wani masifaffen zafi ne taji da yabi kowanne sassa na jikin ta, razananniyar kara ta saki, kara mai bala'in karfi, karar da tafi wacce bokanya Karaba tayi, lokacin da Kiriku ya saka hakorin sa domin cire ƙayar dake a gadon bayan ta, wadda ta mayar da ita matsafiya.

Hindu durkushewa tayi kasa tana cigaba da ihun azaba, lokaci kaɗan Jinah ta hangi ƴarta, haƙoran ta datse kan ƙirjin Hindu, da take ta ihun neman taimako.

-Ki dakata Aya, cewar Jinah, sai dai bata da alamun dakatawa, kamar wani shedani ya shiga jikin ta. Da hakoran ta, ta yage duka fatar jikin Hindu, sannan ta saka hannun ta, ta fizgo zuciyar Hindu da tuni ta jima da mutuwa. Kuma Aya ta sani amma duk da haka bata dakata ba, kuma bata daina maimaita :"Ita ta kashe min dan uwa!" ba, hawaye na zubo mata. Ganin haka, Jinah ta taso ta janye ta, tare da rungume ta, tana lallashin ta.

-Jinah.
Dauda ne da ya karaso wajen ya kira sunan ta. Hannayen sa dauke da gawar Ayu.

-A'a, a'a, ba zan iya jure kallon sa, ba zan iya ba!
Jinah ta faɗa tana kuka, ganin gawar ɗanta. Ɗaki Dauda ya wuce, ya kwantar da shi. Sannan ya dawo da niyyar lallashin Jinah. Kukan Jinah ƙaruwa yayi da ta tsinkayi Fally a kwance dan nesa da ita, rarrafawa tayi wajen sa, ta shiga kokarin tashe shi.

-Ka tashi Fally, kar ka barni, ba yanzu ba, ɗan mu ya mutu, kar ka tafi ka barni!

-Bai mutu ba, cewar Aya.

-Toh me yasa yaki tashi?

-Gangar jikin sa ce ta mutu, amma shi yana raye.

"Toh meye banbanci ya mutun kenan." Jinah ta fada cikin ranta, tana mai shashantar da maganar yar tata, kafin ta cewa Dauda ya tafi da Aya, su ɗan barta ita kaɗai na wani dan lokaci.

Dora kanta tayi kan ƙirjin Fally, ta shiga magana magana ita kaɗai :

-Ku biyu a rana ɗaya, ta fada tare da jan dogan numfashi. Ka kula min da Ayu na idan kuka haɗu, na san shi da taurin kai, amma kar ka dukan min shi, yaron kirki ne, ka faɗa masa ina son shi, da dukan zuciya ta, ba zan taɓa manta shi ba, ba zan taɓa mantawa da ku ba.

-Har yanzu ina nan!
Kamar daga sama taji anyi maganar.

-Fally?
Ta shiga waige waige.

-Ruhina har yanzu yana nan Jinah!
Ya sake maimaitawa, gangar jikin da ke gaban ta, babu alamun rai a tare da ita, bata numfashi, bata magana, amma gashi tana jin muryar sa.

-Toh ka tsaya a nan dan Allah, kada ka tafi, jin alamun ka ya ishe ni, ka tsaya a tare da ni.

-Ba zan iya ba, ko ba jima ko ba daɗe dole zan ɓace na har abada.

-Kada kace haka, b..ba..bana son..

-Ina tune da komai Jinah, ta yaya zaki so kara kasancewa da ni bayan abubuwa nai miki? Kamata yayi ki tsane ni.

-Ban sani ba, kuma bana ma son na sani, idan ba soyayya ba, babu abinda nake ji game da kai...

-Jinah! Bata karasa abinda take son faɗa ba, sakamakon jin Dauda da ya ƙaraso wajen shi da Aya, ya kira sunan ta.

Lokacin da Jinah ta ɗaga idanu ta kalle shi, ya riƙe ƴar wuƙa a hannun sa, ya saita ta daidai zuciyar sa. Yanayin fuskar sa ya canja, kafin tayi wani yunkuri tuni ya cakawa zuciyar tashi wuƙar.

-Dauda!!!!
Jinah ta ƙwalla ƙara, alhali kuwa ƴarta, murmushi ne akan laɓɓanta, tana wani mo-motsa hannuwa, bakin ta na faɗar wasu kalamai, ba tare da Jinah ta fahimci wani abu ba. "Kar dai ita ma ta koma sheɗaniya bayan abinda ta yiwa Hindu". Tunanin da Jinah ke yi kenan.

-Fally! Fally! Shi ma shuru ba amsa, ta rasa su baki ɗaya.

------------------------

A très long chapter, ina fata zaku ji dadin ta!!!

Mu hadu chapter ƙarshe idan Allah ya kai mu.

Merci de toujours être là 💪💪


💞 JINAH (Matar Aljani)💞
by Malik al-Ashtar ✒️

On wattpad 👉 https://my.w.tt/g6epSX3tJ5

You'd like this New ❤️ Story

END

~*Wilaya Writers association of Nigeria*~
(Home of peace & hospitality).💦we are here to educate and entertain the heart of readers,we are the best among the rest💦

Visit to like our page:https://www.facebook.com/Al-wilaya-writers-association-of-Nigeria-113198586763490/?referrer=whatsappwhatsapp

Jinah dafe kan ta tayi sosai da hannayen ta, kamar tana tsoron ya tarwatse, zaune take a kasa, kafin kuma tayi kwance tare da rufe idanunta. Ta gaji sosai, babu wani sauran ƙarfi a jikin ta. Sosai take fatan ace duk wannan abun, mafarki ne ba zahiri ba.

-Na gaji, na gaji da wannan rayuwar, zuciya ta na ƙuna, jiki na ya gaji. Shin yaushe duk wannan zai ƙare, wata ƙila sai ranar da na mutu. Me yasa Allah ba zaka ɗauke ni ba? Ina roƙon ka ka ɗauke ni..!

Jinah ke faɗar haka, idanun ta a rufe, cikin murya mai ban tausayi. Tana magana ne ita kaɗai, sai dai bata karasa kalaman ta ba, taji an ƙatse ta da cewa :

-Astagfirullah! Kada ki ƙara faɗar haka! Idan ba so kike na sake mutuwa ba.

-Fally! Jinah ta faɗa tare da miƙewa da sauri tana mamaki. Eh muryar Fally ce, sai dai lokacin da ta buɗe idanu, Dauda ta gani.

-Me..m..me..
Kalamai suka gagara fita daga bakin ta, ƴarta ta gani tana mata murmushi.

-Mama, su ne! Cewar ƴar tata. Baba da uncle Dauda!

-Zo nan , matso kusa da ni. Cewar shi. Jinah kasa motsawa tayi. Matsowa yayi ya kama hannun ta, take Jinah taji wani abu. Janyo ta yayi jikin sa, sannan ya dora bakin sa kan nata, nan taji wani lantarki ya ratsa ko'ina na jikin ta. Fally ne kaɗai ya iya saka ta a irin wannan yanayin, kuka ta fara sosai, kukan farin ciki sannan ta rungume shi sosai kamar zata tsaga shi ta shiga. Zuwa cen ta sake shi, sannan ta rungume ƴarta tana kukan farin ciki.

Bata san ta yaya hakan ta yiwu ba, bata san ina gangar jikin Fally dake wurin take ba, ko kuma ta yaya Dauda da ya cakawa kan sa wuƙa ɗazun, yake a gaban ta yanzun, bata san ta yaya duk hakan ta faru ba, kuma bata damu da ta sani ba. Gashi sun dawo mata su duka biyun, a cikin gangar jiki daya : Kyakyawar fuskar Dauda, murmushin sa mai sanyaya rai, murɗaɗɗen jikin sa, namijin gaske, namijin da ya cece ta lokacin da take tsaka da neman taimako, namijin da ya juyawa duka dangin sa baya domin ta, namijin da ya dawo mata da murmushi a lokacin da take cikin ƙunci, namijin da ya sota duk da yasan tana son wani, namijin da bata fatan ta rasa shi.

Da kuma daɗin ƙarin ruhin Fally, namijin da idan zata tsaya ta ɓata lokacin bada labarin abubuwan da yayi domin ta tun yarintar su da kuma girma, to ba zata gama ba, namijin da bugun zuciyar sa yafi tsananin gudun jirgin kasa domin sonta, namijin da ta dinga jin kewar sa, alhalin bata ma iya tuna ko shi waye ba.

Samun wannan mazajen, ba karamin farin ciki bane a gare ta, duk da zata yi kewar fuskar Fally, yana nan, tana jin sa a kusa da ita, hakan ma ya wadace ta. Ƴarta, rabin ranta, tana nan bata sauya ba, bata koma sheɗaniya ba. Wannan farin ciki ne marar adadi gare ta!

-Ina son ki, mama! Cewar Aya, kamar tasan tunanin ta mahaifiyar tata take. Murmushi Jinah tayi mata, sannan ta bata amsa :

-Nima haka gimbiyata, nima haka... ƙarasa kalaman nata tayi tare da fashewa da kuka, kafin ta nufi dakin ta inda ta tarar dashi a kwance, Ayu. Shine ya faɗo mata a rai, ƙarasawa tayi kusan shi tare da rungume shi, ƙara fashewa da wani sabon kukan tayi lokacin da ta haɗa jikin ta da nashi.

-Kiyi shuru, ki daina kuka Jinah. Cewar Dauda ko kuma muce Fally, da ya shigo ɗakin yana ɗauke da Aya, da ita ma take cikin damuwa, na rashin wani ɓare nata, kuma abokin ta. Langwaɓar da kanta tayi jikin baban nata, tare da rufe ido, domin bata son kallon gawar ɗan uwan nata.

Daƙyar Fally ya shawo kan Jinah, ta aje gawar ɗan nata, tare da komawa wani ɗakin daban. Sauka Aya tayi daga jikin mahaifin nata, ta kwanta kan gado kusa da mahaifiyar ta, tare da sauya kamanni zuwa na ɗan uwan ta. Murmushi Jinah tayi tana hawaye tare da shafa fuskar ɗan nata.

Sunan sa ta kira, duk da tasan ba shi bane. Ƙara janyo shi tayi tare da ƙanƙame shi jikin ta.

-Duk lokacin da kika yi tunanin sa, ki faɗa min, ni kuma zan zama shi, mama. Hakan zai sa ba zaki yi kewar sa ba.

Cewar Aya, cikin kamannin ɗan uwan ta.

Murmushi Jinah tayi tare da gyaɗa mata kai. Ƙoƙarin barin ɗakin take, tunawa da tayi da su Sarah. Amma Fally/Dauda ya tabbatar mata da zai kula da su, ta koma tayi kwanciyar ta. Ba a jima ba, Jinah bacci ya ɗauke ta, tana rungume da ƴarta, ita ma Aya bata jima ba tayi baccin. Fally ya dan jima a ɗakin yana kallon su, cike da jin zafin ganin halin da suke ciki ba tare da iya yin wani abu ba. Yana jin zafi domin yasan haƙƙin da ya gagara saukewa na daga cikin wahalar da Jinah take ciki.

Fita yayi daga ɗakin, shi kaɗai, ya shiga rera kuka. A gaban Jinah ya iya riƙe hawayen sa, a gaban ta, bai son ya nuna mata gazawar shi. Amma mutuwar ɗansa ta taɓa shi. Durkushewa yayi a ƙasa, ya jingina da bangon ɗakin, ya haɗa kai da gwiwa, yana zubar da hawaye.

Abubuwa da dama sun saka shi kuka, bugu da ƙari mutuwar Ayu. Yanzu ya gane iyayen shi sunyi gaskiya. Da bai auri bil'adama ba da duk wannan bai faru ba.

Fally yayi nadamar abubuwa da dama, abubuwa da dama yaso ina basu faru ba; kamar kowannen mu. Sau tari muna aikata kuskure, wanda daga baya mu zo muna da nasanin aikata shi. Sai dai da na sani, baya wani canja babban abu, idan har bayan mun yi nadama, bamu daina aikata kuskuren ba. Gyara kuskure, shi ne mantawa da shi da sakawa a rai ba zamu sake aikata shi ba.

Fally ya ɗaukar wa kansa wannan alƙawarin, Jinah ba zata sake cutuwa ba, ta dalilin sa, har abada, ba zai sake maimaita kuskuren da yayi a baya ba, tare da yin alƙawarin zata zama macen da tafi kowacce farin ciki a duniya.

Goge fuskar sa yayi, sannan ya ɓace daga wurin zuwa asibiti, Sarah ya tarar a zaune, Nafisa na kwance bisa ƙafafun ta. Ƙarasawa yayi kusa da su.

-Sarah ya kira sunan ta a hankali. Lokaci guda Nafisa ta ɗago.

-Yaya Jinah da ƴan biyu?
Suka tambaya a tare.

-Suna nan lafiya, kar ku damu.

Dauda ya basu amsa a taƙaice, ba tare da ya faɗa masu halin da Ayu yake ciki ba.

-Ita..i..ita kuma mayyar, tana ina?

-ku kwantar da hankalin ku, har abada ba zaku sake ganin ta ba.

-Alhamdulillahi! Cewar Sarah.

-Ban..ban.. ban taɓa jin tsoro da ganin irin wannan halittar ba.

-Nima haka, amma me ya kawo ta, daga ina take?

-Zaku ji komi idan muka koma gida. Ina Abdul yake?

Da jin wannan tambayar, Nafisa ta fara zubar da hawaye kamar fanfo. Dauda ne ya shiga lallashin ta.

-Ina tsoron kar na rasa ɗan uwa na Dauda. Ta faɗa cike da fidda rai daga samun lafiyar ɗan uwanta.

-Zai warke, cewar Dauda. Nayi miki alƙawari!

Miƙewa yayi, Sarah tace :

-A wancen ɗakin suka kai shi. Ta faɗa tana nuna masa ɗakin da yatsa.

-Ina zuwa. Cewar Dauda kafin ya bar wurin. Ɓacewa yayi, sannan ya bayyana cikin ɗakin da aka kwantar da Abdul, ba tare da likitocin na ganin sa ba. Iya ƙoƙarin su suke ganin sun ceto ran Abdul.

-Ina ga sai an wuce da shi birni.

Cewar ɗaya daga cikin likitocin.

-Kana da gaskiya, idan ba haka ba, zamu rasa shi.

Cewar wani likitan.

Matsowa Dauda/Fally yayi kusa da Abdul, tare da ɗora hannun sa bisa goshin Abdul. Ya shiga karanto wasu kalamai, idanun sa a rufe. Bayan wasu yan mintuna, ɗaya daga cikin likitocin yace :

-Allah mai iko! Bugun zuciyar sa ya dawo normal.

Kallon kallo likitocin suka shiga yi, na mamakin ganin Abdul ya dawo hayyacin sa ba tare da sun yi masa wani taimako ba.

Dauda fita yayi ya koma wajen su Sarah, ya bar likitocin cikin ruɗu.

-Har yanzu likitocin basu fito ba?

Ya tambaye su.

-A'a...

Basu ƙarasa ba faɗa ba, sai ga wani likita ya fito. Miƙewa suka yi, suka tarbe shi.

-Ya ake ciki likita? Cewar Sarah.

-Yaya ɗan uwana yake doctor? Cewar Nafisa.

-Zan iya ce maku, yau mun ga ikon Allah, ɗan uwan ku yana nan lafiya, zamu riƙe shi zuwa gobe idan babu sauaran wani abu sai mu sake shi.

Tsalle Nafisa tayi, ta rungume Sarah cike da farin ciki.

-Ko zamu iya ganin sa?

-A'a, ku ɗan ƙara jira, har mu canja masa ɗaki.

Bayan wani lokaci, suka ga Abdul, a hayyacin sa, yayi farin ciki sosai da ganin su cikin ƙoshin lafiya. Tambayar ina Jinah da ƴan biyu yayi, suka tabbatar masa da suna nan lafiya. Sannan hankalin sa ya kwanta.

Komawa Dauda yayi gida, ya tarar da Jinah kwance, amma ba bacci take ba, matsawa yayi tare da zaunawa kusa da ita.

-Yaya Abdul ɗin yake?
Jinah ta tambaye shi.

-Lafiya ƙalau, sun ce zuwa gobe zasu iya sallamar shi.

Ya bata amsa yana mata murmushi, ita ma murmushin tayi cike da farin ciki.

Washe gari, aka sallami Abdul. Da shigar su gidan, Sarah da Dauda da ya koma asibitin da safe, suka nufi ɗakin da Jinah take ita ƴarta.

Sarah ita ce ta riga shiga ɗakin domin ita ce a gaba kuma tafi su sauri, da zumuɗin son ganin Jinah. Da shigar ta ɗakin, ta rungume Jinah sosai.

Sauran su ma haka suka yi, Nafisa da ɗan uwanta, bayan sun gama da Jinah suka koma kan Aya.

Bayan wasu mintuna na farin cikin ganin juna. A tare duka ukun suka tambayi :

-Wai ina Ayu?

-Ta kashe shi. Jinah ta basu amsa a taƙaice.

Abdul dake bakin gadon zaune yayi da jin abinda Jinah ta faɗa, ita kuwa Nafisa ta ƙwalla kara tare da fashewa da kuka, Sarah kuwa hannu tasa ta dafe bakin ta, hawaye na zubo mata, tana maimaita "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un". Kowannen su ya shiga ruɗu, babu wani dake da niyyar lallashin wani.

Washe gari aka kai Ayu makwancin sa. Jinah da Fally suka fayyacewa yan gidan asalin ko su waye ƴan biyu, abinda Hindu take so, yanda Dauda yake a zahiri, a taiƙace dai komai suka basu labari. Sun girgiza, amma kuma basu sha wani wahalan gasgatawa ba, bayan ganin abinda idanun su suka gane musu a cikin gidan. A yanzu sun bar abinda ya faru a matsayin sirrin gidan nasu.

Kwanaki na shuɗewa, kewar Ayu na daɗa damun su. Akwai zafi rasa makusanci, domin kuwa ya tafi kenan, zamu cigaba da rayuwar mu ba tare da shi ba, zamu goge shi daga duk wani program na gobe da muka shirya da shi, zai zamana mun yawaita ambaton sa yayin da muka tuna baya. Akai akai muna ɗorawa kan mu irin tambayoyin nan : idan da wane yana nan, da abu kaza da kaza ga yadda zai kasance, da wane na nan, da zai ce kaza ko kuma yayi kaza. Mu kan yawaita jin rashin sa a kasan zuciyoyin mu. Ga duk wadanda suka rasa makusantan su, Allah ya ƙara maku hakuri da juriyar rashi.

Sarah ce a cikin kitchen tana haɗa karin kumallo, lokacin da Abdul ya shigo.

Gaishe ta yayi, ta amsa a takure. Tun bayan faruwar abinda ya faru tsakanin su, take jin wata matsananciyar kunya, ba kamar kunyar Abdul din, shi yasa take gujewa duk wani wuri da zasu haɗu daga ita sai shi.

-Nazo ne, ina son muyi wata magana.

Benci dake kusa da su suka zauna. Abdul ya fara da cewa :

-Nazo ne na baki hakuri kan duk wani abu da ya faru, na rantse miki ba zan iya tuna komai ba na wata alaƙa da ta shiga tsakanin mu. Amma ina ji a jikina na aikata, ban san yaya zan fahimtar dake, ki gane gaskiya nake faɗa miki. Ba zan iya cigaba da kasancewa da wannan nauyin ba, shi yasa na yanke shawarar komawa Nigeria. Ina son duka mu koma a tare, ni kuma daga cen zan wuce Canada karatu. Ina son ki cigaba da kular min da ƴar uwa kamar yanda kike yi a yanzu. Dan Allah kar kice min a'a, ki sayar da wannan gidan, hankali na zai fi kwanciya idan duka kuna cen. Ina tsoron abinda ya faru da mu, ya sake faruwa.

Sarah ta yarda da maganar sa, kuma bata wani bata lokaci ba ta amince domin gidan nan yana tuna mata da abubuwa marasa kyau. Sai dai ta fara jin ta bakin sauran kafin ta yanke hukunci. Godiya Abdul yayi mata cikin farin ciki.

-Amma ta yaya zaka iya biyan kudin karatun ka a ƙasar wajen?
Sarah ta tambaye shi.

-Akwai gadon da muka gada ni da Nafi na mama mu. Kuma zan nemi scholarship, kar ki damu dama ina da wannan wannan program tun da daɗewa.

-Shikenan. Cewar Sarah.

Mikewa yayi, ya barta. Tarar da Dauda yayi zaune ya tsunduma cikin tunani.

-Kai kuwa, tunanin me kake? Oh ba sai ka faɗa ba ma, na sani na Jinah!

Dariya dukan su suka yi.

-Lallai, ka canka!

-Cikin sauki ma, domin shi kaɗai ka iya.

Dariya suka yi.

-Da gaske, ina son ka faɗa min, naga kwana biyu kana wani nesa nesa da Jinah.

-Na cutar da ita sosai, kuma ina tunanin ba lallai bane ta yafe min. Shi yasa nake ɗan nesa da ita, domin ina tsoron tace bata sona. Ni kuwa ba zan iya jurar hakan ba.

-Ko ma me zai faru, ka fara yi mata magana, ba zaka iya gane me take ji game da kai ba.

-Baka yi karya ba.

-Never man!

Dariya suka yi, kafin ya tashi ya tarar da Jinah cikin daki.

Jinah murmushi tayi da ganin shi, tace a ranta yau ya gaji da gudun. Zaunawa yayi bisa gadon, kusa da ita. Sannan yace:

-Zaki iya yafe min wata rana? Zan iya sa ran haka? Shin zaki iya kallo na wata rana ba tare da kin tuna mutuwar ɗanki ba? Na rantse miki, nayi nadama Jinah, ki yafe min, na tsani kaina ni Fally, irin cutar da Jinah da nayi. Ni...

Sauran kalaman sa, suka tsaya masa a maƙoshi, sadda kai yayi ƙasa, hawaye suka zubo masa.

-Fally, cewar Jinah cikin sanyayar murya, tana mai dago kan shi. Yi tunani ace zafin da nake naji yakai girman tekun maliya, lokacin da naga ka dawo gare ni, baka tafi ba, ina jin kasancewar ka a kusa da ni, na kwanta na tashi kana gefe na, wannan girman tekun maliyan, yana ragewa a duk lokacin da kake kusa da ni. Saboda kai da Aya, yasa bana jin zafin mutuwar Ayu sosai.

Ban manta Wata rana lokacin da muna yara, ka fita kai da baba, ni kuwa ina gida tare da mama lokacin tana bacci, na fita da niyyar na ga gari kuma kasan irin son da sauran aljanu ke min, ta faɗa tana murmushi, domin tasan akasin so suke mata.

Naga irin hantara a ranar, da kuka na koma gida. Raina a bace, naji na tsane su, ta yanda ba zan taba yafe musu ba abinda suka min. Bayan mama ta lallashe ni, nayi shuru, tace min : Jinah, yafiya ita ce babban magani ga zuciyar da aka cutar, yafiya tana haskaka zuciya da ruhi, yafiya tana ƴantar da bawa, yafiya tana gusar da mummunan tunani, yafiya tana saka farin ciki. Kada ki kasance marar yafiya Jinah, idan an cutar dake, ki kalli abu mai kyau cikin cutarwar, idan baki ganshi ba, ki nemeshi zaki ganshi, idan kika yi hakan zaki samu salama da kwanciyar hankali a zuciyar ki. Da jin haka, nace : Kin yi gaskiya mama, da ba'a yimin haka ba yau da ban samu wannan kyakyawar hudubar ba daga gare ki. Dariya tayi sannan ta rungume ni, a wannan lokacin ne, na fitar da duk wani mummunan tunanin da na saka a zuciya ta.

Shuru tayi domin tuna mahaifiyar tata (uwar riƙon ta) da tayi.

-Bana ƙin ka Fally, ta cigaba. A baya da na faɗa maka munanan kalamai, kawai dan ina cikin fushi ne, ina farin ciki na ganin ka kusa da ni, na yanda baka tunani. Ka daina damun kanka Fally, na daɗe da yafe maka.

Da gama faɗin haka, ta rungume shi, Fally kuwa ya riƙe ta sosai kamar zai sanya ta cikin jikin sa.

-Ina sonki Jinah, ina sonki sosai, sosai...


-Nima ina son ka Fally, nayi kewar ka sosai,...


-Za.. zaki iya maimaitawa dan Allah?


-Ina sonka.

Dariya suka yi.

-Fally.

-Hum.

-Zaka iya saki na yanzu, domin bana numfashi da kyau.

-Haha, yi hakuri habibty.

Daga wannan rana, suka fara sabuwar rayuwar soyayya, Jinah da Fally.

Sun fara da barin wannan kauyen, wannan kasar, Niger zuwa wata kasar Nigeria. Dukan su baki daya.

Fally yana kula da Jinah tamkar wata jinjira, baya barin wani abu ya same ta na cutarwa, duk wani abu da zai zo masa a kai, kuma yasan zai daɗaɗa ran Jinah, shi yake yi. Yana rayuwa ne kawai domin ta, farin cikin ta, shi ne nashi. Sanin Jinah tana son zaga duniya, yasa yake nuna mata hotunan wurare masu kyau na cikin duniya, kawai da ta nuna wuri, a take zai ɗauke ta ya kai ta. Cikin kwanaki kaɗan, ya kaita wurare da dama, irin su : Bahamas, pyramids of Giza a kasar Egypte, Hawaii, Paris, Dubai, The Colosseum, Ha Long Bay, Grand Canyon... da sauran su.

Yau ma a wannan lokacin, suna a Pamukkale, ɗaya daga cikin kayataccin wurare a ƙasar Turkey. Jinah kamar ƙaramar yarinya, Fally sai dariya yake mata. Bayan sun gaji da yawo, suka dawo bakin kogi suka yi zaune, ta dora kanta bisa kafadar shi.

-Ina cikin farin ciki sosai Fally.

Bata jira jin me zai ce ba, ta ƙara laɓewa cikin jikin sa.

-Yanzu dai mu koma gida, nayi kewar princess ɗita.

Da fadin haka, sai gasu a Nigeria, da gudu Aya ta ƙanƙame maman ta, lokacin da ta ganta.

-Ina kuka tafi yau? bani labari mama.

-Toh ƴata yanzu kuwa.

Murmushi tayi, mamar ta ta shiga bata labarin duk abubuwan da ta gani a Pamukkale, shi kuwa Fally yana gefe ya zuba masu na mujiya.

Bayan wasu yan mintuna, Nafisa ta shigo, ta basu labarin sun fita ita da Aya, mutane na ta kallon ta kamar sun ga aljana, har yau ma wasu sun nemi da ta zamo ambassador ta wani brand na yara.

-Dan Allah Jinah ki amince, my little princess ta zamo tauraruwa. Tuni har nayi suna cikin anguwar nan dalilin ta, toh ya kike gani idan aka fara ganin ta a social media, wow!

-Ashe dai princess din tawa haka take da kyau!
Cewar Jinah tana murmushi.

-Kamar ke mama!
Cewar Aya. Kuma da gaske tana da kyau sosai ita ma, ko ma taso tafi Jinah, duk da gashin ta bai kai tsayin na mahaifiyar ta ba, amma yana da tsawo shi ma. Idanun ta irin na baban ta ne, a taikace dai ita ma zubin aljanun gareta.

A yanzu, ta iya controlling karfin ta sosai, kuma ta daidaita shekarun ta ba kamar da ba, yanzu da ka ganta yarinya ce yar shekara bakwai kuma tana cigaba da girma kamar kowanne lafiyayyen yaro.

-Kai ya kake gani?
Jinah ta tambayi Fally.

-Idan kin amince, toh nima na amince.
Ya bata amsa murmushi kan laɓɓan sa.

-Ke kuma Aya?
Ta tambayi ƴar tata, Nafisa na mata irin kallon dan Allah ki amince.

-Nima ina so mama!

-Toh shikenan

-Cooool! Nafisa ta daka tsalle. Ina da number daya daga cikin su. Brand din su yafi zama popular, bari na kira shi yanzu.

Akwai wani abu kuma. Cewar ita Nafi, da murmushin mugunta a fuska.

-Menene?

-Na.. na nuna mishi pic din ki, kema yace yana son...

-Ba zai yiwu ba!
Bata kai ga ƙarasawa ba, Fally ya katse ta.

-Kin ji amsar ki.
Cewar Jinah, tana ƙyalƙyata dariya.

-Wai irin namijin kishin nan!
Cewar Nafisa tana masa hararan wasa. Dariya suka yi su duka.

Kafin ta kira mutumin, sai da taji ta bakin Sarah tukun, kuma ta amince. Cikin kwanaki kaɗan ƴar yarinya Aya ta zama Star.

Wata rana da yamma, suna a falo suna fira, wani ya ƙonƙwasa ƙofa. Nafisa ta tafi ta bude, sannan ta dawo tare da wani mutum, da ba zai wuce shekaru 40 ba, irin mai ƙasaitar nan, da kyakyawar fuskar shi daidai gwargwado. Da alama ta san shi.

-Aunty Sarah, uncle Ahmad ke son ganin ki.

Sarah abin yayi matuƙar bata mamaki, bata ƙarasa mamakin ta ba sai gashi ya shigo falon, sauran tashi suka yi suka basu wuri.

-Kin san shi? Fally ke tambayar Nafisa.

-Eh, maƙocin mu ne, gida mai kallon namu.

-Kin san ko me ya kawo shi?

-A'a, ban sani ba.

-Ina da wata dabara!
Cewar Jinah.

-Nima haka cewar Aya.

-Aya! Ban faɗa miki ki daina karanta cikin kawunan mutane ba. Ki daina bana son haka.

-Amma mama, bamu san shi ba, kinga dole muyi takatsantsan.

-Kada ki sake, babu kyau.

Da alama Aya bata so maman tata, ta taka mata birki ba. komawa tayi wajen baban ta tana zumɓuro baki.

-Ba maman ki hakuri. Baban ta ya raɗa mata a kunne.

-Kiyi haƙuri mama. Ta faɗa.

Gyaɗa mata kai Jinah tayi da alamar ta haƙura, sannan ta buɗe hannayen ta, yarinyar bata yi musu ba, tazo ta rungume ta.

Cigaba da hirar duniya suka yi, har lokacin da Sarah ta dawo.

-Me ya kawo shi?
Cewar Dauda cikin nuna kulawa.

-Matar aure yake nema!
Sarah ta faɗa ba tare da ta kalle su.

Washe baki Jinah ta shiga yi.

-Matar aure? Kamar yaya? ke kuma ya faɗawa haka? Ohhhhh ko dai keh..., na gane. Aunty Sarah ki ce kin amince, Uncle Ahmad, mutumin kirki ne, matar shi ta rasu da daɗewa, kuma kinga kyakyawa ne, kuma ga kudi, ina tunanin ƴaƴa biyu kawai gare shi.

Nafisa ce ke ta zuba wannan surutun.

-Toh me kika ce masa?
Cewar Jinah.

-Nace masa sai nayi tunani.

-Da alamun mutumin kirki ne, amma ki ɗauki lokacin nazartar shi kafin nan.
Cewar Fally.

-Ni tuni ma yayi min!
Cewar Jinah.

-Nima haka!
Nafisa da Aya suka haɗa baki. Dariya dukan su suka yi.

Bayan wasu makonni, Sarah ta amince zata auri Ahmad, ta kuwa ɗauki lokaci tana nazartar shi, ta gano mutumin kirki ne, kuma sosai ƴaƴan shi suka shaƙu da ita. Suna jin daɗin kasancewa tare da ita, ba kamar idan Aya na gida suyi ta wasa.

Wata rana, Fally da Jinah su kaɗai a zaune suna fira, Jinah ta kawo zancen da Fally ya tsani jin sa.

-Zan mutu kafin kai. Ni kaga mutum ce, kiyasin shekarun da zan yi ba zasu wuce saba'in ba, wata kila tamanin, nayi masu yawa nayi ɗari. Kai kuma dubunnai ne a gaban ka. Wace kalar mace zaka sake a madadi na?

Jinah tayi masa wannan tambayar domin ayi dariya, sai dai tuni taga yanayin Fally ya canja.

-Ah habiby da wasa fa nake.

-Toh bana son irin wannan wasa, ina shiga damuwa idan na tuna haka Jinah.

-Toh yi hakuri na daina daga yau. Ta faɗa tare da shigewa jikin sa.

Fally ya tsani ayi masa irin wannan zancen, domin yasan dole wata rana haka zata faru, shi yasa yake shiga damuwa sosai.

Duk inda ke da rayuwa, akwai mutuwa, kaddara ce da babu mai iya guje mata. Sau tari, mu matasa, bamu cika tunawa da ita ba, mun fi tunanin tafi daukan tsofaffi. Abin dariyar ma, muna ganin yanda take ɗaukan matasa, yara kanana, hatta da jarirai, amma mu kullum tunanin mu mutuwa ta tsofaffi ce, har mamaki muke idan aka ce ta ɗauki matashi wane. Ya kamata mu daina yaudaran kan mu, mutuwa ba ruwanta da matashi, tsoho, talaka, mai kudi, mai kyau ko mai muni ne. Tana ɗaukan mu ne a lokacin da ta so ko a yanda ta so. Abinda da Sarah da wannan ahali nata suka fahimta kenan.

A wata yammar litinin, dukan su suna gidan Ahmad, gidan da a yanzu Sarah take ciki tun bayan auren ta da Ahmad. Fally, Jinah, ƴarsu, Nafisa da kuma ɗan uwanta da ya daɗe da dawowa bayan wasu shekaru. Sun haɗu domin taya Jinah murnar cika shekaru 27. Suna cikin fira, cikin nishadi, lokaci guda suka bar jin muryar ta, bayan mintuna da yawa, alhali da ita ake ta surutu. Fally ne ya kai hankalin sa gare ta, mamaki yayi da ya ganta da alamun tana bacci, wani irin bugu zuciyar sa tayi. Aya dake waje tare da ƴaƴan Ahmad, ta shigo falon a gigice, da shigowar ta ta durkushe kasa, ta riga da taji a jikinta tun kafin ta shigo falon. Sauran mamaki ne a fuskokin su ganin halin da Aya take, har zuwa lokacin da suka ga Dauda na kokarin tashe da Jinah ya kasa. Falon yayi tsit, suna tunanin ta yaya hakan zai yiwu. Eh tabbas, Jinah rai yayi halin sa, Fally mikewa yayi tare da ɗaukan ta. Sauran basu fahimci komai ba, sai dai jikin su yayi sanyi duk da sun kasa gasgata abinda suke tunanin shi ya samu Jinah, sautin kukan Aya kawai ke tashi a falon.

Fally nufa yayi da Jinah gidan su da ba nisa da na su Sarah, yana shiga ya kaita ɗakin su, ya kwantar da ita bisa gado. Shi ma kwantawa yayi kusa da ita, a take shi ma rai yayi halin sa. Amma kafin ruhin sa ya karasa fita daga jikin sa baki daya, yace :

-Me kike tunani Jinah, dubunnan shekarun da suka rage min na rayu ba tare da ke ba, ba zai yiwu ba. Nima dole na mutu, yayin da nasan kema baki duniyar. Zuciya ta tana bugawa ne a tare da taki, babu abinda zan yi a wannan duniyar babu ke, ni da ke mun haɗu mun zama ɗaya, kuma ɗaya bata taɓa bada biyu ba. Sai mun haɗu a duniyar matattu, Habibty.

Jinah was, is, kuma forever will be matar aljani.

-----------------------------------------

ALHAMDULILLAHI, c'est fini lol. Bye bye matar Aljani.

Ina fata kun faɗakartu, nishanɗantu, kun kuma ilmantu da wannan dogon labarin nawa. Sannan ina mika sakon gaisuwa ta ga masoya wanda suka jima suna bibiyar wannan labari. Allah ya bar hannu da kaifin ido. Ameen ya Allah
Chapter 27 · 0% Book details