CHAPTER 12
Jinah Part 1 Complete Hausa Novel · about 13 min read
~*Wilaya Writers association of Nigeria*~
(Home of peace & hospitality).💦we are here to educate and entertain the heart of readers,we are the best among the rest💦
Visit to like our page:https://www.facebook.com/Al-wilaya-writers-association-of-Nigeria-113198586763490/?referrer=whatsappwhatsapp
A wajen aljanu idan daya daga cikinsu ya fada soyayya da dan adam. To fa mawuyacin abu ne dan adam din nan ya manta da soyayyar dake tsakaninsa da aljanin, sai idan dai wankin kwalwa aka masa kuma hakan na faruwa ne ko daga cikin iyayen aljanin ko kuma shi kanshi aljanin wani yayi wa dan adam din wankin kwalwa ta yanda ba zai kara tuna wata soyayya da yayi da aljanin ba. Wani lokacin kuma soyayyar da dan adam din yake wa aljani idan ya samu wani masoyin da suke jinsi daya wato dan adam kuma har yaji yana kaunar wannan dan adam din to zai gama har da shaukin soyayyar da yake wa aljanin duk ya juyeta akan dan adam din, to hakan na faruwa a hankali zai fara manta soyayyar dake tsakaninsa da aljanin. Shi yasa Fally yayi tunanin babu yanda za'ayi iyayensa su yiwa Jinah wankin kwalwa, dan suna son Jinah kuma ba zasu so ta mantasu ba. Sai dai kuma hakan ce ta kasance, mahaifiyarsa tana son Jinah, saboda haka, bata son wani abu ya samu Jinah, bata son Jinah ta tuna dasu har tayi kokarin nemansu, idan da bata manta komai ba da tuni ta shiga nemansu kuma kafin ta nemosu tana iya fadawa hannun muyagun aljanun dake son cutar da ita, bare kuma yanzu da har tanada tagwayen da kowanne aljani yake da burin mallakarsu ba. Dan haka wankin kwalwa da mahaifiyar Fally tayi mata ba don komai bane face dan ta tseratar da ita.
Ganin yanda Jinah take tadi da Dauda, suna yi suna kyalkyata dariya da irin kallon da suke yiwa junansu yasa Fally yake tunanin soyayyar da Jinah ke masa a yanzu ta koma kan Dauda, wato kenan Dauda ya maye gurbinsa. Tunani ya fara, yanzu duk wannan sadaukarwa da nayi a kanta! Sau da dama har sai yayi yunkurin tafiya ya barta in yaso aljanun su cutar da ita, amma sai ya kasa. Ga kuma 'ya'yansa dake hannunta, yana son yaran sosai domin da ya kalli yaran wani farin ciki ne ke ziyartar zuciyarsa. Suma kuma tagwayen suna ganin Fally amma sun kasa fahimtar waye shi, ba zasu gane matsayinsa ba har sai sunyi shekara daya da haihuwa kuma a kullum wannan ranar yake daukin jira.
Kwanaki da yawa sun shude, Fally bai bar gidansu Sarah ba kuma bai bar ganin abin takaicin dake faruwa ba tsakanin matarsa Jinah da kuma wannan mutumin wato Dauda. Sai dai farin cikinsa a kullum babu yanda za'ayi wani abu ya shiga tsakanin Dauda da Jinah domin har yanzu matarsa ce. Jira kawai yake lokacin da tsautsayi zai dauki Dauda yace zai kusanci Jinah ya gane kurensa. Shima haka take bangaren Dauda, yana ji tamkar ya matso sauran ranakun da suke rage na aurensu, yau ace ga Jinah a dakinsa a matsayin matarsa.
Kamar kowanne Marece tun ranar da yazo, Dauda ne da Jinah a zaune tsakiyar gida suna tadi.
-Kwana biyu kawai ya rage ki zama matata...
Dauda ya fada cikin yanayin farin ciki. Murmushi Jinah tayi. Shi kuma ya cigaba:
-Matata! Oh har na tuna da wata waka, Sunanki mai dadin fadi, kin ratsa zuciya! Kowa yazo za ayi nadi kece Sarauniya....
Dakatawa yayi da wakar ganin Jinah ta kyalkyace da dariya.
-Kushe miji fah ba kyau...
Dauda ya fada yana tamke fuska, irin dagasken nan yake.
-Eh koda yana waka da murya kamar gwangwani!
Ta fada tana dariya.
-Eh din!
Dariya dukansu suka yi. Shuru na dan wani lokaci ya biyo baya, Jinah ta lura Dauda hankalinsa yayi wani gu, ya fada duniyar tunani. Hannunsa Jinah ta kama tareda kallonsa a natse cikin ido.
-Har yanzu baka son fada min dalilin dake sanyaka cikin wannan dogon tunanin. Dan Allah ka fada min me yake damunka?
Wani dogon numfashi Dauda yaja, wanda Jinah bata fahimci komai ba, domin shiga yanayin bakin ciki ba dabi'ar Dauda bace, mutumin da kullum cikin raha yake.
-Me yasa dan Adam butulu ne? Me yasa soyayyarshi da dukiya ta wuce kima? Me yasa in dai akan kudi ne, soyayya, dangi, zumunci ba komai ba ne? Jinah da kinsan abinda ya faru bayan tafiyarki. Ya...
Sauran kalaman tsaya masa suka yi a baki. Hannu yasa yana goge kwallan dake shirin zubo masa.
-Kayi hakuri Dauda...
Jinah ta fada cikin Sanyanyar murya.
-Kinsan me yasa nake sonki, zuciyarki tsarkaka ce! Babu digon hassada ko keta a cikin idonki, fuskarki tana bayyana tsantsar gaskiya da mutuntawa. Imanina yana karuwa ta dalilinki, na kan ce koda munafukai da maciya amana ba zasu dakata da gurbata duniya ba, za'a samu mutanen kirki kamarki.
Ya fada cikin murya mai nuna yakini a maganarsa, wanda kuma yasa Jinah ta yarda lallai akwai wani babban al'amari da ya faru dashi bayan tafiyarta.
-Ka fada min abinda ya faru.
Ta fada cikin raunanniyar murya.
-Lok..loka..lokacin da na farka daga dogon suma, na samu labarin mahaifina ya rasu, anan, na tabbata bakin ciki yayi mana sallama. Yayinda dangi ke cikin jimami, Kawuna Mati, yayan mahaifina yazo, ba mutumin da na tsana kamarshi, tashi da mahaifina bata taba zuwa daya ba, shine kadai dan uwan mahaifina da ba a cikin dangi yake da zama ba. Kwana hudu da faruwar wannan masifa, kawu Mati yazo gida cike da zumudi da murmushi har kunne, ya nemi da dangi su hadu yana son magana damu. Duka muka hadu a tsakar gida, wasu takardu ya fiddo, wasu banzayen takardu wai na masana'antar mahaifinmu da kuma na gidanmu duka nashi ne. Bamu yarda da hakan ba, domin wannan ba zai taba yiyuwa ba, dattijawan garin aka kirawo da yake duk ya siyesu, har da kuma Kawunaina sai daya kawai da yace shi bai yarda ba haka yayi masa korar wulakanci shi da iyalinsa. Gashi manyan yayyena Idrisa da Isa basu duniyar, sauran kuma biyun yayyena sun tafi kasar waje gashi babu takardun dawowa a lokacin. Dayan yayan nawa kuma yi yayi kamar abun bai dameshi ba, ni kuma, nayi iya kokarina daga karshe ma korarmu yayi ni da Mahaifiyarmu da kuma kannena, inda Allah ya taimakemu dangin mahaifiyata sun karbemu hannu biyu. Na samu kuma labarin yace zai auri sauran mata biyun babana, idan basu yarda ba, zasu iya bar masa gida. Kuma kinsan mu anan, mata ba aiki suke ba, kenan ta yaya zasu iya ciyar da ya'yansu idan kuka bar gidan, kuma komawa wajen iyayensu a wannan lokacin abun kunya ne. Haka yasa biyun matan babana suka dawo matan kawuna, saboda ya kori mahaifiyata kuma Tanti Habi ta haukace. Sannan kuma ya sallami wasu kawunaina daga aikin masana'anta domin ya saka yan'yansa da kuma wadansu da suka taimaka masa wajen samun komai. Uwa daya uba daya yake da babana, amma bai ji ko digon imani ba wajen tarwatsa masa ahali. Na kudura a raina sai na yaki wannan zalunci da yayi mana, duk da mahaifiyata tace na manta komai, ba zan iya ba.. Jinah naga tsantsar rashin imani na dan adam...
Shuru yayi, ita kanta bata san me zata ce ba jin kalamansa, ta razana da jin labarin kuma taji ba dadi. Rungumesa tayi dan tunanin shi daya abinda taji zata iya, amma basu dau lokaci ba. Shuru dukansu suka yi, kafin wata murya daga bayansu ta katse shurun.
-Ba laifin kawunka bane, shi ne! _Yana nuna yatsa zuwa sama._ Ba shine ke da ikon komai ba? Me yasa ya bar wannan mutumin ya cika burinsa, kamar kuma yanda ya dauke min mahaifiya?
Abdul ne ke fadar haka lokacin da yaji labarin Dauda. Zaunawa kusa dasu yayi.
-Muna sallah, muna azumi, muna yin duk abinda ya wajaba a kanmu, muna kuma barin duk abinda aka hanemu! Toh me yasa kullum mune cikin masifa? Irin kawunka ya kamata su shiga irin wannan halin ba mu ba!
-Abdul. _Cewar Jinah kafin ta cigaba cikin tausashiyar murya._ Daga Allah muke kuma gareshi zamu koma.
-Amma ya kamata ya barmin ita, naso ace har na kai matsayin da zan sanyata cikin farin ciki, na bata duk wani jin dadi na duniya, na mayar da ita tamkar sarauniya, kar ta rasa komai na rayuwa kuma ta dinga alfahari dani.
-Akwai lokacin da ina cikin damuwa sosai, wani ya taba fadamin, idan bakin ciki ya bubbuga mana kofa, ko ya adadinsa yake, mu kasance masu godiya ga Allah, wannan ba wani abu bane face jarabawa domin jarraba imaninmu. Kuma a lokacin da muka koma gareshi zaka ga ya saka mana da mafificin alkhairi. Komai ya samemu na dadi ko akasinsa dole mu kasance masu godiya ga Allah. Kuma mutumin da ya fada min haka ba kowa bane kai ne Dauda, to kenan kai ba zaka yi amfani da nasihar da kayi min ba? Kai kuma Abdul, uwa bata bukatar zinare, kudi ko lu'ulu'u domin tayi alfahari da danta, yanzu da bata duniya bata bukatar komai illa addu'a.
Dukansu biyun jikinsu yayi sanyi da jin kalaman Jinah. Haka suka cigaba da hira da tayi sanadin gusar da duk wata damuwa tasu, har sai da dare ya tsala sannan kowa ya nufi makwancinsa.
Jinah kasa bacci tayi, tunanin abinda ya faru jiya take, ganin wannan mutumin ba karamin tsoratata yayi ba, ta kasa fahimtar komai game da lamarin, yanke sharawar daukar maganar Dauda tayi kawai ba komai bane face mafarki. Haka tayi ta tunani har bacci barawo yazo yayi gaba da ita.
-Babu abinda za'a yi, kawai ina son a daura auren, to wai ma wa zan gayyata, ba wanda na sani kuma la'akari da abinda ya faru kasan babu wani danginka da zai tako kafa wai da sunan zuwa wajen biki.
Jinah ke fadawa Dauda ana gobe daurin aure.
-Eh, na samu labari duk abinda suka yi maki, kuma har yanzu Mahaifiyata tayi imani da wannan karairayin amma idan muka yi aure, zamu je mu ganta kuma zan canza mata wannan tunanin. Kuma dan Allah kiyi hakuri akan abinda suka yi maki, ki yafe min na rashin kasancewata a wajen domin kareki.
-Me zaka yi kenan? Ai ni naji dadin rashin kasancewarka a gurin, domin ba zan so a dalilina ka samu matsala da mahaifiyarka ba.
-Toh yanzu manta da wannan, ya riga ya wuce, yanzu ne da kuma gobe a gabanmu.
Ya karashe maganar da murmushi a fuskarsa. Ita kuma Jinah fargaba ce duk tabi ta dameta, domin tana ji a jikinta wannan auren ba karamin kuskure bane yinshi. Da sauri ta dawo daga tunanin da take jin daya daga cikin tagwaye ya tsala wani uban kuka, wani lugude zuciyarta tayi kamar zata fito daga kirjinta, tsoro duk ya mamayeta. Domin babu daya daga cikin yaran da ya taba yin irin wannan kukan. Da gudunta ta nufi gurin yaran da ta bari cikin daki tareda Nafisa, Dauda na biye da ita a baya. Tarar da Nafisa suka yi itama na kuka.
-Me ya faru?
Murya na rawa Jinah ta fada tare da karasawa ta dauki danta da yaki daina kuka.
-Na..na..na fita ne yanzu.. naje..debo ruwan sha shine da naji kuka na rugo... shine na tarar da Ayu na kuka...ita..ita kuma Aya ban ganta ba.
Jinah kalmar karshe kawai ta iya rikewa, sai yanzu ta lura da babu Aya.
-Me? _Ta fada da karaji._ Ina 'yata?
-Ku kwantar da hankalinku duka, bazata yi nisa ba. Ke Jinah lallabi Ayu ni zan fita waje ko zan ganta.
Jinah tayi tayi amma Ayu yaki yin shuru, kokowa ma yake yana son uwar ta saukeshi. Abun fa kara ta'azzara yayi lokacin Dauda ya dawo ba tare da Aya ba. Zuciyar Jinah bugawa take da sauri ta yanda tayi tunanin ko fasa kirjinta zata yi ta fito.
(.....)
A waje kuwa, wani masifaffen fada ya turnuke. Fally ji yayi ya fara gajiya, ba zan bari ya tafi da 'yata ba, shine abinda yake ta maimatawa. A takaice dai, aljanun sun gano inda suke, shine daya daga cikin aljanun yake so ko ta yaya ya dauke Aya, kuma yayi nasarar dauketa har ma yayi nisa da gida da ita. Sedai Fally ya tareshi, sai gwabza fada suke tamkar wasu mayunwatan zakuna. Bayan wani dan lokaci, Fally yayi nasara akan aljanin da karfinsa ya kare da kyar ya iya guduwa yana fadar :
-Zan dawo, kuma bani daya ba, ka san da wannan!
A wata bishiya Fally ya zauna yana maida numfashi, Aya kusa dashi, tana masa wani irin kallo. Tabbas dole ya sake daura damarar kare ya'yansa daga waddanan miyagu. Da wannan tunanin ya dauki Aya ya kaita har kofar gida kuma daidai da fitowar Sarah da Abdul cike da mamaki suka ga Aya a waje ita daya. Sarah ta dauketa suka koma cikin gida. Suna shiga Jinah tazo da gudunta, bata tsaya amsa tambayar da Sarah da Abdul ke yi mata ba kan ya akayi Aya ta fita waje ba ta amshe yarta tareda kankameta. Kuma a take Ayu ya daina kukan da yake yi.
-Wai mun gode Allah, _Cewar Dauda tareda ajiyar zuciya._ Shikenan daina kukan tunda an ganta.
Da Nafisa yake da ke ta rizgar kuka tana tunanin laifinta ne. Yayanta ya matso kusa da ita tare da rungumeta yana lallashinta. Shi da Sarah basa bukatar wani dogon bayani akan me yakai Aya a waje, komai ya wuce tunda dai gashi an ganta.
Washe gari, ranar daurin aure, ba tare da wani shagali ba aka daura aure a masallaci kamar yanda Jinah ta bukata. Duk da ba wani jagali ba aka yi amma kowa gidan cikin farin ciki yake. A marecen ranar ma basu yi bacci ba. Suna ta hirar duniya. Abdul da Nafi har sun saba da zaman gidan, duk da har yanzu zaman jiran mahaifinsu suke domin su koma cen asalin gidansu...
-Sarah, wata alfarma nake son ki yimin.
Cewar Dauda cikin yanayin dagaske yake. Shuru kowa yayi yana sauraron me zai ce.
-Ina sauraronka Dauda.
-Kamar yadda kuka sani, yau Jinah ta zama matata, tawa, toh shine...
-Ahan muna sauraronka.
-Shine... Nake son ki dauki yaran, ni kuma sai na dauki matata.
Dariya Abdul yayi, su kuma matan rike baki suka yi suna mamakin Dauda...
-Bakada dama Dauda, toh shikenan, dare yayi yanzu ni zan je in kwanta. Sai da safenku.
-Toh yara kuma ku tashi dare yayi aje a kwanta.
Dauda ke fadawa Abdul da Nafi yana dariya. Seda suka dan taba raha kafin su je su kwanta. Ya rage sai amarya da Ango.
-Kinsan wani abu Jinah, har yanzu na kasa gasgata yau kece a matsayin matata, komai ina jinsa kamar a mafarki. Yanzu da nake a tare dake sai nake ji kamar babu wani abu na bakin ciki da ya faru dani a baya. Kin baiwa rayuwata ma'ana Jinah. Nayi maki alkawarin har indai ina raye, zaki kasance cikin farin ciki.
Murmushi Jinah, tayi sosai kalamansa suka tabata.
-Kayi min abinda ba zan taba mantawa ba Dauda, kayi abinda ba kowanne namiji zai iya yi ba. Ba zan boye maka ba, a duk lokacin da ka furta min kalmar "Ina sonki" na kanji ba zan iya baka amsa ba, amma kuma duk da haka bani nadamar aurenka, ina fatan wata rana na soka, son da yafi kalmar so.
Hannu Dauda ya kai kan fuskarta ya janye gashin kanta da ya zubo a fuskarta zuwa bayan kunnenta sannan ya kai mata lafiyayyen kiss a kumatu. Mikewa yayi tsaye sannan ya mika mata hannu ta kama ta tashi tsaye. A haka har suka je daki. Ba tare da bata lokaci ba, ya fara kwabe mata kaya, zafin da a duk lokacin da ya rabeta yake ji, yanzun ma shi yake ji, sedai wannan karon zafin yafi na ko yaushe, hakan bai dakatar dashi ba domin shima sha'awar da yake tattare da ita mai karfi ce. karfi biyu ya hadu a lokaci daya, sai duka suka bayar da masifaffen zafin da yafi wuta. Da taimakon dan hasken dakin da kuma na farin wata, Dauda ke karewa kyakyawar surar Jinah kallo, zafin jikinsa karuwa yayi, idanunsa suka kafe, ya fadi gefenta matacce ko sumamme...!
Da alama shi Dauda aljanin bai bari yaje ko'ina ba lol. 😂
------------------------------
Salam, fatan kuna nan lafiya? Kuma ina fata zaku ji dadin wannan chapter kuma ta fanshe fushin da kuke yi dani na rashin posting da wuri? 😊
Ina jiran jin ra'ayinku 🤓
Mu hadu a wata chapter bayan sallah idan Allah ya kaimu. 🤗
©El_Ashtar
💞 JINAH (Matar Aljani)💞
by Malik al-Ashtar ✒️
On wattpad 👉 https://my.w.tt/g6epSX3tJ5
You'd like this New ❤️ Story
(Home of peace & hospitality).💦we are here to educate and entertain the heart of readers,we are the best among the rest💦
Visit to like our page:https://www.facebook.com/Al-wilaya-writers-association-of-Nigeria-113198586763490/?referrer=whatsappwhatsapp
A wajen aljanu idan daya daga cikinsu ya fada soyayya da dan adam. To fa mawuyacin abu ne dan adam din nan ya manta da soyayyar dake tsakaninsa da aljanin, sai idan dai wankin kwalwa aka masa kuma hakan na faruwa ne ko daga cikin iyayen aljanin ko kuma shi kanshi aljanin wani yayi wa dan adam din wankin kwalwa ta yanda ba zai kara tuna wata soyayya da yayi da aljanin ba. Wani lokacin kuma soyayyar da dan adam din yake wa aljani idan ya samu wani masoyin da suke jinsi daya wato dan adam kuma har yaji yana kaunar wannan dan adam din to zai gama har da shaukin soyayyar da yake wa aljanin duk ya juyeta akan dan adam din, to hakan na faruwa a hankali zai fara manta soyayyar dake tsakaninsa da aljanin. Shi yasa Fally yayi tunanin babu yanda za'ayi iyayensa su yiwa Jinah wankin kwalwa, dan suna son Jinah kuma ba zasu so ta mantasu ba. Sai dai kuma hakan ce ta kasance, mahaifiyarsa tana son Jinah, saboda haka, bata son wani abu ya samu Jinah, bata son Jinah ta tuna dasu har tayi kokarin nemansu, idan da bata manta komai ba da tuni ta shiga nemansu kuma kafin ta nemosu tana iya fadawa hannun muyagun aljanun dake son cutar da ita, bare kuma yanzu da har tanada tagwayen da kowanne aljani yake da burin mallakarsu ba. Dan haka wankin kwalwa da mahaifiyar Fally tayi mata ba don komai bane face dan ta tseratar da ita.
Ganin yanda Jinah take tadi da Dauda, suna yi suna kyalkyata dariya da irin kallon da suke yiwa junansu yasa Fally yake tunanin soyayyar da Jinah ke masa a yanzu ta koma kan Dauda, wato kenan Dauda ya maye gurbinsa. Tunani ya fara, yanzu duk wannan sadaukarwa da nayi a kanta! Sau da dama har sai yayi yunkurin tafiya ya barta in yaso aljanun su cutar da ita, amma sai ya kasa. Ga kuma 'ya'yansa dake hannunta, yana son yaran sosai domin da ya kalli yaran wani farin ciki ne ke ziyartar zuciyarsa. Suma kuma tagwayen suna ganin Fally amma sun kasa fahimtar waye shi, ba zasu gane matsayinsa ba har sai sunyi shekara daya da haihuwa kuma a kullum wannan ranar yake daukin jira.
Kwanaki da yawa sun shude, Fally bai bar gidansu Sarah ba kuma bai bar ganin abin takaicin dake faruwa ba tsakanin matarsa Jinah da kuma wannan mutumin wato Dauda. Sai dai farin cikinsa a kullum babu yanda za'ayi wani abu ya shiga tsakanin Dauda da Jinah domin har yanzu matarsa ce. Jira kawai yake lokacin da tsautsayi zai dauki Dauda yace zai kusanci Jinah ya gane kurensa. Shima haka take bangaren Dauda, yana ji tamkar ya matso sauran ranakun da suke rage na aurensu, yau ace ga Jinah a dakinsa a matsayin matarsa.
Kamar kowanne Marece tun ranar da yazo, Dauda ne da Jinah a zaune tsakiyar gida suna tadi.
-Kwana biyu kawai ya rage ki zama matata...
Dauda ya fada cikin yanayin farin ciki. Murmushi Jinah tayi. Shi kuma ya cigaba:
-Matata! Oh har na tuna da wata waka, Sunanki mai dadin fadi, kin ratsa zuciya! Kowa yazo za ayi nadi kece Sarauniya....
Dakatawa yayi da wakar ganin Jinah ta kyalkyace da dariya.
-Kushe miji fah ba kyau...
Dauda ya fada yana tamke fuska, irin dagasken nan yake.
-Eh koda yana waka da murya kamar gwangwani!
Ta fada tana dariya.
-Eh din!
Dariya dukansu suka yi. Shuru na dan wani lokaci ya biyo baya, Jinah ta lura Dauda hankalinsa yayi wani gu, ya fada duniyar tunani. Hannunsa Jinah ta kama tareda kallonsa a natse cikin ido.
-Har yanzu baka son fada min dalilin dake sanyaka cikin wannan dogon tunanin. Dan Allah ka fada min me yake damunka?
Wani dogon numfashi Dauda yaja, wanda Jinah bata fahimci komai ba, domin shiga yanayin bakin ciki ba dabi'ar Dauda bace, mutumin da kullum cikin raha yake.
-Me yasa dan Adam butulu ne? Me yasa soyayyarshi da dukiya ta wuce kima? Me yasa in dai akan kudi ne, soyayya, dangi, zumunci ba komai ba ne? Jinah da kinsan abinda ya faru bayan tafiyarki. Ya...
Sauran kalaman tsaya masa suka yi a baki. Hannu yasa yana goge kwallan dake shirin zubo masa.
-Kayi hakuri Dauda...
Jinah ta fada cikin Sanyanyar murya.
-Kinsan me yasa nake sonki, zuciyarki tsarkaka ce! Babu digon hassada ko keta a cikin idonki, fuskarki tana bayyana tsantsar gaskiya da mutuntawa. Imanina yana karuwa ta dalilinki, na kan ce koda munafukai da maciya amana ba zasu dakata da gurbata duniya ba, za'a samu mutanen kirki kamarki.
Ya fada cikin murya mai nuna yakini a maganarsa, wanda kuma yasa Jinah ta yarda lallai akwai wani babban al'amari da ya faru dashi bayan tafiyarta.
-Ka fada min abinda ya faru.
Ta fada cikin raunanniyar murya.
-Lok..loka..lokacin da na farka daga dogon suma, na samu labarin mahaifina ya rasu, anan, na tabbata bakin ciki yayi mana sallama. Yayinda dangi ke cikin jimami, Kawuna Mati, yayan mahaifina yazo, ba mutumin da na tsana kamarshi, tashi da mahaifina bata taba zuwa daya ba, shine kadai dan uwan mahaifina da ba a cikin dangi yake da zama ba. Kwana hudu da faruwar wannan masifa, kawu Mati yazo gida cike da zumudi da murmushi har kunne, ya nemi da dangi su hadu yana son magana damu. Duka muka hadu a tsakar gida, wasu takardu ya fiddo, wasu banzayen takardu wai na masana'antar mahaifinmu da kuma na gidanmu duka nashi ne. Bamu yarda da hakan ba, domin wannan ba zai taba yiyuwa ba, dattijawan garin aka kirawo da yake duk ya siyesu, har da kuma Kawunaina sai daya kawai da yace shi bai yarda ba haka yayi masa korar wulakanci shi da iyalinsa. Gashi manyan yayyena Idrisa da Isa basu duniyar, sauran kuma biyun yayyena sun tafi kasar waje gashi babu takardun dawowa a lokacin. Dayan yayan nawa kuma yi yayi kamar abun bai dameshi ba, ni kuma, nayi iya kokarina daga karshe ma korarmu yayi ni da Mahaifiyarmu da kuma kannena, inda Allah ya taimakemu dangin mahaifiyata sun karbemu hannu biyu. Na samu kuma labarin yace zai auri sauran mata biyun babana, idan basu yarda ba, zasu iya bar masa gida. Kuma kinsan mu anan, mata ba aiki suke ba, kenan ta yaya zasu iya ciyar da ya'yansu idan kuka bar gidan, kuma komawa wajen iyayensu a wannan lokacin abun kunya ne. Haka yasa biyun matan babana suka dawo matan kawuna, saboda ya kori mahaifiyata kuma Tanti Habi ta haukace. Sannan kuma ya sallami wasu kawunaina daga aikin masana'anta domin ya saka yan'yansa da kuma wadansu da suka taimaka masa wajen samun komai. Uwa daya uba daya yake da babana, amma bai ji ko digon imani ba wajen tarwatsa masa ahali. Na kudura a raina sai na yaki wannan zalunci da yayi mana, duk da mahaifiyata tace na manta komai, ba zan iya ba.. Jinah naga tsantsar rashin imani na dan adam...
Shuru yayi, ita kanta bata san me zata ce ba jin kalamansa, ta razana da jin labarin kuma taji ba dadi. Rungumesa tayi dan tunanin shi daya abinda taji zata iya, amma basu dau lokaci ba. Shuru dukansu suka yi, kafin wata murya daga bayansu ta katse shurun.
-Ba laifin kawunka bane, shi ne! _Yana nuna yatsa zuwa sama._ Ba shine ke da ikon komai ba? Me yasa ya bar wannan mutumin ya cika burinsa, kamar kuma yanda ya dauke min mahaifiya?
Abdul ne ke fadar haka lokacin da yaji labarin Dauda. Zaunawa kusa dasu yayi.
-Muna sallah, muna azumi, muna yin duk abinda ya wajaba a kanmu, muna kuma barin duk abinda aka hanemu! Toh me yasa kullum mune cikin masifa? Irin kawunka ya kamata su shiga irin wannan halin ba mu ba!
-Abdul. _Cewar Jinah kafin ta cigaba cikin tausashiyar murya._ Daga Allah muke kuma gareshi zamu koma.
-Amma ya kamata ya barmin ita, naso ace har na kai matsayin da zan sanyata cikin farin ciki, na bata duk wani jin dadi na duniya, na mayar da ita tamkar sarauniya, kar ta rasa komai na rayuwa kuma ta dinga alfahari dani.
-Akwai lokacin da ina cikin damuwa sosai, wani ya taba fadamin, idan bakin ciki ya bubbuga mana kofa, ko ya adadinsa yake, mu kasance masu godiya ga Allah, wannan ba wani abu bane face jarabawa domin jarraba imaninmu. Kuma a lokacin da muka koma gareshi zaka ga ya saka mana da mafificin alkhairi. Komai ya samemu na dadi ko akasinsa dole mu kasance masu godiya ga Allah. Kuma mutumin da ya fada min haka ba kowa bane kai ne Dauda, to kenan kai ba zaka yi amfani da nasihar da kayi min ba? Kai kuma Abdul, uwa bata bukatar zinare, kudi ko lu'ulu'u domin tayi alfahari da danta, yanzu da bata duniya bata bukatar komai illa addu'a.
Dukansu biyun jikinsu yayi sanyi da jin kalaman Jinah. Haka suka cigaba da hira da tayi sanadin gusar da duk wata damuwa tasu, har sai da dare ya tsala sannan kowa ya nufi makwancinsa.
Jinah kasa bacci tayi, tunanin abinda ya faru jiya take, ganin wannan mutumin ba karamin tsoratata yayi ba, ta kasa fahimtar komai game da lamarin, yanke sharawar daukar maganar Dauda tayi kawai ba komai bane face mafarki. Haka tayi ta tunani har bacci barawo yazo yayi gaba da ita.
-Babu abinda za'a yi, kawai ina son a daura auren, to wai ma wa zan gayyata, ba wanda na sani kuma la'akari da abinda ya faru kasan babu wani danginka da zai tako kafa wai da sunan zuwa wajen biki.
Jinah ke fadawa Dauda ana gobe daurin aure.
-Eh, na samu labari duk abinda suka yi maki, kuma har yanzu Mahaifiyata tayi imani da wannan karairayin amma idan muka yi aure, zamu je mu ganta kuma zan canza mata wannan tunanin. Kuma dan Allah kiyi hakuri akan abinda suka yi maki, ki yafe min na rashin kasancewata a wajen domin kareki.
-Me zaka yi kenan? Ai ni naji dadin rashin kasancewarka a gurin, domin ba zan so a dalilina ka samu matsala da mahaifiyarka ba.
-Toh yanzu manta da wannan, ya riga ya wuce, yanzu ne da kuma gobe a gabanmu.
Ya karashe maganar da murmushi a fuskarsa. Ita kuma Jinah fargaba ce duk tabi ta dameta, domin tana ji a jikinta wannan auren ba karamin kuskure bane yinshi. Da sauri ta dawo daga tunanin da take jin daya daga cikin tagwaye ya tsala wani uban kuka, wani lugude zuciyarta tayi kamar zata fito daga kirjinta, tsoro duk ya mamayeta. Domin babu daya daga cikin yaran da ya taba yin irin wannan kukan. Da gudunta ta nufi gurin yaran da ta bari cikin daki tareda Nafisa, Dauda na biye da ita a baya. Tarar da Nafisa suka yi itama na kuka.
-Me ya faru?
Murya na rawa Jinah ta fada tare da karasawa ta dauki danta da yaki daina kuka.
-Na..na..na fita ne yanzu.. naje..debo ruwan sha shine da naji kuka na rugo... shine na tarar da Ayu na kuka...ita..ita kuma Aya ban ganta ba.
Jinah kalmar karshe kawai ta iya rikewa, sai yanzu ta lura da babu Aya.
-Me? _Ta fada da karaji._ Ina 'yata?
-Ku kwantar da hankalinku duka, bazata yi nisa ba. Ke Jinah lallabi Ayu ni zan fita waje ko zan ganta.
Jinah tayi tayi amma Ayu yaki yin shuru, kokowa ma yake yana son uwar ta saukeshi. Abun fa kara ta'azzara yayi lokacin Dauda ya dawo ba tare da Aya ba. Zuciyar Jinah bugawa take da sauri ta yanda tayi tunanin ko fasa kirjinta zata yi ta fito.
(.....)
A waje kuwa, wani masifaffen fada ya turnuke. Fally ji yayi ya fara gajiya, ba zan bari ya tafi da 'yata ba, shine abinda yake ta maimatawa. A takaice dai, aljanun sun gano inda suke, shine daya daga cikin aljanun yake so ko ta yaya ya dauke Aya, kuma yayi nasarar dauketa har ma yayi nisa da gida da ita. Sedai Fally ya tareshi, sai gwabza fada suke tamkar wasu mayunwatan zakuna. Bayan wani dan lokaci, Fally yayi nasara akan aljanin da karfinsa ya kare da kyar ya iya guduwa yana fadar :
-Zan dawo, kuma bani daya ba, ka san da wannan!
A wata bishiya Fally ya zauna yana maida numfashi, Aya kusa dashi, tana masa wani irin kallo. Tabbas dole ya sake daura damarar kare ya'yansa daga waddanan miyagu. Da wannan tunanin ya dauki Aya ya kaita har kofar gida kuma daidai da fitowar Sarah da Abdul cike da mamaki suka ga Aya a waje ita daya. Sarah ta dauketa suka koma cikin gida. Suna shiga Jinah tazo da gudunta, bata tsaya amsa tambayar da Sarah da Abdul ke yi mata ba kan ya akayi Aya ta fita waje ba ta amshe yarta tareda kankameta. Kuma a take Ayu ya daina kukan da yake yi.
-Wai mun gode Allah, _Cewar Dauda tareda ajiyar zuciya._ Shikenan daina kukan tunda an ganta.
Da Nafisa yake da ke ta rizgar kuka tana tunanin laifinta ne. Yayanta ya matso kusa da ita tare da rungumeta yana lallashinta. Shi da Sarah basa bukatar wani dogon bayani akan me yakai Aya a waje, komai ya wuce tunda dai gashi an ganta.
Washe gari, ranar daurin aure, ba tare da wani shagali ba aka daura aure a masallaci kamar yanda Jinah ta bukata. Duk da ba wani jagali ba aka yi amma kowa gidan cikin farin ciki yake. A marecen ranar ma basu yi bacci ba. Suna ta hirar duniya. Abdul da Nafi har sun saba da zaman gidan, duk da har yanzu zaman jiran mahaifinsu suke domin su koma cen asalin gidansu...
-Sarah, wata alfarma nake son ki yimin.
Cewar Dauda cikin yanayin dagaske yake. Shuru kowa yayi yana sauraron me zai ce.
-Ina sauraronka Dauda.
-Kamar yadda kuka sani, yau Jinah ta zama matata, tawa, toh shine...
-Ahan muna sauraronka.
-Shine... Nake son ki dauki yaran, ni kuma sai na dauki matata.
Dariya Abdul yayi, su kuma matan rike baki suka yi suna mamakin Dauda...
-Bakada dama Dauda, toh shikenan, dare yayi yanzu ni zan je in kwanta. Sai da safenku.
-Toh yara kuma ku tashi dare yayi aje a kwanta.
Dauda ke fadawa Abdul da Nafi yana dariya. Seda suka dan taba raha kafin su je su kwanta. Ya rage sai amarya da Ango.
-Kinsan wani abu Jinah, har yanzu na kasa gasgata yau kece a matsayin matata, komai ina jinsa kamar a mafarki. Yanzu da nake a tare dake sai nake ji kamar babu wani abu na bakin ciki da ya faru dani a baya. Kin baiwa rayuwata ma'ana Jinah. Nayi maki alkawarin har indai ina raye, zaki kasance cikin farin ciki.
Murmushi Jinah, tayi sosai kalamansa suka tabata.
-Kayi min abinda ba zan taba mantawa ba Dauda, kayi abinda ba kowanne namiji zai iya yi ba. Ba zan boye maka ba, a duk lokacin da ka furta min kalmar "Ina sonki" na kanji ba zan iya baka amsa ba, amma kuma duk da haka bani nadamar aurenka, ina fatan wata rana na soka, son da yafi kalmar so.
Hannu Dauda ya kai kan fuskarta ya janye gashin kanta da ya zubo a fuskarta zuwa bayan kunnenta sannan ya kai mata lafiyayyen kiss a kumatu. Mikewa yayi tsaye sannan ya mika mata hannu ta kama ta tashi tsaye. A haka har suka je daki. Ba tare da bata lokaci ba, ya fara kwabe mata kaya, zafin da a duk lokacin da ya rabeta yake ji, yanzun ma shi yake ji, sedai wannan karon zafin yafi na ko yaushe, hakan bai dakatar dashi ba domin shima sha'awar da yake tattare da ita mai karfi ce. karfi biyu ya hadu a lokaci daya, sai duka suka bayar da masifaffen zafin da yafi wuta. Da taimakon dan hasken dakin da kuma na farin wata, Dauda ke karewa kyakyawar surar Jinah kallo, zafin jikinsa karuwa yayi, idanunsa suka kafe, ya fadi gefenta matacce ko sumamme...!
Da alama shi Dauda aljanin bai bari yaje ko'ina ba lol. 😂
------------------------------
Salam, fatan kuna nan lafiya? Kuma ina fata zaku ji dadin wannan chapter kuma ta fanshe fushin da kuke yi dani na rashin posting da wuri? 😊
Ina jiran jin ra'ayinku 🤓
Mu hadu a wata chapter bayan sallah idan Allah ya kaimu. 🤗
©El_Ashtar
💞 JINAH (Matar Aljani)💞
by Malik al-Ashtar ✒️
On wattpad 👉 https://my.w.tt/g6epSX3tJ5
You'd like this New ❤️ Story