← Book details Hauwa Kulu Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 4 OF 29

Sashe 4

Hauwa Kulu Part 2 Complete Hausa Novel · about 5 min read

**** **** ****
(A GIDAJEN MALAMAI NA SABUWAR JAMI’AR BAYERO).
G
idan Prof. Abbas Shanono ya kacame da hayaniya a tsakanin jama’ar gidan da kawayen ‘ya’yansu da jama’ar mahaifiyar su da aka gayyato domin taya Surayyah Shanono, murnar kammala digirin ta na farko, bayan dawowar su daga filin ‘convocation’ na cikin jami’ar Bayero.
Anan cikin gida bayan kawayen Surayyah sun gama dabdalar su sun tafi, Mama ta hada musu (get together party) su’I’su, domin kwarai tayi alfahari da sakamakon Surayyah, koda yake abin kamar a jinin ‘ya’yan ta ne, in dai ta fannin karatun boko dana addini ne basu da na biyu.
‘Get together party’ din da Mama Mai Shari’ah Haj. Maimuna ta shirya na abu biyu ne; bayan taya Surayyah murnar kammala karatunta da kyakkyawan sakamako (first class degree) ya kuma kunshi sallama da auta Sumayyah, wadda ita kuma zata tafi Jeddah nan da kwana uku domin fara nata karatun, can a jami’ar da Abba Prof. yayi mata alkawari tutuni, wato Sumayyah zata tafi inda Bhaiyanta (SARHAM) yake itama a cikin satin nan da yardar Ubangiji.
Tsananin kaunar juna irin na wannan family, da yadda basa yin wani abu babu sanin dayan su, yasa sun kasa cika farin cikin ranar yau ba tare da shi ba, musamman da ya kasance a lokacin wayar zamani ta tafi da gidan ka ta fara yawa a Najeriya (amma dai ba a kowanne gida ba), to shima dai Abba Prof. kamar sauran manyan ma’aikatan gwamnati a Kano ya mallaki tasa, har yana arawa iyalin sa lokaci-lokaci su kira dan uwan su dake nesa su gaisa.
To yau ma hakan ce ta kasance. Sumayya ta ce “Abba ka kira mana Bhaiya ayi komai ‘live’ a kunnen sa”. Abba yace “kin manta Sarhamu jarrabawa yake yi?”
Sumayyah ta hau roko “Abbah don Allah, ko na minti biyu ne, bazan ja shi da surutu ba”. Surayyah kuma ta ce “Abbah ni zan biya ka kudin da zamu cinye maka a wayar”. Abba Prof. yace “da can dana ke baku aron wayar kuyi wayar da shi biyana kuke yi?” Suka hada baki wajen cewa “tuba muke Abbanmu! Abbanmu like no other Babanmu maganin kukan mu”.
Prof. yayi dan murmushi kafin ya danna masa kira, ba jimawa Sarham ya amsa masa da cikakkiyar amsa sallama, da muryarsa dusassa, wadda a kullum yanayinta kamar na mai fama da mura. Sarham yace (cikin hausar shi wadda yanzu ta daina fita sosai yadda ya kamata).
“Daga bangarena ina kokarin kiran ku ne fa Abba, naka kiran ya shiga nawa shiga, in ban manta ba yau ne graduation din ‘Surry Darling”.
Surayya ta saki dariyar farin-ciki jin yau wai Bhaiya ya kira ta da ‘Darling’ tana fadin “yau kuma?” Shima daga nasa bangaren dariyar yayi, yace “Surry rigima, Surry masifa Surry mathematician, Surry Darling!”. Duk falon aka kwashe da dariya da alama yau dukkansu cikin nishadi suke, abinda basu sani ba ya fi su nishadin wannan ranar, domin tayi daidai da ranar zagayowar haihuwar sa, kuma a daidai lokacin wani babban abun farin ciki ya same shi, wanda daga shi sai Allah suka san shi, wato wani ‘gift’ ne na musamman na taya murnar zagayowar ranar haihuwa Madinah ta kawo masa...
Don haka don yau ya kira abokiyar fadansa da ‘darling’ bai ji faduwa ba ko kankani, karewa ma, har shirin fita ‘outing’ (picnic) na musamman ya yi niyyar shirya mata shima idan yazo, ko a TIGA DAM ko a DAMBATTA DAM, inda suka saba zuwa don ‘celebrating’ wasu ranaku masu muhimmanci da suka shafi dayan su.
Sannan kuma gashi yana shirin ‘surprising’ dinsu su duka, domin a lokacin ya riga ya yanki tikitin tahowa gida kwatakwata, ba tare da ya gayawa kowannen su ba, tuni kuma yayi ‘booking’ din jirgin dare, bayan kwashe shekaru uku yana zullewa Mamansa Haj. maimuna, a kan dai maganar aure.
Yanzu kam da kwarin guiwar sa zai iso gida, kuma da abinda ya tabbatar zai baiwa kowa a gidansu kwanciyar hankali, abinda ya tabbata zai faranta ran Mama, ya kuma wanke bacin ranta da shi, wato maganar auren sa. Shi yasan inda abinda iyayensa ke so su ji a yanzu to bai wuce yayi aure hakanan ba, iyayen sa sun matukar daga hankalin su a kan rashin auren sa a wannan dan tsakanin ya rasa meyasa, ya manta shekaru talatin da biyu a wancan lokacin har ya wuce matakin samartaka, ya shiga na tuzuranci a al’adance, har hakan na neman ya shafi zaman lafiyar sa da su, don Mama ta dade da daina kiran sa a waya tace yayi abinda yake so tunda ya badawa idon sa toka ya ki auren diyar aminiyar ta Barr. Hannatu wato Sadiya Maijama’a, har wani ma sa’ar yayi wuf da ita (ya aure ta).
A yanzu kam Dr. Sarham Abbas yana cikin wani farin ciki maras misaltuwa. At last, at very long last, he found his first and true love, bama mai kama da ita ba, ba mai irin kokarin ta ko kamanninta ba (kamar yadda Mama tai masa fata), a’ah, ita din ce da kanta ba sako ba, wato (his ex) Madinah Attahiru ba wata ba! Kuma har sun daidaita sabanin dake tsakanin su, duk tsayin wannan lokacin na komawarsa Jeddah suna tare da Madina Attahirusun sake hadewa acan jami’ar sarki Abdul Azeez (KAU) Jeddah.
**** ***** ****

WAIWAYE ADON TAFIYA (1)
(DR. SARHAM SHANONO A JEDDAH)
Chapter 4 · 0% Book details