Sashe 8
Hauwa Kulu Part 1 Complete Hausa Novel · about 9 min read
Hayaniyar Malaman jinyar sa, da ta dattijuwa Innar Hauwa data dage bazata tafi ba sai yar ta Hauwau ta ga likita, koda kuwa dukan ta zasu yi karewar rashin kunya, tace ban haife ku ba? ta kuma ce ai asibitin ba nasu bane na gwabnati ne, don haka basu isa ba da zasu hana ta ganin likita, inji dattijuwar, don sun kure hakurin ta, wannan hayaniyar ta hana shi fuskantar rubutun ma da yake yi yadda ya kamata. Gashi kuma a kofar ofishin sa ake ta wannan taqaddamar.
Su Nosis din sun dage da rashin mutuncin tunda ta bari sai da ido ya rube zata zo asibiti, to ta je ta nemi sandar yi wa yar ta jagora zuwa bara. Amma bazata batawa likita lokaci ba, a lokacin da ba abunda zai iya tabukawa wadannan idanun da hakiya ta gama canyewa murus.
Innar Hauwa har da kukan ta, don taga alamar fada ba zai bi da su ba, tana rokon su da muryar ban tausayi su bar yar ta ta gan shi kada ta makance, ta yarda ta yi laifi amma a taimaka musu su ga likita don Allah, ta tuba. Kuskure ne ta riga ta yi. Nan gaba zata kiyaye. Amma maaikaciyar jinyar nan ko a jikin ta, ta dora kafa daya kan daya akan kujera tana karkadawa ta hana su shiga ta yi rantsuwa da Jesus din ta, ba zata bari su batawa likita lokaci a kan idonnan da sun riga sun kashe shi a banza ba.
Me ke faruwa haka? Hayaniyar me kuke yi mata haka? Ke Maria, meye haka kike yi? Wannan ya dace da maaikacin jinya? Sister Saratu wannan matar bata girme ku ba?”
Dakusassar muryar DR. SARHAM, irin ta mai fama da sabuwar mura, ta karade wurin, yana maganar yana furzar da dan tari, don sosai yake fama da mura daga jiya zuwa yau da ya dan sha ruwan sanyi, jikin sa baya son sanyi ko kadan.
Muryar tasa ta dira a kunnen su da sigar tambaya daga inda yake tsaye a jikin kofar ofishin sa, hannayen sa duka biyu zube cikin aljihun bakar Jacket din sa, yana dan yamutsa fuska cikin gajiya da alamun jin yunwa, don tun safe yake aikin duba marassa lafiya har zuwa yanzu da agogo ya buga karfe biyun rana, wato lokacin cin abincin ranar sa kenan da zuwa yin sallahr azuhur, lokacin tafiyar sa gida yayi kenan. Don haka ya fito ne don tafiya gida.
Yana sanye da bakaken ‘suit’ da ya zanzare kugun sa a cikin su, ya dora bakar jacket a kan su, wadda ta sauko har zuwa gwiwar sa, ta bada suurar cikakken dan gayun likita kuma dan kwalisa dashi na wancan zamanin, masu yawan yin zanzaro da belt.
Bafullatanin Shanono mai kakkaifar murya, amma a halin yanzu ta dushe, ta dakushe da alama yana fama da ‘Catarrh’.
Yanayinsa na Kanawan usli ne, amma yanayin zubin jikin sa na Fulani ne, sabida sirantar sa da ta zabge masa cika ido kai bazaka ce yayi shekaru ashirin da takwas din da yake da su bama.
Sister Saratu ta hau raba ido tsakanin Innar Hauwa da Likita Sarham, ta ki cewa komai, don a dan zamansa da su na dan gajeren lokacin da bai wuce sati biyu ba da aka yi masa transfer daga asibitin Abdullahi Wase (Nassarawa hospital) zuwa nan wajen su, sun fahimci halinsa na kirki yayi yawa a kan marassa lafiyan sa, (hes very compassionate and caring to his patients), shi yasa a halin rashin mutunci irin nasu suke cewa ya fiya iyayi da kidifiri.
Ilai kuwa ya fahimci komai tun ma kafin su bashi amsa, don ya san ba yau suka fara ba, wulakanta marassa lafiyan da suka rainawa ajawali halin maaikatan su ne, daga zuwan sa zuwa yanzu ya gama shaidar hakan, kuma yana cikin sahun likitocin da suka san darajar dan adam, basa yarda da hakan, sai dai in an yi ne a bayan idon su.
A fusace ya soma fadin wato Metron Maria, Sister Saratu, Nos Mairo ba zaku daina wulakanta bayin Allah ba ko? Shin anya kun san aikin ku? Wannan ba shine halin da aka san maaikacin jinya na hakika da shi ba, hakan cin amanar aiki ne babba, kuma tozarta dan adam ne.
Ina humanity din ku da aka hore ku da shi matsayin ku na maaikatan jinya, dana kiwon lafiya?
A gaskiya na gaji da halin ku, ko jiya na raba ku fada da patient. Idan baku yi hankali kun yi aikin da ya kawo ku yadda ya kamata ba wallahi duk sai na yi reporting din ku.
Ya dubi Innar Hauwa data sunkuyar da kai kasa tana tsane ido, yace.
Baiwar Allah me ya faru? Waye babu lafiyan?
Innar Hauwa ta ji dan kwarin guiwa ya shige ta, saboda a cikin muryar sa mai dushewa da rashin karsashi saboda mura, akwai (caring) wato kulawa da darajja dan Adam, ta rausayar da kai gefe ta ce,
dama yarinya ce na kawo tana ciwon ido, to sun ce ban zo da wuri bane shiyasa bazan ga likita ba, shine dalilin da nake ta basu hakuri”.
Tausayin matar ya kama shi, ya dubi yarinyar da take rike da hannun ta, yadda hakiya ta cinye rabin idon sai da tsigar jikin sa ta tashi, zuciyar sa ta tashi, ga kwantsa babu kyawun gani, da sauri ya dauke idon sa daga kallon yarinyar, ga kafafun su futu-futu da kura tabbacin sun sha tafiyar kasa mai nisa kafin su iso asibiti, sai ya karbi katin su daga hannun maaikaciyar jinyar da katin ke hannun ta wato Nos Maria, ya kuma yiwa Inna umarnin su biyo shi a baya zuwa cikin ofis din.
Sai lokacin Inna ta gane shine likitan da ake musu rowar gani.
“Iya yaya aka yi aka bar idon yaci hakiya sosai har haka?
Dr. Sarham ya tambayi Innar Hauwa, yana haska cikin idanun Hauwa da yar tocilan din sa mai tsananin haske, yana magana cikin tsantsar damuwar da ta kasa boyuwa a muryar sa, yana cigaba da haska cikin idanun bayan ya gwale su sosai, Inna bata iya ta ce komai ba amma guilt ya bayyana akan dattijiyar fuskar ta ainun.
Dr. Sarham ya gama duba idon Hauwa da tocilan din sa, ya kuma gama nazarin sa gabadaya duk cikin dan lokaci, sai ya koma ya zauna a bakar kujerar sa mai juyawa, itama yace ta zauna a kan kujerar zaman maras lafiya da ke fuskantar sa, ya bude mata fayil a take don ya gama gano Hauwa na bukatar aikin ido na gaggawa kawai, don a cire hakiyar. Ya sunkuyar da kai yana rubuce-rubuce a cikin fayil din ta, kafin ya gama ya dago ya dubi Inna.
A hankali kuma cikin tsanaki, Dr. Sarham Abbas Shanono, ya shiga yiwa Innar Hauwa bayanin amfanin zuwa asibiti da wuri, da zarar an ga alamun ciwo, ba sai ciwo ya ci ya cinye ba, cikin tausasawa da lallashi da fasahar harshe irin nasa yake mata magana, ya gaya mata yanzu ba abinda zaa iya yiwa Hauwa a ceci idanun ta illa cataract surgery watau (fida don cire hakiya) ta gaggawa.
Likitan ya saka musu ranar aiki jibi-jibin nan, ya kuma fada musu kudin aikin. Duk da Innar Hauwa ta tsorata da yawan kudaden bata nuna ba ko a fuska. Duk da ta san kuwa bata da su a ajiye.
Da suka koma gida Inna ta shiga cikin matsananciyar damuwa, na farko bata da kudin da likita ya bukata a yanzu, ko jarin wake da shinkafar ta ba zai yi kwatan su ba, abu na biyu tana ganin bazata iya bari a farkawa Hauwan ta ido ba haka kawai. A je garin neman gira a rasa ido. Ko a jangwalo wani abun da yafi karfin su.
Amma Hauwa ta dagewa Inna ita dai tana so ayi mata aikin nan. Inna ta gaya mata abinda take tsoro da kuma rashin kudin aikin a hannu, nan Hauwa ta dinga magiya har da kuka, tana rokon Inna ta amince in yaso ko dan taure daya ne cikin dabbobin ta a sayar a biya. Komai ya faru daga Allah ne.
Haka kan dole Inna ta amince da shawarar ta, don bata son kukan Hauwa ko bacin ranta. Ta fidda Akuya budurwa aka sayarwa mahauci. Washegari, wato ranar da aka basu, da sassafe suka koma asibitin Murtala.
Likita da abokan shiga tiyatar sa suka gama shirin yi wa Hauwa aiki, aka nemi Inna da ta saka hannu, Inna ta saka hannu amma da ganin ta zaka fahimci a matukar firgice take, gani take kamar aka shiga da Hauwa tiyatar nan bazata fito a raye ba, Inna ta soma hawaye tana sharewa da habar zanin ta, tana kankame da hannayen Hauwa.
Ganin haka Dr. Sarham ya shiga yi wa Innar Hauwa maganganu na kwantar da rai yana cewa kada ki damu Innar mu, lafiya zan maido miki ita, da iznin Ubangiji, da kiyayewar sa, da albarkar sa zaa yi aikin nan lafiya a fito lafiya, in sha Allahu.
Idanun Hauwau su koma tangaras, kamar yadda suke a baya su rabu da hakiyar da ke cikin su, hakiya musiba ce ga ido, kin ji ko Inna?.
Ta daga masa kai, ba don ta gamsu ba, amma bata fasa zub da hawayen ba.
A haka aka shiga da Hauwa dakin tiyata. Ko kafin masu allura su yi mata allurar tafi-da-ran ka wato (anaesthesia) fuskar Dr. Sarham Hauwa ta kurawa ido tana cewa a ranta inama tana ganin sa tar-tar, domin ta ji dadin abinda ya cewa Inna.
Haka ta cigaba da kallon saitin fuskarsa kamar tana ganin sa sosai, alhalin inuwar sa da karshen tsayin sa kawai take iya gani, bata san me yasa take son sanin yaya kamannin sa na halitta suke ba, ko don tausasan kalaman bakin sa ne da yadda yake lallaba mata rikitacciyar Innar ta, domin a lokacin bata ganin komai dadai ama dai tana ganin haske cikin idanun ta.
Murmushin da Dr. Sarham yayi mata a lokacin kamar ya san me take ciki da zuciyarta ne, taji sautin murmushinsa a kunnen ta, ji tayi kamar ya fahimci ba abinda take son gani a lokacin sai hakikanin kamannin fuskar sa, ba don komai ba sai don ta kwatanta su da kyawun kalaman bakin sa.
Ta kasa manta sautin murmushin nasa. Haka kalaman karfafawa marar lafiya zuciya cikin mutumtawa wadanda Dr. Sarham ya yi mata a lokacin, bata jin har abada zata manta su. Ya bata hope na cewa zata rayu, kuma zata warke cikin yarda da amincewar Ubangiji; wanda ya saukar da cuta kowacce iri tare da maganin ta.
Tsananin tsoron da Dr. Sarham ya gani cikin idanun Hauwa-Kulu, da karkarwar da jikin ta ya fara lokacin da zaa yi mata allurar anaesthesia, ita ta saka shi dakatawa daga abinda yake yi wato saka safar hannu, ya sake matsowa daidai kanta har tana iya jin kamshin balaraben turaren sa, cikin taushin murya da lallashi Dr. Sarham yake cewa,
Relax Hauwau. Zamu yi aikin nan lafiya da iznin Ubangiji kinji, kuma zaki samu lafiya Insha Allahu, zaki warke, saki ranki kin ji ko Hauwau?
Daga haka aka soka mata allurar ‘tafi-da-ran ka wanda hakan yasa Hauwa runtse idanun ta, kuma ta tafi cikin barcin ne da mafarkan kamannin LIKITA SARHAM! Da fatan ko a lahira Allah ya hada fuskokinsu.
Don gani take kamar ta tafi kenan, duk kuwa da hope din da ya bata, har abada ba zata farka ba.
Wato dai Hauwa ta tafi barcin ne da kintacen fuskar Likita Sarham a zuciya da kwakwalwar ta, na wani irin kintace, da dakace, da kuma hasashen ko shin yaya kamannin sa na zahiri suke?
Idan aka yi laakari da irin kyawawan furucinsa/kalaman sa???
Su Nosis din sun dage da rashin mutuncin tunda ta bari sai da ido ya rube zata zo asibiti, to ta je ta nemi sandar yi wa yar ta jagora zuwa bara. Amma bazata batawa likita lokaci ba, a lokacin da ba abunda zai iya tabukawa wadannan idanun da hakiya ta gama canyewa murus.
Innar Hauwa har da kukan ta, don taga alamar fada ba zai bi da su ba, tana rokon su da muryar ban tausayi su bar yar ta ta gan shi kada ta makance, ta yarda ta yi laifi amma a taimaka musu su ga likita don Allah, ta tuba. Kuskure ne ta riga ta yi. Nan gaba zata kiyaye. Amma maaikaciyar jinyar nan ko a jikin ta, ta dora kafa daya kan daya akan kujera tana karkadawa ta hana su shiga ta yi rantsuwa da Jesus din ta, ba zata bari su batawa likita lokaci a kan idonnan da sun riga sun kashe shi a banza ba.
Me ke faruwa haka? Hayaniyar me kuke yi mata haka? Ke Maria, meye haka kike yi? Wannan ya dace da maaikacin jinya? Sister Saratu wannan matar bata girme ku ba?”
Dakusassar muryar DR. SARHAM, irin ta mai fama da sabuwar mura, ta karade wurin, yana maganar yana furzar da dan tari, don sosai yake fama da mura daga jiya zuwa yau da ya dan sha ruwan sanyi, jikin sa baya son sanyi ko kadan.
Muryar tasa ta dira a kunnen su da sigar tambaya daga inda yake tsaye a jikin kofar ofishin sa, hannayen sa duka biyu zube cikin aljihun bakar Jacket din sa, yana dan yamutsa fuska cikin gajiya da alamun jin yunwa, don tun safe yake aikin duba marassa lafiya har zuwa yanzu da agogo ya buga karfe biyun rana, wato lokacin cin abincin ranar sa kenan da zuwa yin sallahr azuhur, lokacin tafiyar sa gida yayi kenan. Don haka ya fito ne don tafiya gida.
Yana sanye da bakaken ‘suit’ da ya zanzare kugun sa a cikin su, ya dora bakar jacket a kan su, wadda ta sauko har zuwa gwiwar sa, ta bada suurar cikakken dan gayun likita kuma dan kwalisa dashi na wancan zamanin, masu yawan yin zanzaro da belt.
Bafullatanin Shanono mai kakkaifar murya, amma a halin yanzu ta dushe, ta dakushe da alama yana fama da ‘Catarrh’.
Yanayinsa na Kanawan usli ne, amma yanayin zubin jikin sa na Fulani ne, sabida sirantar sa da ta zabge masa cika ido kai bazaka ce yayi shekaru ashirin da takwas din da yake da su bama.
Sister Saratu ta hau raba ido tsakanin Innar Hauwa da Likita Sarham, ta ki cewa komai, don a dan zamansa da su na dan gajeren lokacin da bai wuce sati biyu ba da aka yi masa transfer daga asibitin Abdullahi Wase (Nassarawa hospital) zuwa nan wajen su, sun fahimci halinsa na kirki yayi yawa a kan marassa lafiyan sa, (hes very compassionate and caring to his patients), shi yasa a halin rashin mutunci irin nasu suke cewa ya fiya iyayi da kidifiri.
Ilai kuwa ya fahimci komai tun ma kafin su bashi amsa, don ya san ba yau suka fara ba, wulakanta marassa lafiyan da suka rainawa ajawali halin maaikatan su ne, daga zuwan sa zuwa yanzu ya gama shaidar hakan, kuma yana cikin sahun likitocin da suka san darajar dan adam, basa yarda da hakan, sai dai in an yi ne a bayan idon su.
A fusace ya soma fadin wato Metron Maria, Sister Saratu, Nos Mairo ba zaku daina wulakanta bayin Allah ba ko? Shin anya kun san aikin ku? Wannan ba shine halin da aka san maaikacin jinya na hakika da shi ba, hakan cin amanar aiki ne babba, kuma tozarta dan adam ne.
Ina humanity din ku da aka hore ku da shi matsayin ku na maaikatan jinya, dana kiwon lafiya?
A gaskiya na gaji da halin ku, ko jiya na raba ku fada da patient. Idan baku yi hankali kun yi aikin da ya kawo ku yadda ya kamata ba wallahi duk sai na yi reporting din ku.
Ya dubi Innar Hauwa data sunkuyar da kai kasa tana tsane ido, yace.
Baiwar Allah me ya faru? Waye babu lafiyan?
Innar Hauwa ta ji dan kwarin guiwa ya shige ta, saboda a cikin muryar sa mai dushewa da rashin karsashi saboda mura, akwai (caring) wato kulawa da darajja dan Adam, ta rausayar da kai gefe ta ce,
dama yarinya ce na kawo tana ciwon ido, to sun ce ban zo da wuri bane shiyasa bazan ga likita ba, shine dalilin da nake ta basu hakuri”.
Tausayin matar ya kama shi, ya dubi yarinyar da take rike da hannun ta, yadda hakiya ta cinye rabin idon sai da tsigar jikin sa ta tashi, zuciyar sa ta tashi, ga kwantsa babu kyawun gani, da sauri ya dauke idon sa daga kallon yarinyar, ga kafafun su futu-futu da kura tabbacin sun sha tafiyar kasa mai nisa kafin su iso asibiti, sai ya karbi katin su daga hannun maaikaciyar jinyar da katin ke hannun ta wato Nos Maria, ya kuma yiwa Inna umarnin su biyo shi a baya zuwa cikin ofis din.
Sai lokacin Inna ta gane shine likitan da ake musu rowar gani.
“Iya yaya aka yi aka bar idon yaci hakiya sosai har haka?
Dr. Sarham ya tambayi Innar Hauwa, yana haska cikin idanun Hauwa da yar tocilan din sa mai tsananin haske, yana magana cikin tsantsar damuwar da ta kasa boyuwa a muryar sa, yana cigaba da haska cikin idanun bayan ya gwale su sosai, Inna bata iya ta ce komai ba amma guilt ya bayyana akan dattijiyar fuskar ta ainun.
Dr. Sarham ya gama duba idon Hauwa da tocilan din sa, ya kuma gama nazarin sa gabadaya duk cikin dan lokaci, sai ya koma ya zauna a bakar kujerar sa mai juyawa, itama yace ta zauna a kan kujerar zaman maras lafiya da ke fuskantar sa, ya bude mata fayil a take don ya gama gano Hauwa na bukatar aikin ido na gaggawa kawai, don a cire hakiyar. Ya sunkuyar da kai yana rubuce-rubuce a cikin fayil din ta, kafin ya gama ya dago ya dubi Inna.
A hankali kuma cikin tsanaki, Dr. Sarham Abbas Shanono, ya shiga yiwa Innar Hauwa bayanin amfanin zuwa asibiti da wuri, da zarar an ga alamun ciwo, ba sai ciwo ya ci ya cinye ba, cikin tausasawa da lallashi da fasahar harshe irin nasa yake mata magana, ya gaya mata yanzu ba abinda zaa iya yiwa Hauwa a ceci idanun ta illa cataract surgery watau (fida don cire hakiya) ta gaggawa.
Likitan ya saka musu ranar aiki jibi-jibin nan, ya kuma fada musu kudin aikin. Duk da Innar Hauwa ta tsorata da yawan kudaden bata nuna ba ko a fuska. Duk da ta san kuwa bata da su a ajiye.
Da suka koma gida Inna ta shiga cikin matsananciyar damuwa, na farko bata da kudin da likita ya bukata a yanzu, ko jarin wake da shinkafar ta ba zai yi kwatan su ba, abu na biyu tana ganin bazata iya bari a farkawa Hauwan ta ido ba haka kawai. A je garin neman gira a rasa ido. Ko a jangwalo wani abun da yafi karfin su.
Amma Hauwa ta dagewa Inna ita dai tana so ayi mata aikin nan. Inna ta gaya mata abinda take tsoro da kuma rashin kudin aikin a hannu, nan Hauwa ta dinga magiya har da kuka, tana rokon Inna ta amince in yaso ko dan taure daya ne cikin dabbobin ta a sayar a biya. Komai ya faru daga Allah ne.
Haka kan dole Inna ta amince da shawarar ta, don bata son kukan Hauwa ko bacin ranta. Ta fidda Akuya budurwa aka sayarwa mahauci. Washegari, wato ranar da aka basu, da sassafe suka koma asibitin Murtala.
Likita da abokan shiga tiyatar sa suka gama shirin yi wa Hauwa aiki, aka nemi Inna da ta saka hannu, Inna ta saka hannu amma da ganin ta zaka fahimci a matukar firgice take, gani take kamar aka shiga da Hauwa tiyatar nan bazata fito a raye ba, Inna ta soma hawaye tana sharewa da habar zanin ta, tana kankame da hannayen Hauwa.
Ganin haka Dr. Sarham ya shiga yi wa Innar Hauwa maganganu na kwantar da rai yana cewa kada ki damu Innar mu, lafiya zan maido miki ita, da iznin Ubangiji, da kiyayewar sa, da albarkar sa zaa yi aikin nan lafiya a fito lafiya, in sha Allahu.
Idanun Hauwau su koma tangaras, kamar yadda suke a baya su rabu da hakiyar da ke cikin su, hakiya musiba ce ga ido, kin ji ko Inna?.
Ta daga masa kai, ba don ta gamsu ba, amma bata fasa zub da hawayen ba.
A haka aka shiga da Hauwa dakin tiyata. Ko kafin masu allura su yi mata allurar tafi-da-ran ka wato (anaesthesia) fuskar Dr. Sarham Hauwa ta kurawa ido tana cewa a ranta inama tana ganin sa tar-tar, domin ta ji dadin abinda ya cewa Inna.
Haka ta cigaba da kallon saitin fuskarsa kamar tana ganin sa sosai, alhalin inuwar sa da karshen tsayin sa kawai take iya gani, bata san me yasa take son sanin yaya kamannin sa na halitta suke ba, ko don tausasan kalaman bakin sa ne da yadda yake lallaba mata rikitacciyar Innar ta, domin a lokacin bata ganin komai dadai ama dai tana ganin haske cikin idanun ta.
Murmushin da Dr. Sarham yayi mata a lokacin kamar ya san me take ciki da zuciyarta ne, taji sautin murmushinsa a kunnen ta, ji tayi kamar ya fahimci ba abinda take son gani a lokacin sai hakikanin kamannin fuskar sa, ba don komai ba sai don ta kwatanta su da kyawun kalaman bakin sa.
Ta kasa manta sautin murmushin nasa. Haka kalaman karfafawa marar lafiya zuciya cikin mutumtawa wadanda Dr. Sarham ya yi mata a lokacin, bata jin har abada zata manta su. Ya bata hope na cewa zata rayu, kuma zata warke cikin yarda da amincewar Ubangiji; wanda ya saukar da cuta kowacce iri tare da maganin ta.
Tsananin tsoron da Dr. Sarham ya gani cikin idanun Hauwa-Kulu, da karkarwar da jikin ta ya fara lokacin da zaa yi mata allurar anaesthesia, ita ta saka shi dakatawa daga abinda yake yi wato saka safar hannu, ya sake matsowa daidai kanta har tana iya jin kamshin balaraben turaren sa, cikin taushin murya da lallashi Dr. Sarham yake cewa,
Relax Hauwau. Zamu yi aikin nan lafiya da iznin Ubangiji kinji, kuma zaki samu lafiya Insha Allahu, zaki warke, saki ranki kin ji ko Hauwau?
Daga haka aka soka mata allurar ‘tafi-da-ran ka wanda hakan yasa Hauwa runtse idanun ta, kuma ta tafi cikin barcin ne da mafarkan kamannin LIKITA SARHAM! Da fatan ko a lahira Allah ya hada fuskokinsu.
Don gani take kamar ta tafi kenan, duk kuwa da hope din da ya bata, har abada ba zata farka ba.
Wato dai Hauwa ta tafi barcin ne da kintacen fuskar Likita Sarham a zuciya da kwakwalwar ta, na wani irin kintace, da dakace, da kuma hasashen ko shin yaya kamannin sa na zahiri suke?
Idan aka yi laakari da irin kyawawan furucinsa/kalaman sa???