← Book details Hauwa Kulu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 20 OF 27

Sashe 20

Hauwa Kulu Part 1 Complete Hausa Novel · about 1 min read

Washegarin ranar Sarham ya ga cewa ya kamata ya je wa su Inna sallama, kai zai yi kewar kawar sa Inna Safiyya… yadda baa zato, tsakanin itada Sumayyah bai san wa zai fi kewa ba.
Wata zuciyar a can kasan kirjinsa tayi whisphering a sace, inda tace masa MISKINIYA KULU!” Da sauri Sarham ya kalubalanci zaciyar sa da cewa capital NO! he will never HAUWA_KULU, zai yi kewar kowa tabbas, har Surayyah da basa jituwa, amma ko kadan ba zai yi kewar Maijidda ba, ba don komai ba ko don halin koin kulan ta da miskilancin da take nuna masa, da rashin maganar ta da sakewa da mutane wanda baya bari ayi sabo mai shiga jiki da ita irin wanda har zaayi kewar ta don an daina ganin ta a wuri.
Shin wai kodai shi kadai Maijidda take nunawa halin koin kula, da shariya, da miskilanci, da rashin walwala wani lokacin ma sai ya ga kamar sad face a tare da ita idan taji muryarsa a gidan su???
Chapter 20 · 0% Book details